Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
wayarta tana jan tsaki, kallonta Umma tayi haɗe da cewa, "badai har ya iso ba?" "Ya iso mana kinsan tafiyar jirgi ba ɗai take data ƙafa ba, gaskiya ni bazan sake zuwa irin wannan wajen ba Umma." "Ashe ko bakya son maganin wannan kangararren mijin naki dake nema ya kwaso maki masifa da bala'i acikin gida, dan kishiya bala'i ce yarinya ni zan faɗa mako hakan, dan uwarsa duk data iskoni da mijina sai da tasan yadda tayi ta shiga tsakanina dashi yadda baya ganin kowa da mutunci da kima acikin gidan idan ba ita ba." "Mtss shine dan baƙinciki nima zai mun kishiyar? To ai gani gashi wallahi sai nasa ya gwammace dama bai ɗauko zancen auren nan ba." Taƙare zancen dai-dai lokacin da suka fito bakin titi suka shiga mota ta tayar suka bar wajen. Mutallab kuwa shiru yai ya ƙurawa wayar idanuwa data kashe tamkar mai karatun wani abu, lambar Afrah yaga tafito a jikin screen wayar tana ƙara, ajiyar zuciya yaja ya sauke kafin ya ɗaga yakai ga kunnensa haɗe dayin sallama, murmushi ta saki tana kallon Aïcha dake zaune tana wasa da yatsun hannuwanta dan ita ta matsa mata da takirasa taji idan sun sauka lafiya sannan tace, "Barka da hanya yayana kun isa lafiya?" "Lafiya kalau Afrah yasu Dada?" "Lafiya kalau ai nakira ya Jalil dan nazata kama kwanta lahira dan kada na dameka Aïcha ta matsa wai nakiraka naji idan ka sauka lafiya." Murmushi ya saki a ransa yana cewa ashe ta damu dashi har haka, a zahiri kuma cewa yai "lafiya muka sauka bata wayar." Afrah na dariya ƙasa-ƙasa ta miƙawa Aïcha dake harararta wayar dan bayani tsammanin zata faɗa masa cewa ita tace akirasa ba sannan tafiya, shiru Aïcha tayi koda takai wayar a kunnenta, haka shima baice komai ba na tsawon mintuna sai sautin fitar numfashin junansu da suke ji kawai, ganin da gaske baza tayi magana ba ya sashi cewa, "idan kinsan bakya da buƙatar ji daga gareni meyasa kika matsa da a kirani kiji yanda na sauka." Duk da Aicha taji haushin maganar tasa bata ce komai ba har sai daya sake cewa, "Shikenan ki kashe wayar bana tunanin wannan kiran nada muhimmanci agunki, Bakisan irin azabtar da zuciyata da kikeyi ba shiyasa kike mun wulaƙancin, da wannan shirun da kika yimani dama kin barshi kawai mutafi a haka, ina sonki Aïcha so mai tsanani da bazan iya kwatanta wa ba sai dai narasa meye aibina da kika kasa karɓar soyayyata ba..." Bai ƙarasa ba yaji an wabce wayar dake kunnensa, ɗago kan da zaiyi yaga Meenal ce a tsaye gabansa tana faman cika saboda tsananin ɓacin rai, zai yi magana ta ɗaga wayar ta buga ƙasa gabaɗaya ta watse tana cewa, "Na rantse da Allah Mutallab baka isa ka shigo cikin gidannan ba ka tsiri waya da wata shegiya ballagaza wadda bata iya ramen kanta, duka-duka mintunanka nawa da baro can ƙasar da zata fara bibiyarka? To bazan lamunta ba kuma sai dubu idan ka sake waya da ita acikin gidannan ni kuma sai nafasa wayarka sau dubu, azzalumi mugu kawai da baisan halacci ba, wallahi tallahi sai Allah ya saka mani akan ƙanwarka abinda kayi mani na ƙara aure ko wata huɗu banyi acikin gidanka ba." Iska Mutallab yaja ta baki ya furzar yana kallon wayarsa da tayi ɗai-ɗai a tsakar ɗakin tare da ƙoƙarin danne fushin dake taso masa ta ƙasa zuciya sannan ya miƙe yaje ya ɗauke sim ɗinsa, tsaye yayi a gabanta haɗe da cewa, "baza'a taɓa yiwa ƙanwata haka ba Meenal saboda tasan ciwon kanta, tasan haƙƙoƙan mijinta akanta, ina da yaƙini akan cewa ita ba ballagaza bace da zata kasa kulawa da tsabtace wajen baccin mijinta, cinsa da kuma shansa, don haka sam wannan addu'ar bazata taɓa tasiri akanta ba, ban hana wasu ƙannen nawa ba daban amma in sha Allah badai Afrah ba, aure kuma bazan fasa ba idan kina ganin ta hakan zaki iya dakatar dani, kisani kinyi nasara wajen fasa mani waya. amma bazaki taɓa nasara ba wajen hanani kawota cikin gidannan ba ko kuma hanani sayen wata wayar nayi wayar da nake so da ita, sakarya kawai wacce bata san kanta ba." Yaƙare zancen tare da ɗaukar kayansa ya mayar sannan yafice daga ɗakin, rasa inda zai sa kansa yai gashi yana jin gajiya sosai a jikinsa, sashen tante ya shiga ya tadda ita tana fitowa daga ɗakin baccinta, da mamaki ta kallesa haɗe da cewa, "Mutallab baka ji gajiya bane naga har yanzu baka samu kayi wanka ba ka shirya ga abinci Fannah ta aiko mana dashi?" "Wallahi kuwa tánte ina makullin wancan ɗayan sashen?" Sai da taje ta ɗauko masa key ɗin sannan ta kallesa haɗe da cewa, "Lafiya Mutallab?" ganin yadda idanuwansa suka sauya sukayi jajir saboda tsananin ɓacin rai,  bai iya cewa komai ba ya karɓi makullan ya fice, sashen nasa ya koma ya haɗo kayan da yake buƙata sannan ya wuce ɗaya sashen dake kallon na Meenal yayo wanka ya shirya, cike da takaici yawuce sashenta tana zaune palournta dake hargitse ita da Asiya, ba tare daya damu da amsa gaisuwar da Asiyar keyi masa ba yace, "karki kuskura na dawo na sami ɗakina a yadda na iskoshi, idan ba haka ba zaki haɗu da ɓacin rai marar misaltuwa awajena." Yadda taga fuskarsa ɗaure babu alamun wasa aciki yasata haɗiye kalaman da tayi niyar mayar masa, sai daya fita tabi bayansa da harara tana sakin tsaki haɗe da cewa, "ɓacin rai kuma na nawa, ai wallahi ni dakai munsa ƙafar wando guda kenan." "A'a Meenal kedai kiyi yadda yace ko kin manta da maganin da zakiyi amfani dashi da kuka karɓo keda Umma, idan har baki bi umurninsa ba taya zaki iya amfani dashi ba jituwa tsakaninku? Ai samu zakiyi ki lallaɓasa ko don kisamu kibiya buƙatarki" "Allah Asiya bazan iya ba, nifa nafaɗa makinko ɗakunan ban iya gyarawa balle na wani, gashi matar nan taƙi dawowa daga zuwa ƙauye ganin gida." Cewa da mai aikinta, dariya Asiya tayi haɗe da cewa, "haba Meenal Rashida fa guduwa tayi ba wani ganin gida da tajeyi ƙauye, aikin ne taga yayi mata yawa kuma ance ki ƙara kuɗi kinƙi shiyasa taƙi dawowa." "Can! Lallai matar nan to anfaɗa mats ƴar iska ce da zan ɗauki kuɗi har dubu ishirin mana ƴar aiki sai kace ina buga kuɗi? cinta fa da shanta duka suna cikin gidannan sannan ace zan biyata har Naira dubu ashirin sai kace mai aikin gwamnati na state." Shiru Asiya tayi dan tasan kwanan zancen, dubu goma ne Meenal ke biyan mai aikin sai Umma takarɓa ta bata dubu uku, da taga aikin yayi mata yawa shine ta buƙaci Umma da aƙara mata, ita kuma Umma bazata iya ƙara mata ba acikin dubu goma ɗin shine tace wa Meenal aƙarawa mai aikin kuɗi har dubu goma su zama ashirin saboda duk aikace-aikacen gidan da gyaran dakin mai gida akanta yake, da Meenal taƙi ƙarawa itama Umma taji bazata iya ƙara mata ba shine mai aikin tayi ƙaryar zata je ganin gida ƙauye, sai da taje takira Umma tace mata bazata iya aikin ba su nemi wata, Umma kuma sai tabarshi a haka bata sanarwa da Meenal ba dan kada asirinta ya tonu tunda Meenal bata san abinda take ba matar ba. "Yanzu dai muje na tayaki ni bana son ku sake samun matsala dashi." jin haka yasa Meenal miƙewa suka nufi sashen Mutallab, zaune Meenal tayi gefen bedside Asiya ta gyara ɗakin ta shiga toilet ta wanke sannan suka fito ta gyara palourn ta feshishi da room freshnerss masu ƙamshi data gani cikin ɗakin, sashen Meenal takoma ta ɗauko burner da turaren wutar data gani masu ƙamshi da Momy ta haɗa mata akan madubin ta tazo ta jona ta turara sannan ta kalli Meenal tana cewa, "muje to tunda angama." "Ni jeki Asiya ni anan zan zauna ƙamshin yai mun daɗi sosai." Wani irin takaici ya rufe Asiya taji kamar tarufeta da duka, wato tana son taga waje tas yana ƙamshi amma bata iya tashi ta gyara sai dai a gyara mata dan ta rena mutane, ga kayan ƙamari can birnin akan madubinta amma bazata iya sarrafasu ba ba abinda ta taɓa aciki, kwafa tayi cike da takaici sannan ta nufi sashen Meenal ɗin ta bude ɗakinta ta shiga ta kwaso turaren jiki dasu khumras da collacam da spray masu ƙamshi takai cikin kayanta ta ɓoye tana cewa, "koda wannan na samu na rage hassahi dake bakar ƙaramar banza Allah yasa ma ya auri maki uku lokaci ɗaya." Mutallab kuwa sashen tánte yawuce ta zuba masa abinci sannan yamiƙe yana faɗin, "bari naje wajen Aryan kar laifin nawa yaƙaru." "To adawo lafiya a gaishesa shi da ummiensa kafin nake." "Zasu ji." Yafaɗa tare da ficewa, yana fitowa daga mension ɗinsa ya haɗu da Jalil shi da Fannah cikin mota alamun zasu fita abun gwanin sha'awa, tsaida motar Jalil yai haɗe da sauke glass ya gaishesa kafin itama Fannan ta ɗan duƙar dakai cikin jin kunya tace, "Yaya ina wuni andawo lafiya." Cikin dakin fuska yace, "Lafiya kalau Fannah ya muka sameki?" "Lafiya kalau." "Ina dai lafiya ko Jalil naga zaku fita daga dawowarsa bayan nafaɗa maka ka zauna wajen iyalinka ka huta." Sai da Jalil ya kalli Fannah data sun kuyar dakai ƙasa sannan yace, "Batajin daɗi ne shine bata faɗa mani ba sai da muka dawo na iskota a galabaice gashi ta wahalda kanta da girke-girke, shine nace ta shirya muje na kaita asibiti adubata sai mudawo." "Ayya to Allah yaƙara sauki, kuje sai kun dawo". Suka amsa da amin mai gadi ya bude masu gate suka fita shima ya buɗe motarsa ya shiga ya tayar sannan yafice daga gidan, yadda yaga Jalil da iyalinsa kaɗai ya sake jefasa cikin damuwar halayyar nasa iyalin, ajiyar zuciya yaja ya sauke haɗe da cewa Allah ya kyauta yana jawo wayarsa ɗaya a aljihu, Aryan yakira Yana tambayarsa inda yake ya sanar dashi gasu diamond hotel shi da Mahmoud yazo duba abokanansa da suka taho saboda ɗaurin auren nasa dan tunda suka iso ƙasar shi Mahmoud wajen Aryan ya isa yai masa ma sauki, sai daya fara biyawa YAMUSAMU Communication wajen sai da wayoyi ya sayi sabuwar waya aka saita masa layoyansa aciki suka hau sannan ya nufi hotel ɗin yana ƙoƙarin kiran lambar Aïcha. Bugu ɗaya a nabiyu ta ɗaga tare da kaiwa ga kunnenta tayi sallama, wani lumshe idanuwa yai kafin yace, "Ina jinki Aïcha, ɗazu an samu matsala ne wayar ta tsinke shiyasa kika ji shiru." "Ehm ya gajiyar hanya?" "Alhamdulillah amma ba wannan nake son ji ba, ya akayi ɗazun baki kirani da wayarki ba?" Yai maganar cikin taushin murya haɗe da sanyaya zuciyar mai saurare. "Am Sorry?" "For what?" Tayi shiru bata ce komai ba, shurun nan nasa ba ƙaramin kashesa yakeyi ba sam baya sonsa, jin har lokacin taki cewa komai ya sashi cewa, "Ehim ina saurarenki." "Ya Mutallab!" Murmushi ya saki jin yadda takira sunan tamkar a bakinta aka raɗa shi, zai iya cewa tafi kowa iya faɗar sunan yadda ya dace, kamar daga sama ya tsinkayo muryarta tana cewa, "Banyi tsammanin kalamaina zasu ɓata maka rai ba dan har zuciyata gaskiya nake faɗa, akwai tazara mai nisa tsakaninka dani da nake tunanin ban cancanci soyayyarka ba, zaifi dacewa ace kasamu dai-dai dakai nima kabarni na samu daidai dani..." "Ya isa haka Aïcha". Yafaɗa yana jin zafi a ransa tare da kashe wayar yana dukan stearing wheel ɗin motar... #Mutallab Asad #Ƴan Tagwaye #Nana Diso #Billy s Fari. SHAFI NA TAMANIN DA BIYAR *MUTALLAB ASAD*      Arewabook:- billysfari       Paid book ne, N500 via ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A, Gt bank, sai shaidar biya ta +234 704 040 2435 ko +234 809 845 6130 Ga masu son vip post 1k ne.   Bakaramin biki akasha ba Na aryan ko'ina sai yawo akeyi dashi a social media kai kace wani attajiri ne yayi aure Amma dayake kowa yana masa kallon Aminin Mutallab asad hakan yasa har gidan jaridu sai da suka yada. A bangaren meenal kuwa babu kalar wulakanci da cin mutuncin da batayiwa Mutallab sosai yashiga damuwa gashi duk yayi rama saboda tsananin sha'awar dake damunsa duba da kusan sati biyu da dawowar Afrah kuma itama tana gab da karasa karatunta dan kuwa gobe ma zata rubuta final exam dinta.Yanzu ma sakkowa tayi daga saman Mutallab din tagama gyara masa ko'ina Naciƙin dakunan da bandaki ganin yana kokarin shigowa set room dinsa yasata karasawa kusa dashi tana masa sannu da zuwa. Dago idanuwansa yayi yana kallonta wanda ko baiyi magana ba kasan Akwai tsantsar damuwa aciƙinsa. " Ya mutallab bakada lafiya ne?" Dan kallonta yayi yace " Am okay Afrah Nace zaki kammala karatun naki nan idan kingama ko zaki cigaba awaje? Dan yalura itama bayan auran Aryan bakaramun rama tayi ba gaba daya ta canza hatta magana sai data rage. " A'a yaya zankarasa kawai Anan." " Okay badamuwa kunyi Abinci? Yafada yana kara kallonta." Cike da tausayin yayan nata tace " Nakaimaka shi sama." " Nagode Allah yayi miki Albarka." Ameen tace haɗe da barin daƙin. Ko yaya yatuno da Aicha sai yaji tsigar jiƙinsa ta miƙe yanzu ma layin da yake gwadawa yakirata baya shiga kwatakwata sai dai wani zubin idan yakira dada yaƙanjiyo muryarta wanda hakan na masa sanyi sosai Aransa. Jin shirun meenal yau bata likosa ba yasashi saurin miƙewa domin yaje yaga lafiyarta. Yana tura kofar Yayi karo da Amai a baƙin gadonta ganinta agefe tana cin gauva yasanyashi karasowa kusa da'ita yana faɗin " are you okay? " " sai yanzu zakacemun am I okay? Bansaniba Nifa kaga nagaji da zama dakai dan na lura ba kaunata kakeyi ba kaga wannan ciƙin ma da yake wahalar dani Wallahilazim zubar dashi zanyi kowa ya huta." Da ɗan hanzari ya kalleta sannan yaƙafeta da idanunsa yce " Meenal cikine dake?" Tsaki taja tace " Eh shine dani kuma abortion zanyi." Matsowa tayi jiƙinta duk yadda tayi datti ga warin hammata datake fama dashi kai kace ba matar attajiri ba diyar attajiri ga ƙanta dayayi futu futu babu gyara haka ya rungumota yashiga shinshinata yana sauke ajiyar zuciya " Komai zakiyimun ina kaunarki Amma kada kiyimun wasa akan abunda kinfi kowa sanin yadda Nake mutukar kaunarsa da sonsa danAllah cikine dake." Rabon dataji Nutsuwar dataji yau tamanta kasancewa yana rungume da'ita ajiƙinsa turo baki tayi tace " Bakace kishiya zakayimun ba." " Matata" yafada da wata murya datasanya duk gabban jiƙinta sauka. Yadda yazuba mata idanuwa yasanya tsigar jiƙinta mikewa a hankali yasanya baƙinsa cikin nata yashiga kissing dinta duk da yanayi na rashin kamshi da wari dake tashi ajiƙinta kunsan ita hammata iska kadan take jira ta fidda abunda ke ciƙinta, sakin guava din dake hannunta tayi tashiga turo masa Nononta haƙan yabashi damar aza hannunsa aƙansu yaashiga murza matasu cikin wani yanayi tace " inada 3 months pregnant." Baisan sanda ya cafko baƙinta ba yashiga sumbata yana masa wani kalar tsotsa mai Nuni da abuƙace bake. Cikin narkakkiyar muryar da take kokarin Nuna ba ciƙin Nutsuwa yake ba yace " Ɗan Allah kada kiyimun wasa da hankalina kitaimaka danAllah. Batasan sanda ta marairaice masa ba tana gayamasa tare da umma sukaje asubuti. Wani dadi yaji haƙan yabashi damar cire mata komai Na jiƙinta Amma ya zuba mata idanu tunowa dayayi suna an ƙare da sperm dinsa ga kwanaki da suka wuce ya ganta tana barbada masa magani aciƙin bandaƙinsa sai data gama yakira afrah ta wanke masa shiyasa aduk lokacin da zai sauke gajiyarsa yana Nutsuwa sosai domin kula da duk wani motsinta." To kataɓani mana tafaɗa cike da shauki." Duk wani kokarin da zaiyi mata sai da yayi mata har tasamu Nutsuwa kallonta yayi da idanuwansa da suka canza saboda jaraba yace " meenal touch me mana." " Intaɓaka inyimaka me kaga Ni gaskiya ka kyaleni tafaɗa tana tureshi daga jiƙinsa." Haba meenal meisa kikeyimun haka danAllah fa nace." " kaga malam kyaleni danAllah ko kazata na manta da batun ƙarin auren da zakayi abeg kyaleni kuma narantse da Allah idan kayi aure sai na fidda cikinnan." " No please meenal inason cikin nan sosai karkiyi aikin jahilci please meenal You know I ..." excuse me nagayamaka billahilazi sai na zubar sai dai idan kafasa aure.." murmushi yayi yace " Yes na fasa please.." da dan hanzari ta ƙalleshi da gaske?" Daga mata kai yayi yana kara janta jiƙinsa . babyna please karki illatarmin dakanki da kuma ciƙin dake jikinki kinji inasonku dayawa maganar Aure ki ajiyeta gefe babu ita yanzu yafada dab ya kwantar mata da hankali." " Kanason cikin nan ko?" " Sosai Meenal." " To kayimun alkawari bazakayi aure ba." " Yanzu dai nace kibar maganar ko tashi muje kiyi wanka." Nanuƙe masa jiki tayi tana faɗin " Ni to kakaini part dinka." Babu musu yasaka mata hijjabi ya riko hannunta suka Nufi bangarensa direct sama sukayi da ƙanshi yasakar mata shower din sanna yace tashiga taje tayi dafarima haka tace shi zaiyi mata yanzu kuma shi gaba daya baya mood dinnan na wanka. Ko da yafito wayarta yaga tayi Alamun an aiko mata da sako yana buɗewa yaga anrubuta " Ke meenal ki tabbatar yau dinnan ki kwaso mana sperm dinnan Wallahi nagayamiki.." murmushi yayi yana ajiye wayar yarasa wanne hukunci zaiyiwa umma dalilin dayasa yake dagawa meenal kafa kenan dan ya lura umma ce ke zugata awash abubuwan nata sau biyu kuma yanasakata a islamiyya amma yarinyar nan ta kafe akan itafa ba jahila bace ba babu inda zataje. Ko datafito daga bandaƙin daure da towel dinsa wani mugun bacci taji yana kokarin kwasarta. Kallonsa tayi tanajin sanyi Aciƙin ranta kamin tace " Nifa gurasa da kayan ciki nakeson ci." Da mamaki sosai ya kalleta yace " shikenan abunda kikeso kokuma akwai wani abun dakikeso." Zuba masa idanuwa tayi tanajin zuciyarta na mata wani sanyi kamin tace " To kadaina sakani aiki likita yace adaina sakani komai kuma katambaye umma." " indai aikine kindaina kinji babyna yanzu kigayawa mumy takawo miki mai aiki kinji. " " mumy bazata kawomin ba sai dai umma." " Tohm kisa akawomiki." " kuma guda biyu nakeso yanzu." Murmushi yayi yana jan hancinta sannan yashafa ciƙin dake jiƙinta yace " Bakida matsala matar mutallab." Yadda daƙin ya dauki sanyi yasa takara bararrajewa ga kuma turare mai sanyin kamshi da yatafi da tunaninta. Fitarsa keda wuya Umma tashiga kiranta awayarta."kinga message dina?" Dubawa meenal tayi kamin tace " Gaskiya banga message ko daya yashigo ba." " ko sharrin network ne?" " inaji to." " Yanzu kinsanar masa kinada cikin ne?" Murmushi meenal tayi tana tuna irin yadda ya sumbaceta sosai dazu tace " Umma yafasa karo aure fa yace ma abar maganar." " au karatun tsotsi tsotse yayi miki? Shine zaki yarda da namiji? Ke kuwa diyarnan kinada hankali? To wallahi kinaji nagayamiki ko ko kina kauna ko bakya kauna narantse miki da Allah sai yayi auren nan indai baki samo mana wannan maniyyin nasa ba ke bayagamiki ana yarda da namiji ? Ashe kuwa kuka yasameki." " Ai nagayamasa umma wallahi yakara aure sai na zubar da ciƙin dake jikina." " Uhmm kome dai kikagayamasa indai wannan yaron ne da yake atsaye wallahi Allah sai yakara." Jikin meenal ne yayi mugun sanyi tace " To yanzu umma yazanyi." " Kudi zakiyita cazarsa tunda kinga yanason haihuwar kamar kamar Me sannan kiyi kokarin kwaso mana wannan abun ko?." " To umma zanyi yadda kikace nagode ina bangarensa kada yashigo sai anjima." Sai da yasiyo mata gurasar sannan ya kawo mata tanata bacci yahuce kasuwa duba da akwai abubuwan da zaiyi." ***** Jamil kasheni kakeso kayi so kakeyi ka salwantar dani? Nace uban me zanyi maka yanzu million har goma jamil me kayi dasu? " kai kam abba da tambaya kake saboda Allah nagayamaka yan dam fara yahaɗu dasu shine zakace me yayi dasu babu damar jarabawa tasamu mutum shi wancan dan naka da yake ta hau hawa saboda kudi baka taba tuhumarsa ba sai wanda kasan tushen sana'ar sa? Menene hakan kakeyi saboda Allah? Nifa banason a takurawa yarana." " To bazan biya ba banida kudi yadaga gidajensa da filayensa yabiya wallahi sai dai su daureshi." Da mamaki da yakusa girgiza umma ta dago ƙanta tace " kace? Bangane me kake Nufi ba kwata kwata ne ai? Yasiyar? Dame." " Nace miki yasiyar da gidansa wallahi ficika bazan biyaba." Anty Amarya da wata kalar murna ta mamayeta tace " To saboda Allah kai jamil ko tausayin mahaifinka bakayi? Kana ganin Mutallab ke kokari gurin ciyar da kowa?" " Ke iya bakinki yafada jamil yana mikewa." " To idan baka bayarba sai menene yafada yana ficewa daga daƙin." Umma kuwa mutuwar tsaye tayi tare da kasa magana sai kawai sukaga ta Mike ta fice daga daƙin batare da tace musu uffan ba. Ko data karasa bangarenta aata kara tasaka sannan ta tsugunna karkashin gadonta nan ta tarar babu kwarya babu kashin bera innalilahi ta ambata gana fitowa palour inda jidda da zuwanta kenan take zaune sai asiya. " dan ubanku wanene ya dauki kwarya a karkashin gadona." Jidda ce ta jiyo tace " Ai ni nazata shara ce shine jiya nafasa nasaka acikin dustbin." Saukar lafiyayyan mari taji." Dan ubanki Ni nasakaki yar iskar yarinya da Auranta bai tsina namun da komai ba sai jaraba shegiya daga yawo gida kullum bakida aiki dake da dan iskan mijin naki shine.." "To wai umma menene dan na zubar ashara." Wani marin umma ta sakar mata tace " Uwarki ne nace miki uwarki ne." Umma kiyi hakuri asiya tafada." " Asiya kiramun hajiya atene kice ba lafiya tazo yanzu yanzun nan. Abba da yakalle anty Amarya yace " Amma har yanzu bandainajin gabana yana faduwa ba." Ka kwantar da hankalinka zaka dainaji Abba kacigaba da shan ruwan magaryar nan sannan kayi kokarin cigaba da karatun Alkur'ani. " To inshaa Allahu zanyi haka. Tunda yadawo yatarar tanata baccinta batare da damuwa ba sai ya ajiye mata yafita zuwa gurin su Tante. Sallama yayi yaga Afrah na video call itada Aicha zubawa tab din idanuwa yayi yana kallonta kamin ya dauke idonsa ganin vest ce kawai ajiƙinta ga breast dinta sun cika sunyi fuffu ga kanta da babu dankwale ta tufke gashin nata." Wai Aicha bazakizo gidan mu ba danAllah tunda kunyi hutun makarantar kizo." " Hadda fa kinga ina zuwa islamiyya kuma yaya mahmud yanamin lesson dazuma bari kiga kayan da yasiyomin kigayamun wanne takalmi zansiya musu tatashi daga zaunen datake wani gajeran wandone ajiƙinta ya kamata sosai sai vest wani kalar zafi yaji ajiƙinsa a lokacin yayi gyaran murya sannan yace " afrah ina tante?" " Yaya ta kwanta tafada tana kallon wayar tata ". Aicha kuwa tana sauraronshi amma kwata kwata bata ki cigaba da magana ba." Kamar zaiyi magana sai kuma baice komai ba yafita wayarsa yaciro yashiga kiran Numbar aicha da ya dauka wayar Aciƙin wayar afrah kusan kira 4 kamin ta dauka da Sallama. cikin zafin rai yace " Wacce kalar shiga ce haka kikeyi acikin gidan da kikasan maza da mata suna shawagi?" Cike da rashin da muwa tace " Wake magana danAllah?" Wani abu yaji ya tsaya masa acikin ransa yace mata " Mutallab ne." Au yayanmu ina wuni banida numbarka ne shiyasa Am sorry please." " Aicha hauka kikeso nayi akanki? Yakikeso nayi yanzu wannan shigar takamaceki?." "Yayanmu suis désolé (kayi hakuri) dagani sai dada ina daƙinta shiyasa Amma bana fita ahaka." " Wayabaki waya?" " Ya mahmoud ne yasiya mun. " " Banason kina karbar komai agurin kowa kince nafita daga rayuwarki but ina ganin kin daukeni amatsayin yayanki ko?" " Eh." " To please focus a karatunki shine abunda kike bukata yanzu ba shirmen nan ba I hope am clear." " but shima yayanane ai." " Aicha am talking fa kiduba yadda kike Kula samari dada inaji rannan tana miki fada why ." " Nifa babu wanda nake kulawa kuma ai dada ke fadin in gaisa dasu kuma ma ni banason mai mata wallahi ko zanyi saurayi mara mata zanyi." " Nahanaki kula kowa." " Babu kyau wulakanci ai." Cikin zafin rai yace " Zan batamiki aicha." SHAFI

Chapter 48 of 54