ya gama nasara,
Amal ta tsaya cak, zuciyarta tana bugawa ta ce
“Meyasa ku ka yi haka ba tare da kun sanar mun ba?”
A'isha ta ce "unsuspecting ne ai..."
A fusace Amal ta ɗauki kayayyakin da aka siya, ta nufi inda yake. Tana isa ta watsa kayayyakin a gabansa, wasu suka bugu akan fuskar sa.
Cikin fushi, da murya mai ƙarfi take cewa
“Ka fita daga rayuwata, Maleekh! Ban sonka, bana kuma son abinda ya fito daga hannunka!”
Wurin ya cika da mutane suna kallo. Wasu suna mamaki, wasu suna kwaɗaituwa da magana...
A’isha ta ɗaure fuska, zuciyarta na tafarfasa ta ce
“Amal! Ki daina wannan rashin mutuncin a bainar jama’a!”
Amal ta ce
"To dole ne? dole ne sai yayi rayuwa dani?..."
Ta kalli Maleekh tana nuna masa yatsa ta ce
"Kana ji ba, ka saurare ni, kana tunanin kaci nasara ne akan soyayyata? fitowa television da kayi ba shine yake nuna cewa na amince da kai ba, saboda haka join yourself..."
Maleekh ne ya kamo hannunta da ƙarfi yana faɗin.
"Wallahi sai kin Aure ni dole..."
Yana ƙoƙarin sanya mata wani zoben gold a yatsanta, wanda haka na nufin ƙarfafa soyayya...
Kokuwar janye hannunta take tana faɗin
"Ka sakar mun hannu nace, Maleekh..."
Da ƙarfi ta janye hannunta daga riƙon da yayi mata, cikin ɗaga murya ta ce
"I said join yourself..." ta tafka masa wani irin gigitaccen mari.......Har sai da ya karkatar da wuyansa tare da kama wurin marin da hannu, yana mata kallon mamaki...."
Amal idonta a cikin nasa tana kuka domin bata so ta mare shi ba..
Kowa ya firgita da ganin wannan al'ajabin...
A'isha dake gefe sakin baki tayi tana kallon ikon Allah..
Jama'a kuwa sun daɗe suna ɗaukar video...
PA ɗin Maleekh ne ya nufi Amal yana zagin ta da cewa
“Ke wace irin yarinya ce? wacece ke har zaki ci mutuncin Boss ɗina haka a gaban mutane? Ke ba kya da hankali ne?”
Maleekh ne ya juyo da sauri, ya ɗaga hannu ya zabga wa PA mari yana huci cikin fushi ya ce
“Kaɗan ya rage in kore ka! Waye kai da zaka ɗaga mata murya? Ka sani kamar yadda nake a matsayin Boss ɗinka, Amal ita ma Madam ɗinka ce. Ka girmama ta!”
PA ya sunkuyar da kai yana bashi haƙuri....
Sannan Maleekh ya maido da idonsa kan Amal, cikin fushi ya dam'ko hannunta cikin ɗaga murya ya ce
"Ko ki soni, ko kar ki soni wannan ya rage naki, zan tafi dake dole sai kin soni..."
Ya fara jan ta zai shigar da ita mota, a lokacin Amal ta fara ihu tana neman taimako..
"Ka sake ni, ka sakar mun hannu nace bana sonka, ka sake ni Maleekh..."
A'isha ce ta buɗi baki ta ce
"Ina zaka kaita Yaya?..."
Wasu matasa ne ƴan daba su biyar suka sha gaban Maleekh suna faɗin
"Ina zaka kaita, a gaban mu zaka sace ta? ashe ma bata sonka har da fitowa gaban tv kana zayyana soyayya?..."
Maleekh cikin fushi ya ce "su waye ku? ku matsa mun daga kan hanya..."
"Matasan suka ce
"Baza ka tafi da ita ba..."
Maleekh ya ce "Ku dakatar dani idan kun isa..."
Ai kuwa Matasan nan suka afko masa, Maleekh ne ya sakar wa Amal hannu tare da tinkarar su, nan take suka fara gwabzawa, matasa su biyar suka rufu masa, shima Maleekh haka yake kai musu naushi, duk wanda ya samu a cikinsu zai kaiwa naushi....
Ganin haka yasa PA ɗinsa shiga masa, shima PA haka yake kai musu duka, mutum biyu suka haɗu wa PA, mutum uku kuma akan Maleekh...
A'isha ba abinda take sai ihu tana faɗin
"Wayyo Allah zasu kashe mun Ɗan uwa, taimako jama'aaaa...."
Amal kuwa gaba ɗaya ta rikice, ba abinda take sai kuka, tana so ta dakatar da mutanen amma ta kasa...
Kafin sai ga motar security Maleekh da ta police, a nan aka raba su, a fusace Maleekh ya ciri bindiga daga aljihun ɗaya daga cikin security sa ya kunna kunamar bindigar yana shirin harbe su...
Wani ɗan sanda ya riƙe shi yana bashi haƙuri...
Ga yanda suka fasa masa lips ɗin baki, duk da suma matasan sun ji jiki, domin ba ƙaramin naushi suka sha a wurin Maleekh ba, duk da su uku ne amma haka suka kasa kayar da Maleekh, haka shima PA ɗinsa ya nuna jarumta sosai domin duka yayi wa sauran biyun da suka yi kansa...
Ƴan sandan ne suka kama matasan duk suka sa musu ankwa, za'a kulle su...
Maleekh kuwa Security sa ne suka shigar da shi mota suka tafi...
Amal da gudu ta tari napep ta koma gida a tsorace, bata ma lura da zoben da ya sa mata ba, sai sheƙi yake a hannunta....
A'isha kuwa itama motarta ta shiga a tsorace tabi bayan motar su Maleekh...
🌹 Page 15–16 ends here 🌹
asmeetahwriter✍️
*🎤AMALEEKH🎤*
*AMAL AND MALEEKH*
Together, they stand between love and loyalty, between public duty and private longing, two hearts bound by fate, yet tested by truth.
*Writing and Storytelling By*
Asma'u Muhammad Auwal
Asmeetah writer
*HASKEN JAJIRTATTU*
*MARUBUCIYAR:*
*Matar Damisa*
*My Enemy*
*Hasken Ruhi*
*And know AMALEEKH*
Bauchi State Nigeria.
*WhatsApp 09065443871*
Follow my channel 👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
"Jajirtattu mu ne ƙarfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faɗuwa. Mu ne tarihi da ake ginawa!" 💪🔥✨
BOOK ONE page 17 to 18
🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹
🌹🌹
🌹
Maleekh yana zaune a motar zuciyarsa na tafasa a yayin da PA ɗin sa yake driving...
Ga wasu motocin security a tafe a bayansu..
Maleekh ya lumshe idanu yana faɗi a hankali cikin rawar murya ga lips a fashe sai ɗigar da jini yake..
“Duk abinda tayi min zan rama. Amma sai soyayyata ta mallake ta gaba ɗaya kafin ta san irin azabar da zata fuskanta.”
PA ya jinjina kai yana ƙara zuga shi da cewa
“Boss, yarinyar nan ba ƙaramin raina ka tayi ba. Lokacin fansa ne kawai ya rage.”
Maleekh ya yi murmushi mai cike da takaici da mugunta, yana shirin sabuwar dabarar da zai ɗauka a kan Amal…
Tin a napep Amal ta lura da zoben da Amal ya sanya mata da ƙarfi, ɗago hannunta tayi tana kallon zoben sai sheƙi yake, ga wasu zafafan hawaye dake zubo mata...
Amal na dawowa gida, zuciyarta ta rikice tamkar an jefa ta cikin ramin da babu mafita. Tana shiga ɗakinta ta rufe da karfi tare da sakale sakata, ta sulale a ƙasa tana kukan da ya huda zuciya. Hannayenta na rufe akan fuska, zuciyarta na bugawa da sauri, tana jin nadamar yadda ta wulakanta Maleekh a gaban duniya.
Cikin kuka take faɗin
"Me yasa na bari masifar zuciyata ta rinjaye ni? Me yasa na zubar da mutuncinsa haka?” Ta tambayi kanta cikin kuka...
Amma duk da haka, wani ɓangare na zuciyarta ya ƙi yarda da cewa kuskure ne, sai cewa tayi a fili
“Zan cigaba da gwada shi har sai na tabbatar da gaskiyar soyayyarsa. Idan ya fita daga rayuwata saboda wannan, to shi ba nawa bane.”....
A gefe guda kuwa, Maleekh ya koma cikin duniyar gidansa cikin bacin rai. Zuciyarsa ta ƙone da wuta..
Bayan ya shiga falonsa, ya zauna a kujerarsar falon, sai sauƙe numfashi yake yi tamkar wanda aka ɗora masa wani nauyi...
Ya jan yo shisha gabansa, yana zuƙar hayaƙi tamkar yana neman mafita daga rantaƙiyar da ke ci masa zuciya. Idanunshi sun sauya launi, wani yanayi na ɗacin rai yana wanzuwa masa..
A fizge yake faɗin
"Amal… wannan wulakanci ba zai tafi a banza ba. sai na nuna miki kuskuren da kika fara tin farko har zuwa yanzu...”
Yana raba hayaƙi, fuskarsa kamar wanda aka watsa wa tafashashshen ruwan zafi...
《☆☆☆》
Bayan kwana biyu
A Abuja, gidan su Maleekh.
Farha tana kwance a kan tsararren gadonta, ta kifa kanta sai sharar kuka take, zuciyarta na ƙuna da kishin da ya kasa boyuwa...
Sai ga ƙofar ɗakin ya buɗe a hankali, Hajiyar gidan wanda duk gidan ke ƙiran ta da Ammy, mahaifiyar Maleekh kenam, ta shigo cikin nutsuwa. Tana sanye da kayan alfarma, kyakkyawar mata mai cike da ƙima da isa..
Ta zauna a bakin gadon, ta dafa kafaɗar Farha cikin lallashi...
“Meye amfanin kukan nan, Farha?” Ammy ta tambaya cikin murya mai taushi mai cike da iko..
Farha ta ɗago da idanunta da suka yi ja, kuka ya sa sun kumbura, ta ce cikin karyayyen murya.
“Haba Ammy! Baki ga abin kunyar da Maleekh ya jawo mana ba? Yana fitowa a television yana yayata soyayyar wata matsiyaciyar yarinya, ƴar talaka marar gata! Wannan ba mutuncinsa bane…”
Ta fashe da wani sabon kuka tana girgiza kai, sannan ta cigaba da magana cikin zafin rai.
“Ammy, ya zanyi da soyayyarsa? Har yanzu yaƙi kallona a matsayin masoyiyarsa, yaƙi saurarona, kuma nasan saboda waccan yarinyar yaƙi dawowa daga Kaduna. Wallahi idan baki aura mun Maleekh ba, mutuwa zanyi!”
Ammy ta sauƙe dogon numfashi, tana kallon Farha da idanun ta cike da wani irin haske na muguwar natsuwa. Ta ɗan yi shiru, sannan ta furta
“Ki kwantar da hankalinki, Farha. Bazan taɓa barin Maleekh ya auri wata matsiyaciyar yarinya ba. Na miki alƙawarin Maleekh naki ne, kuma zan aura miki shi.”
Farha ta share hawayenta da sauri, tana kallon Ammy da wani irin hope ta ce.
“Ammy… amma ba ya sona fa. Ko kallona baya yi…”
Ammy ta ɗaga gira, ta murmusa da irin murmushin mace mai cike da shirin da babu wanda ya iya fassara shi, sannan ta ce
“Dole zai soki, Farha. Zan sa ya dawo daga can Kaduna, kuma da kansa zaki ga yadda zai fuskanci soyayyarki. Ba zai ƙi umarnina ba.”
Farha ta rungume Ammy da sauri, hawaye suna sake zubo mata amma wannan karon hawaye ne na begen cikar burinta....
Farha yarinyar ƙanwar Ammy ce, iyayenta da ita suna zaune a ƙasar London, ita farha ta dawo Nigeria ne saboda Maleekh, tana zaune a gidansu a gaban Ammy..
Suna zaune Ammy da Farha sai ga Arfat ƙanwar Maleekh ta shigo da gudu tana kwallawa Ammy ƙira
“Ammy! Ammy!!”
Ammy ta zabura ta kalleta, zuciyarta na bugawa cikin firgici ta ce
“Meya faruwa ne haka, Arfat? Wannan irin ƙiran fa sai ki tsoratar da mutum!”
Arfat ta fitar da numfashi kamar wanda tayi gudun kilo mita hamsin, tana zufa tana huci ta ce
“Ammy, zo kiga television… Yaya Maleekh ake nunawa! Budurwa ta mare shi a bainar jama’a, ta wulakanta shi sannan tasa yayi faɗa da wasu matasa. Kamar ya ji ciwo!”
Da gudu Ammy ta miƙe, Farha ma ta miƙe duk suka fice zuwa babban falo inda television ke kunne...
A can kuwa rahoton yana ci gaba. An nuna video Amal ta ɗaga hannunta, ta zabga mari a fuskar Maleekh a gaban jama’a, da irin wulakancin da ta masa..
Gari ya ɗauki zafi. Kaduna ta kaure da maganganu. Duk inda aka shiga sai a ji ana maganar “Wai Amal ta mari ɗan gidan minister Alhaji Abdul-majeed a bainar jama’a!”
Anata posting a social media, hotunan sun bazu fiye da yanda ake tsammani..
Maleekh, a ɗaki ya jingina da kujerarsa, idanunsa sun kaɗa sunyi jaa, yana kallon television. Ganin yadda Amal ta mare shi duba da ƙarancin asalinta, hakan ya sa ya rafka uban harara, zuciyarsa na tafarfasa kamar wuta. Ya riƙe sumar kansa yana cukurkudawa, kamar zai haukace da kunyar da aka jawo masa.
Amal kuwa a ɗakinta a Kaduna, ta shagaltu da damuwa. Kuka ne kawai ke tserewa daga idanunta, saboda ta san duniya ta fara kallonta da ido ɗaya, suna tallata wannan abin kunya da ita da Maleekh.
A Abuja, Alhaji Abdulmajeed mahaifin Maleekh, yana zaune a ofis ɗinsa, an kawo masa rahoton. Yana ganin hoton yadda mace ta sa hannu ta mari ɗansa a bainar jama’a, ransa ya yi matuƙar ɓaci...
Ammy ma ta ji tamkar ta haɗiye ranta saboda takaici. Farha kuwa ta daure ta furta cikin ƙiyayya.
“Ammy, yanzu da ni nayi masa haka, kin san ba zan kwana da ƙafafuna ba. Da ya kakkarya ni tun a wurin! Amma ga matsiyaciyar yarinya ta mareshi a bainar jama’a, kuma sannan ya sharar da ita. Har da faɗa saboda ita!”
Ammy tana cikin tsananin fushi, hannunta na rawa saboda takaici. Ta kasa furta komai...
A ɓangaren Mahaifinsa dake office.
A fusace ya ɗauki wayarsa, ya ƙira lambar Maleekh.
A ɗayan ɓangaren, Maleekh ya ɗauki ƙiran da muryar da ta sha bamban, kamar wanda ya yi shaye-shaye. Ya ce
“Hello, Abba…”
Abba bai tsaya gaisawa ba. Da murya mai nauyi ya ce.
“Inaso ka dawo Abuja yau ɗinnan. Kada ka ƙara kwana a Kaduna.”
Maleekh ya lumshe idanu, ya sauƙe ajiyar zuciya sannan ya ce
“Na ji, Abba…”
Ya amsa a taƙaice, zuciyarsa na nuni da cewa daga wannan rana lamarin zai ɗauki sabon salo....
Maleekh yana jingine da kujera, hannunsa na riƙe da wayar da ya gama magana da mahaifinsa. Zuciyarsa ta cika da tsananin fushi, amma fuskar sa ta nuna sanyin jiki..
Ya ɗaga shisharsa ya shaƙi iska mai ƙamshi, ya sauƙe ta cikin takaici yana faɗin
“Kaduna… ban shirya barin cikinki ba saboda ban gama aiki akan Amal ba. Amma yanzu Abba ya ƙira ni, dole sai na koma Abuja.”
Ya juya yana kallon PA ɗinsa, wanda ya tsaya a gefe yana huci shima.
Maleekh ya ce
“Ka shirya kayana. Ba zan ƙara kwana a nan ba. Abuja na jira.”
PA ɗinsa ya yi shiru na ɗan lokaci, sai ya ce cikin ɗan ɗaga murya
“Boss, wannan yarinyar ta raina mu sosai. Wallahi ban taɓa ganin mace ta yi maka irin wannan ba… me za ka yi game da ita?”
Maleekh ya ɗan yi murmushi, murmushin da ya ƙunshi mugunta da takaici ya ce
“Ba yanzu ba. Amma zan nuna wa Amal bana yafiya. Da zarar na koma Abuja, za ku ga yanda zan karkatar da komai zuwa hannuna.”
Ya miƙe tsaye, ya nufi bedroom ɗinsa, PA ne yabi bayansa, yana shiga ya nufi wardrobe yana ɗaukar kaya masu tsada yana ajiye wa PA don shirya masa a jakunkuna.
Zuciyarsa ta yi nauyi sosai. Amal ta mare shi a bainar jama’a, abin da bai taɓa faruwa da shi ba tun da aka haife shi. Yanzu kuwa duniya ta gani, duniya ta yi sharhi. Kuma mahaifinsa ya ƙira shi da umarni mai zafi...
Ya tsaya a gaban madubi, ya kalli fuskar sa, saitin wurin da ta mare shi. Hannunsa ya ɗago a hankali ya taɓa fuskar, zuciyarsa ta cika da tsanar Amal...
“Amal…” ya furta cikin sirri. “Kin fara yaƙi, amma ni zan kawo ƙarshensa. Abuja ce matakin farko.”
Sai ya juya ya saka agogon hannunsa mai tsada, ya ɗauki wayarsa yana faɗin
“PA, ƙira min jirgin Abuja. Na fi son private jet ɗina ya jira ni kafin karfe biyu na rana.”
“Yes, Boss.” PA ɗin ya ce, yana bin shi da idanu, zuciyarsa na mamakin irin natsuwar da Boss ɗinsa yake nuna wa duk da irin wutar da yake ƙonewa a cikin zuciyarsa..
♡
Amal ta zuba wa wayarta ido, tana dubanta, ta kasa natsuwa. Kwana biyu kenan bata ji ƙiran Maleekh ba, bata kuma ga saƙonsa ba. Zuciyarta ta ƙara rikicewa, zuciya na ta bugawa kamar zata fito.
Ta jawo wayarta ta sake dubawa. Sai lambar A’isha ta faɗo mata a rai. Cikin tsoro da shakku ta danna ƙira.
A can ɓangaren A’isha kuwa, tana zaune taji wayar tana ringing. Takaici ya cika mata zuciya a fili take faɗin
“Amal ce? Wacce ta mari Yayana a gaban jama’a? Haka nan kuma duniya ke yi masa ba’a saboda ita?” Ta jinjina kai cikin ɓacin rai,
Ta ɗauki lokaci kafin ta ɗaga. A ƙarshe ta ɗauka tare da faɗin.
“Assalamu alaikum.”
Amal ta runtse idanu, muryarta na rawa ta ce
“Dan Allah A’isha kiyi haƙuri da abinda ya faru. Nasan bakiji daɗi ba…”
A’isha ta amsa cikin ƙunshi, tana ɗan sauƙe ajiyar zuciya ta ce
“Ba komai. Amma yanzu, meya faru ne?”
Amal ta yi shiru na ɗan lokaci, sannan ta furta cikin rauni.
“Maleekh ne… ban ji labarinsa ba, na damu sosai. Shin yana lafiya?”
A’isha ta yi dariya sannan ta kaɗa kai kamar tana magana da kanta...Ta ce
“Yanzu kuma Yaya Maleekh kike tambaya? Bayan wulakanta shi da kika yi a bainar jama’a? Haba Amal, kin bani mamaki. Kin san irin takaicin da iyayensa zasu ji akan wannan al'amarin? Taya kike tunanin zasu bar shi ya cigaba da zama a Kaduna bayan sun ga abinda kika masa? Ina mai miki fatan kada Allah yasa mahaifiyarsa ta biyo ki har nan kaduna domin tafi wuta ƙuna, saboda bala'inta yasa mahaifin mu ya raba musu gari da mahaifiyata, ita tana can Abuja da iyalanta, mahaifiyata kuma tana nan kaduna da mu, saboda bala'i kinga ko bikina mahaifiyarsa da ƙannensa basu zo ba sai iya Yaya Maleekh ne kawai ya ziyarci bikina, kin yi kuskure Amal .."
Zuciyar Amal ce ta karye, hawaye suka fara zubo mata. Tayi ƙasa da murya, tana jin kamar zuciyarta zata fashe ta ce
“Maleekh ya koma Abuja kenan…?”
A’isha ta lumshe idanu, ta amsa da taƙaice.
“Eh.”
Ba tare da ƙarin magana ba, ta kashe wayar.
Amal ta zube akan gado, kuka mai tsananin raɗaɗi ya kwace mata. Zuciyarta na tsananta da tambayoyi.
“Shin hakan me yake nufi kenan? Shin shikenan ya gudu daga gare ni saboda abin da na yi masa? Ko kuwa iyayensa ne suke ƙoƙarin rabani dashi?”
Inna ce ta shigo ɗakin, ganin Amal tana kuka yasa tayi ƙwafa ta ce "kaɗan kika gani, indai mutum wulakanci ya iya wata ran zai cusa barkono ne a tsuriyarsa ba tare da saninsa ba..."
Inna tayi tsaki bata ma son kallonta. Tun bayan abin da ya faru ta daina kula ta, domin a idanunta Amal ce ta jawo musu ƙasƙanci da tozarci...
ABUJA CITY
Maleekh ne yake zaune a bakin katafaren gadonsa dake cikin tsararren bedroom ɗin sa...
Yana sanye da short 3quarter da rigarsa mai gajeren hannu na shan iska.. shi kaɗai yasan irin tunanin da yake yi..
Bai san an buɗe ƙofar ɗakin bama tsabar yayi nisa a tunanin da yake.
Sai ji yayi an rufe ƙofar da ƙarfi, bugun ƙofar da akayi ne yasa ya dawo daga tunanin da ya zurfafa, sleepy eyes ɗinsa ya sauƙe akan mahaifiyarsa, wacce kallo ɗaya zaka mata kasan tana cikin fushi...
A tsawa ce ta fara faɗin.
"Maleekh! Wannan abinda kayi a Kaduna ai babban abin kunya ne. Haba! kai fa mutum ne babba, ɗan manya, ya za ka bari wata ‘yar talaka ta mare ka a bainar jama’a? A fuska fa? Ka sani kai ba kamar kowa bane."..
Maleekh yana ɗaure da fuska, ya ce
"Ammy, ba wai ban san darajata bane. Amma wallahi soyayya ce ta ruɗani. Ban taɓa ɗaukan Amal a matsayin ‘yar talaka ba. A idanuna… ita ce komai."
Ammy cikin jin haushi ta ce
"Komai? Komai har da wulakantaka a gaban mutane? Ka ji abin da kafafen yaɗa labarai suke ta yayatawa kuwa? Wannan ai abin kunya ne ga iyayenka. Ni fa ban yarda da wannan Amal ba, ba za ta taɓa zama matarka ba! Ga Farha wacce take masifar son ka amma ka ƙi ta gida kana ƙoƙarin jan yo mana magana..."
Maleekh yana huci, ya ɗan miƙe yana fuskantar Ammy ya ce
"Ammy, me yasa kullum sai Amal kike gani a matsayin barazana? Ta fi kowa gaskiya da amana! Ni dai ba zan iya auran Farha ba, ko da kin tilasta ni."
Ammy cikin ɗaga murya ta ce
" Farha ai ba irin waccan Amal ɗin bace matsiyaciya. Farha ‘Yar manya ce, ‘yar dattawa, ta girma kuma da tarbiya, za ta kare mutuncinka, ba wai ta zubar maka ba, Kuma duba iyayenta, za ka samu haɗin kai da amfanin ahali, Kai fa dole ne ka auri Farha!"..
Maleekh yana kallonta cikin rashin fahimtar abinda take nufi da dole sai ya Auri Farha, haka yake yatsina fuska ya ce
"Wallahi ba zan aure ta ba! Ni bana sonta, bana ma jin ko daɗin ganin ta. In har Ammy aure kike so, sai dai ki manta da ni. Soyayyata ta tsaya ne akan Amal, kuma ba zan canza ba!"
Daga nan Maleekh ya fice a ɗakin, da sauri yake sauƙa daga upstairs zuwa ƙasin falo, yana sauƙa ya zauna a kujerar falon yana fuskantar plasman...
Farha wacce fitowar sa kenam, ganin Maleekh yasa ta huce wurin ƙaton frig ta ɗauko juice da glass cup guda ɗaya, ta nufi cikin tsakiyar falon yanda yake zaune...
Farha ta shigo da murmushi, ta kawo masa juice tana faɗin
"Sannu Yaya Maleekh, na zo ne saboda Ammy ta ce kana cikin damuwa. Ka sha ruwa, ka huta."
Maleekh ya karɓi glass ɗin, ya ajiye shi ba tare da ya sha ba ya ce
"Farha, kin dai san bana buƙatar wannan kulawar da kike yi. Me ya sa baza kiyi zuciya ki daina zuwa gidan nan ba? ya kamata ki koma Ƙasar da kika fito, zai fi kyau ki zauna a gaban iyayenki, Ni bana sonki, bana son wannan abokantaka ma."...
Farha ranta ne ya ɓaci, amma tana ƙoƙarin yin murmushi domin danne ɓacin ran, ta ce
"Ban yi zaton zaka furta haka ba a fili, Yaya Maleekh. Inda kara ai nan gidan ma gidan iyayena ne, tinda Ammy Yayar mahaifiyata ce, maganar soyayya kuma na ɗauka lokaci ne kawai zaka buƙata domin yin tunani akan soyayyata...."
Maleekh yana kallonta cikin tsana ya ce
"Lokaci? Ko shekara ɗari ne ba zan canza ra’ayina ba. Ni bana sonki Farha. Don Allah ki bar cikin rayuwata. Kar ki takura ni, kar ki takura kanki."
Ammy wacce sauƙowar ta daga upstairs kenam ta ce
"Maleekh! Yanzu duniya tana magana ne akan wannan Amal ɗin. Me yasa kake ƙara damuwa a kanta? Ka manta da waccan yarinyar, ka zaɓi Farha ka huta."..
Maleekh fuska a ɗaure, yana danna wayarsa ya ce
"Ammy, sau nawa kike so na faɗa miki ne? Ba ni da wata mace sai Amal. Ko duk duniya ta tsaneta, ni ba zan ƙi ta ba. Ba zan iya rabuwa da ita ba."
Farha tana kallonsa cikin hawaye ta ce
"Ni fa ban taɓa jin ciwo irin haka ba, Yaya Maleekh. Amma me Amal ta baka da har ka manta da mutuncin kanka?"
Maleekh yana murmushi ya ce
"Amal ta bani abin da ba ku fahimta ba, soyayya ta gaskiya. Kuma duk abinda zaku ce, wallahi bazan taɓa sakinta."
Ya miƙe cikin fushi ya fita daga falon, yana tafe cikin izza, ya bar su cikin bacin rai, kai tsaye waje yayi ya nufi wurin parking motoci, kafin ya isa ya matsa key ɗin motar da zai shiga nan take ƙofar motar ta buɗe, shiga yayi a ɗari ya bi hanyar da zai kai shi get.
Mai gadi ne yayi saurin buɗe masa ya bar gidan gaba ɗaya, cikin ƙananun kaya na shan iska...
A Kaduna... Bayan wata guda..
Amal tana juya zuciyarta, tana kai-komo tsakanin tsoro da ƙauna. Duk lokacin da ta tuna da fushin Maleekh da kuma shiru da ya yi mata, sai zuciyarta ta cika da kunci. A ƙarshe ta yanke hukuncin cewa ba zata iya ci gaba da hukunta kanta ba...
Ta sanar wa Inna cewa zata je Abuja...
Inna a firgice ta dafa kirjinta tana faɗin:
"Abuja dai? Uban me zakiyi acan, garin manyan mutane zaki dosa?... Amal kin san garin bana wasa bane..."
Amal ta ɗago ido cikin nutsuwa ta ce:
"Inna, babu abinda zai faru. Ni addu’arki kawai nake nema. Ba don komai ba, sai don zuciyata ta huta daga wannan azabar shirun."
Inna ta juya kai, hawaye suna cika a idonta. Tana kallon jikar tata mai ƙaramin hali da girman zuciya. Cikin taushin murya ta ce:
"To Allah ya kare mun ke Amatullah. Ki sani ba ki da wani gata sai addu’ata. Ki kula sosai… Amma nasan Maleekh ɗin zaiji daɗin ganin ki."
Amal ta jingina kanta a kafaɗar Inna, tana jin wani irin ƙarfin hali ya mamaye ta...
Da Asuba bayan ta idar da sallah, already ta kammala shiryawar ta...
Ta shirya tafiya. Ƴan kuɗaɗen da ta daɗe tana ajiye su, ta raba gida biyu. Rabi ta ba Inna, tana faɗin:
"Inna, wannan ki riƙe, ko kayan abinci ya ƙare, ko wata buƙata ta taso, za ki samu. Ba daɗewa zan yi ba, iya kwana ɗaya ne kawai."
Inna ta karɓa cikin jinƙai, zuciyarta cike da addu’a.
Ƙarshen rabin kuɗin kuma Amal ta tanada shi domin kuɗin mota da ƙananan buƙatu.
Ta ɗauki jaka ta rataya a kafaɗarta, ta zuba ido tana kallon Inna da murmushin dole.
Ta ce
"Inna, ni
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 62