suka sake zuba sosai. Ta tsaya gefe da hanya ta jingina kanta da sitiyari tana kuka kamar wata ƙaramar yarinya...
A zuciyarta tana addu’a:
“Ya Allah, idan ina tare da gaskiya, idan ina son shi da zuciya ɗaya, ka dawo min da shi. Kada ka bar soyayyarmu ta mutu haka kawai. Ka tsare shi da cuta, ka tsare shi da mugunta… ka shiryar da zuciyarsa gare ni.”
Numfashinta ya yi nauyi, amma har yanzu zuciyarta na ambaton sunansa:
_“Maleekh… Ya Maleekh…”_
______________________________________
Maleekh yana zaune a gadon sa yana jingine da pillow, idanunsa na kallon Zayd wanda ke zaune a gefen gado da murmushin nishaɗi a fuska.
Zayd ya gyara zama ya ce:
“Bros, wallahi yau a zuwana gidan nan na haɗu da wata pretty yarinya… gaskiya ta kwanto min a rai sosai. Amma fa tana da ɗan jiji da kai, duk da haka babu matsala, soyayyata zata sauƙe mata wannan girman kan.”
Maleekh ya ɗan ɗago ido ya kalle shi, sai kawai ya yi murmushi mai rauni sannan ya ce:
“So cute, na tayaka murna.”
Zayd ya girgiza kai yana dariya:
“Hmm, Bros, kai da kanka ka san idan Zayd ya fara, to babu gudu babu ja da baya.”
Maleekh ya ce cikin dariyar dole:
“Ni dai ina fatan kada ta kawo maka wahala.”
Zayd ya lumshe ido ya ce cikin salo:
“Amma ka san wani abu? Na yi big mistake wallahi. Ban tambayi sunanta ba, ban kuma karɓi address ɗinta ba. Kuma a lokacin ma she is so weak… kamar mai ciwo.”
Maleekh ya yi dariya kaɗan, yana kallon shi da murmushin tausayi:
“To sai ka yi searching ɗinta a zuciya, ko? In ka ci gaba da yi mata addu’a za ku haɗu da ita in Allah ya so.”
Suka yi dariya duka.
Sai Zayd ya matsa kusa da shi ya ce:
“Amma fa Bros, sai ka daure. Na san kana da wani abu a zuciya, amma ina maka addu’a zaka samu nutsuwa. Kai fa ba kawai yayana ba ne kai ne abokin rayuwata. Duk ciwonka, duk damuwarka, ina tare da kai har ƙarshe.”
Maleekh ya ɗan rufe ido, zuciyarsa ta yi nauyi. Amma saboda ƙoƙarin kada ya nuna raɗaɗinsa, ya ce cikin murmushi:
“Na gode, Zayd. Allah ya saka da alheri. Kai kaɗai ne kake bani nishaɗi a wannan lokacin.”
Zayd ya bubbuga kafaɗarsa yana dariya:
“To ai ba komai ba. Ni dai na ce maka ka shirya, very soon zan zo maka da labarin soyayya irin ta film. Ka ga na fi ka nasara kenan.”
Duka suka sa dariya.... dariya mai saurin yankewa daga gefen zuciyar Maleekh saboda ciwon da yake boyewa.
Bayan dariyar ta ɗan lafa, Zayd ya tashi daga gefen gadon ya ce:
“Ni dai zan je in huta. Amma Bros, ka kwanta ka cire damuwa daga ranka. Komai zai daidaita da izinin Allah.”
Maleekh ya yi ƙoƙarin mayar da murmushi:
“Na gode sosai, Zayd. Allah ya sa ka samu farin cikin da kake nema.”
Zayd ya yi masa _thumbs up_ ya fice daga ɗakin cikin nishaɗi.
Maleekh ya zauna a gefen gadon na ɗan lokaci, hannunsa yana shafa hoton da yake a gefen bedside table. Wani irin numfashi ya sauƙe, ya kwanta da baya ya rufe idanunsa.
Amma duk da ƙoƙarinsa, hoton Amal ya bayyana cikin zuciyarsa kamar tana tsaye a gabansa. Kukan da ya ji daga gare ta a falon gida, hawaye a fuskarta, da muryarta tana ƙiran sunansa duk suka sake dawo masa.
Ya rufe fuska da hannayensa yana ambaton:
“Ya Allah… me yasa har yanzu zuciyata ta kasa daina ji da ita?..”
Wani irin raɗaɗi ya shige shi, amma duk da haka ya danne shi, yana son ya nuna ƙarfin hali gaban kowa. Sai dai a zuciya, ya san ciwon Amal ba zai bace masa da sauƙi ba.
____________________________________
A wannan daren...
Amal tana kwance kan gadonta, ƙwance cikin duhu, idanunta suna kallo ceiling ɗin ɗakin amma zuciyarta ta kasa samun nutsuwa.
Ta juyo gefe tana riƙe da pillow kamar zata matse shi. Hawaye suka zubo a kuncinta tana faɗin cikin rauni:
“Maleekh… duk duniya babu wanda na so kamar kai. Ko da baka yarda dani ba, ni nasan gaskiya zata bayyana wata rana…”
Ta runtse idanu tana ƙoƙarin yin bacci, amma duk lokacin da ta lumshe ido, hoton Maleekh ne yake bayyana, yana mata tsawa da maganarsa mai ciwo.
Sai kawai ta yi shahada a hankali, tana roƙon Allah ya ba ta ƙarfin zuciya:
“Allah ka bani haƙuri da ƙarfin zuciya akan wannan jarabawa…”
Ta zauna bakin gado tana kallon taga, tana jin wani irin ƙarfi a zuciyarta cewa ko da Maleekh ya ƙi ta, ta tabbata ba haka zuciyarsa take ji ba.
_WASHEGARI_
Da safe suna zaune tare a dining area, an shirya breakfast.
Zayd yana cin toast yana kallon Maleekh cikin annashuwa ya ce:
“Bros, shin wani matsayi za’a bani a cikin company ɗinka?..”
Maleekh ya ɗan ɗaga kai daga coffee cup ɗinsa, ya girgiza kai tare da faɗin:
“Zan iya faɗa maka Zayd, amma ka bari mu je muji daga bakin board kafin a sanar maka matsayi.”
Zayd ya lumshe idanu yana murmushi ya ce:
“Gaskiya fa, ina so ace an bani matsayin assistant ɗinka. Ka san muna tare a koda yaushe.”
Ƙaramin murmushi ya bayyana saman fuskar Maleekh sannan ya ce:
“Akwai wacce take kan wannan matsayi. Ban yarda da cire wanda yake kan mukaminsa kawai don wani ya shigo ba. Abin da ya dace shine, zan baka matsayin da ya yi daidai da kwarewarka. Duk wanda yake matsayin assistant burinsa shine ya haura gaba, ba ya tsaya nan ba.”
Zayd ya ɗan saki baki cikin rashin fahimta ya ce:
“Oh, kenan ban dace da matsayin ba?..”
Maleekh ya ɗago idonsa ya kalle shi da nutsuwa ya ce:
“Ba haka nake nufi ba. Zayd, adalci ne yafi komai. Idan na sauƙe wacce take assistant ɗina kawai saboda kai, ai na zalunce ta. Ina fatan zaka fahimce ni.”
Zayd ya lumshe ido cikin murmushi ya ce:
“Shikenan, no problem. Na yarda da kai.”
A haka suka gama breakfast ɗin suka nufi company ɗin tare...
_Campany_
Yayin da suka shigo cikin babban reception ɗin, ma’aikata suka fara gaishe da Maleekh da girmamawa.
A nan suka tsaya kafin su nufi sama, sai kawai ƙofar glass ta buɗe.
Amal ce ta shigo cikin tsararren kaya, tayi dressing cikin class, high heels ɗinta na danna tiles ɗin ƙasa tana tafiya cikin ƙasaita. Duk wajen ya ɗan tsaya cak.
Zayd ne ya fara hangen ta, ya yi ido huɗu da ita.
Ya buɗe baki yana cewa cikin farin ciki:
“Wowww… Allah ya sake haɗa mu, my beautiful pretty!”
Duk reception suka juyo da kallon mamaki, suna kallon Amal da Zayd.
A hankali Maleekh ya juya kansa saboda jin yanda Zayd ya ƙira pretty.
Idonsa ya sauƙa kan Amal, zuciyarsa ta buga da ƙarfi! Ya dunƙule hannunsa da ƙarfi tare da haɗiyar yawu...
Amal ta tsaya cak, idonta akan Maleekh, jikinta yana rawa da tsoro.
Maleekh ya ɗan jinjina kai da ƙarfi, yana murza yatsansa cikin tafin hannu, sannan cikin nutsuwa ya ce da karfin zuciya:
“Fatan alkhairi…”
Ya nufi escalator..Yana zuwa ya ɗaga ƙafarsa ya hau escalator, amma idanunsa suna kan Amal har sai da ya haura.
Amal itama idonta akan sa har sai da ya ɓacewa gani.
Zayd yana nan tsaye kamar wanda ya ci jackpot, yana murmushi ya ce da Amal:
“Pretty, ke ma a nan company kike aiki? Alhamdulillah! Wannan babban alheri ne. Ni ma yau zan fara aiki anan. Kinga yanzu za mu zama ɗaya kullum…”
Amal bata ko kalleshi ba, kawai ta ratsa gefensa cikin isa, ta nufi elevator.
PA ɗin Maleekh dake tsaye a reception ya yi murmushi ya ce wa Zayd:
“Your welcome sir. Waccan ce assistant CEO ɗin company.”
Idon Zayd ya buɗe da mamaki ya ce:
“What! Assistant CEO? She?…”
Kafin ya gama, Amal ta shige elevator.
Da sauri Zayd ya nufi wurin yana cewa:
“Wait, pretty! Ki jira mana please!”
Amma elevator ɗin ya rufe a gabansa, Amal ta tafi sama ta barshi tsaye a ƙasa yana ƙoƙarin numfasawa da murmushi marar dalili...
A wannan rana haka Zayd yake ta shishshige wa Amal.
Zayd ya ci gaba da zagaye Amal a cikin company...
Ko da break-time sai ka ganshi ya shigo office ɗinta da excuse: “Pretty, kin ci lunch kuwa?..."
Anjuma kaɗan sai ya dawo ya ce "Pretty, kin huta kuwa?.."
Bayan wasu ƴan mintuna sai ya sake dawowa Ya ce "Pretty, kin sha ruwa kuwa?”..
Duk da Amal tana ƙoƙarin sharar da shi da kakkaucewa, Zayd ya kasa nisanta daga gare ta...
Ba yanda ta iya haka take biye shi suna fita tare da sauran staff, yana yi mata hira da dariya. Duk wanda ya gansu zai ce soyayya ce mai tasowa...
Amma Amal a ranta tana jin nauyi, tana jin ba komai bane idan ba da Maleekh ba….
A gefe kuwa, Maleekh shiru yake. Duk lokacin da ya hango Zayd yana yi wa Amal hira, idonsa na canzawa. Yana jin zafi a zuciyarsa amma baya nuna komai. Kishi na cin ransa, amma sai ya dake, yana bawa kansa hujja:
“Ba ni da masoyiya, na sallame ta, so… me yasa kike jin zafi Maleekh?”
☆☆☆☆☆
Two days after Zayd started working at the company….
Wata rana, bayan aiki, Amal ce ta ɗauki babban fayil ɗin takardu. Su ne takardun da Maleekh bai samu damar dubawa ba lokacin da yake jinya. Ita ce assistant, dole ta kai masa domin ya sanya hannu kafin ranar ƙarshe.
Tana shiga cikin office ɗin sa.
Ƙamshin turarensa ya buga mata kai.
Maleekh yana zaune shi kaɗai, ya jingina a kujerarsa, hannunsa riƙe da pen yana rubuce-rubuce.
“Excuse me, sir…” Amal ta furta a hankali, zuciyarta na tsalle-tsalle.
Ya ɗago idonsa, suka yi ido huɗu. Zuciyarsa ta buga, amma bai nuna ba.
“Zo,” kawai ya ce da muryar kasaita.
Ta matsa kusa da desk ɗinsa, ta aje fayil ɗin.
“Wannan su ne takardun da ba a duba ba lokacin da kake jinya. Na yi reviewing, sai ka sanya hannu.”
Ya ɗauki pen ɗinsa, ya fara dubawa.
Amal ta tsaya a tsaye tana kallon gefe, zuciyarta na rawa. Duk da ita ce assistant ɗinsa yanzu, ba zai taɓa sauƙin kasancewa da shi cikin ɗaki guda ba.
Shiru ya mamaye office ɗin, sai ƙarar bugun zuciyoyinsu da suke jin shi su kaɗai.
Bayan ɗan lokaci ya ɗago ya ce da muryar nutsuwa:
“Na gode da kula da company lokacin da ban samu dama ba.”
Amal ta ɗan runtse ido, ta ce cikin sanyin murya:
“It’s my duty, sir.”
Suka yi shiru.
Takardun suka koma magana tsakanin su.
Babu wata hirar soyayya. Babu wata rigima.
Sai dai ƙirji biyu suna bugawa cikin ciwo da sha’awar da suke ɓoyewa.
Amal tana tsaye a gaban desk, tana nuna wa Maleekh inda zai sanya hannu a cikin fayil.
Shi kuma yana kallon takardu, sai lokaci-lokaci idanunsa su kai kanta, sannan ya ɗan janye kai kamar bai kula ba.
Shiru ya rufe office ɗin, bugun zuciyoyinsu na ci gaba da daɗa karfi.
Kawai aka buɗe ƙofa, Zayd ya shigo da murmushi a fuskarsa..
“Prettyyy! Ashe kina nan…”
ya faɗa yana matsowa cikin sanyi.
Amal ta juyo da sauri, idanunta suka firgita.
“Zayd… kai fa…”
Maleekh kuwa ya ɗago daga rubutunsa, ya kalle shi da idon da ba a iya fassara ba. Idonsa cike da kishi da takaici, amma fuskarsa na ɗauke da ɗan murmushin da ya fi zafi fiye da faɗa.
Zayd bai damu ba, ya ƙarasa gaban Amal, har yana ƙoƙarin kai hannu zai ɗauki fayil daga hannunta..Yana cewa
“Kin wahala fa Pretty. Ina gaya miki, idan kin gaji da yawa sai ki bar sauran a hannuna.”
Amal ta janye hannunta da sauri, ta ɗan ɗaure fuska sannan ta ce:
“Ba sai haka ba, Zayd. Ina yi ne saboda aikin company.”
Maleekh ya jingina da kujerarsa baya, ya ɗau pen ya fara jujjuyawa a yatsansa..
Da wata muryar ƙasaita mai sanyi amma mai tsanani, ya ce:
“Mr. Zayd… wannan office ba wajen hira bane. Idan akwai aikin da ya shafe ka, zaka iya aiko da secretary ɗinka.”
Shiru ya ɗan ɗauki ɗakin.
Zayd ya murmusa, yana son nuna bai damu da tsawar ba ya ce:
“Sorry, sir. Ni dai kawai na zo in ga Pretty—ehm… Amal ko ta gama da waɗannan takardu.”
Amal ta ji kunya sosai, zuciyarta na buga wa...
Maleekh kuwa idanunsa sun ƙanƙance, ya dafa desk ɗin da hannu ɗaya.
Cikin natsuwa amma muryarsa ta sauya, ya ce:
“From now on… babu wanda zai ƙira assistant ɗina da wani suna daban a nan cikin office.”
Zayd ya ji an kulle masa baki.
Amal ta kasa ɗaga kai saboda kunya da bugun zuciya.
Amal jan jikinta tayi ta bar Office, Zayd ganin haka yasa shi bin bayanta yana faɗin
"Ya za ki tafi ki bar ni ehhh pretty tsaya manaa..."
Bayan antashi daga wurin aiki..
Amal ta fito daga building tana riƙe da jaka a hannu. Zayd ya biyo bayanta da sauri, yana ɗan tafiya da wani irin sanyi da yanga.
“Pretty,” ya ƙira ta da fara’a, “nasani kin gaji sosai yau. Ki bari ni na kai ki gida da kaina a mota.”
Amal ta tsaya, ta kalle shi da ɗan murmushin ladabi, sannan ta girgiza kai.
“A’a, ka barshi. Zan tafi da motata. Sai gobe ka fito da wuri kar ka makara.”
Zayd ya yi dariya yana jingina da jikinsa kamar wanda ya ci nasara...
“To my pretty, ai ko ba komai … saboda naga wannan kyakkyawan fuskar taki zan fito da safe.”
Amal ta yi shiru kawai, ta buɗe motarta ta shiga. Ta ja motarta ta tafi cikin nutsuwa.
A gefe kuma…
Maleekh yana cikin motarsa, hannunsa yana ta matsa sitiyarin kamar yana son ya murƙushe shi. Fuskar tasa ɗauke da murmushi marar annuri, idanunsa sun cika da wani irin haske na kishi da haushi.
Ya kalli hanyar da motar Amal ta bi, zuciyarsa na karyewa da tunanin:
“Tana iya yin dariya da shi… ta kyale shi yana ƙiran ta da suna da ni kaɗai na san darajarsa… amma ni na rasa komai. Na bar komai.”
Bayan mintuna kaɗan, Zayd ya ƙaraso motar Maleekh da murmushi a fuskarsa. Ya buɗe ƙofar ya shiga cikin nishaɗi tare da faɗin.
“Bros Maleekh! Wallahi wannan assistant ɗinka…ehm sorry—Amal—she’s so wonderful! Ka ga irin yadda take da nutsuwa? Kuma gaskiya she’s different, ba kamar sauran mata ba…”
Maleekh ya ɗauke kansa daga kallonsa, ya mayar da hankalinsa kan hanya.
Zayd yana ta zuba maganganu yana yaba Amal kamar wanda ya gano wani abu na musamman.
Shi kuma Maleekh ba ya cewa komai.
Sai dai idanunsa suna ƙara yin ja saboda haushin maganganun Zayd, zuciyarsa na ƙonewa cikin silent fire.
Sai kawai ya murɗa accelerator, motar ta yi wani irin gudu kamar yana zubar da ɓacin rai cikin gudun...
Zayd ya ɗan tsaya yana kallonsa, ya ce da dariya:
“Bros… wai kai ba ka ganin irin yadda Amal take kyakkyawa ne? Ai ba a barta haka kawai ba.”
Maleekh ya ɗan yi murmushi mai sanyi, wanda bai nuna farin ciki ba.
Ya ce cikin wata murya mai sanyi da raɗa:
“Ka cigaba da yaba ta, Zayd… kai dai ka tabbatar baka makara a aiki gobe ba.”
Shiru ya rufe motar. Zayd bai fahimci nauyin kalaman ba, ya cigaba da hira, yayin da Maleekh zuciyarsa ke tafasa cikin silent jealousy...
_AMAL_
Ta riƙe sitiyarin da hannayenta biyu kamar mai gudun kada zuciyarta ta tsinke.
Tun lokacin da ta hango Maleekh a reception, har lokacin da ya haura saman escalator ba tare da ya yi mata magana ba, zuciyarta ta kasa natsuwa.
“Ya kalle ni… amma ya ɗauke kai. Ya jinjina kai kamar wanda ya gama da ni. Amma shin da gaske ya gama da ni? Har yanzu idanunsa sun cika da soyayya ta… na gani, na ji. Zuciyata ta ce haka. Amma me ya sa yake ƙoƙarin nuna babu ni a ransa?”
Ta hura iska mai zafi, idonta ya ɗan kaɗa da hawaye.
“Wannan sabon ma'aikacin fa?, Zayd… yana ƙirana da pretty kamar yana wasa... Bai san darajar sunan pretty a zuciyar Maleekh ba. Sunan da nake adanawa cikin zuciyata a matsayin sirri na soyayya. Amma yanzu? Zai zama abin dariya ne? Maleekh ya ji? Ya ji ana ƙirana da pretty? Ya ji, na san ya ji… amma bai ce komai ba. Shiru ya fi komai ciwo.”
Ta girgiza kanta da sauri tana ƙoƙarin daurewa...zuciyarta ne ya fara magana da cewa:
“Amal, ki nutsu. Wannan company aikin ki ne, ba wurin soyayya ba. Ki bar komai ga Allah.”
Sai ta ɗaga idonta, ta share hawayen da ya fito.
Sai dai duk da haka, zuciyarta na ci gaba da bugawa da irin ƙarfi da ta fi jurewa… saboda har yanzu Maleekh ne kaɗai burinta da farin cikinta...
Suna shigowa bakin ƙofar falo Farha ta nufo su da murmushi a fuskarta. Tana sanye cikin doguwar riga mai walƙiya, ta riƙe jakarta kamar wacce ta fito daga party. Da zarar ta hango Maleekh, ta miƙe da sauri ta tareshi, tana gyara gaban rigarsa tana cewa:
"Sannu da dawowa Ya Maleekh, Allah ya ƙara lafiya."
Maleekh ya ɗan ja gefe yana ƙoƙarin kaucewa hannunta, cikin dannewar takaicin da ke cinsa. Duk da haka, ya daure fuskarsa saboda yana jin nauyin yayanta Zayd, wanda ke tsaye a gefensa yana kallon komai.
Zayd ya zaro ido tare da dariya ya ce:
"Uhmm, soyayya kenan fa ta tashi. To Yaya Maleekh, kai dai ka ce zaka jira fiancé ɗinka?.."
Sai ya ɗan buga kafaɗar Maleekh cikin zolaya.
Farha ta yi wani irin kallo, idonta ya ƙanƙance kamar za ta cinye shi. Ta ce cikin tsawa:
"Haba Yaya! Wace fiancé kuma? Karka yi wasa da irin wannan magana a gabana fa!"
Zayd ya yi dariya ya ɗaga hannunsa:
"Ooops, sorry sorry sorry my sweet sis. Na manta baki son irin wannan zolayar… Amma albishirinki.."
Farha ta ɗan sassauta fuska, tana jinjina kai cikin jin daɗi:
"Goro fari tasss, albishir ɗin me?"
Zayd ya zaro idanu tare da murmushi mai ɗauke da annashuwa:
"Nayi gamo da wata pretty, Farha! Wallahi in kin ganta kamar aljana tsabar kyau. Kin san irin kyawun ‘yan India? To, ta wuce su gaba ɗaya."
Ya yi ƙaramar shiru kamar yana sake jin yadda Amal ta tsaya a gabansa a reception.
Maleekh kuwa ya tsaya daga gefe yana kallonsa da idon da ke iya fashewa da wuta, amma ya danne komai, ya wuce da sauri ya haura sama part ɗinsa bayan ya yi gaisuwa da Ammy.
Ƙannensa suka taru da murmushi suna yi masa sannu da zuwa, amma zuciyar Maleekh babu inda take sai a wajen Amal da kalaman Zayd.
Ammy kuwa, jin daɗin hirar ya ɓace mata, zuciyarta ta tsinke da sauri. Ta kalli Islam da ke gefenta, tana murmushi amma a zuciyarta tana tunanin:
"Wayyo Allah, wannan labarin 'pretty' bai yi min daɗi ba. Ni dai burina Islam ta zauna da Zayd, amma idan aka ce ya kama wata daban fa?.. Hmm…"
A gefe kuma, Farha ta tattara baƙin cikin rashin jin daɗi, ta kalli Zayd da harara:
"Yaya, wai ka haɗu da wata kuma?.."
Zayd ya ɗan yi dariya mai sauti yana ɗaga hannunsa sama kamar mai rantsuwa:
"Eh mana, ba wasa nake ba. In kin ganta kin ga kamar aljanar gaske ce ta bayyana.. Wallahi pretty ce, Farha."
Farha ta ce tana haɗa rai:
"Kai dai kawai, zan ga yadda wannan maganar ka zata ƙare."...
Farha ta juyo tana kallon Ammy domin suna son haɗa soyayyar Zayd da Islam.
Duk da Islam bata jin wani soyayya a ranta kuma bata san ana wannan haɗin ba...
(To pah Farha, kema yaushe soyayyarki ta settling balle ku seta soyayyar wasu 🤣🤣, Su Hajiya Ammy da duk kan alamu fa Zayd ya fiki bariki..😅😅..)..
To masu karatu sai NEXTTT...
asmeetahwriter✍️
*🎤AMALEEKH🎤*
*AMAL AND MALEEKH*
Together, they stand between love and loyalty, between public duty and private longing, two hearts bound by fate, yet tested by truth.
*Writing and Storytelling By*
Asma'u Muhammad Auwal
Asmeetah writer
*HASKEN JAJIRTATTU*
*MARUBUCIYAR:*
*Matar Damisa*
*My Enemy*
*Hasken Ruhi*
*And know AMALEEKH*
Bauchi State Nigeria.
*WhatsApp 09065443871*
Follow my channel 👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
"Jajirtattu mu ne ƙarfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faɗuwa. Mu ne tarihi da ake ginawa!" 💪🔥✨
BOOK ONE page 47 to 48
🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹
🌹🌹
🌹
Maleekh ne ya rufe ƙofar ɗakinsa a hankali, ya jingina bayansa da ƙofar yana riƙe da kirjinsa da hannayensa biyu. Numfashinsa ya ɗauki nauyi, zuciyarsa na bugawa kamar ƙarar gangar yaƙi.
Ya taka a hankali zuwa jikin gilasan window, ya zuba ido waje yana kallon sararin sama. Fitilun gari suna walƙiya amma idanunsa sun rufe da hazo na baƙin ciki.
A zuciyarsa ya ce:
"Zayd… pretty… Amal. Wannan sunan har yanzu ba ya barin kunnena. Ashe ita ce wacce ya haɗu da ita? Ita ce yake cewa kamar aljana tsabar kyau?.."
Ya girgiza kai da ƙarfi, yana ƙoƙarin danne hawayen da suka cika idanuwansa.
"Ni na furta mata bana sonta, na koreta daga rayuwata… Amma yau zuciyata ta tabbatar min ban taɓa son kowa irin ta ba. Duk da na yi ƙoƙari in kore ta daga zuciyata, amma ganin Zayd yana kiranta da pretty… Ya Allah, yaushe wannan ciwon zai daina cin raina?.."
Ya tafi ya zauna a gefen gado, ya jingina kansa da tafukan hannunsa, yana ƙoƙarin hana hawayen sauƙa. Amma hawayen ya ƙi tsayawa, ya gangaro yana shigar masa da zafi kamar wuta.
A wancan lokacin, ƙarar dariyar Zayd daga ƙasa ta sake taso masa a kunne, kamar an kunna masa kaset. Wannan dariyar ta cika masa zuciya da kishi da ɓacin rai.
Sai kawai ya daki tebur da ƙarfi, ya furta a hankali cikin rawar murya:
"Amal… pretty ɗin Zayd… wallahi wannan abu ba zai yiwu ba."
Washe gari tun safe, babban harabar CashTalk Empire Holdings ta cika da ɗaukakar jama’a. An kawata wurin da flowers masu kyau, ana kunna kiɗa mai laushi a gefe. Fitilun gilasa na haskawa suna ba da hoton kamfani mai ƙima da daraja.
Manyan baƙi daga ƙasashen waje sun iso cikin manyan motoci masu sheƙi. Ana tare su da farin cikin manyan jami’an company.
Maleekh ya fito cikin suit baƙi da red tie da ya kara masa ƙwarin girmamawa. Fuskarshi cike take da kalar nutsuwa, ko da zuciyarsa na tafasa, bai bari kowa ya hango hakan ba.
A gefe kuwa Amal ce ta biyo shi, sanye da skirt suit navy blue mai matuƙar kyau. A daidai wannan rana dukkan ma’aikata sun tabbatar da cewa ta cancanci matsayinta na assistant CEO. Duk da kalar gajiya a idanunta, kwarjini da kyan tafiyarta ya zame musu abin sha’awa.
Zayd kuma cikin farin ciki yake ta shawagi a wajen, yana ɗan tsokanar Amal cikin sirrin murya:
“Pretty, idan kika tsaya gefe, to kowa zai ce kina ɗauke da kyakkyawar kwalliya fiye da CEO ɗin kansa. Kar ki barni na rikice.”
Amal ta dube shi da idanu masu sanyi, ta ɗan harare shi a hankali, sannan ta matsa gefe. Amma duk wanda ya kalla ya fahimci ba ta ɗaukar abin da yake cewa da muhimmanci.
Maleekh da kansa ya gabatar da su a gaban baƙi:
“Wannan ita ce Assistant CEO, Amal Abdulsamaad, tana kula da aikace-aikacen da ke hannun shugabanci... Wannan kuwa shine younger brother ɗina, Zayd, wanda ya dawo domin cigaba da aiki tare da mu a nan company. .”
Baƙin suka yi mamaki da yabawa. Wani daga cikin su ya ce:
“Wannan company tana da hazikan matasa. It’s a pride to invest here.”
Ana haka aka shiga babban hall ɗin taro. Tables sun jera, projectors suna nuna hotuna da bayanan nasarorin company. Maleekh ya tsaya yana gabatar da jawabi cikin harshen Turanci, yana nuna sabbin shirye-shiryen da zasu ƙara bunƙasa hannun jari.
A yayin da yake magana, idanunsa na kai ga Amal a gefe ba tare da kowa ya lura ba. Sai dai kowane lokaci idan ya hango Zayd yana yi mata magana ko murmushi, zuciyarsa ta sake yi masa raɗaɗin kishi.
A ƙarshe bayan an gama taro, baƙin sun tsaya suna tattaunawa da ma’aikata daban-daban. Wani babban baƙo ya matso ya kalli Amal da murmushi sannan ya ce:
“Young lady, you really impressed me. You have a bright future in this industry.”
Amal ta yi murmushi cikin ladabi ta ce:
“Thank you, sir.”
Zayd kuwa yana tsaye a gefenta yana faɗin:
“Of course sir, she is more than just impressive… she is my pretty.”
Baƙon ya yi dariya, ya ɗauki abin a wasa. Amma Maleekh da ke gefe sai ya matse yatsunsa da ƙarfi, yana ɓoye zafin zuciya cikin annashuwa.
An jera baƙi a babban hall, manyan keken Turawa da wasu manyan ‘yan kasuwa daga ƙasar waje suna zaune cikin nutsuwa. An yi musu hidima sosai aka jera musu juice da snacks a kan teburori masu sheƙi.
Sai ga Farha ta shigo. Ta sha kwalliya fiye da yadda aka saba ganin ta, fuska ta cika da powder, jan baki ya ƙara mata ɗaukar ido, riga da siket masu sheƙi sun matse jikinta kamar yadda ta saba. Da sallama ta gaisa da baƙin, ta yi murmushin ƙarfin hali.
Bata tsaya ko
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 32 Chapter of 62