Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ƙudin littafin nan 500 Naira only Zaki biya ta wannan account ɗin👇🏻 0020428430 Ishaq Fatima A GTBank KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya 07040402435, 0903 056 9336 *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k #Mutallab Asad #Ƴan Tagwaye #Nana Diso #Billy S Fari. *MUTALLAB ASAD MUTALLAB*                 (MAM) NA BILLY S FARI & NANA DISO    *SHAFI NA TARA* _RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU._ _TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA_ Sai data kashe motar sannan tafito ta shiga cikin gidan batare data amsa gaisuwar da ma'aikatan gidan keyi mata ba, tana shiga palourn tashiga ƙwalawa mutanen gidan kira, "Maama, grandma, Aunties kufito gani naƙaraso". tafaɗa tana faɗawa kan kujera haɗe da maida numfashi ɗaya bayan ɗaya. Wata dattijuwace tafara fitowa tana faɗin "Shalele ɗiyar Dadynta har kin ƙaraso". Murmushi Meenal tayi tace,  "Eh mana ba kun taso ni ba cikin uwar ranar nan, wai ina suke ne grandama nifa bana son jira da ɓata lokaci, yanzu nan sai nayi tafiyata gurin ƙawayena mu shirya komai tare dasu". "To mara kunya ai sai ki tashi ki tafi dama ba don zuwa gidan nan kikeyi ba sai dole kin zaɓi matar ubanki da ubanki". Maama ɗinta dake shigowa palourn tare da Aunty Nusrah tafaɗa tana zaunawa kusa da Meenal ɗin data shiga cuno baki jin mahaifiyarta ta zagi mahaifin nata, Aunty Nusy ce data shigo palourn yanzu tafara yimata kirari tana faɗin "Kaga ɗiyar Dadynta mai wanka da swan, ja ragamarki ƴar gaban goshi taka kowa ki wuce lafiya, yi lokacinki ƙara dana wasu ƴan baƙinciki sai dai su mutu, ƴar gidan Dady kike kune gari idan babu ku babu gari ƴan matan Maama". Dariya Meenal tayi tare da buɗe ƙaramar handbag ɗinta ta swag ta fiddo rafar ƴan naira hamsin-hamsin ta jefawa Aunty Nusy tana cewa, "Yi maleji da wannan Aunty Nusy ban fito da kuɗi ba amma kin bini sauran tukuici". Ihu Aunty Nusy ta saka bayan ta daɓe kuɗin tana shinshina rafar cike da farinciki, Maama kuwa kallon Meenal tayi tace, "Love ina fatar wannan sakarar matar baban taki batasan da wannan zancen ba ko?" "And so what idan ma ta sani Maama, ni kina bani mamaki da kike tunanin zata iya hana Dad ɗina yimini abu, wacece ita?" Kafin taƙarasa Aunty Nusy data gama adana kuɗinta a gefen sket tace "Matar ubanki mana da kika kasa fitarwa Meenal, ni wlh Maama bansan tayaya har yanzu Meenal ta kasa korar shegiyar matar nan ba". Maama da kullum da wannan takaicin take kwana a ranta ta kalli Meenal tace "Waya sani ko tafi ƙarfin tane shiyasa takasa tsinana komai take nema tabani kunya sai kace ba ƴata ba har yanzu nakasa jin komai daga gareta". Sai da Meenal ta ɓata rai sannan tace, "Uhm Maama kenan dake da Nusy bakusan ko waye  matarnan ba, wallahi wulaƙanci  da cin mutumci babu wanda banayi mata har wanda baku sani nayi mata ba, but  wlh ko ajikinta fa, idan nice ita yadda Dadyna ke wulaƙantata akaina bazan taba zama ba amma still  ko ajikinta. Fuska a ɗaure Maama ta kalli ƴar tata tace, "Kin taɓa zagin ubanta?" "No Maama ban taɓa ba". Meenal ta bata amsa tana kallonsa, "Kin taɓa marinta?" "Ban taɓa ba Aunty Nusy taya zan iya hakan". "Ok sai kije yanzu kifara dasu dole ta magantu a wannan karon".  Maama ta faɗa tana maida kallonsa ga tv fuskar nan a ɗauke ba ɗigon annuri ko ɗaya akai, Nusy ce taci gaba da cewa, "Look Meenal su matan uba da kike gani azzalumai ne, idan bakiyi da gaske ba kina gani zasu hana mahaifinki yimiki komai, dole ki saka wando ɗaya da ita sannan ki ɗauri aniyar ko ke ko ita a gidan, hakan kawai zai sa kimorewa dukiyar mahaifinki cikin kwanciyar hankali da salama, Azzaluma mata ta ina zata damu tunda bata so takoma cin masara da sawa a gidan father, ai idan tata ƴar ce take riƙewa bazata dinga saka mata baki ba kamar yanda take yimiki ba ke da mahaifinki ba". "Ni dai mubar wannan zancen zan ji da ita Maama fiye da tunaninmu, bakusan yadda Dady ke ƙaunata ba da kunsani da baza ku koma ɓata bakinku ba abanza, yanzu muyi zancen birthdayparty na, a ina kuke tunani za'a yi shagalin, wani gurin event ya dace da ƴar gidan Maama". Ta ƙare zancen cike da zolayar mahaifiyar tata data lura haushinta take ji na rashin fidda Mommy a gidan mahaifinta, harara Maama ta balla mata kafin tace, "Ƴar gidan Dady da Mommy dai, wace Maama ɗin kuma?" Nusrah ce da tunda suka zo wajen bata ce komai ba tayi hamma tana rufe baki haɗe da cewa, "Am sleepy nidai bari nashiga daga ciki." Daman itace kaɗai bata saka bakinta aduk kalar zagin da za'ayiwa Mommy, Bata sakawa sannan kuma bata hanawa iyakarta dasu idanuwa, tayi ƙoƙari tacewa Meenal kedai kiyi mai kyau don ki girbi mai kyau idan taji suna hure mata kunne, don hatta grandama haka ake zaunawa da ita a zabe Mommy tas, ita har ma Dadyn haɗawa takeyi dashi babu ruwan ta, wannan dalilin yasa Meenal ɗin bata shiri da Aunty Nusrah ita kuma bata shiga harkarta. Muryar Grandma data fito daga ɗauki Meenal taji tana cewa,  "Ku kama Abnu event center mana tunda dai uban naki nada halin biya indai ba matarsa ta hanasa ba." Duk abun Maama sai data zaro idanuwa tace, "Grandama Abun event center fa kika ce? Kusan fa 4million ake kama wajen". Meenal tace "So what Maama, Dady zai iya biya mani ko nawa ne tunda yana da kuɗin bawai baida su ba?" "Barta Meenal tahana ya kashe maki yaje ya kashema wata banzar dako haihuwa batayi dashi ba ita da ƴan uwanta". "Duk da haka grandama is too expensive fa, birthday fa ne ba bikin aure ba?" Tsabar takaici Grandma taja tsaki haɗe da cewa, "Tunda kinfison uban nata yadinga ɗaukar kuɗi yana miƙawa matarsa akan ɗiyarki sai kubar shi". Tabar wajen ranta aɓace ganin Mommyna har yanzu takasa fahimtar asarar data takawa kanta na baro gidan Dadyn Meenal da ayanzu ne zatayi amfani da damar data samu na ƴarta suma su samu wani abun, Aunty Nusy ce ta kalli Maama tace, "Dafa gaskiyar grandama Maama, matarnan da kike gani ba'a banza tabar Dadyn Meenal ba, kigafa motar da take hawa, itace kika zo da ita Meenal ko?" "Yeah! But that one is nothing akan abinda Dadyna ke kashe mani". Wani baƙin cikine ya tasowa Maama jin hakan tace "Love dama ba motarki bace?" "No Motarta ce Maama kusan 8m yasiya mata a lokacin da zai canza mani rawa ni da ya Kamal". Cike da takaici Maama tace "Dan ubanki shine har kike faɗa bakisa Dadynki ya karɓe ya baki ba ko kika sa aka saceta kin kawowa uwarki ta hau ba, wlh na tsani wannan ƴar gidan matsiyatan, shi Kamal uwar me yakeyi a Egypt ɗin da har yanzu bai dawo ba". "Maama comedown mana.. wanna is not a big deal fa, mayi maganar daga baya, oya Aunty Nusy call event center muji tsarinsu." Da sauri Nusy ta ɗakko wayartaa ɗaki ta dawo ta zauna ta kirasu suka yimata bayanin komai sannan ta ajiyar wayar tana jan ajiyar zuciya jin yawan kuɗin haɗe da cewa, "Dady girl kinji komai da komai 4.5m ne and su zasu bada abinci da komai har deco". "Haƙan yayi zan sanarwa Dady". Ihu Nusy ta saki tana cewa, "kice yarinyar Dady zata fasa garinnan da labarin birthday ɗinta, Huhuhu gobe akwai ɗaukar magana in and out kuma everywhere, zamu gas masu kai mu kuma tayar masu da hankali". "Ana magana Aunty Nusy, Bari kawai natafi pls ku turawa duk wasu friends and family nina wuce sai gobe idan mun haɗu". Meenal tafaɗa tana miƙewa Maama tace, "To da zaki tafi ubanki ne zai bani kuɗin kayan da zan saka?" Kallonta Meenal tayi tace, "Maama 1m ɗin dana turo maki shekaranjiya fa, me kikayi da ita?" Ɓata rai Maama tayi tana harararsa tace, "Ban sani ba don ubanki". "Sorry shikenan kuje keda su grandama kowannen ku yazaɓi kaya a Amni store kuturomin sai na haɗawa Dady a list ɗin abinda nake so yabiya zan kuma turo mako kuɗin sai dai bada yawa ba kinga gobe akwai hidima gabana", miƙewa  Maama tayi ta rungumeta tana cewa, "ko kefa bye bye see you tomorrow". Tare da ɗaya mata hannu bayan sunyi breaking hug ɗin. Meenal na barin gidan bata tsaya ko ina ba sai gidansu Zee, daga nan suka kira sauran ƙawayenta suka shiga tsara yanda komai zai gudana ta wajensu, basu tashi wajen ba sai da suka sanar da duka sauran friends ɗin su tace suma su gayyato nasu ƙawayen da family nasu. Nan tayiwa Dady waya yaturo mata kuɗi na abubuwan da zata siya da zata saka gobe kama daga kan zirga-zirga da za'a yi da motoci, kayan da zata saka da kuma takalmi da komai ya turo mata 3M ta kashesu tare da ƙawayenta tas dasu Maama data yiwa alƙawari kamin tadawo gidan ta saka delivery yakai masu mama nasu gida. Yanda taga babbar ƙawar Tata Zee tunda aka fara zancen bata ce komai ba yasa tana shiga gida bayan tayi parking takira lambarta, bugu ɗaya ta ɗaya tace, "Bestie naji Baki ce komai ba wajen shirye-shiryen abinda za'a yi gobe na birthday na, to na siya mana kayan da zamu saka Ni dake don Allah kada ki kwafsa mani". "Meenal you mean wai da gaske celebrating zakiyi kuma a Abnu event center." "Eh mana kina kokwantone?" "Kinsan maƙudan kuɗin da ake kashewa kuwa wajen? Akan birthday zakije ki almubazzarar da tarin kuɗaɗe masu matuƙar yawa haka bayan..." "Hold it zee..zaki zo ko baza ki zo ba?" Meenal tafaɗa ranta aɗan ɓaci tana fitowa daga cikin motar, "Meenal ba bazan zo bane, amma wajen da gwamnoni da manyan ƴan siyasa ke taro zakiyi celebrating na birthday wajen? Kuɗin da sunyi yawa Meenal anya kina tuna gobenki kuwa". "Look zee nafa lura kin fara mini baƙin ciki, kuɗin nan fa na ubanane kin ga ne?" "Is ok Meenal ya Isa haka kada ki zageni, kuje kiyi shagaliki ni bazanzo ba". Tana gama faɗar hakan ta kashe wayarta. Wani mugun tsaki Meenal taja tana rufe motar tare dasa masu aiki su kwashe kayan dake ciki su shigo mata dasu, tana shiga ta yadda Dady zaune a palour, da sauri ta ƙarara wajensa ta rungumesa tana faɗin, "I miss you Dady". "Miss you too Babyn Dady, tun ɗazu nakasa kwanciya ina jiranki kidawo ki sanarmin inda za'a kama na tura masu kuɗinsu da wuri kada suyi Mali African time". Cikin shagwaɓe murya tace, "Dady Abnu event center na kama hop kuma zaka je?" "Wow abu dole my Baby, akwai wani yaro dake aiki wajen dana sani, i think kuɗinsu bazai wuce 4.m ba bar nakirasa ya bani details na account ɗinsu na tura masu, hop shikenan babu wani abu da kike buƙata". "Yes Dady but banda isasshen kuɗi a hannuna fa". "Never mind, kizo da safe nabaki, ƙarfe nawa ne kuka tsara birthdayparty ɗin?" "8 na dare zuwa 10". "That's good, lokacin kowa na gida, kije ki huta sai da safe ko?" hugging ɗinsa ta sakeyi haɗe da cewa, "Ok Dad thank you so much". "Take care my Baby". Ya faɗa yana ɗaga mata hannu don tuni ta nufi benen zuwa ɗalibta, Mommy dake ƙokarin fitowa daga ɗaƙi sai data dakata jin inda Meenal zatayi taron birthdayparty ɗinta da sai yanzu tasan da zancen, Abnu event center taƙara maimaitawa tana fitowa daga cikin ɗakin batare data san maganar tafito fili ba sai Jin muryar Dady tayi yace, "Yason ranki? ƴata ce kuma kuɗi na ne". Kafin ta tanka Meenal da bata ida ƙarasa hayewa ba tace, "Dama Dady nasan zatayi mini baƙin ciki saboda ni ba ƴarta bace shiyasa take jin haushi". "Ƙyaleta baby ai sai dai kuwa baƙin cikin yasan yanda zaiyi da ita". Ya miƙe tare da shigewarsa sashensa, Meenal kuwa warar ɗuwawu tayi mata sannan ta haye abunta cike dajin daɗi. A ɓangaren Mommy kuwa har ga Allah ba baƙin cikin kashe mata kuɗin takeyi ba, mamakin kawai inda Meenal takai kanta da Allah bai kaita ba takeyi, don kuwa duk babu wanda bai san cewa wajen na manyan mutane da hamshaƙan masu kuɗi bane da kuma ƴan siyasa. _(Ehmmm..bari dai muyi shiru kar muyi magana ƴar gidan Dady tace muma baƙin ciki mukeyi🙄🤭)_ Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only Zaki biya ta wannan account ɗin👇🏻 0020428430 Ishaq Fatima A GTBank KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya 07040402435, 0903 056 9336 *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k #Mutallab Asad #Ƴan Tagwaye #Nana Diso #Billy S Fari. *MUTALLAB ASAD MUTALLAB* (MAM) NA BILLY S FARI & NANA DISO *SHAFI NA GOMA.* _RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU._ _TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA_ Washegari kuwa yakama laraba, ƴan makaranta sunata shirye-shiryensu, ma'aikatan gidan kowa na gudanar da aikinsa, masu girka breakfast ma suna gudanar danasu, kasancewar yau girkin Aunty Amarya ne sai ya zamana itama tana kitchen ɗin ana haɗa breakfast da'ita. Ita kuwa Umma tunda ta tashi take jiran shigowar Jamil cike da farinciki don tasanar dashi nasarar da suka samu wajen Abba na ɗaukar nauyin karatun Sadeeq zuwa ƙasar U.S.A America,  gashi taga har bakwai tana ƙoƙarin gotawa bai shigo ba, ɗiyar tata kuma ƴar autarta wato Jidda ce ta shigo cikin ɗakin a shagwaɓe tana bubbuga ƙafafuwa hannunta riƙe da uniform ɗinta na school har lokacin bata shirya ba, miƙewa tayi daga kan gadonta ta nufi wajenta tana cewa, "ke lafiya? Me akayi kika shigo mani a haka? Ke shikenan a haka rayuwarki take babu damar a tashi da safe sai kin sani magana? Me yafaru naga uniform ɗinki a hannu har yanzu baki shirya ba?" sai data matso kwallan dake cikin idanuwanta sannan ta kalli mahaifiyartat tace "Umma ko ba uniform ɗina bane sukayi datti kuma sauran ba a goge suke ba, ni gaskiya yau bazanje makarantar ba sai dai idan na Afrah zaki karɓo mani nasaka." Murmushi Umma tayi tana girgiza kai kafin tace, "Yanzu shikenan akan ɗan wannan abun kike ɓata ranki Jidda hadda su hawaye? menene abun damuwa bayan kinsan da akwai na Afrah? Ba sai kije da kanki ki karɓe ba tunda yasan dai yanzu ba makarantar takeyi ba". "Ni bazan je ba ta renani Umma". "To shige muje ni nakarɓo Mali, me zatayi dasu idan bata baki ba tunda ancireta makarantar?" Umma tafaɗa tana wucewa gaba Jiddah tarufa mata baya cike da farinciki tana share ƙwalla, cike da soyayya Umma data juyo tana kallonta ta maka mata harara da wasa tana cewa "Ke bakisan ni banason wannan kukan naki ba yana ɗagamin hankali? Ke ko kunya bakyaji kin girma amma kullum sai yarinya kike sake koma mani?". Ɗan turo baki Jiddah tayi lokacin da suke bawan stairs ɗin tana ɓata rai kamar zatayi kuka Umma tace, "Ya isa haka dawasa nake yimaki, duk girman nan naki har yanzu baby nake kallonki bazan kasa ɗaukar gimarki ba, yanzu dai kiyi haƙuri tunda ga kayan ƴar uwarki sai kiyi amfani dasu, zan yiwa Abbanki magana a canzamiki wasu tare ma da wardrobe ɗin gaba ɗaya, ai ina Shikenan ko?" Rungumeta Jiddah tayi lokacin da suka ƙarasa hawowa saman tana dariya haɗe da cewa "Yauwa Ummata, shiyasa nake masifar sonki". Ba tare data amsar ba tana murmushi ta tura kofar ɗakin na Afrah, wanda hakan yasa afrah saurin ɗago idanuwanta daga saka takalminta da takeyi saye da uniform ɗin da Jamal yakawo mata sannan ya wuce ɗakin Abba gaishesa shiyasa ma basu haɗu da Umma ba, Ras! Umma taji gabanta ya daɗi lokacin da idanuwanta suka sauka akan Afrah ganin yadda tayi wani irin masifaffen kyau acikin sabbin uniform ɗin nata data saka, kamar Afrah ta san mene zuciyar Umma ta shiga karanto addu'o'i cikin ranta kafin cikin girmamawa tace, "Umma barka da safiya, ina kwana?" ta gaisheta lokaci ɗaya tana mai miƙewa daga tsugunnan da take. Wani kallo Umma tayi mata dake cike da hasada da kuma ƙiyayya na ganin da tayi mata a yanayin da bata taɓa tsammanin kasancewarta aciki ba kafin tace, "Ke ni ɗauke mun idanuwanki haka sai kace wata aljana". Ba musu Afrah ta ɗauke kanta ta mayar ƙasa sannan Umma tace, "Har kinyi shirin zuwa makarantar kenan? To kodai ji tsoron Allah kada kije ki biyewa mutane da abun magana baya yimusu wahala, yanzu ne zasuce anyi bambanci tsakaninki da ƴan uwanki da aka cireki a makarantar da sukeyi don bakida uwa agida bayan ko da anyi miki faɗa akan shegen lalacinki na gyarawa kutafi makaranta ba ji kikeyi ba, shiyasa ma banga laifin Abbanki ba ɗaya cireki gwara ki zauna wannan makarantar itace daidai da rashin son karatunki ko a samu ki sauya". Afrah dai batace komai ba don ita har mamakinsa takeyi nacewa bata don karatu, bayan ba daga gareta bane ciwone yake durƙufar da ita tare da hanata zuwa makarantar amma sai suyita ɗora laifin akanta bayan suma basu wuce Allah ya jarabcesu da ciwon ba, ƴar ajiyar zuciya ta sauke tana kallon ƴar uwar tata tace, "Jiddah lafiya naga baki shirya ba, kada fa kizo ki makara". Harararta Jidda tayi haɗe da cewa, "Meye damuwarki da hakan idan har na makara? ina ruwanki ne?" taƙarasa tana ƙara dallah mata wata harara. "Allah yabaki haƙuri". Afrah tafaɗa tana kai kallonta ga Umma ce data nufi wardrobe ɗin kayanta tana buɗe wa, a yadda kaɗai tagansu tsaf a gyare sai da abun ya ɓakanta mata zuciya tare dajin wani ɓaci rai ya tunƙusheta duk da rashin yawansu, ba kamar na Jidda ba da kusan kullum sai tasaka ƴan aiki sun gyara mata amma kuma kullum ba kyan gani, ita dai Afrah batace komai ba sai ma mamaki daya cikata ganin yadda Umma ke zubo mata kayannata a ƙasa tamkar wacce tayi sata ko ake neman wani abu a wajenta, sai da umma tawatso kayan duka aƙasa kafin ta kalleta cike da takaici tace, "Wai a ina kika kai uniform ɗinki ne kina kallo ina faman zubo kaya a ƙasa bazaki faɗa ba tunda ancireki daga makarantar ai sai kiba Jiddah". "Bansan su kike nema ba Umma shiyasa". Afrah ta faɗa tare da isowa gaban wardrobe ɗin data yiwa wani irin tsari na musamman ɓangarori daban daban, gefe ɗaya kayanta ne na zaman gida, ɗaya gefen kayan fita haka idan ta kama, daga ƙasa kuma kayanta ne na makarantar islamiya, gefe kuma kayan boko da duk wani tarkacen daya shafi karatunta na boko, sai kuma ƴar lokar dake laƙe can ƙasa gabaɗaya da take jefa undies ɗinta da pad, ƙasan ta ɗan duƙa inda Umma ke tsaye daga gefen da take sanya kayanta na boko ta ɗakko uniform ɗin acan ƙasa data kaisu ta miƙawa Jidda, sai data harareta sannan ta wafci kayan tayi tafiyarta Umma ma tarufa mata baya, kallo ta bisu dashi har suka fice a hankali ta sausauke ajiyar zuciya tana maido hankalinta ga kanta dake zube ƙasa sannan ta duƙa tafara ninkewa wasu hawaye masu matuƙar zafi na tarar mata a idanuwa, suna fita kuwa Jiddah kallon Umma tayi tace, "Umma bara naje nayi sauri na shirya shegiya kada tarigani". Tana sauka step ɗin da sauri da sauri, murmushi Umma ta saki haɗe da cewa, "Ki sauka a hankali mana bazata rigaki ba Jiddah, ko bakiga yadda na watso mata da kayanta ƙasa ba, na tabbata yanda kayan nan suke a gyara tsaf na watse mata su bazata iya fita ba har sai ta sake gyarasu, kin santa da shegiyar tsafta da adana komai a muhallin da kamar uwarta". Dariya Jidda data ƙarashe sauka tana sauraren abinda mahaifiyar tata ke faɗa tashiga yi tare da Jinjinawa baseera da makirci irin na Ummantata kafin ta shige ɗakinta, A gaggauce ta ƙarasa gyarawa bayan tafito wanka ta saka kayan jin muryar su khalid na kiran Afrah da har ta sauko tagama karyawa, tamkar wacce aka koro tafito tana saka ɗayar Safar hannunta lokacin har Afrah ta nufi shashin mahaifinsu dan kullum ne sai sunje sun gaishesa da safe kamin su tafi makaranta, Aunty amarya ta iske a gaban dinning tana shirya masa abinci cikin girmamawa tace, "Aunty ina kwana an tashi lafiya?" Ɗago kai tayi cikin jin daɗi tana danne ƴar dariya dake taso mata ganin wasu uniform a jikin Afrah da tun jiya Jiddah ta bata labarin Abba ya canza mata school amma sai tayi kamar bata saniba tace, "Ke kuma ya naganki da wuɗannan uniform ɗin?" Kafin tarufe baki Khalid dake gefen mahaifin nasu zaune yace, "Aunty Abba fa ya canza mata makaranta saboda lattin da take sakamu, shikenan yanzu mun daina makara balle a dake mu". Dariyar ce tafitowa Aunty Amarya ba tare data shirya yin hakan ba tace, "Ai an huta mugun halinta ya ja mata har aka canza mata makarantar, yarinya kullum ba tada aiki daga yau ba lafiya gobe sai tashi a makare, tunda ita bata shiryawa karatun ba ai shikenan ita tasani". Wannan karon Abba har cikin ransa yaji wani abu ya sakar masa zuciya akan kalaman Aunty amma wani abu maiƙarfin gaske da bazaice ga komai bane yasa bakinsa yimasa nauyin daya kasa cewa komai kamar yadda Afrah ɗin takasa cewa komai itama, murmushi kawai ta ɗan saki daga gefen da take tsaye tunda ta shigo tace "Abbanmu ina kwana?". "Lafiya". Yafaɗa ba tare daya ɗago kai ya kalleta ba saima wasa yake yiwa Khalid da Walid dake yimasa surutu, dai-dai nan Jidda tashigo tana cewa, "Abba ina kwana?" Tare da juyawa tana kallon Afrah, hannu Abbaban nasu daya gama maido hankalinsa gabaɗaya yanzu akan Jiddah ɗin ya miƙo mata yana cewa, "Lafiya klw ƴar albarka har kin shirya?" A shagwaɓe Jiddah ta saki murmushi tana miƙa masa hannu tace, "Na shirya Abba tun ɗazu, uniform ɗin a na duba naga ashe ba guba shine naje Afrah ta bani nata ta ɓata mani lokaci". "So takeyi kema ki makara tunda halinta kenan". Ya ƙare maganar yana jawo drawer ɗin dake kusa dashi dake jikin table ɗin dake tsakiyar palourn aka ɗan jawo masa shi zuwa gabansa ya ɗakko kuɗi yana miƙa wa Khalid, "ungo kai Khalid ga dubu ɗaya kai da yayanka, kema Jidda ga taki" ya miƙa mata dubu ɗaya sannan ya miƙa wa Afrah ɗari biyar, Kallonsa Afrah tayi tace, "Abba khalid ma fa ɗari biyar-biyar kabasu dai-dai dani bayan nima Auntynsu ce?" Wani mugun kallo yayi mata haɗe da cewa, "idan bakya so bani abuna ko makaranta ɗaya kuke yanzu da zan baki kuɗi dai-dai da Jiddah? Faɗa mun naji ɗaya suke?", Shiru tayi ta sadda kai ƙasa tana girgiza masa kafin can Aunty Amarya da itama taji haushin bawa yaranta ɗari biyar-biyar bayan Jidda Naira dubu ɗaya ya bata tace, "Kema dai Afrah da neman magana kike wallahi, bakiga ko su Khalid dake makaranta ɗaya da Jiddah ba ɗari biyar-biyar aka basu, ina laifin ke abaki ɗari uku ma don ma kin samu an dai-dai taki dasu shine zakiyi ƙorafi saboda ci da zuci yayi maki yawa?". Ta ƙare zancen tana samun wuri kusa da Abba ɗin ta zauna tanaci gaba da cewa, "Nan fa makarantar da kike yi take bakin titi kusa da gida, Naira ɗari ma idan aka baki ta wadatar tunda duka-duka abun da ake saidawa acikin makarantar bazai wuce, awara da ƙanƙarar ƙwame ba". Dariya Khalid da Jiddah suka shiga yimata batare da tace komai ba kuka na taso mata tace "Shikenan Abba kayi haƙuri na gode Allah yasaka da Alkhairi". Sannan ta juya tana barin bangaren inda Abba yabita da kallo har tafice, su kuma su Jidda har lokacin dariya suke yimata Aunty Amarya na tayasu. Afrah na fitowa ƙwallon da suka taru acikin idanuwanta suka shiga saukowa ta nufi ɓangaren yayun nata, ɗakin ya Jalil tafara tsayawa tana buga masa ƙofa bai buɗe ba dan haka saita ƙarasa daƙin ya Mutallab tana shirin yimasa knocking yafito sanye da Jallabiya ruwan ƙasa ajikinsa, "Afrah". Yafaɗa yana kallonta a maimakon ta amsa shi sai kawai tafaɗa jikinsa ta fashe da kuka, ƙyaleta yayi na kusan mintuna biyu a jikinsa tana kukan kafin ya ɗago fuskarta da tafin hannuwanta yace, "Menene kuma Afrah? Me yasa kuka baya yimiki wahala, ina alkawarin da kika yimani be a strong mana". Jalil ne ya yaɓude kofar daƙinsa dai-dai lokacin ya fito yana hamma tare da kallonsu yace, "Ai yaya indai bazaka riƙa yimata tsawa ba wannan

Chapter 6 of 54