ka ɗauke min Amal a haka! Kar in rasa ta a idanuna…!”
Elevator ya kai shi kai tsaye hawa na goma sha takwas. Bai tsaya ko da dakika ɗaya ba, ya fito da gudu kamar mahaukaci. Kai tsaye ya nufi ofishin Amal.
Da ya shigo, ya nufi window sides ya hango Amal a kasalance tana riƙe da ƙarfen da hannu ɗaya, ɗayan hannun nata ta riƙe da ƙafar Farha, yayin da Farha ke ta dukanta da ƙarfi.
A lokaci guda, tsananin ciwon da Farha ta jefa hannun yasa Amal ta sake ƙafar, saboda tsananin gajiya yasa ta sake ƙarfen da take riƙe da shi gaba ɗaya..
Tayi wani irin ihu, cikin kuka ta ce
“Maaaaleeeeekhhh!!!”
A nan ne Maleekh ya yi wani irin tsalle mai ban mamaki ya kama hannun Amal kafin ta yi ƙasi gaba ɗaya...
Maleekh cikin rawar murya yake faɗin
“Amal! Bazan bar ki ba! Bazan taɓa barin ki ba! Ki riƙe ni sosai!”
Amal cikin kuka da firgici ta riƙe hannunsa, jikinta na lumshewa saboda gajiya.
Farha kuwa, ganin Maleekh ya riƙe Amal, ta fara ture shi da ƙarfi tana ihu:
“Ka saketa ta faɗa! Ka barni na huta da ita! Ka saketa, so nake ta mutu ta bar rayuwarka har abada!”
Cikin ɗacin rai, Maleekh ya kasa jurewa. Ya zabga mata mari da hannunsa na hagu...yayinda yake riƙe da hannun Amal da ɗayan hannunsa..
Maleekh cikin tsawa ya ce
“Ke wace irin marar imani ne!? Ke wace iriyar marar tausayin ɗan adam ne!? Ki ture ƴar uwarki haka bayan kinsan ba cigaba da rayuwa zata yi ba, da zaran ta faɗa?!”
Da hannu ɗaya ya ƙara tura Farha gefe, sannan ya ɗaga Amal da ƙarfin zuciya. Ya yi ƙoƙari sosai har sai da ya jan yo ta sama da hannaye biyu, ya rungume ta sosai a jikinsa.
Amal ta saka ihu tana kuka, tana riƙe Maleekh da ƙarfi kamar zata shige jikinsa.
Tana kuka ta ce
“Wayyo Maleekh… na shiga uku…Sauran kaɗan na mutu..!”
Maleekh kuwa yana huci, zuciyarsa kamar zata fashe, yana fitar da numfashi cikin tsananin tashin hankali.
A gefe, Farha cikin tashin hankali, Ta riƙo Amal tana ƙoƙarin janye ta daga jikin Maleekh.
Farha cikin hauka take faɗin
“Na ce maka sai ta mutu! Sai ta tafi yanda ba'a dawowa! Ni kaɗai ce za ta zauna da kai!!!”
A wannan lokacin, Maleekh ya ɗauki kwalbar ruwa mai kauri da ke kan window side table, ya fasa kwalbar da jikin bango, ƙasan kwalbar ta zama makami mai kaifi.
Ya riƙe Farha da ƙarfi, ya manna ta da bango. Idanunsa sun kaɗa da ja, yana shirin caka mata kwalbar a kirjinta.
Maleekh cikin kakkauran murya ya ce
“Kafin ki kashe ta ni zan fara kashe ki Farha! Na rantse da Allah, idan kika sake kusantar Amal zan caka miki wannan kwalbar yanzu yanzu!!!”
Farha ta zaro idanu, jikinta ya fara rawa, zuciyarta ta nuna tsoro karara.
Amal kuwa cikin tsananin firgici da kuka, ta ruga da sauri ta riƙe hannun Maleekh.
Cikin kuka da roƙo take faɗin
“A’a Maleekh… Dan Allah… kada ka aikata haka! Ka dube ni, ni kake son karewa, ni kake so, amma…! Kada ka zubar da jinin mutum saboda ni… Dan Allah ka janye wannan hannun!”
Amal ta sake ihu tana faɗin
“Ka tuna Maleekh, idan ka kashe ta, za ka zama mai kisan kai… Ni ba zan iya rayuwa da hakan ba! Ka ajiye kwalbar, Dan Allah…!”
Maleekh yana rawar hannu, idanunsa na tsananin huci, zuciyarsa na girgiza tsakanin ƙaunar Amal da kuma mugun fushin da yake ji.
Maleekh yana tsaye yana riƙe da kwalbar da aka fasa, idanunsa sun ƙanƙance, jikinsa na rawa. Wani irin huci yake yi kamar zaki da aka tsokane.
Amal kuwa tana kuka tana roƙonsa, tana riƙe hannunsa da ƙarfin hali.
Amal ganin ya ƙi ajiye kwalbar sai za'kami yake tayi ga yana shaƙe da wuyan Farha, ba ƙaramin shaƙa kuma yayi mata ba domin har ta fara firfito da eyes, Amal ta ce da shi..
“Maleekh… ka duba idanuna… ka ga soyayyata gare ka… kada ka yi hakan. Idan ka kashe ta, kai da kanka ka hallaka ni, saboda ni ba zan iya rayuwa da mai kisan kai ba… Dan Allah, ka ajiye wannan kwalbar…”
Wannan kalmomin Amal ne suka shiga zuciyar Maleekh kamar ruwan sama da aka zuba wa wuta. Numfashinsa ya sake nauyi, amma zuciyarsa cike da raɗaɗi da fushi.
Ya ɗaga kwalbar da sauri, sannan da ƙarfi ya jefa ta ƙasa!
Tsssssshhhhh!
Ƙarar fashewar kwalbar ta cika wurin, sassan gilash suka watse a ko’ina. Amal ta runtse idanu tana riƙe da kunnenta saboda tsoro.
Maleekh ya janye daga bangon da ya manne Farha, yana huci da ƙarfi. Hannunsa na rawa, idanunsa sun cika da ƙwallah.
Maleekh da murya mai sanyi da ƙarfi ya ce
“Farha… wallahi kin kusa hallaka ni yau...Amma kin san meye? Idan ba saboda Amal ba… da yau kin daina numfashi. Ki fita a rayuwata, ki fita a raina, ki fita a zuciyata! Na tsane ki!”
Amal ta riƙe hannunsa tana kuka, tana ƙoƙarin kwantar masa da hankali.
Amal ta ce:
“Shhhh… ya isa haka, my bee… don Allah, ka kwantar da zuciyarka. Ka bar komai a hannun Allah…”
Maleekh ya dafe kansa yana huci, sannan ya durƙusa a ƙasa, yana maida numfashi da ƙyar. Amal ta durƙusa a gabansa, ta rungume shi tana hawaye...
A gefe kuwa, Farha tana tsaye tana jijjiga jikinta cikin tsoro, tana mamakin ganin yanda Maleekh ya kusan hallaka ta saboda Amal....
Cikin takaici ta ɗauki kwalbar da ya dagargaje a ƙasi ta yi masa kyakkyawan riƙo kamar zata yanka wani, sai kawai ta saita tsakiyar tafin hannunta ta yanka da ƙarfi...tayi haka ko zata fi samun sauƙin raɗaɗin da take ji a zuciyarta.....
_*NEXT NEXT NEXT*_
asmeetahwriter✍️
*🎤AMALEEKH🎤*
*AMAL AND MALEEKH*
Together, they stand between love and loyalty, between public duty and private longing, two hearts bound by fate, yet tested by truth.
*Writing and Storytelling By*
Asma'u Muhammad Auwal
Asmeetah writer
*HASKEN JAJIRTATTU*
*MARUBUCIYAR:*
*Matar Damisa*
*My Enemy*
*Hasken Ruhi*
*And know AMALEEKH*
Bauchi State Nigeria.
*WhatsApp 09065443871*
Follow my channel 👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
"Jajirtattu mu ne ƙarfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faɗuwa. Mu ne tarihi da ake ginawa!" 💪🔥✨
BOOK ONE page 37 to 38
🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹
🌹🌹
🌹
Ma’aikatan company da security ne suka ruga da gudu cikin tashin hankali. Wasu suka tsaya a bakin ƙofa suna leƙowa, wasu kuma suka kutsa ciki.
Suka tarar da Amal tana durƙushe tana rungume da Maleekh tana kuka, shi kuma yana riƙe da kanta yana huci kamar zakin da ya ga nama. A gefe kuwa Farha ce take riƙe da hannunta da jini ya ɗan zubo mata sakamakon gilashin da ta yage fatar tafin hannunta da shi..
Gaba ɗaya ofishin ya hau hayaniya, kowa sai tambayar:
“Me ke faruwa haka?!”
“Lafiya dai CEO?!”
Sai kuwa suka jiyo muryar Maleekh, mai ƙarfi cike da fushi, har sai da ofishin ya amsa:
“Ku saurara mun haka..."
Ya maida kallonsa kan Farha cikin fushi..
Ofishin ya ɗauki shiru daga ɗaruruwan idanu da ke kallonsa. Kowa sai ya juya kai yana kallon Farha...
Maleekh ya ce yana nuna ta da yatsa:
“Kin kusan kashe Amal yau! Idan ba saboda Allah ya tsare ta ba, da yanzu tana gadon asibiti ko kuma kabari. Amma ki sani, inda ace wani rauni ya same ta uhmmm! Wallahi wallahi wallahi da sai na kashe ki...Sai dai na ƙare rayuwata a gidan prison ko kuma nima a kashe ni.
Kuma last warning da zan miki shine daga yau bana son ganin ki a cikin wannan kamfani! Babu inda kika dace a rayuwata, babu inda kika dace dani..! Fita! Fitaaa daga nan kafin na manta da cewa ke mace ce!”..
Wannan kalmomin sun soki zuciyar Farha fiye da kowanne mari. Ta ji kamar ƙasa ta buɗe ta shige. Idanunta suka cika da hawaye, tana rawar jiki ta fara ja da baya. Mutanen company suna kallonta da mamakin rashin zuciyarta...
Farha ta dafe ƙirji tana kuka ta fita da gudu daga ofishin, tana rera kuka tare da faɗin
“Zan rama! Zan rama wannan wulakanci!”
Ta shige cikin motarta a harabar company tana huci, sai kawai ta yi ƙwafa da gudu ta bar wajen.
A ciki kuwa, Amal har yanzu tana kuka tana riƙe da Maleekh.
Maleekh ya tallafo fuskarta da hannuwansa biyu, yana share mata hawaye, yana furta cikin tausayi:
“Beb… shhh… ki kwantar da hankalinki. Na yi miki alƙawari, a duniyan nan bazan bari wani ya cutar dake ba. Ki bar komai a hannuna.”
Security da sauran ma’aikata suka tsaya kallonsu cikin nutsuwa, suka ga irin soyayyar da Maleekh yake nunawa Amal, sai su kaɗai suka fahimci asalin darajar Amal a zuciyar CEO.
Farha ta isa gida cikin rawar jiki, idonta jawur tsabar kuka, tana ihu kamar wacce ta rasa iyayenta. Ta buge ƙofar falon da ƙarfi, cikin ƙyarma ta na ihu:..
Ammy tana zaune a kujerar falo ita da yaranta Islam da Arfat.
Ammy hankali a tashe ta ce
"Lafiya kuwa?.."
Farha tana kuka ta ce:
“Ammy! Yaya Maleekh ne ya mun duka a kan Amal! Yayi mun wulakanci a gaban mutane!”
Ta nuna hannunta da ta yanka da kwalba, jini ya ɗan zube kadan a gefen yatsun hannunta. “Kinga! Ya yi min haka saboda ita! Ya yi min haka saboda Amal!”..
Ammy ta yi saurin tashi daga kujerar falon, idonta cike da takaici. Ta kalli Arfat da Islam sannan ta ɗaga muryarta, tana faɗin:
“Kada ku tsaya ɓata lokaci! Ku tafi ku je gidan su Amal ku murkushe ta, kuyi mata dukan da sai an kwantar ta a gadon asibiti...!”
Ta kalli Farha sannan ta ce
"Wa ta ƙila ki rage raɗaɗin da kike ji yanzu haka..."
Arfat da Islam suke yiwa Ammy kallon kama-da-wane; sun san halin mahaifiyarsu, sun san ba sauƙi ne da ita, kuma abin magana bata gudunsa...
Islam ce ta buɗe baki zata yi magana Ammy ta katse ta da tsawa mai nuni da umarni:
“Na ce ku tafi! Wannan umarni ne ba shawara ba!”
Farha, tana kuka cikin rawar murya, ta ce:
“Ni ma zan tafi! Zan rama! Zan nuna mata cewa ba za a wulakanta ni a haka ba!”
Daga nan ta fice daga falon.
Arfat da Islam duk suka bi bayan Farha cikin sauri, suna ƙara shirya kansu da mugun nufi. A zuciyarsu dai akwai haɗuwa tsakanin kishin ɗan uwa da kishin gida...
✦ A gidan Amal..
Amal ta bar company cikin halin damuwa sosai. Ta yi kuka sosai a cikin motarta, a zuciyarta tana godewa Maleekh saboda yadda ya tsaya mata; hakan ya ƙara bata tabbacin: akwai wanda yake kula da ita sosai..
Ta isa gidan su, bayan ta shiga parlour, ganin ba kowa a falon yasa ta jingina da bango sannan ta sauƙe nannauyar numfashi....
Inna, itama shigo wa tayi alamun daga unguwa take, ganin Amal yasa ta yi turuss tana kallonta, ta ƙaraso wurin ta da tsananin mamakin ganin halin da jikarta take ciki, Inna riƙo hannun Amal tayi tare da zaunar da ita akan sofas, itama ta zauna kusa da Amal, ta riƙe hannunta cikin tausaya wa ta ce:
“Amatu… me ya faru? Ki gaya mini komai.”
Amal ta share hawaye, rai-rai ta fara ba da labari, ta faɗa wa Inna yadda abubuwa suka faru, yadda Farha ta zo ofis da irin maganganun ta, yadda rikici ya tashi har Maleekh ya zo ya ceci ta. Inna ta rufe bakinta hannayenta nata zazzaro ido tare da faɗin
"Ki ce yau ina zaune sai dai a kawo mun gawarki Amatu, wannan yarinya Fara Allah dai ya kwashe mata wallahi..."
Inna ta gama surutan ta sannan ta fara yi wa Maleekh addu’ar fatan alkhairi...
✦ A CashTalk.
A company kuma, Maleekh ya tsaya ƙarasa aikin da ya taru masa. Bayan tashin hankali, ya tsaya a ofishinsa yana ƙoƙarin tsara abin da bai kammala ba; kansa yana cike da damuwa. PA da wasu ma’aikata suka tsaya wajen, suna ta dubansa cikin kulawa kowa na gani ya san wani abu ya faru, amma babu wanda ya san cikakken abun da ke faruwa sai PA...
PA ya kawo masa wasu takardu, ya ɗan yi magana cikin natsuwa:
“Boss, kana lafiya? Na ga ka kusan kammala wa duk da iya na yau ne, Madam Amal duk tayi maka sauran ayyukan, abu ɗaya ne ya rage. Zan kawo maka summary ɗin meeting ɗin yau da safe.”
Maleekh ya ɗan miƙe, ya ɗaga kansa ya kalli taga inda gilashin building yayi hasken yamma...
Ya ce:
“Na gode. Ku ci gaba, ku shirya komai kamar kullum.”
Ya juyo, idonsa ya tsunduma cikin duhu na tunani; ya yi alƙawarin in Allah ya yarda, zai ɗauki mataki akan duk wanda ya cutar da masoyiyarsa ya kuma sani, ya zama dole ya natsu yanzu, ya dawo daga wannan tashin hankali don kada ya yi abin da zai yi nadama.
Zama ya yi tare da kifar da kansa akan table ɗin office, yana ta tunani da dama...
A zuciyarsa akwai ƙauna mai zurfi ga Amal, amma akwai kuma rashin sulhu da mahaifiyarsa da bukatar girmamawa ga Malam. Yana jin nauyin zaɓin, amma a zuwansa yanzu akwai abu ɗaya: kare Amal, dawo da kwanciyar hankalinta, da gyara duk irin barnar da rikici zai iya haifarwa.
✦
Misalin ƙarfe 6 na yamma...
Babban falo ya cika da shiru, sai ƙarar plasman da yake haske yana nuna wani shirin fim. Amal da Inna tare da mata masu aikin gidan guda biyu suna zaune suna kallo, kowannensu cikin nutsuwa.
Sai kuma kwatsam! Suka ji an turo ƙofar falon da ƙarfi, Farha ta shigo a gaba tana huci, a bayanta Arfat da Islam. Fuskar Farha ta cika da tsananin fushi, idanunta sunyi jawur alamar ta sha kuka sosai..
Amal ta miƙe tsaye da gaggawa, idonta na kallon Farha da tambaya:
“Me kuke nema a gidana, zaku wani shigo wa ba sallama kamar wanda aka muku sata?”
Farha ta yi tsaki, ta kalli Amal daga sama zuwa ƙasa:
“Ai satar kika yi, baki sani bane? kin sace mun abu mafi girma a cikin zuciyata, yanzu shi nazo karɓa..."
Amal tayi murmushi sannan ta ce:
"Ai abin da ya fito daga cikin zuciya ba ya koma wa gurbinsa, sai dai kawai ki haƙura..."
Farha ta harare ta tare da faɗin:
"Kina mun abubuwa da yawa, Amal! Ke ce kika jawo min wulakanci a company, kika sa Yaya Maleekh ya wulaƙanta ni a gaban jama’a! To yau sai kin sha ɗan buro uban duka, domin ban zo da niyar koma wa haka nan ba...”
Inna ta miƙe cikin mamaki, ta ɗauki gyalenta ta ɗaura a kunkumi, ta kalli Farha da mugun kallo ta ce:
“Ke yarinya! Wani dalili ne zai sa ki shigo gidanmu kina wasu surutan banza? Waye ya turo ku?”
Arfat ta sa dariya, tana duban Inna cikin raini sannan ta ce:
“Kowa ya turo mu, mu ne za mu koya muku hankali yau.”
Islam dai tana tsaye gefe, zuciyarta na bugawa. Tana ganin tashin hankali yana ƙaruwa, amma ta kasa shiga tsakaninsu.
Nan take cacar baki ta 6arke, Amal da Inna suna mayar da martani cikin rashin mutunci. Sa’annan rikici ya tashi!.
Farha ta rufe Amal da duka lokaci guda, Arfat itama ta rufu kanta, haka suka kai mata duka da hannaye..
Amal tana ƙoƙarin kare kanta da ƙarfi, amma sarkin yawa ya fi sarkin ƙarfi. Duk da ƙoƙarin ta, haka suka kayar da ita ƙasa, suka ci gaba da dukan ta ba ƙaƙautawa.
Inna kuwa da ta ga haka, ta sa karfi ta shiga tsakani, tana kai musu duka itama duk da tsufarta. Ganin ba sa bi ta kanta ne yasa ta cafke Farha ta garzaya mata uban cizo akan nonuwanta.. 🤣🤣
Lokaci guda Farha ta saki ihu cikin zama ta ture Inna da ƙarfi, har sai da tsohuwar ta kife a kan kujera. Masu aikin gidan ne suka yi saurin ɗaga Inna cikin tashin hankali, suna ƙiran Amal da ta tashi ta karɓi ƴancin ta..
Amal kuwa tana ƙoƙarin miƙewa, tana mayar da martani amma duk da haka suka ci galaba. Farha da Arfat suka yi mata duka har sai da ta kasa tashi...
Islam dai tana tsaye gefe, zuciyarta ta riga ta ɓaci da tunanin:
“Idan Yaya Maleekh ya ji labari, shin wane hukunci zai ɗauka akanmu?”
Bayan sun gama dukan Amal, sai Farha ta ɗauki ƙarfen flower stand ɗin falon, tare da Arfat suka fara bugun plasman. Sai da suka farfasa gilashin nan baki ɗaya, suka bar shi a wargaje a ƙasa.
Daga nan suka kama hanyar fita cikin dariyar mugunta. Amal kuwa ta kwanta a ƙasa tana kuka, tana ihu cikin rauni...
Inna da zuciyarta ta ƙone saboda zafin ganin yadda aka rufe jikarta da duka, ta nufi kitchen da gudu, ta ɗauko wuƙa mai kaifi, ta fito da gudu tana bin Farha da Arfat tana faɗin:
“Sai na yanke muku wuyan ku yau! Ku tsaya in kun isa, dabbobin yara kawai, marasa hankali..”
Da ganin haka Farha, Arfat da Islam suka ruɗe da tsoro, da gudu suka fice daga gidan. Motarsu suka shiga cikin sauri, suna dariya mai cike da mugunta da rashin imani.
Inna ta tsaya a bakin get tana huci, ga wuƙar a hannu, tana faɗin:
“Wallahi sai Allah Ya isa tsakanina da ku!”
Falon ta koma cikin ruɗani plasman a wargaje, Amal a ƙasa tana kuka cikin jin raɗaɗin abin da suka mata, masu aiki suna ta duban ta cikin tashin hankali...
Inna tana huci, tana zazzaro ido da ƙarfi ta ce wa masu aikin gidan:
“Ku ƙira mun Maliku yanzu-nan! Yazo ya ga irin tashin hankalin da ‘yan uwansa suka kawo mana cikin gida.”
Ba tare da ɓata lokaci ba suka ɗauki waya suka ƙira Maleekh.
A lokacin kuwa Maleekh yana mota, yana kan hanyar komawa gida... Amma da jin ƙiran gaggawa daga gidan Amal, zuciyarsa ta bada saƙo mai nauyi. Nan take ya juyar da motarsa cikin sauri ya nufi gidan Amal.
Da isarsa, ya tarar da tashin hankali! Ga Amal a ƙasan carpet tana kuka, jikinta cike da raunukan yakushi da duka, jikinta ya yi jawur abin ka da farar fata ga duk sun yayyaga mata kayan jikinta da ƙarfi.. Ga plasma falon a farfashe, wargajjen gilashi ya bazu a ko’ina...
Zuciyar Maleekh ta tsaya cak, ya zaburo yana tambaya cikin tashin hankali:
“Meya faru haka? Shin 6arayi ne suka shigo muku?..”
Inna, wacce ranta yake har yanzu tana huci, ta zaburo ta dubi Maleekh tana faɗin da tsawa:
“Ɓarayin ƙannenka marasa mutunci baaa! Sun zo nan suka yi wa Amatu dukan tsiya, sannan suka farfasa mana tv muna kallo! Wannan marar mutunci, yarinyar nan Fara, ta hankad’e ni da ƙarfi har sai da na kifu a kujera, da ba ƙaramin sa’a na yi ba, da karyewar wuyana kenan! To wallahi, Maliku, ko ka dakatar da su yanzu, ko kuma na ɗauki hukunci da kaina!”
Zuciyar Maleekh ta buga sosai. Ya sauƙe dogon numfashi, zuciyarsa ta yi nauyi. Ya rasa kalma da zai furta a daidai lokacin, domin wutar tashin hankali ta yi yawa sosai.
Sai ya durƙusa a gaban Amal, yana riƙe da hannunta, yana share mata hawaye cikin sanyin murya ya ce:
“Yi haƙuri Amal… ki yi haƙuri dan Allah.”
Hannunsa ya yi sanyi kamar ruwan sanyi a zuciyarta, duk da hawayenta basu tsaya ba.
Ya juya ya kalli Inna, shi ma a sanyaye ya ce:
“Inna, ki yi haƙuri… Ni zan gyara komai, ki bar komai a hannuna. Dan Allah ki kwantar da hankalinki.”
Sai da ya rarrashe su sosai, kafin Inna ta samu ta zauna tana huci tana girgiza kai.
A daren nan kuwa, Maleekh ya tabbatar da an kawo musu sabon plasma wanda ya fi wanda aka farfasa girma da tsada, domin ya gamsar da Inna da Amal, ya kuma dawo da nutsuwa a gidan.
Bayan ya tabbatar sun samu natsuwa, da kansa ya ɗauki motarsa, ya fita daga gidan Amal cikin damuwa. Kai tsaye ya nufi gidansu, zuciyarsa cike da tunani marar daɗi...
☆☆☆▪︎☆☆☆
Arfat, Islam da Farha suna zaune suna dariyar abin da ya faru, suna ta hira akan irin dukan da suka yi wa Amal. Har Arfat tana ɗaga hannu tana nuna yadda Amal ta faɗi, suna dariya kamar masu hauka..
Sai ga ƙarar motar Maleekh ya shigo cikin compound da ƙarfi. Zuciyarsa cike da fushi, fuskar nan ta kumbura kamar an hura wuta a cikinta.
Ko sallama bai yi ba, ya shigo falon da gaggawa. Kafin kowa ya yi wani motsi, sai ya rufo kan Arfat ya ɗago ta da ƙarfi ya zabga mata mari har sau biyar a jere!
“PAT! PATT! PATTT! PATTTT! PATTTTT!”
Arfat ta fasa wani irin ihu tana riƙe da kunci tana karkarwa...
Bai tsaya ba, ya juyo ga Islam, ya ɗago ta da mugun fuska. Da sauri Islam ta durƙusa tana kuka:
“Dan Allah Yaya kayi haƙuri! Wallahi banda ni… su Aunty Farha ne suka ce muje…”
Maleekh ya tsayar da hannun nasa yana huci, idonsa jawur, ta wani ɓangare baya son taɓa Islam domin kaf yafi ji da ita, jininsu yafi haɗuwa...
Farha da take zaune a gefe ta ga abin da ke faruwa, da sauri ta miƙe da niyyar guduwa. A fusace Maleekh ya kai mata harbi da ƙafarshi, ya canke ta kamar kwallo. Sai da tayi sama ta doki a ƙasa da ƙarfi...
Kafin ta samu daidaita kanta, ya ɗago ta a fusace tare da yin wurgi da ita da ƙarfi har sai da goshinta ya bugi a jikin bango, nan goshin ya fashe sai jinin da yake zubo wa nan take...
Arfat kuwa tana durƙushe sai ihu take, Maleekh ne ya ƙara ɗagota ya ɗaga ta sama kafin ya buga ta da ƙasa. Ihun ta ɗaya ya tsaya cak – ta sume!
Islam ta sulale ta shiga bayan kujera tana kukan razana, jikinta sai rawa yake kamar zata mutu..
Maleekh ya sake rufa kan Farha, ya ɗago ta ya ƙara buga kanta da jikin bango a karo na biyu. Jinin na ƙara zuba, ta saki ihu tana neman taimako...
A nan ne Ammy ta fito daga part ɗinta cikin razana, ta tsayar da kallon ta kan Maleekh!
A tsawace ta ce:
“Subhanallah! Maleekh!!! Wannan wanne irin hauka ne ka shigo da shi gidan nan?! Zaka kashe su ne saboda sun je sun taɓo ƴar gold? To ni na tura su, eh! Ni na ce su je suyi wa yarinyar can dukan tsiya, shine yanzu zaka zo ka kashe mun ‘ya’yana?!”
Ta nuna Arfat dake sume a ƙasa ta ce;
“Ka kashe mun yarinya saboda waccan matsiyaciyar ƴar talaka?! Ashe haka ƙiyayyarka ta kai?!”
Ta dubi Farha da jini ke kwarara daga goshinta tana kuka.
Nan ma Ammy ta ce:
“Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un! Matar da zaka aura kayi mata irin wannan mummunan duka na wulakanci? To wallahi, na rantse da Allah, gobe za a yi taron aurenka da ita! Ba wani shiri tinda kai ɗan banza ne! Kai ba ɗa bane da zan tsaya kallon abin da kake aikatawa!...”
Maleekh ya juyo a fusace, yana huci kamar wuta zata fito daga bakinsa ya ce:
“Ammy, ki saurare ni da kyau…! Wallahi sai dai a ɗaura auren da gawa ta! Ki je ki shirya jana’iza, amma ba aure da ni da Farha! Na tsani wannan yarinyar fiye da mutuwata..!!!”
Ammy ta zaburo, idonta cikin nashi, a tsawace ta ce:
“Kai Maleekh, Saboda wata ‘yar matsiyaciya ka juyawa mahaifiyarka baya? Ɗan banzan yaro kawai, sai ka auri Farha, ko da kuwa ta sanadiyyar haka zaka rasa rayuwarka! A gabana sai an ɗaura wannan auren..!”
Islam ta miƙe da sauri tana kallon Ammy jin furucin da tayi..
Maleekh jinjina kai ya yi yana murmushin dole ya ce:
“A gabanki da duniya gaba ɗaya, ba za a taɓa ɗaura auren nan ba! Wallahi Farha bata da wata nasaba da ni, domin ita ɗin maƙiyata ce! Duk inda Amal take, ita ce ƙauna ta, ita ce zuciyata ni da ita zan zauna har ƙarshen rayuwata..!”
Ya juyo yana kallon Farha wacce ke kuka ga jini duk ya ɓata mata fuska, ya ce:
“Ke kuma, ki ci gaba da shirinki, Amma wallahi zan nuna miki cewa ni ɗan halak ne, sannan ni ba ragon namijin da zaki raina bane, ki ci gaba da shishshige mun rayuwata wata rana wallahi sai kin rasa numfashinki ta sanadiyya ta...."
Har ya juya zai nufi part ɗinsa...Sai ya ji an ƙira wayar gida (telephone)..
Maleekh da sauri ya nufi wurin ya ɗaga ƙiran, jin ana ta ambatar.
"Hello Hajiya, Hajiya kina ji na?...idan kina ji na aikin Maleekh zai tabbata.."
Maleekh kallon Ammy ya yi tare da saka wayar a speaker..
Kowa yana ji, domin
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 26 Chapter of 62