ta ce:
“Alhaji, wannan makirci ne! Amma waye zai iya yin haka? Me ya ja wannan makircin?”
Abbah ya dube ta cike da damuwa.
“Sai na gano asalin komai. Kuma zan rantse da Allah, duk wanda ya sa hannu a cikin wannan sharrin, sai gaskiya ta fallasa shi, akwai lauyoyina da suke nam zasu tsaya masa gobe, domin daga yau insha Allahu bazai ƙara kwana cell ba.”...
_Washegari_
A ɓangaren Maleekh kuwa..
Wani sanyi na fluorescent ne yake dukan saman ɗakin ƙaramin cell ɗin, ƙaramin taga da ke da reja a kai ya nuna ƙaramin layin haske mai ƙarfi kamar sanda. Maleekh ya farka da sabon rikicin zuciya, ba bacci mai annashuwa, sai gajiyar damuwa da rashin sanin makoma. Hannayensa na rawar sanyi, ya leƙa gefensa ya ga babu komai a tattare da shi. Ba wayoyinsa, babu passport, babu komai... Jakarsa na ƙarƙashin kulawar hukumomi...
Ya dafa kansa da hannu, yana ƙoƙarin tunawa...
Barinsa gidansu, zuwa gidansu Amal, ganin Amal da Zayd a gado ɗaya...
Zuwansa filin jirgi, da sauƙarsa anan ƙasar london, jin muryar wani jami'in da ya ce “we have an issue here.” Sai kuma lokacin da aka ɗaure masa hannu, an ɗauke masa komai. Cikin zuciyarsa akwai tambaya ɗaya mai ƙwazo:
“Ta yaya abubuwa suka kai ga haka? Wanene zai yi mun haka? Amal? Ko Zayd?..”
Sai murmushi marar daɗi ya bayyana a leɓensa. Tunanin Amal ya dawo masa kamar an ƙwanƙwasa masa ƙirji...
A lokacin aka buɗe ƙofar cell ɗin, wani jami’in interrogations ne ya shigo da fuska mai tsanani, yana riƙe da wani babban fayil. Ya zauna a gaban Maleekh tare da ajiye takardun a teburin gefensa.. ya kallesa kamar wanda yake auna abu.. kafin daga bisani ya ce:
“Mr. Maleekh,” sannan ya fara da harshen Ingilishi mai sautin hukunci, “you are being charged with possession and intent to distribute controlled substances under UK law. We discovered illegal substances in your luggage upon arrival. Do you understand the charges?”
Maleekh ya tashi a hankali, idonsa sun yi ja, zuciyarsa na duka kamar za ta fashe.
A hankali ya furta.
“No... no, I don’t understand. This is not mine. I swear wallahi ba na da hannu a ciki. Someone planted it. Ask my family. Ask my lawyers!”
Jami'in yana girgiza kai ya ce
“We will try to engage a local counsel, Mr. Maleekh. The Embassy can assist with consular visits, but legal representation is a matter you must fund or your family must arrange. The process here is strict possession with intent can lead to very severe penalties if convicted.”
(Zamu yi ƙoƙarin neman lauya daga cikin mutanen garin nan, Mr Maleekh.
Ofishin jakadanci zai iya taimakawa wajen ziyarar diflomasiyya, amma batun lauya wanda zai kare ka dole ne kai ko iyalinka ku biya kuɗin sa ko ku shirya hakan da kanku.
Tsarin shari’a a nan yana da tsauri, kama mutum da kayan da ake zargi yana da niyyar amfani da su na iya haifar da hukunci mai tsanani idan aka same shi da laifi...)
Cikin ƙaryewar murya Maleekh ya furta:
“Ina Abbah?... ina Ammy... Ina fatan sun yi wani abu. Don Allah ka taimaka.”
Lauyan ya dinga rubutu. Cikin akwai rashin tabbaci. Wannan hukuma ce mai tsauri, ba kamar wajen zaman gida can Nigeria ba inda magana za ta warware cikin husuma. A nan, takarda, hujjoji, signatures, da scanning ne suke magana.
Washegari da safe an shigar da Maleekh kotu..
Ga lauyoyin da Abbah ya kawo domin kare Maleekh, Abbah da Ammy su ma duk suna zaune cike da tausayawa yaronsu...
Maleekh yana tsaye a gaban kotu, a can ne ya ga idanuwan mutane daban-daban: wasu suna kallonsa da tausayawa, wasu suna ganin shi kamar wanda ya yi kuskure mai muni. an umurce shi ya zauna a gefen matsayi. Alkali ya duba takardu, ganin babu wasu hujjoji ne yasa shi faɗin:
“The court hereby remands Mr. Maleekh in custody pending further investigation and trial. He is to remain in custody.”
(Kotun nan ta bayar da umarni cewa a tsare Mr Maleekh a gidan yari har sai an kammala bincike da shari’a.
Za a ci gaba da tsare shi a halin yanzu...)
Wannan hukunci ya sauƙa a cikin zuciyarsa kamar dutse. Duk mafarkinsu da tsarinsu na rayuwa a cikin kunnuwa abbah da yake zuba fata ga shi yanzu ya koma ruwa...
Bayan zaman kotu, an mayar da shi cell, inda ya zauna.
A wannan dare Maleekh yana zaune sai tunani yake. Tare da maganar zuci.
“Idan suna so in faɗi, to kuwa za su faɗi tare da ni. Zan yi yaƙi da wannan, zan nemi wakilcin lauya. I will not die as someone’s pawn.”
《》《》《》《》《》《》《》《》
A can Abuja
A yau Amal tayi dare a wurin aikinta ga ana ruwan sama.
Ta fita zatayi gida. Sai taga wasu black cars guda biyu na binta A baya..
Haka ta ƙara gudun mota suma suka ƙara gudu.
Tana gudu da mota su ma suna binta da gudu..
Har tayi kusan accident sauran kaɗan motarta ta faɗa cikin wani rami.
Sai ga wani mota ya sha gaban motarta sai motarta ya daki motar da yasha gabanta...
Da karfi ta buga kanta da sitiyarin motar...
A gigice ta buɗe ta fito, a lokacin motar da yasha gabanta Zayd ya fito a ciki yana ƙiran sunanta pretty...
Amal tayi gudu ta nufi wurinsa tana faɗin "Zayd dan Allah ka taimaka mun wasu ne suke bina da gudu.."
Bata san Zayd fuska biyu yake nuna mata ba, da sa hannunsa a cikin waɗanda ake bibiyanta, amma a gaban idonta sai ya nuna tausayawa, ya riƙe ta tare da rarrashinta yana faɗin
"Kar ki damu ina tare da ke, ba abunda zai same ki..ina sonki sosai har yanzu..."
Sauran motocin kuwa juyawa sukayi suka tafi...
Zayd ya rakata har gida kafin ya tafi yana murmushin mugunta. A ransa yake faɗin
"Haka zaki cigaba da zaman tsoro da firgita yarinya, wanda zai kare ki bayanan ya tafi...kuma ba dawowa..."
Bayan tafiyarsa ta shiga gida tana tunanin mafarkin da tayi a office ɗinta akan Zayd.. Sai ta ƙara tsorata da shi, amma wani zuciyan ya sanar mata cewa
"Ai mafarki ba gaskiya bane..."
Rana ya ta yau ne za'ayi zama na ƙarshe a kotu.. an kawo shi gaban kotu a tsare, hannayensa a jikin sarkar da ke ɗaure. Idanuwansa sun yi ja. A katu mutane sun hallara: lauya, ‘yan jarida, ma’aikatan jakadanci, 'yan uwa, da sauran masu sha’ani. Kowa ya mayar da hankali ga taron zama na uku, za a gabatar da sababbin shaidu...
Alkali ya yi shiru, ya duba takardun da ke gabansa, ya ce cikin murya mai nauyi:
“An kawo shaidar da zata buƙaci sauraro. Prosecution, ku gabatar.”
Wani jami’in ofishin tsaron filin jirgi daga Najeriya ya hau gaban kotu. A nutsuwa ya na ɗauke da wani fayil na hotuna da video. An kunna allon domin a nuna wasu frames na CCTV.
A cikin video ɗin da aka kunna, an ga hoton tashar jirgin Najeriya, hoton check-in counter. Jakar guda biyu sun bayyana, ɗaya tana da tambarin kamfanin jirgin, ɗayan kuma jakar Maleekh wanda ya kasance iri ɗaya ne. Sai kuma an ga mutanen biyu daga cikin su wani ya ɗauko jakar, ya maida ta a kan trolley, tare da musayar sa da wani mutum da ya yi kama da ma’aikacin tashar. A frame ɗaya kuma an nuna wani mutumi ya ɗago jakar da sauri, ya tura ta cikin wani trolley daban.
Lauyan Maleekh ya tashi tsaye, fuskarsa ta cika da bege. Ya miƙa hannu ya ce:
“My Lord, wannan hoton ne zai nuna muhimmin abu: an maye jakar ƙasa a filin jirgi kafin tafiyar zuwa London. Wannan bayanin yana tabbatar da cewa jakar da aka tsare a Heathrow ba ta da alaƙa da abun da Mr. Maleekh ya shigo da shi.”
Prosecution ya yi ƙoƙarin tada tambayoyi, amma mai gabatar da bincike daga Nigeria ya ci gaba da bayanin:
“Mun gano ta hanyar passport da address an yi scanning a tasha. Jakar da aka samu a London ta fito ce sakamakon bayanan da muka samu a check-in. An duba signatures, an kwatanta lambar tag da passport kuma mun gano cewa jakar an sauya ta a Abuja, kafin jirgin ya tashi.”
An kawo shaidun da suka nuna ticket number, boarding pass da hoton wanda ya aika da jakar, an gano sunan wani mai aiki a kamfanin tafiye-tafiye da ya shiga da wani ɓangare na aikin amintacce. An kuma gabatar da labarin forensic, analysis ya nuna cewa abubuwan da aka samu cikin jakar sun bambanta da abubuwan da ke cikin irinsa a Nigeria, hakan ya nuna maye gurbi ne...
An yi tir da shaidu na prosecution waɗanda suka riƙe cewa an samu abubuwa masu haɗari a cikin jakar Maleekh. Amma bayan ganin hoton musayar jakar a Nigeria, da bayanan check-in, da kuma sakamakon forensic da ya nuna ana samun bambanci a cikin jaka ɗaya da ɗayan, alkali ya yi shiru na ɗan lokaci kafin ya yi magana.
A wannan lokaci, lauyan Maleekh ya tashi ya gabatar da jawabi:
“My Lord, abun da Allah ya nuna a bidiyon nan ya bayyana gaskiyar cewa an maye jakar. Abun da aka samu a London ba shi ne abin da Mr. Maleekh ya ɗauka daga Nigeria ba. A cikin wannan hali, akwai shakku mai zurfi. Babu cikakken hujja da za ta tabbatar da laifin wanda aka zarga. Mun roƙa a saki Mr. Maleekh domin babu hujjar da ta gamsar.”
Prosecution ya yi ƙoƙarin ɗaga murya, ya nunawa kotu wasu bayanai amma dukan bayanan sun rushe ta hanyar hoton musayar jaka. Alkali ya ɗago idonsa, ya kalli lauyan da ke tsaye, sannan ya yi jawabi cikin murya mai tsanani:
“Bisa ga abin da muka gani a gaban kotu, an samu cikakkiyar shaidar musayar jaka a tashar jirgin Nigeria. Hakan ya kawo shakku mai zurfi a kan sahihancin hujjojin da ake amfani da su a wannan shari’a. A saboda haka, kotu tana yanke hukunci cewa babu isasshen hujja da za ta tabbatar da laifin Mr. Maleekh Abdul-Majeed.”
A nan ne ɗakin shari’a ya yi wani irin murna da farin ciki. Wadansu suka yi shiru. Maleekh ya ji kamar wani nauyi ya faɗi daga kansa, hawaye na zubo daga idonsa. Abbah ya miƙe tsaye cikin zaune, ya kalli ɗansa, idanunsa cike da hawayen murna. Ammy kuwa ta faɗi ƙasa cikin kuka ta rungumi Abbah.
Jami’in ofishin jakadanci ya tashi ya tafi kusa da Maleekh ya ce cikin rarrashi:
“Mr. Maleekh, your release is granted. We will assist with your travel documentation and liaise with authorities in Nigeria to investigate further the persons responsible.”
Maleekh ya juya ya kalli alkali, ya yi godiya da karyayyen muryarsa:
“Allah ya saka da alkhairi. Na gode. Na gode sosai.”
Lauyoyi kusan huɗu ne waɗanda sukayi fice da shige wurin kwato Maleekh domin duk mutanen Abbah, wasu daga Nigeria wasu kuma daga nan ƙasar...
A waje kuma ‘yan jarida da ke jiran fitar da sakamako sun yi ta dropawa da tambayoyi, Ammy da Abbah sun ɗauki lokaci suna rungumar ɗan su.. hawayensu na haɗuwa da godiya da jin daɗi. Amal dake can Niger ta ji labarin a wayarta ta hanyar wani abokin aiki ya ƙira ta:
“Wallahi an wanke shi.” Ta ji kamar zuciyarta ta yi tsalle da daɗi sai kuma fargaba ta dawo: “Amma me zai faru gaba?” Ta rungumi kanta, tana addu’a a hankali...
Ammy ta yi ta godiya, tana ta furta:
“Allah mun gode maka! Waɗanda suka yi wannan sharrin ba zasu yi nasara ba.”
Acan ɓangaren Alhaji Wadata da Alhaji Gusau da shi kanshi Zayd da mahaifiyarsa sun yi baƙin cikin fitowar Maleekh...
Bisa tsaron jami'ai aka shigar da Maleekh mota tare da iyayensa suka nufi gida dake nan London..
Sai dai kuma, a ƙarshen wannan rana, akwai wani abu da ya rage: tambayar wanene ya maye jakar? Kuma wa zai amsa saboda irin wannan sharrin? Wannan tambaya ce da zata jefa labarin cikin sabon babi, bincike mai zurfi, haɗin gwiwar lauyoyi, da faɗakarwa ga wanda ya yi shirin.
A babban falo duk suka hallaru..
Komai ya lafa sai nutsuwa, amma zuciyoyin su na ɗauke da abubuwan da suka sha wahala akan sa..
Maleekh ya zauna ya jingina da kujera, yana riƙe da wayarsa. Idanunsa sun yi ja saboda rashin bacci da damuwa.
A hankali ya kunna wayar, sai ga jerin saƙonni daga Amal guda sama da ɗari!
“Maleekh please ka yarda da ni…”
“Wallahi ban san da komai ba…”
“Don Allah ka amsa wayata…”
“Ina cikin fargaba…”
"Naji labarin kana cell sakamakon abin da aka samu a jakar ka, shin gaskiya ne?..."
"Allah ya fitar mun da kai Maleekh..."
Saƙonni suna ta shigo wa a jere, kamar ruwa da aka buɗe masa hanya.
Ya runtse idonsa da ƙarfi. Zuciyarsa na bugawa. Duk da ciwon da yake ji a cikin ransa, har yanzu yana sonta amma hoton da ya gani ita da Zayd a ɗaki yana bin kwakwalwarsa kamar wuta.
Wayar ta sake yin ƙara, “Amal Calling…”
Sai dai ya tsaya kawai yana kallo, bai ɗaga ba.
Ya rufe idonsa, yana sauƙe numfashi mai nauyi.
A gefe kuwa, Abbah da Ammy suna zaune suna kallonsa cikin tausayi da godiyar Allah.
Haka abokansa suka rinƙa ƙira suna masa fatan alkhairi, duk ƙiran da ya shigo sai ya ɗauka amma banda ta Amal, tana kiransa akai akai amma sam ya ƙi ɗaukan kiranta...
Abbah ya murmusa kaɗan, yana cewa cikin murya mai nutsuwa,
“Alhamdulillah, Allah ya tabbatar mana da gaskiya. Na gode da irin juriyar da kayi, ɗana. Wannan komai ya zama tarihi yanzu.”
Ammy ta ɗan share hawaye, ta ce,
“Ni har yanzu jikina yana rawa idan na tuna da wancan ranar… amma Alhamdulillah ka fito lafiya.”
Maleekh ya ɗan sunkuyar da kai, yana cewa cikin murya mai sanyi,
“Ni ma haka nake ji, Ammy. Amma har yanzu kamar mafarki nake kallon abun, ban taɓa zato cewa zan shiga irin wannan masifa ba.”
Sai Abbah ya gyara zama, yana ɗan murmushi da girmamawa:
“Maleekh, yanzu dai lokaci ne na farin ciki. Da zarar mun koma gida, zan so mu fara shirye-shiryen auranka da Amal.”
Ammy ta zabura da sauri, tana kallon mijinta da fuskarta cike da mamaki:
“Haba Alhaji! Daga fitowarsa a cell sai aure? Ai yaron nan har yanzu yana cikin tashin hankali, bai da cikakkiyar nutsuwa.”
Abbah ya jinjina kai, yana dariya kadan.
“Maryam, aure ma wani hutu ne. Kuma ya dace mu gyara kuskuren da ya faru. Maleekh da Amal sun jima da haɗuwa da soyayya, babu dalilin da zai sa mu jinkirta.”
Maleekh ya ɗan motsa, yana kallon iyayen nasa. Zuciyarsa na bugawa da sauri.
Sai dai ya ƙudura a ransa ya gama da soyayya.
Ya ce da murya mai natsuwa da kuma cike da rauni,
“Abbah... ta mun laifi sosai. Don haka a barni in huce tukun kafin a kai batun aure.”
Abbah ya kalle shi da ƙarfi, yana murza agogon hannunsa.
“Wannan ba mai yuyuwa bane, domin bazaka lalata wa yarinya Aure ita da ɗan uwanta ba kuma kai ka ƙi aurenta, wannan kuskure ne da kuma yaudara, don haka dole ne aure..."
Shiru ya cika falon.
Sai Maleekh ya sauƙe numfashi, ya ɗan murmusa cikin gajiyar rai.
“Shikenan Abbah... ba damuwa. Na amince.”
Abbah ya saki murmushi, yana duban Ammy da fuska mai natsuwa.
“Alhamdulillah. Da wannan magana, zuciyata ta huta.”
Ammy kuwa ta yi shiru kawai, tana kallon Maleekh, zuciyarta na ɓoye da damuwa, saboda ta san ba soyayya bace ta sa ya amince ba, kawai biyayya ce ga mahaifi. Kuma sannan ba wani ƙaunar Amal take ba..."
Ammy ta buɗi baki ta ce.
"Amma da sharaɗin idan mun koma za'a je a fito da Farha..."
Abbah ya ce "wannan ba abun damuwa bane.."
Sai falon ya sake komawa cikin nutsuwa, sai muryar TV da take showing a gefe.
Zuciyarsa ta mutu, amma fushin da yake da Amal bai mutu ba…domin har yanzu yana kallon ta da Zayd ne a kan idonsa.
Kuma ya ci alwashi duk san da ya ƙara ganin su a haka sai yayi musu hukunci marar misaltuwa...
Yana cikin duba wayarsa, ga kuma saƙon WhatsApp da suke ta shigo masa, bai yi niyyar duba wa yanzu ba har sai ya gama huta gajiyarsa kwatsam sai yayi ido huɗu da wani group da bai san shi ba samm...
Saboda wannan group ne yasa shi shiga WhatsApp, kai tsaye kafin ya duba meye a cikin group ɗin sai da ya duba su waye a ciki, ganin duk babu wanda ya sani sakamakon rashin sanin numbobin, yana shiga group ɗin abinda ya gani kawai a cikin group ɗin shine photuna..
Da farko yayi tunanin group ɗin BF ne har zai fita kafin photunan su buɗe, sai kawai ya hango fuskar Amal da wani a rungume da ita ta bayanta.. ga videos..
Zaro ido yayi yana duba wa. Nan ƙirjinsa ya tsananta bugawa..
Abbah da Ammy ganin canjin da ya shigo lokaci guda yasa su tambayarsa "lafiya kuwa?.."
A zabure ya ɗago kamar zai fashe da kuka ya ce.
"Ba komai, komai na ga campany na ya ja baya, babu wani ribar da ake samu yanzu..."
Abbah ya ce "kuma shine abun damuwa? Kana komawa komai zai yi normal...itama Amal bata cikin nutsuwa shiyasa..."
Ammy dai kawar da kai gefe tayi, ta bar su da halin halinsu domin yanzu ta cire hannunta. A cewar ta...
Abbah ya kuma cewa.
"Amma babu wani damuwa akan batun auren koh?..."
Maleekh ya jinjina kai cikin sassanyar murya ya ce
"Sosai ma.."
Daga nan ya bar falon, kai tsaye bedroom ya nufa. A wannan ranar gaba ɗaya ya kasa bacci sai kallon hotunan da video....
_NEXT NEXT NEXT_
asmeetahwriter✍️
*🎤AMALEEKH🎤*
*AMAL AND MALEEKH*
Together, they stand between love and loyalty, between public duty and private longing, two hearts bound by fate, yet tested by truth.
*Writing and Storytelling By*
Asma'u Muhammad Auwal
Asmeetah writer
*HASKEN JAJIRTATTU*
*MARUBUCIYAR:*
*Matar Damisa*
*My Enemy*
*Hasken Ruhi*
*And know AMALEEKH*
Bauchi State Nigeria.
*WhatsApp 09065443871*
Follow my channel 👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
"Jajirtattu mu ne ƙarfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faɗuwa. Mu ne tarihi da ake ginawa!" 💪🔥✨
BOOK ONE page 67 to 68
🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹
🌹🌹
🌹
Yamma liss misalin ƙarfe 6:30. Rana ta faɗi sai launin duhu dake sauƙa daga sararin sama..
Amal ta fito daga Office ɗin “The Awaken Project” dake cikin Campany CashTalk, da gajiya a fuskarta domin tun safe take aiki ba kakkautawa, tana bin bayanin wasu bayanai da ta samu daga manema labarai game da batun shari’ar Maleekh da kuma waɗanda suka kitsa sharri a kansa...
A cikin zuciyarta akwai farin ciki, saboda labarin cewa Maleekh ya fito daga kurkuku ya bazu, amma ba ƙaramin tsoro ke ratsa jikinta ba tun mako guda take jin ana bibiyarta..
Ganin duk ma'aikata sun tashi babu kowa yasa itama ɗaukan jakarta ta nufi harabar campany domin shiga motarta... Sai security ne kawai dake ta zirga-zirga....
Ta kunna motarta cikin nutsuwa, ta ɗan lumshe ido sannan ta ce a hankali:
“Ya Allah, ka tsare ni daga sharrin makiya...”
Motar ta tafi a hankali ta bar harabar kamfani.
Titunan Abuja suna cike da hasken fitilu, yanzu kusa magariba, cunkoso yayi yawa.
Amal ta zaɓi hanya mai sarari domin gujewa cinkoso, hanyar da bata da yawan jama’a, Airport link road extension..
Sai dai yau, ƙaddara ta rubuta wani abu dabam...
Da ta shiga tsakiyar hanya, kwatsam sai ta hangi wata baƙar mota daga nesa, black Prado tana tahowa da sauri kamar mai tuƙi cikin fushi.
Tana tunanin kamar motar da yake bibiyanta ne, cikin kankanin lokaci motar ta iso gabanta, ta shige mata gaban hanya da ƙarfi!
Amal a firgita ta ce,
“Subhanallah!”
Ta juyar da sitiyarin cikin hanzari, tana ƙoƙarin kaucewa.
Amma kafin ta daidaita kansa sai ga ƙaton trailer daga bayan ta, yana tahowa da gudu!
Wani irin ƙara trailer ya yi, “Tuuuunnn!!!”
Sai a nan lokaci ya tsaya!
Komai ya haɗu cikin daƙiƙa:
Motar Amal ta yi wani irin juyin juyi, ta yi tsalle kamar ƙwallon roba, sannan ta faɗa cikin rami mai zurfi a gefen hanya.
Wurin babu jama’a, hanya ce da ba a yawan bi.
Taya ta ƙone, gilashin motar suka watse.
Cikin hayaki da ƙura, motar ta tsaya cak.
Sai ɗaya daga cikin mutanen cikin baƙar motar ya fito, sanye da farin riga da hula baki, ya duba cikin ramin da wayar torchlight.
Yadda Amal ta kwanta, jini na malala daga goshinta, jikinta ba motsi.
Ya ce da muryar ƙarfi,
“Boss, ta gama! Babu numfashi!”
Wani daga cikin motar ya amsa daga ciki cikin murya mai sanyi:
“Ka tabbatar. Ba zan so a bar wata shaida ba.”
Sai ɗayan ya ɗaga torchlight ɗin ya sake duba jikin Amal, ya taɓa ƙirjinta da yatsansa.
“Laf! Ta mutu... Babu motsi ko numfashi.”
“Good.”
“Mu tafi.”
Motarsu ta bar wurin da sauri, tana shirin bacewa cikin duhun dare.
A bayan su, motar Amal tana nan cikin rami, tana ta hayaƙi kamar wanda akayi gobara...
Dare ya gama shigowa, iska tana busa ganyaye a hankali.
Cikin duhun da bai da haske, ƙarar wata ƙaramar tsuntsuwa ce kaɗai ke ji kamar tana kuka...
Sai dai a can nesa, wani mai babur dake wucewa ya tsaya yana kallon hayaƙi da ke tashi daga ƙasa.
Ya ce da mamaki:
“Innalillahi… wace irin hatsaniya ce kuma haka?”
Ya fara saukowa daga babur ɗinsa zuwa ƙasan ramin, yana ƙira da murya mai sauti:
“Hello! Hello! Wani yana ciki?!”
A lokacin da ya haska torchlight ɗinsa, fuskar Amal ce ta bayyana jini a goshinta, numfashinta a hankali kamar wacce duniya ta fara barinta...
Ganin irin halin da take ciki ne yasa ya lalumo wayarsa zai ƙira ƴan sanda, cikin tashin hankali ganin ba credit a wayar ne yasa ya dubi Amal da rabin kunkuminta ke cikin mota, zuwa samanta kuma na wajen motar..
"Baiwar ALLAH! Baiwar ALLAH kina ji na?..."
Haka yake ta tatta6a fuskarta babu wani motsi... anan ya cigaba da gadinta ko akwai wanda zai zo.
Shiru babu kowa ga dare yayi sosai, gashi har 11 ta wuce.
Anan wani dabara yazo masa, ya fara bincika motar ko zai samu wayarta yayi amfani da ita, cikin sa'a ya samu amma sai dai ta farfashe.. Amma bata mutu ba, sai dai kuma wani tashin hankali akwai security. Ganin Amal ta tafi dogon suma yasa yayi amfani da fingerprint ɗinta, cikin sa'a ya buɗe anan ya samu damar ƙiran lambar gaggawa ta police (199)...
Asuba, gari ya ɗan fara waye wa.
A kan titin da hatsarin Amal ya faru, an riga an zagaye wurin da igiya, motar FRSC da ta ‘yan sanda na wurin tun cikin dare duk ana bincike kuma har yanzu ba'a samu wani shaidar da zai sa da ganga akayi hatsarin...
A lokacin da suka ciro Amal daga cikin motarta, jikinta a jike yake da jini, rigarta kalar fari duk ya rine kamar ba farin riga ba, idanunta a rufe kamar wacce take barcin mutuwa.
“Gaggawa! Ku ƙira ambulance!”
“Ba zata iya rayuwa ba idan ba a kai ta yanzu ba!”
Motar ‘yan sanda ce ta ɗauke ta, aka nufi babban National Hospital Abuja da ita.
Likita ne yake bada umarni cikin tashin hankali:
“Blood level ɗinta ƙasa da kashi 10%. A nemo masu jini nan take! Waye ‘yar uwarta? Waye nata?”
Amal na kwance babu numfash..Da farko duk wanda ya ganta bazaiyi tunanin akwai rai a jikinta ba..
🇬🇧 A London
A gidan da Abbah da Ammy ke zama, labarin hatsarin ya iso da safiyar nan.
Wani daga cikin ma'aikata campany ne ya ƙira:
“Sir, Madam Amal had an accident last night... she’s in a critical condition.”
Da wannan kalma guda, wayar Maleekh ta sulale daga hannunsa..
Hankalinsa ya tashi kamar wanda aka cire masa rai.
“What? Amal? Accident?!”
Ya ɗauki wayarsa ya nufi part ɗin da Abbah yake da sauri.
“Abbah! Amal ta samu hatsari! Ba zan iya zama ba, dole mu tafi yanzu!”
Ammy ta riƙe ƙirji, ta ce cikin tsoro:
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Meya haddasa hatsarin?... Allah Ya bata lafiya, idan kuma ta mutu Allah ya jikanta. Amma meye namu da zamu tafi haka da gaggawa sai kace Islam ce ko Arfat tayi hatsari..”
Abbah ya ce "Insha Allahu tana nan da ranta, kuma itama Amatu ƴa ce a wurina, dole
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 44 Chapter of 62