yanzu? Wancan matsiyaciyar yarinyar nan da bata da komai face tsiya? Wallahi bazan yadda ta shigo gidanmu a matsayin suruka ba!.."
Abbah yana kallonta cikin tausasawa ya ce:
"Maryam, ki kwantar da hankalinki. Wannan al’amarin ya rigaya ya fita daga ikonmu. Maleekh yana sonta, kuma na ga soyayyar nan bata wasa bane. Ki barshi ya samu nutsuwa..."
Ammy ta dafe ƙirjinta cikin jin haushi ta ce:
"Nutsuwa kake faɗa? Wato bayan duk abinda aka riga aka shirya, bayan Farha, yanzu za’a wurgar da ita kamar jaka saboda wata yar talaka? Alhaji, wallahi wannan ba zai taɓa faruwa ba! Ba da ni ba!.."
Abbah ya miƙe a hankali yana dubanta da murmushi mai natsuwa ya ce:
"Maryam... na fahimci kina son Farha kamar ƴarki. Amma mu bar Allah ya zaɓa wa ɗanmu abinda ya fi alkhairi. Duk mu mun ga yadda yake fama tun da aka fara wannan maganar. Ki duba zuciyarsa, ya fita hayyacinsa saboda soyayya..."
Ammy ta juyo da ƙarfi tana nuna shi da yatsa tare da faɗin
"Kai dai ka sani, ko Maleekh ya auri Amal, wannan ba zai taɓa zama cikin farin ciki ba idan har ba a daidaita al’amura ba!.."
Abbah ya zauna yana tambaya cikin natsuwa.
"Me kike nufi da “daidaita al’amura” Maryam?.."
Ammy ta tsare shi da ido, muryarta ta ɗan yi sanyi ta ce:
"Sharadina guda ɗaya ne, Alhaji. Idan har kana so in yarda Maleekh ya auri waccan Amal ɗin, to sai ya haɗa aure da Farha. Na ce dole sai ya auri mata biyu Amal da Farha a lokaci guda. Idan ba haka ba, wallahi ba zan taɓa yadda da wannan auren ba!.."
Abbah ya tsaya kallonta cikin mamaki, yana jin nauyin maganarta ya ce:
"Maryam… wannan sharaɗi naki yana da nauyi sosai. Kin tabbata wannan shine abin da ke ranki?.."
Ammy ta ɗaga kai da tabbaci ta ce:
"Na tabbata. Idan har Amal zata shigo gidan nan, to Farha ma zata shigo a lokaci guda. Babu mace guda da zata mallaki zuciyar ɗana gaba ɗaya..."
Abbah ya sauƙe numfashi, yana jinjina kai ya ce:
"To... Maryam, na ji. Amma ki sani, wannan al’amari sai dai mu bar Allah ya hukunta shi. Domin soyayya bata da dokar da mutum yake rubutawa da hannunsa...
Ammy ta ɗan juya tana kallon ƙasa ta ce
"To kai dai ka sani Alhaji, na faɗa maka abinda ke cikin zuciyata. Wannan shine sharaɗi na ƙarshe..."
Ta juya ta bar falon, tana daidaita numfashinta. Abbah ya zauna yana kallonta a yayin da take barin falo, ya dafe kansa da hannuwa biyu, yana faɗin a hankali...
“Subhanallah… soyayya ta fi ƙarfin iko. Amma wannan gwagwarmaya zata ba da tarihi mai tsawo.”
Washegari da sassafe a gidan su Maleekh. Sanyin safiya na shiga cikin babban falon da yake cike da nutsuwa da ƙamshi. Abbah yana zaune a kan kujera mai faɗi, A gefe Ammy tana zaune cikin ɓacin rai. Maleekh yana gefe yana jujjuya zoben hannunsa, Farha na kusa da shi tana ɗaure fuska. Sai ga Amal an kawo ta gidan cikin hijabi, idonta cike da nutsuwa amma a bayyane akwai tsoron abin da ke gabanta...
Abbah a hankali, yana kallon Amal ya ce:
"Ki zauna nan, ‘yata. Muna so muyi magana cikin natsuwa..."
Amal ta durƙusa har ƙasi ta ce:
"Na’am Abbah… ina kwana.."
Abbah ya amsa da...
"Lafiya lau..."
Amal ta gaishe da Ammy. Ammy ta kawar da kai tare da jan dogon tsaki ta kawar da kai gefe...
Abbah yana fuskantar Amal ya ce.
"Kin ga, wannan magana ba ta yara bace, saboda tana da nasaba da rayuwar mutane uku — ke, Maleekh da kuma wannan yarinya (ya nuna Farha).
Ni dai ban so wannan rikici da ya faru ba, saboda ni kai na na ji kunya a gaban jama’a..."
Maleekh ya ɗago kai da ƙarfi ya ce.
"Abbah, ni ba na jin kunya! Na aikata abinda na yi ne saboda bana so a cuce ni. Amal tawa ce, kuma ba zan bari a ɗaura mata aure da wani ba!.."
Ammy ta tsawata masa da cewa:
"Kai kayi mun shiru, Maleekh!
Tun da na haifeka ban taɓa tunanin zaka zubar min da mutunci irin haka ba.
Ka shigo cikin manya, kana ɗaga wuƙa da alfaharin zaka kashe mutum! Idan ba hauka ba, menene haka?.."
Maleekh yana yatsina fuska ya ce:
"Hauka kike cewa? Saboda ina son Amal?
Ammy, ina girmamarki, amma ki sani soyayya ba ta kallon arziki..
Kina so ne in auri wadda kike so, ba wadda nake so ba?.."
Farha cikin muryar kuka tana kallon Maleekh ta ce:
"To me yasa sai ita?
Ina sonka Maleekh, ka san hakan.
Tun muna yara ake cewa mu biyu mun dace da juna, Amma yanzu, sai wata talaka ta kwaceka? Me take da shi da ni ban dashi?.. "
Amal tana kallon Farha cikin nutsuwa ta ce:
"Farha… ban so in shiga tsakaninku ba.
Farha, wallahi ba ni na nemi wannan soyayya ba. Ƙaddara ce ta haɗa ni da shi. Ba nayi ne da ganganci ba. Ki daina ganina a matsayin mai kwace...."
Ammy ta tsuke baki, tana dariya cikin raini ta ce:
"Kaddara ko? Kaddarar talauci?. Ki ji ni da kyau Amal, bana son ki cusa kanki a cikin zuciyar ɗana. Idan kika ci gaba da kusantarsa, sai kin ga abin da bai miki daɗi ba!.."
Abbah ya ɗaga hannu cikin natsuwa ya ce:
"Maryam! Iska ce ta fi zafi yanzu. Ki bari nayi magana..."
Ya kalli Amal da ta sunkuyar da kai.
"Amal, na san kina cikin tashin hankali. Amma ki sani, ba wanda zai iya raba soyayya ta gaskiya da niyyar Allah.
Ni da kaina na ga irin ruɗanin da Maleekh yake ciki, kuma wannan abu ba zai daidaita sai an zauna an fahimta..."
Ya kalli Maleekh da idanu masu nauyi sannan ya ce
"Kai kuma, Maleekh, daga yau ban so in sake jin tashin hankali daga gareka.
Idan wannan soyayyar taka gaskiya ce, za mu bi ta hanya mai kyau. Amma idan wata zuciya ce ta hauka, ka kwantar da kai ka gyara halinka..."
Maleekh ya sauƙe numfashi, yana girgiza kai ya ce:
"Abbah, wallahi bana hauka.
Ni dai ba zan bar Amal ba. Idan za’a hukunta ni saboda haka, to na amince..."
Abbah da murya mai tausayi ya ce:
"To idan haka ne, za mu fara da sulhu.
Na ƙira ki (ya nuna Amal) da ke (ya nuna Farha) domin yau in ji gaskiya daga bakin kowanku.
Saboda wannan soyayyar ta zama rigima..."
Yana kallon su uku a jere Maleekh, Amal, Farha.
Abbah ya sauƙe murya cikin tausayi ya ce:
"Wannan gida nawa ne. Ba zan bari soyayya ta zama dalilin rarrabuwar kai ba. Amma duk wanda ya ci gaba da tada hankali to dole sai ya fita daga rayuwarmu..."
Amal ta share hawaye, ta yi murmushin ƙarfin hali. Maleekh ya ɗaga kai yana kallon mahaifinsa da girmamawa, sannan ya kama hannun Amal a hankali yana farin cikin haɗuwarsu. Abbah ya yi shiru, ya zuba musu ido cikin tausayi, yayin da Ammy ta ɗauke kai tana jin haushi...
Maleekh cikin murya mai taushi ya ce:
“Abbah, ni fa ba zan bari a ɗaura auren Amal da wani ba. Tunda rayuwata ta haɗu da tata, ita ce nake so, kuma ba zan iya rabuwa da ita ba.”
Ammy tana huci ta ce
“Ka daina faɗin hakan, Maleekh! Wallahi bana so inji sunan wannan yarinyar a bakinka. Yarinyar da bata da asali, jikan talakawa, matsiyaciyar da ta lalata gidanmu! Ba zan yarda ka aureta ba!”
Maleekh ya ɗaga kai yana kallonta kai tsaye ya ce:
“Ammy, ki ce komai, amma ba zaki raba ni da ita ba. Ni Amal zan aura, ko da zan rasa komai.”
Ammy ta miƙe tsaye tana daka masa tsawa..
“To shikenan! Idan har ka nace zaka auri wannan yarinyar, to sai ka aura da Farha a lokaci guda. Ita da Amal! Wannan shine sharadina, kuma haka na tsara da mahaifinka, in shi ya kasa sanar maka to ni zan faɗa domin ba tsoronka nake ji ba..!”
Abbah ya ce cikin murya mai nutsuwa..
“Ka ji abin da mahaifiyarka tace, yarona. Ka yarda da ita. Ita uwa ce. Ka faranta mata, ka bi umarninta. Ka aure su duka biyun, Allah zai sa albarka.”..
Ya kalli Farha, wacce ke zaune cikin jin daɗi da ƙasa da murya:
“Ke kuma Farha, na roƙeki da ki riƙe Amal, ki zauna da ita lafiya. Bana son tashin hankali a cikin gidan.”
Sai ya kalli Amal, wacce take gefe, idonta cike da hawaye..
“Amal, kiyi haƙuri. Komai sai da jarumtaka. Wannan rayuwa ce, kuma idan kika dage da addu’a, Allah zai saka miki. Ki yadda a haɗa ku, domin zaman lafiya.”
Amal da murya mai rauni ta ce..
“Na ji Abbah… amma…” (ta kasa magana, tana share hawayenta)...
Maleekh ya ɗaga kai, yana murmushin dole, cikin dariyar da ke cike da ciwo ya ce:
“To, idan haka ne, zan yarda in aure su biyu…”
Kowa ya kalle shi da mamaki.
Sai ya juyar da kallonsa zuwa ga Farha.
Maleekh cikin murya mai ƙarfi, yana kallonta kai tsaye ya ce:
“Amma kafin hakan ta faru, akwai sharaɗi guda ɗaya. Idan Farha tana so in aureta, to sai ta zauna a gaban television ta amsa laifinta. A gaban kowa.”
Kowa ya juyo, yana kallonsa da tambaya.
Ammy ta ce:
“Laifi kuma? Wane laifi?”
Maleekh yana numfasawa cikin fushi ya ce:
“Laifin da ta aikata wa Amal. Farha ce ta haɗa shirin da kawayenta suka tozarta Amal, suka kai ta gidan club, suka mata ƙaryar cewa na ina wurin, sannan suka yi sharri da cewa ta zubar da ciki! Duk ita ce ta tsara komai, saboda kishin da take yi. Sai ta faɗi gaskiya a gaban kowa kafin wannan auren ya tabbata!”
Faloo ya ɗauki shiru.
Farha ta zaro ido, ta kasa motsi.
Ammy ta kalle ta cikin mamaki.
Abbah ya ɗan murmusa, yana kallon Maleekh cikin gamsuwa da jarumtar sa.
Maleekh ya miƙe ya ƙarasa kusa da Farha yana faɗin
“Idan kina so a ce ni mijinki ne, sai kin faɗi gaskiya yau. Idan ba haka ba, auren nan ba zai taɓa faruwa ba.”
Amal ta ɗago kai, hawaye suna sauƙa a kumatunta, amma bata ce komai ba.
Farha ta fara kuka tana faɗin:
"Wallahi Ammy kuyi hakuri, ba haka nake nufi ba… kawai ina son… ina son Maleekh ne shi yasa nayi wannan sharrin. Ban san zai kai haka ba..."
Abbah ya juyo da sauri, yana duban ta da fushi ya ce:
"Farha! Kin san abinda kika aikata kuwa? Kin yi ƙarya akan yarinya marar laifi, kin wulakanta sunanta a gaban duniya! Wannan abin kunya ne, har ga iyayenki!"
Ammy ta share gumin fuska da mayafi tana faɗin:
"To ai abunda ya wuce ya wuce, ba sai an je Television ba. Me kake nufi Maleekh? Kanaso ka zubar da mutuncin ‘yar uwarka ne saboda waccan marainiya? Hakan ba za ta iya dawo da darajarta ba."
Maleekh ya ɗago kai, idonsa ya rine da ƙwalla, amma muryarsa cike da ƙarfi ya ce:
"OK. To a idonku Amal ba ta da daraja, ko? Fine. Amma a idon al’umma tanada matsayi. Kuma zan dawo da martabarta, ta hanyar wanke sunanta daga ƙarya da zargi. Na ɗauki alkawari a gaban kowa sai na goge wannan ƙazantar da aka ɗora mata."
Sai ya juyo da fushi ya dubi Farha:
"Ki tashi yanzu mu tafi kamfani. A gaban kowa, a gaban ‘yan jarida da kafafen TV, zaki faɗi gaskiya. Zaki faɗi abinda kika aikata da bakin ki!"
Farha ta dafe ƙirjinta cikin tsoro, tana kallon Ammy:
"Ammy don Allah… ki ce masa ya barni. Na tuba wallahi…"
Ammy ta ce cikin gaggawa:
"Ba sai an kai hakan ga jama’a ba Maleekh. Ka daina. Wannan magana ta gida ce, mu rufe ta a gida."
Abbah ya sau numfashi yana tsaki ya ce:
"A’a. Ba a rufe gaskiya da sirri. Farha, tashi ku tafi. Ka ji, Maleekh? Kaje ka tabbatar gaskiya ta fito. Ba mu da wani abin da muke tsoro idan gaskiya ce."
Maleekh ya ɗauki makullin motarsa yana cewa cikin daci:
"Mu tafi yanzu. Amma Amal ma zata tafi. Domin yau zan tabbatar duniya ta san cewa ita ce wacce aka zalunta, ba wacce ta aikata zunubi ba."
Sai suka fita gaba ɗaya, Maleekh, Farha, Amal.
Zasu nufi kamfanin CashTalk Media House, da niyyar wanke gaskiya a gaban kowa...
Ammy tana zaune a kujera, tana riƙe da kai cikin damuwa, yayin da Arfat da Islam ke kallonta cikin shiru, Farha na kuka a wajen ƙofa, sai dai ba mai dawowa daga wannan hukuncin da Maleekh ya ɗauka...
🎬 GASKIYA ZATA BAYYANA...
Location: babban studio na TV station, mutane da yawa sun hallara, cameras suna kunne, haske na ɗaukar fuska, murya tana rawa. A gefe Maleekh da Amal suna tsaye, fuskokinsu a cike da damuwa. A gefe kuma Farha ce tana sanye da farar riga mai sauƙi, ba kwalliya, idonta jawur kamar marar bacci, tana kallon camera a gajiye...
🎙️Presenter a hankali ya furta:
“Yanzu muna da bayani mai mahimmanci wanda zai iya canza fahimtar jama’a game da shari’ar Amal da Maleekh... Gaskiya zata fito daga bakin Farha da likita da suka san komai.”
Camera ta tsaya kan Farha. Microphone a gabanta. Jikinta yana rawa...
Cikin kuka ta fara da cewa:
“Ni... ni ce... na jawo komai! 😭
Ni ce na tura Amal gidan club... Na yi mata ƙaryar cewa Maleekh yana can yana jiran ta...
Na kuma tura wasu ƙawayena suka ba ta kwayoyi, suka haɗa mata da abin sha da maye...
Lokacin da ta suma, suka kwantar da ita a toilet suka zuba mata jini a jikinta...
Sannan suka ajiye maganin zubar da ciki a gefe don a nuna kamar ita ta yi ne!”
(ta share hawaye, tana karkarwa)
“Ni... ni ce silar rabuwar da suka shiga. Saboda kishi, saboda tsanar ganin Maleekh na son wata mace fiye da ni...”
(Camera ta ɗan matsa kusa. A gefe Amal ta fashe da kuka, tana riƙe da hannun Maleekh. Abbah yana kallon TV a gida yana girgiza kai. Inna kuwa ta dafe ƙirji tana kuka tana faɗin:
“Subhanallah! Ashe hakane? gaskiyar ta fito... Ashe jikata bata aikata komai ba...”
Farha: ta cigaba da kuka sosai tana bayani..
“Bayan haka... na je wurin Doctor ɗin da ya karɓi Amal lokacin da Maleekh ya kaita asibiti.
Na ba shi kuɗi masu yawa... Na roƙe shi da ya rubuta result ɗin ƙaryar cewa Amal ta zubar da cikin wata huɗu...
Ya yarda... ya karɓi kuɗin... ya karya gaskiya saboda ni... saboda son zuciyata!”
(Ta durƙusa ƙasa tana kuka sosai. Muryar ta na rawa.)
“Na aikata zunubi! Na lalata rayuwar mutane biyu da soyayyarsu ta gaskiya! Na aikata laifi ga Allah, ga Maleekh, ga Amal...”
(Camera ta motsa zuwa likita wanda yake zaune a gefe yana sanye da farar rigar doctors. Ga fuska a farfashe duk ya kumbura kamar wanda yayi hatsarin mota, wannan hukuncin Maleekh ne kafin ya bayyanar da a gaban television..)
Doctor ya ce:
“Eh... abin da Farha ta faɗa gaskiya ne. Ni na karɓi kuɗi daga gareta.
Na rubuta result ɗin ƙarya domin na kare mata suna... Na karya alƙawarin da na ɗauka a matsayin likita.
Na tuba... Na nemi gafara daga Allah da daga waɗanda na cuta.”
(Camera ta dawo kan Farha da Amal. Amal ta kasa tsayuwa, ta durƙusa tana kuka. Maleekh ya rungume ta yana lallashi cikin taushi, ya ce:)
“Na yarda dake, Amal... na yarda dake tun farko, sai dai zuciyata ta kasa yarda da gaskiyata. Amma yanzu na san... kina da gaskiya tun farko.”
Farha tana kuka sosai, tana faɗin:
“Don Allah ku yafe mini... Wallahi ba da gangan nake son kashe muku soyayya ba, kawai zuciyata ce ta rufe ni da kishi!”
(Camera ta rufe da slow zoom inda Amal da Maleekh suka rungume juna tana kuka, Inna tana kallon TV tana hawaye, Abbah yana dafe kai da tausayi, yayin da Farha ta durƙusa tana kuka tana karanto istigfari...)
🎬 Fade out background voice:
“Gaskiya ba ta ɓuya. Ko da ta jinkirta, sai ta fito...”
NEXT NEXT NEXT...
asmeetahwriter✍️
*🎤AMALEEKH🎤*
*AMAL AND MALEEKH*
Together, they stand between love and loyalty, between public duty and private longing, two hearts bound by fate, yet tested by truth.
*Writing and Storytelling By*
Asma'u Muhammad Auwal
Asmeetah writer
*HASKEN JAJIRTATTU*
*MARUBUCIYAR:*
*Matar Damisa*
*My Enemy*
*Hasken Ruhi*
*And know AMALEEKH*
Bauchi State Nigeria.
*WhatsApp 09065443871*
Follow my channel 👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VbBCNlqJUM2RQwWncg43
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.
"Jajirtattu mu ne ƙarfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faɗuwa. Mu ne tarihi da ake ginawa!" 💪🔥✨
BOOK ONE page 59 to 60
🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹🌹
🌹🌹🌹
🌹🌹
🌹
Daga cikin gidansu Maleekh labarai a TV suna nuna yadda Doctor da Farha suka amsa laifinsu. Wani ɗan shiru ne ya rufe falon. Bayan nan duniya ta fara girgiza da labarin…
TV na kunne, labarin yana fita:
“...an tabbatar da cewa Farha, tare da haɗin gwiwar wani likita, sun yi amfani da miyagun dabaru wajen cutar da Amal... Hukuma ta tabbatar da kama su don bincike...”
Ammy ta miƙe a hankali daga kujera, tana kallon TV da rikitattun idanuwa.
cikin zafin rai ta ce:
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Maleekh kenan, abun nakan har ya kai ga yaudara mu? har zaka kai ƴar uwarsa hukuma? Ya kai ƴar uwarsa hukuma? Wannan wane irin hauka ne haka?!”
Abbah ya kalli Ammy cikin nutsuwa sannan ta ce
“Maryam ki kwantar da hankalinki... gaskiya dole ta bayyana, ko ta ɓoye shekaru goma. Amma ni ma ban yarda da matakin da Maleekh ya ɗauka ba. Ya kamata ya bari mu muyi hukunci a gida, ba a kai hukuma kai tsaye ba.”
Ammy ta girgiza kai tana hawaye.
“A’a Alhaji! Wannan abun zai tarwatsa zumunci! Farha ai ɗiyar ƙanwata ce... yanzu duk duniya sun ganta a TV kamar wata mai babban laifi, hakan ma bai wadatar ba har sai a haɗa da hukuma?..!”
Zayd ya shigo cikin fushi, yana ɗauke da wayarsa...Yana faɗin
“Abbah, Ammy... yanzu danginmu suna ƙira suna zagin Maleekh a WhatsApp group ɗin family! Wasu suna cewa Maleekh ya fifita wata ƴar talakawa akan jinin jikinsa... kuma nima nace Maleekh bai mun adalci ba, inda kara ai Farha ƙanwata ce jini ɗaya, shin zai iya aikata haka wa ƴar uwarsa uwa ɗaya uba ɗaya?...”
Ammy ta kalli Zayd da ido mai cike da hawaye da fushi ta ce:
“Ai wannan abin kunya ne Maleekh ya aikata, ni dana haife shi ma zai iya yi mun abunda yayi wa Farha balle, Hmmm! yau ya juya mana baya saboda yarinyar da bamu san asalinta ba!”
Abbah ya miƙe, yana kallon su sannan ya ce
“Kuyi shiru kawai! Ku manta da jinin dangi idan ana magana akan gaskiya. Farha ta yi abin da ba ta kamata ba. Likita ya ci amanar ƙasa. Kuma Maleekh yayi abin da ya dace, ya tabbatar da gaskiya. Idan mu ne, mu ma da za mu yi haka!”...
Ammy a hargitse tana kallon Abbah ta ce
"Eh! Ai daman kai da ɗanka bakwa son farin ciki na, duk abinda yayi da mai kyau da marar kyau koda yaushe kana kan goya masa baya, to wallahi zaku ji kunyar duniya ne wata rana..."
Daga nan Ammy ta bar falon..
Shima Zayd a fusace ya wuce ɗakin da yake..
Shiru ya rufe falon. Sai wayar Abbah da ke yin ƙara, ƙira daga wurin ɗan uwansa, Malam Salihu, daga Kano....
Sai ji nayi ABBAH na cewa:
“Salihu, naji... eh, gaskiya ne. Eh, shi ya kai Farha hukuma... to ai doka ta fi zumunci idan zunubi ya wuce ƙima. Ka daina magana da fushi, mu ma muna cikin zafin lamarin...”
Daga nan ya kashe wayar a hankali yana sakin numfashi...
Ƴan uwa sun taru suna kallon TV. Muryar TV na fita, hoton Farha tana riƙe da hannun Police...
Sam babu wanda yaji daɗin wannan al’amarin..
Daga ƙasar london, saƙo ya iske su...
Mahaifin Farha kamar zai yi hauka, ya rasa yanda zai yi, gaba ɗaya yaji ya tsani Maleekh da yarinyar da yayi wa ɗiyarsa wulakanci akan ta...
Mahaifiyarta tana kuka tana faɗin.
“Ya Allah, wannan wane irin abin kunya ne? Maleekh ya lalata sunanmu! Ashe Maleekh bashi da tausayi, sai ya wulaƙanta ƴar uwarsa haka, me muka masa haka?”
Mahaifin yana huci ya ce:
“Wallahi wannan Maleekh ɗin ya raina mu. Ba zai ƙara samun goyon bayanmu ba. Ya fifita wata banza akan jininsa, yanzu abun da zamu yi shine zamu koma Nigeria, domin bazan bari ɗiyata ta wulaƙanta ba...!”
Hajiya Sa’adatu uwar Farha ta ɗauki waya ta ƙira Zayd, bugu ɗaya ya ɗauka. Yana ɗaga wa ta fara zaginsa da cewa:
"Kai wawa ne marar amfani, kana kallon ina har Maleekh zai tozarta ƴar uwarka haka? Meye amfanin zamanka a Nigeria idan bazaka iya kula da Sister ka ba? Mun tura ka can ne fa akan ka sa ido akan Family gidan, sannan ka rasa Maleekh da yarinyar da yake nema amma har yanzu bamu ga wani abun arziki ba, Zayd kana ji ba? Aiki na ƙarshe da zan saka yi mun shine, inaso ka kashe mun Maleekh, bana so na ƙara ganinsa a duniya, daman abu ɗaya ne yasa zan haɗa ƴata da shi shine munaso mu karɓe duniyar da mahaifinsa yake da shi, da shi kansa Maleekh ɗin amma tin da hakan bai yi ba, just ka kawar da shi daga doron duniya...."
Daga nan suka katse wayar...
A washegari jirgin su zai ɗaga zuwa Nigeria...
JAMA’A A SOCIAL MEDIAyy
Hotuna na yawo a Instagram, TikTok, da Twitter. Hashtag ɗin #JusticeForAmal da #FarhaTrial sun ɗauki hankalin jama’a...
COMMENT 1:
“Allah ya saka wa Amal! Yau kowa ya ga irin zaluncin masu kuɗi, Allah ya tabbatar da gaskiyar Amal!”
COMMENT 2:
“Farha da likita sun jawo wa family ɗin su abun kunya. Amma ai gaskiya ta fi komai!”
COMMENT 3:
“Maleekh ya yi abin da ɗan gaske zai yi, sai dai ya lalata zumunci, meyasa bai yi hakuri an magance matsalar a cikin gida ba?”
A TV, ana nuna Amal tana fita daga ofishin lawyers da hawaye a idonta duniya ta fara rarrabe tsakanin masu goyon bayan Amal da masu kare Farha...
GIDANSU AMAL
Inna tana kallo, tana jin labarin da murmushi mai sosa zuciya.
“To Alhamdulillah... Allah ya fito mana da gaskiya. Amma wannan rikici ne da zai shude, mu dai mu ci gaba da addu’a. Gaskiya da zuciya sun fi dangi da dukiya.”
Amal wacce ta dawo gida ta share hawayenta tana kallon Inna..
“Ni banji daɗi da ya kai su kotu ba, Inna... amma ni dai na gode Allah da gaskiya ta fito fili. Duk duniya ta san ba laifi nayi ba.”
Inna ta ɗora hannu a kafaɗarta tana faɗin
“Toh hakane Amatu. Komai ya wuce, sai ki tashi ki roƙi Allah ya sassauta zuciyoyin jama’a. Duniya da baka zaune da ita lafiya, sai gaskiya ta baka kariya.”
Su Malam Yawale sun zuba ido basa cewa komai, tin da Auren nan ya wargaje gaba ɗaya suka cire hannunsu akan lamarin Amal...amma har yanzu suna zaune a gidan..
A wannan ƴan kwanaki.
Ba Maleekh ba hatta Abbah ya samu matsin lamba a wurin ƴan uwa... domin duk dangi babu wanda ya goyi bayan Maleekh...
Abbah yana zaune a part ɗina bakin gado yana ta tunanin wannan al’amarin..
“Lokacin da gaskiya ta fito, ba kowa ne zai iya jure ta ba. Amma wanda yake da gaskiya, ko duniya ta juya, Allah zai tsaya masa.”
Abbah yana maganar zuci...
A babban falo.
Maleekh ya shigo cikin gidan, fuskar sa cike da gajiya, idanunsa sun ɗan kumbura kamar wanda bai kwanta ba tun jiya. Yana shigowa falon Ammy ta taso a zabure. Kafin ya iya cewa komai, ta ɗaga hannu ta zabga masa mari sau ɗaya, sau biyu, sau uku, sau huɗu, har sau biyar a take... har sai da gefe na bakinsa ya fitar da jini, abunka da mai taushin lips...
AMMY cikin ɗaga murya take faɗin:
“Wai me kake nufi da wannan haukan, Maleekh?! Aure kai da Amal na janye! Na janye wallahi! Ni ce na yarda akan ka aure ta da Farha amma yanzu na fasa! Na fasa gaba ɗaya!”....
Maleekh yana tsaye cikin shiru, hannayensa a sake alamun babu wani ƙarfi a tattare da shi, ga saƙonni na zagi da ƴan uwa suke ta turo masa, yana ɗan girgiza kai cikin kunar rai.
AMMY ta cigaba da cewa
“Yanzu ina Farha? Kasa an kaita cell ko? Daga nan sai kotu! Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Maleekh, anya ni ce na haife ka kuwa?! Ka zubar mana da mutunci a idon duniya! Kai ɗa ne da ake alfahari da shi yanzu ka zama abin tausayi da zargi!”
Da sauri Abbah ya fito daga upstairs, yana sanye da jallabiya, yana kallon Ammy da Maleekh ya ƙarasa kusa da su.
Cikin
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 39 Chapter of 62