kika san cewa ni ce fiancée ɗin Maleekh.”
Farha ta ɗago hannayenta sama ta ɗora akan Amal sannan ta ce.
“Nayi miki alkawari Amal. Wallahi ba zan faɗa wa kowa ba. Wannan sirri ne a tsakaninmu.”
Yanayin ya sauya daga damuwa zuwa fara’a. Inna ta ɗan sake fuska, Amal ta yi murmushi...
Farha ta share hawayenta cikin dariya ta ce.
“To, yanzu bari mu koma magana ta bikin. Ya labarin anko ne? Don naga ana ta shiri sosai.”
Amal ta yi dariya cikin salo.
“Ku ai a ɓangaren maza kuke, ni kuma ban da wasu kawaye balle nayi maganar anko…”
Farha ta kwaɗaita idanu sannan ta ce.
“Da ke kawai za’a iya yin anko fa! Ni zan miki odar ankon daga Dubai, ko ya kika gani?”
Amal ta yi murmushi, ta dafa kafaɗarta ta ce.
“Ki bar wannan sai gobe, zan gaya miki irin launin da nake so. Yau dai naji daɗin ganinki.”
Farha ta ɗan miƙe da murmushi itama ta ce.
“Ni ma Amal. Na gode da yafiya, Allah ya albarkaci bikin ku.”
Ta rungumi Amal a karo na ƙarshe. Inna ta ɗan amsa mata da murmushi mai nauyi, sannan ta rakata har ƙofar get. Lokacin da Farha ta tafi, Inna ta juya ta kalli Amal da nutsuwa, tace:
“Kin ga yadda komai yake dawowa daidai. Allah yana da tafarkin sa.”
Amal ta yi shiru tana kallon ƙofar da Farha ta fita.
“Eh Inna… amma har yanzu zuciyata tana jin tsoron abinda ke tafe.”...
Farha tana cikin motarta zuwa gida..
Sai tunani take tayi akan maganar da taji iyayenta suke akai, cewar "za'a kashe Amal. Sannan su sukayi silar hatsarin Amal, to meyasa suke neman rayuwarta?..."
Wannan tambayoyin sun tsaya mata a rai..
_NEXT NEXT NEXT_
asmeetahwriter✍️
*🎤AMALEEKH🎤*
*AMAL AND MALEEKH*
Together, they stand between love and loyalty, between public duty and private longing, two hearts bound by fate, yet tested by truth.
*Writing and Storytelling By*
Asma'u Muhammad Auwal
Asmeetah writer
*HASKEN JAJIRTATTU*
*MARUBUCIYAR:*
*Matar Damisa*
*My Enemy*
*Hasken Ruhi*
*And know AMALEEKH*
Bauchi State Nigeria.
*WhatsApp 09065443871*
Follow my channel 👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
"Jajirtattu mu ne ƙarfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faɗuwa. Mu ne tarihi da ake ginawa!" 💪🔥✨
BOOK ONE page 71 to 72
🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹
🌹🌹
🌹
Ranar Alhamis da safe a gidansu Maleekh.
Ranar ta fara da motsin ma’aikata, sautin “sweep! sweep!” na tsabtace gidan yana tashi a ko’ina. Gaba ɗaya gidan ya canza kalar sa, ga sabon fenti ya ratsa bango.
A jikin bango an rataye hoton Maleekh da Amal, wanda aka tsara cikin kwali mai tsada, an rubuta a ƙasa:
“Forever Begins Here A&M.”
Sabbin kayan alatu daga Dubai sun cika falon. Kujeru masu launin royal blue, tagogi sun ɗauki labulen silk masu sheƙi, ƙamshin turaren oud yana yawo har ƙofar shiga.
A waje, ana gyaran lambu. Ƙamshin furanni na tashi, ga murya ta masu gyara suna dariya da raha..kowa da farin ciki akan fuskarsa.
A gefe, ana ɗora manyan fitilu masu walƙiya crystal chandeliers waɗanda zasu haskaka gidan..
A cikin babban falo, Maleekh yana tsaye a bakin window yana kallon aikin. Ya zura hannuwansa cikin aljihun wando, idanunsa a kan yanayin gidan yana tunanin Amal.
A hankali, murmushi ya suɓuce masa.
“Ko gidan ma ya fahimci farin cikin da zuciyata take ciki…”
Ya faɗa a hankali, yana shakar ƙamshin sabon fenti.
Gidansu Amal kuwa, ya koma aljanna ta mutane.
Daga ƙofar shiga har cikin tsakar gida, an yi ado da furen gwangwani, fitilun string lights suna walƙiya kamar taurari.
Ƴan uwan mahaifinta daga Borno sun iso, suna ta dariya da raha cikin ƙayatattun kaya.
Ƴan uwan mahaifiyarta daga ƙauyen Kaduna suma sun iso, wasu suna kitchen suna dafa girki, wasu suna gyara falo, wasu kuma suna saka kayan ado.
An saka sabon carpet, an canza labule zuwa pink and silver launin da Amal tafi so.
Daga sama har ƙasa gidan yana sheƙi.
Ana ta shirya turaren wuta, ga ƙamshi ta ko ina, an haɗa wa Amarya wasu arnar turaruka na jiki dana wanka dana ɗaki dana kaya dana gaban mace, su almisk da sauran su dake ƴan uwan mahaifinta daga Borno duk ƴan shuwa ne....
Ga kayan lefen da aka kawo daga gidansu Maleekh da kayan ɗaki...
A ɗaya sashen, Amal tana tsaye a gaban mirror tana kallo, tana murmushi cike da nauyin zuciya. Ta taɓa fuskar ta a hankali.
“Wannan ce ni?... fiancée ɗinsa tun yarinta...”
Ta faɗa a hankali, muryarta kamar sirri..
Sai kawai ta ji Inna daga ƙasa tana faɗin:
“Amatu! Ki sauƙo ki gani, ƴan uwan mijinki sun kawo kayan lefe ɗin Dubai!”
Da gudu Amal ta sauƙo. Kayan lefen sun cika babban falo, akwatuna masu launi, wasu gold-plated, wasu rose pink, wasu silver diamond design.
Daga cikin akwatunan akwai turaren jiki, kayan kwalliya, riguna, takalma, jewelries, hijabai, kayan sallah, kayan kwanciya. komai sabo daga Dubai. Ni kaina bazan iya misalta yawan kayan ba..
Ƴan uwa suna tafa hannu suna yaba wa kyawun kayan..
“Wallahi Maleekh yayi ƙoƙari sosai!” wata daga cikin dangin tace da dariya.
“Ai Amal ta same shi a sa’a,” wata kuma ta ƙara.
Inna ta yi murmushi kawai tana kallon jikarta, hawaye na farin ciki suna shirin zubo mata..
Abin da ba kowa ya sani ba shine gaba ɗaya Maleekh ya saka CCTV a gidansu Amal, daga ciki har waje.
Yana kallon ta a gida, yana lura da komai cikin sirri.
Yana ganin yadda take murmushi, yadda take tafiya, har yadda take gaishe da mutane.
Wani lokaci yakan tsayar da bidiyon ya ƙara kallon fuskar ta yana murmushi.
“Ni da ke mun wuce nisan duniya, Amal…”
Ya faɗa cikin lumshe ido, yana jin wani irin nutsuwa ta ratsa shi.
A wannan ranar da daddare za'a gudanar da waliman aure..
Rana ta fara faɗuwa, hasken rana ya dushe.
Gidansu Amal yana cike da hayaniya, dariya da nishadi.
Ƴan uwa suna ta ɗora shirin walima, masu kwalliya suna yi, masu saka kayan walima, Inna tana tsara jeren kayan lefe..
Amal tana tsaye a jikin tagar ɗakinta, tana kallon sararin sama, zuciyarta na bugawa da jin daɗi da shakku lokaci guda.
Ta ɗago hannunta ta murza zoben da Maleekh ya sanya mata lokacin da suka samu matsala a kaduna..
“Gobe fa za a ɗaura auren…”
Ta faɗa a hankali.
Sai murmushi ya suɓuce mata amma a cikin murmushin akwai ƙanƙanin hawaye..
Gidan da Maleekh ya kera domin Amal, ya zama abin da ake kallo kamar aljannar duniya.
Yana cikin unguwa ta manyan mutane, inda kowane gida yake da bango mai tsayi, fitilu masu sheƙi, da ƙofar wuta mai sarrafa kanta.
Gidan Amal ya fi yawancin sauran tsari da kyau sabuwar ƙira ce ta zamani, storey building mai parts uku:
Part ɗin Amarya da Ango
Part ɗin baƙi masu ziyara
Sai Garden Area da aka tanadar don walima..
Wurin da za'a gudanar da walima.
Hasken fitilu masu launin warm gold sun lulluɓe wajen, suna kyalli a cikin iska mai sanyi.
A ƙofar shiga, banner ɗin da aka tsara na rataye da rubutu:
“Welcome to the Union of Hearts Amal ❤️ Maleekh 2025”
Ƙamshin turaren oud da vanilla rose yana gauraya da ƙamshin furen da aka shuka a jikin hanyar shiga.
A gefe kuma, ana busa saxophone mai daɗi, yana haifar da nutsuwa da nishaɗi.
An kafa big white tent mai gilashin bango da fitilu masu walƙiya a ciki.
Kujeru sun jeru cikin tsari, kowace kujera da flower centerpiece a tsakiyarta.
Jerin kujerun mazan gefe ɗaya, na mata gefe ɗaya kowa cikin kwalliya da annuri.
Ƴan uwa da abokai, Kaduna, Abuja, Lagos, Borno, England, American, Dubai, da sauran manyan ’yan siyasa da ’yan kasuwa duk sun hallara.
Wani lokaci zaka ji wani daga cikin jama’a yana faɗin:
“Wallahi wannan shi ake ƙira bikin manya."
A bakin shigowa, ma’aikatan walima suna ta yin ushering cikin ladabi.
Ƙamshin abinci yana yawo fried rice, jollof, salad, grilled chicken, pepper soup, da non-alcoholic champagne da aka shigo da su daga Italy.
Fitowar Amarya
Kowa ya ɗaga kai lokaci guda!
Sai Amal ta shigo cikin long gown mai kyalli, launin champagne gold ɗauke da silver stones.
Rigar ta zagaye jikinta cikin salo da nutsuwa, ta ɗora veil ɗin light gold net da aka shafe shi da diamonds.
Ƙamshin turarenta ya cika wajen, haɗin Ajmal Amber da Mukhallat Shams...
Da kallo guda zaka fahimci ba kawai kyanta ake gani ba, ana ganin natsuwa, kunya, da hasken zuciya.
Ƴan uwa mata suka tashi suka fara shewa:
“Amarya ta fito! Amarya ta fito!!”
Sai hayaniya ta barke, ana ta tafi da waka da ihu cikin nishadi.
Wata daga cikin danginta tana dariya ta ce:
“Allah ya sa albarka cikin wannan aure.”
Amal tana murmushi, tana tafiya a hankali, hannunta a cikin hannun kawarta Aisha da ke rakiyarta zuwa kujerar amarya..
Fitowar Ango Maleekh..
Sai kuma Maleekh ya fito daga sashen sa, cikin white suit mai sheƙi, da black tie, gold wristwatch, da shoes masu glass shine.
A gefe ɗaya Abbah ne yana murmushi da alfahari, yana zaune.
Duk inda ya taka sai jama’a sun juya suna kallonsa..
Ga wasu manyan abokansa a gefe da gefensa.
Ga ƙannensa Islam da Arfat suma sun fito, sun sha kyau sosai..
Hankalinsa duk yana kan Amal.
Idanunsa sun haɗu da nata.
A lokacin, duniya ta tsaya cik a gare su.
Babu kowa a cikin ido sai su biyu...
A gefe, Ammy ba ta hallara ba.
Tana zaune a gida cikin living room ɗinta, tana kallon walimar ta hanyar TV live broadcast..
A gefe ta ajiye cup ɗin tea amma ba ta sha ba.
Tana kallon Amal a fusace.
“Yaron nan... wannan ce mace da zai ɗauka? Wannan ce har zai ce ta fi masa kowa?”
Ta lumshe ido, ta ɗaga hannu a hankali tana faɗin:
“Allah Ka kare ɗana daga halin da bai sani ba...”
A zuciyarta akwai ƙunci da kuma wani ɓangare na soyayyar ɗanta da ta kasa fitarwa...
An kunna lights show, DJ ya saka waka mai nutsuwa.
Amal da Maleekh suka zauna kusa da juna a kujerar aure, fuskokinsu cike da annuri.
Ƴan uwa suna ta ɗaukar hotuna, ana ta murna, ana dariya.
Maleekh ya juyo a hankali yana kallon Amal.
“Yau kowa yana gani… amma ba kowa yake fahimtar yadda zuciyata ke bugawa saboda ke ba.”
Amal ta yi murmushi, ta ɗaga kai ta ce:
“Daga yau ni ce matar da zaka ƙira naka… har abada.”
Sai suka kalli juna lokaci ɗaya fitilun wajen suka sauya launi zuwa gold and white.
Jama’a suka tashi da tafi da shewa:
“Auren shekaraaa!!! 🎉🎉🎉”
Daren Walimar Aure
An rufe taron da murna da nishaɗi. Wurin ya cika da farin ciki, kiɗa, da ƙamshin turaren da ke fita daga ko’ina. Kowa na faɗin,
“Allah ya kaimu gobe lafiya, Allah ya tabbatar da ɗaurin auren lafiya.”
Yamma ta wuce, dare ya sauƙa da sanyin iska mai ɗauke da ƙamshin furanni. Gidaje suna walƙiya da hasken fitullun gilashi da aka rataya a ko’ina.
Misalin ƙarfe 9 na dare
Kowa ya koma gida, Amal ta cire veil ɗinta, ta zauna gaban madubi tana duban kanta da murmushi. Cikin ranta tana jin kamar ta shiga mafarki auren da ta jima tana mafarki da shi, yanzu gobe ne.
A gefe kuma Farha, Aisha da wasu ‘yan uwanta mata suna zaune a akan gado suna ta dariya, suna tsokanar Amal:
Farha wacce yau ta kasance a wurin hidima kuma ta shiga sahun ƙawayen Amarya, yau a gidansu Amarya zata kwana cikin ƙawaye...
Farha ta ce “Ke fa Amal, kin san idan aka ɗaura auren nan gobe, gobe da dare ba zaki huta ba!”
Duk suka yi dariya.
Aisha ta ce “Ke Farha ki bari mana amarya ta huta, kin manta da walimar yau? Duk jikinta a gajiya yake, kika sanar mata wannan al'amarin ai sai ta tsorata kuma...”
Suka kwashe da dariya gaba ɗaya.
Amal ta ɗago kai daga madubi, tana murmushi cikin kunya.
“Ku dai ku bar ni in sha iska, na gaji sosai.”
Wata daga ciki ta ce
"Ji sai kace wacce kika yi wani rawar azo a gani..."
Amal ta ɗan harareta tana shirin tashi kenan, sai wayarta ta yi ƙarar message.
Ta ɗauka, zuciyarta na bugawa. Number ɗin “Amaleekh ❤️” ce, ta bayyana...
“Please Beb, ki fito waje yanzu... inason ganin kyakkyawar fuskarki kafin na wuce gida.”
Amal ta ji zuciyarta ta yi wani irin sanyi. Ta tashi, ta saka veil, ta ɗauki jakarta da wayarta ta ce da murmushi:
“Ina zuwa yanzu…”
Farha ta ce da dariya:
“Ango yayi ƙira kenan, to Ya Maleekh amarya zata fito!”
Aisha ta miƙe da sauri tana faɗin.
"Tsaya a kwaskware miki fuskar mana.."
Nan aka sake tsara mata sabon makeup..
Ta matsu ta fita saboda kar ta ɓata masa lokaci..
Farha ta ce "Dan Allah ku barta haka kar Ango ya gudu.."
Suka kwashe da dariya gaba ɗaya, Amal ta fita tana murmushi.
A Harabar Gidan
Daren ya yi shiru. Iska mai sanyi na busowa, Haske na haskaka filin gidan...
Amal ta iso bakin get, ta ce wa mai gadi cikin ladabi:
“Please ka buɗe mun ƙofa, ina dawowa yanzu.”
Mai gadi ya buɗe, yana murmushi.
“To Amarya, ki kula fa, dare yayi.”
Tana tafiya a hankali cikin doguwar gown mai ruwan milk, tana ɗauke da ƙamshi mai sanyaya zuciya. Ga takalminta mai tsini sosai, ta ɗan ɗaga rigarta kaɗan saboda kar ta taka takalmin..
A gaban get ta hango wata babbar mota baki mai taya ta baya, fitilunta a kashe. Ta ɗan yi murmushi a zuciya ta ce, “Laa, har yanzu yana nan a mota yana jirana.”
Tana kusantowa ta buɗe motar ta shiga da murmushi.
Bayan ta shiga ta rufe ƙofar, ta tsaya cak ganin wasu mutane daban a ciki..
Kafin ta yi magana, wani mutum daga bayan kujerar ya damƙeta da ƙarfi, ya sanya handkerchief mai ɗauke da turare a hancinta.
Amal ta fara ƙoƙarin yin ihu, amma muryarta ta sare. Idanunta suka fara lumshewa, numfashinta ya yi rauni.
“Ssshhh… shiru, komai zai dai-daita,”
wani murya mai sanyi ya faɗa, kafin komai ya rufe mata duhu.
A lokacin ta sume domin turaren irin mai saurin sumar da mutum ne...
Motar ta tashi da sauri cikin dare, ba kowa ya lura ba.
Sai ƙarar motar ta ɓace cikin shiru...
🕛 A cikin gidan kuwa.
Lokaci yana tafiya. 11 na dare.
12.
Har 1 na dare.
Farha ta miƙe daga inda suke zaune, tana kallon agogo cikin tashin hankali.
“Ni fa har yanzu hirar bata ƙare bane? Ko kuwa ta koma wajen Maleekh ne da kwana?”
Aisha ta ce:
“Ai ta ce ‘ina zuwa yanzu’. Ta tafi ne kamar za ta dawo nan da minti goma…”
Farha ta ɗauki wayarta ta ƙira Amal ringing... amma ba’a ɗauka ba.
Ta sake ƙira still not picking.
“Ba’a ɗauka ba. To bari na ƙira Yaya Maleekh.”
Ta ƙira. Switch off.
Farha ta kalli Aisha cikin tashin hankali.
“Wayarsa a kashe... wannan ba daidai bane.”
Aisha ta ce: “Ku tashi mu fita mu duba waje.”
Suka fita zuwa harabar gidan, suka tambayi mai gadi.
Mai gadi ya ce musu: “Ai ta fita ta ce za ta dawo yanzu. Ban gani ta dawo ba.”
Farha ta ce da mamaki:
“Ba yanda za'ayi Ya Maleekh ya tsaya a waje ba tare da shigo wa gidan ba… wannan abin akwai matsala.”
Mai gadi ya buɗe musu gate.
Suka fita, waje wayam. Shiru. Hasken fitullun titi kawai ke haskawa.
Suka dawo cikin gidan, zuciyoyinsu na bugawa. Amal ba ta dawo ba.
Haka suka yi ta ƙira, har wayarta ta daina shiga gaba ɗaya.
A cikin daren kafin Asuba misalin ƙarfe 3, Inna ta fito daga ɗaki da tsoro a idonta jin hayaniya..
“Wai menene ke faruwa?”
Farha ta ce cikin kuka:
“Tun jiya da daddare Amal ta fita, bata dawo ba har yanzu.”
Anan aka ƙira Abbah, aka sanar masa.
Abbah ya ƙira Maleekh, ya tambaye shi cikin tashin hankali:
“Maleekh, ina Amal take? Ya zaka ɗauke ta ba tare da ka sanar ba?.”
Maleekh ya amsa da muryar bacci:
“Amal kuma? Wallahi bayan mun rabu a walima ban sake ganin ta ba. Na shiga ɗakina kai tsaye bayan na dawo. Me ke faruwa ne?”
Kowa ya rikice. Cikin mintuna kaɗan gida ya cika da hayaniya, kukan mata da ruɗanin dangi.
“Amarya ta ɓace! Amarya ta ɓace fa a daren daurin auren ta!”
A daren Abbah da Maleekh suka zo gidansu Amal..
Mai gadi yana ta rantsewa:
“Ni wallahi ta fita da kanta, motar baki ce kawai na gani.”
Abbah ya riƙe kai yana cewa:
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un… Amal fa yarinya ce mai kamun kai… wa zai yi haka?”
Maleekh kuma yana tsaye, a filin gidansu Amal da Abbah da kowa da kowa.
Zuciyarsa na bugawa cikin tashin hankali, bai san ko mafarki yake ba ko gaskiya.
Daren farin ciki ya koma daren kuka.
Amarya ta ɓace a daren kafin ɗaurin aurenta.
Gobe da safe, duniya za ta firgita.
Da safe gari ya waye cikin tashin hankali da hayaniya.
Labarin bacewar Amal, amaryar da za a ɗaura aurenta yau, ya baza ko’ina.
Daga unguwa zuwa social media, daga bakunan dangi har zuwa gidajen makwabta kowa na magana:
“Amarya ta ɓace kafin ɗaurin auren ta!”
“Wai me ya faru ne?!”
Gidansu Amal ya cika da jama’a, wasu suna kuka, wasu suna addu’a.
Abbah ya ƙira Maleekh, yana faɗin cikin tashin hankali:
“Ka ƙira ‘yan sanda yanzu, ba za mu zauna mu jira ba. Dole a bincika ko ina!”
A Ofishin Tsaro
Maleekh yana zaune cikin tashin hankali da damuwa, idonsa ya kumbura saboda rashin bacci.
Jami’an tsaro suna zagaye da shi a ofishin CCTV, ana kallon footage ɗin gidansu Amal.
A screen ɗin aka ga Amal ta fito daga gidan da kanta, cikin doguwar riga, ta tsaya a bakin get.
Ta yi magana da mai gadi, sannan ta nufi wata baƙar mota mai gilashin tint.
Ta buɗe motar da kanta ta shiga, ba wanda ya ja ta ko ya tilasta mata.
Jami’an tsaro suka kalli juna.
Ɗaya daga cikinsu ya ce,
“Gaskiya, daga yadda ta fito da kanta, wannan ba sacewa bace. Wannan alama ce ta wanda aka ƙira a waya.”
Wani jami’i ya ƙara cewa,
“Yuwuwar saurayinta ne ya ƙira ta. Yana waje, sai ta fito.”
Maleekh ya cije leɓensa yana duban screen ɗin da idanu jawur.
Ya ce da mai sarrafa CCTV:
“Please, ɗan dawo baya. Inason duba wani abu kafin ta shiga motar.”
Aka dawo kaɗan, sun ga lokacin da Amal ta ɗaga kanta sama, ta dubi CCTV camera kafin ta shiga motar.
Kowa ya yi shiru.
Sai Maleekh ya furta cikin ƙasa-ƙasa:
“Ta san ana kallonta... ta kuma san za a ga wannan... Amma duk da haka ta tafi.”
Wani jami’i ya ce cikin sanyi:
“Yallabai, wannan ai kamar ta tafi da niyyarta ne. Ba alamar karfi ko tsoro a jikinta.”
Maleekh ya dafa kansa, sannan cikin ƙarfi ya ce:
“Enough! Ku bar komai. A janye ƙarar. Idan da gaske sace ta akayi, da wata alama za ta nuna. Wannan dai ita ce ta shirya tafiyar.”
Ya tashi tsaye, ya dube su da idon da ke cike da ɓacin rai.
“Munafurcinta ne kawai. Idan ta gama sharholiyarta, zata dawo kamar yadda ta tafi.”
Jami’an suka kalli juna cikin mamaki. Amma babu wanda ya ce komai.
A gida kuwa, Abbah, Inna, Farha, Ammy da dukkan dangi sun hallara.
Kowa na jiran zuwan Maleekh da wani labari.
Inna tana kuka sosai, ta miƙe tsaye cikin tashin hankali, ta damƙi rigar Farha tana faɗin:
“Da haɗin bakinki kika sa aka sace mun Amatu na ko? Ki gaya min gaskiya a gaban kowa! Daman tubarki ba gaskiya bace! Na san halinki!”
Farha ta ruɗe, tana kuka tana cewa:
“Wallahi Inna, bana da hannu! Tallahi bana da hannu akan bacewar Amal! Na tuba, amma wannan ba laifina bane!”
Abbah ya matsa kusa da Inna ya ce cikin tausasawa:
“Kinga Mama, ki bari ta sake jikinta. Babu tabbacin haka. Mu saurare ta.”
Ya juyo ya kalli Farha cikin nutsuwa:
“Ki gaya mana gaskiya, Farha. Shin da haɗin bakinki aka ɗauke Amal?”
Farha ta share hawayenta, ta ce da rawar murya:
“Wallahi Abbah, ban san komai ba. Ni yanzu nayi hankali, wallahi zuciyata tsaf, bana da hannu a bacewar Amal.”
Ammy, ta ce cikin murya mai ƙarfi:
“Haba Alhaji! Ta ce ba ita bace, me yasa za ku tozarta yarinya haka a gaban jama’a? Ba zaku iya ɗora mata laifi ba akan abin da babu tabbaci!”
Inna ta ce cikin kuka mai ƙarfi:
“Na rantse da Allah idan ba ta da hannu, to waye zaiyi haka! Wayyo Amatu na... wayyo yarinya ta!”
Ta rushe da kuka, tana faɗin,
“Ai wannan bikin ya zama bakin ciki! Waye zai iya jurewa?”
Kowa ya kame yana ta sauraron ruɗani a cikin falon.
Sai ga Maleekh ya shigo cikin hanzari, fuska cike da ɓacin rai.
Kowa ya juya yana kallonsa.
Sai shiru ya mamaye falon gaba ɗaya.
Maleekh ya tsaya a tsakiyar falon, ya ce da murya mai sanyi.
“Farha bata da hannu a bacewar Amal.”
Duk suka juya suna kallonsa, suna jiran abin da zai ce.
Ya ɗauko laptop daga hannun ɗaya jami’i, ya kunna bidiyon CCTV.
A screen ɗin aka ga Amal ta fito da kanta, ta dubi sama, ta nufi mota, ta shiga da kanta.
Kowa ya kalli juna, wasu da hawaye, wasu da mamaki.
Maleekh ya ce cikin muryar da ta karye:
“Ga shaida. Ita da niyyarta ta fita daga gidan, ba wanda ya sace ta. Ta ƙi auren saboda ta tozarta ni. Ta bi wani saurayi daban.”
Wani ƙara ya fito daga bakin Inna:
“Karya ne! Ƙarya kake Maliku! Amal ba zata yi haka ba!”
Abbah ya ce cikin ɗaga murya:
“Kai Maleekh, kana hauka ne? Taya yarinya a daren aurenta zata bar gida da kanta? Tana so fa, ba wai tilasta ta akayi ba! Taya zaka ce ta tozarta ka?”
Maleekh ya ce cikin tsanani:
“Haka ta tsara makircinta! Da gaske bata so na. Ta yi wannan don ta ɓata min suna.”
Aisha, ƙawar Amal, ta ce cikin tsoro:
“Amma fa, kafin ta fita, mun ga text ɗinka a wayarta! Ka turo mata message cewa ta same ka a waje!”
Maleekh ya juyo da idanu masu cike da zafi:
“Ta nuna muku message ɗin ne? Ta nuna muku number da ya turo mata ne?”
Aisha ta girgiza kai, hawaye na gangarowa.
“A’a... bata nuna mana ba...”
Farha tana kuka, ta ce:
“Ni dai na tabbata akwai lauje cikin naɗi. Amal ba zata aikata haka ba. Tana ƙaunarka fiye da komai. Wallahi akwai wanda ya shirya wannan.”
Maleekh ya ja dogon numfashi, sannan ya ce cikin sanyi da raɗaɗin zargi:
“Ku bar komai. Kada kowa ya saka kansa a cikin damuwa. Idan ta gama shan sharholiyarta, zata dawo. Ba zan ƙara bata minti ɗaya daga zuciyata ba.”
Ya juyo cikin fuska mai cike da ciwo, ya fita daga falon, ya buga ƙofar da ƙarfi.
Shiru ya rufe wurin.
Kowa ya kame, zuciya cike da tambayoyi.
“Amal ta tafi da kanta?”
“Ko dai wani ya yi amfani da sunan Maleekh ne ya jawo ta?”
Duk suka kalli juna cikin shiru, duniya ta canja musu launi a ranar da ya kamata ta zama farin ciki...
《》《》《》《》
Haske kaɗan ne ya shigo ta ramin taga. A cikin ɗakin, Amal tana zaune a kujera; an ɗaure mata ƙafa da hannu, an toshe mata baki gam. Jikinta gabaɗaya na rawa, idanuwanta sun kumbura, hawaye suna zuba amma ba za ta iya ihu ba. A gefenta wasu gafza-gafza matasa ne, fuskokinsu a rufe da baƙar hula, hannayensu na riƙe da bindigogi. Tana ta kuka a sirrance..
Farha ta koma gidansu. Mahaifiyarta ta sata a gaba sai masifa take ta mata.
"Wallahi yanzu ban san wani irin rashin zuciya Allah ya ɗora miki ba Farha, saboda rashin zuciya har kije bikin Maleekh? Mutumin da ya gujeki ya nuna baya ƙaunarki har ki saura da shiga jikinsa, wani abun baƙin ciki har ki kwana a gidan su Amal? Mutanen da suka tozarta ki suka durkufa ki a gaban kotu suka sa kika zauna a prison amma har ki shiga jikinsu....
Gashi abinda ya faru ai, Ƴar su ta gudu sun makala miki sharrin ke kika sa aka sace ta, madalla gobe kya ƙara zuwa yanda suke ai.."
Farha tana kallon mahaifiyar ta, idanu cike da hawaye ta ce,
“Mom... anjuma ma zan koma gidansu Amal na ji ko an samu labarinta… wallahi ban san yanda matsalar take ba ..”
Hajiya Sa’adatu tana ɗaga murya ta ce,
“Kin yita marar zuciya! A haka zaki ƙare! Banza shashasha! Sai sun ƙara makala miki wani sharrin ai…”
A wannan lokacin Zayd ya shigo cikin falon, ya tsaya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 47 Chapter of 62