Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ka faɗi gaskiya kuma, Yanzu dai mu bar wannan maganar ya ake ciki?" "Dai-da wlh dama nazo in sanar maka da cewa na samu aiki kuma zuwa Monday zan fara zuwa in Sha Allah". wani irin ƙayataccen murmushi Mutallab ya saki cike da farinciki lokaci ɗaya damuwar dake kan fuskarsa na gushewa yace, "Alhamdulillah, kace mun samu aiki Aryaan, at least kaga ɗayan mu yarage zaman banzan da muka shekara biyu muna yi ba aiki ko kuwa?" "Haka Mamma tace, saura kai inshaa Allahu na tabbata naka na zuwa daya zarta nawa". Murmushi Mutallab yayi yace, "idan akace Allah angama komai, amma ni nafara fidda rai saboda ban hango alamun haka ba, kana fa ganin yanda Abba yayi banza da zancen nan nawa, ga ƙasar nan ta koma yanzu waka sani waye ya sanka, tunaninsu kawai yanzu nakoma na ƙarasa masters ɗina, in har Abba zai amince mani to hakan zafi mun daɗi a yanzu." "Gaskiya kayi tunani ƙara ka shata gaba ɗaya in zai amince tunda yaƙi saka maka hannu a zancen samun aikin naka. Hakanma shawara ce mai kyau Allah yasa ya amince ta wannan fannin ya saka mana hannu". "Amin ya rabbi Aryaan". sun jima suna tattaunawa akan matsaltsalun Mutallab ɗin da mahaifin nasa da ako yaushe ke nuna halin ko inkula ga lamurransa shi da ƴan uwansa tamkar ba shine ya haifesu ba kafin suyi sallama ya wuce shi kuma ya koma cikin gidan. Sai daya koma ya duba Afrah da har bacci ya ɗauketa sannan ya sauko ya koma sashensu. gugar kayansu ya tadda Jalil nayi ya nemi gefen katifar dake cikin ɗakin nasu ya zauna yana cewa, "Ba nace kabar gugar nan ba zan bayar ayi mana ko nagoge mana da kaina? me yasa kake son wahalar da kanka da yawa, kai ne wanki yanzu kuma kaine guga". Ɗago kai Jalil yayi ya kallesa sannan ya maida hankalinsa ga gugar da yakeyi haɗe da cewa, "Allah ya tsare ya Mutallab ace ina raye kana guga da kanka, kabarni kawai nariƙa yimana ba wani abubane, nan har na mutane zan iya karɓowa nayi idan zasu biyani yaya don na rage maka tarin matsaltsalunmu dake kanka, ai kasan bahaushe na cewa babu maraya sai rago". sosai tausayin ɗan uwan nasa ya kanshi jikinsa duk yayi sanyi, addu'a yakeyi cikin zuciyarsa Allah ya sama masu ƴancin da Mahaifinsu zai basu kulawa da gata tamkar yanda yake yiwa ƴan uwansu domin zuciyarsa tafara raunata da kallon yanda ƴan ƙannen nasa ke haɗar baƙin ciki da damuwa a zukatansu saboda shi suga farincikinsa, a ɗaya ɓangare na zuciyarsa kuwa addu'a yakeyi Allah ya nuna masa hanyar da zai tsaya masu koda basu samu hakan a wajen Mahaifinsu ba har zuwa ƙarshen rayuwarsa. Afrah kuwa sosai baccin yayi mata nauyi saboda rashin runtsawar da bata samu tayi ba daren jiya, can cikin barci ta taji an turo ƙofar ɗakin nata da ƙarfi, Muryar Umma taji da ƙarfi saman kanta tana kiran sunanta, "ke Afrah idan kin gama baccin naki na asara sai ki tashi kije Alhaji na kiranki". Ɗan yamutsa fuska Afra tayi tana tashi zaune saboda nauyin da kanta yayi mata haɗe da cewa, "Umma banida lafiya ne bawai baccin kawai nakeyi ba." tsaki Umma taja haɗe da cewa, "Allah dai ya waddaran halin maƙaryaci, ke wai ko kunya bakya ji ki riƙa ƙaryar ciwo don tsabar jawowa kai mugun abu, da wani shegen fari kamar na aljanu, waya sani ma ko hakan ne ke hanaki lafiya, zaki tashi ne ko sai na mammakeki kin wani zo kin  bararraje akan gado." A hankali ta sauko kan gadon tanufi toilet ita kuma umma ta fice tana surutanta, fuskarta ta wanko ta shiga tunanin shin yaushe ne matan ubansu zasu so su? Yaushe zasu daina nuna masu tsana alhalin wacce sukeyi masu hakan dinga ta riga tabar masu duniya?  taƙare wannan tunanin cikin ranta tare da fitowa toilet ɗin tana gyara ƙaramar hularta dake kanta, ƙasa ta sauko ta nufi zuwa shashin mahaifin nasu, sallama tayi masa kamin tashiga yana zaune akan lafiyyan farin carpet ɗin dake cikin palourn ta gaida mahaifin nata cikin girmamawa, Umma dake zaune gefensa tana masa hira ta taɓa baki haɗe da cewa, "Sai yanzu kika ga damar zuwa Afrah anya kina so ki gama lafiya kuwa?" "Ƙyaleni da ita shashashar yarinya, ya kike so nayi miki akan makaranta kullum kece latti saboda lalaci kina bacci baza ki tashi ki shirya ba har lokaci ya wuce ki jawa ƴan uwanki duka a school, shin ke kika fi kowa jin daɗin bacci ne da baza ki tashi ki shirya akan lokaci ba?, ko kuwa dai aure ne kike so na aurar dake kowa ma ya huta?" tunda mahaifin nata ya fara magana bata yanka masa ba kanta ke ƙasa har sai da taji yayi wannan zancen da sauri ta ciri kai tana kallonsa tare da girgiza kai tana cewa,  "A'a Abbana kayi haƙuri ba haka bane". "To menene Afra? yanzu ma ƙarfe ɗaya saura da akaje bacci aka isko kinaji, shikenan fanɗare Mani zakiyi keda ƴan uwanki ku koma marasa ilimi da tarbiyya acikin gida? sai an fara magana ku riƙa sissinne kai ƙasa sai kace munafukai", "Kayi hakuri Abbana jiya banyi bacci ba banda lafiya, yau ma a kwance na wuni bawai bacci nakeyi ba, ka tambayi Umma kaji". "A'a Afrah me zai tambaye ni kuma Ni da na iskoki kwance kin bararraje akan gado kina kwasar baccinki hankali kwance, yanda kika shirgo masa ƙaryarnan yanzu nima haka kika shirga mani ita ba don na tabbatar ba tunda hali nan dai zaune lafiyarki kalau". "Yaya Mutallab ya bani magani daya shiga dubani shi yasa jikinsa yayi sauƙi Abba". Afrah ta faɗa cikin sanyin murya tana son mahaifin nata ya yarda da gaskiyar ta, sosai yake jin tausayi ta a ƙasar zuciyarsa amma ya rasa dalilin daya sa sam baya iya riƙe kansa da nuna mata fushinsa, Umma data gama cika da takaicin Afrah ɗin tace, "Kedai ki fadi gaskiya don su iyaye ba'a yi masu ƙarya", " barni da ita Hajiya sun maidani ɗan iska kullum sai dai nayi asarar kuɗina amma basa karatun, shi yayan nata ma ya gagara tsayawa da ƙafafuwansa yaje ya nemi aiki duk kuɗin dana kashe a karatunsa sun tashi a banza, shi kuma ɗayan naga ya dawo ya zauna wai ni yake jira na sake dunƙular kuɗina biya masa kuɗin registration ga Asad ɗin ƴan iska ko?, to na gama wahalar da kaina akanku tunda baku kaɗai na haifa ba,  in zasu je su nema da kansu suje su nema idan kuma baza su iya ba su suka sani, ke kuma ki buɗe kunnenki ki jini, daga yau na cireki daga wannan makarantar da kukeyi *Leaders spring international* take ko meye? don na gaji da asarar kuɗina tunda bakya son karatun na mayar dake makarantar bakin titi ya sunanta ma hajiya?" Umma da daɗi ya kasheta tana murmushi cike da mugunta tace, "Academy". "To kinji academy dan haka na tura yayanku Jamil yau yaje yayi mako duk abinda ya kamata, jibi idan sun kawo maki uniform zaki fara zuwa". take taji zazzaɓin daya kwanta mata na neman dawo mata saboda tsananin tashin hankalin data shiga jin kalaman da suka gama fitowa daga bakin mahaifin nata, wannan wacce kalar masifa da bala'i ne ace makarantar ma baza'a barta tayi inda ƴan uwanta keyi ba ta samu ilimi ingantacce, wasu zafafan hawaye taji sun zubo mata a fuska da sauri tasa hannu ta goge tunowa da yadda yayansu kullum yake masu nasiha akan duk hukuncin da mahaifinsu zai yanke tsakaninsu da ƴan uwansu kada su taɓa yimasa musu ko gardama domin baza a taɓa canzawa tuwo suna ba shi ɗin dai mahaifinsu ne kuma su ƴaƴansa ne, Cikin rauwar muryar dake nuni  da tsantsar damuwar da kalaman suka haifar mata tace, "Shikenan Abbanmu zanyi yanda kake so duk da nafiso nayi karatu inda ƴan uwana suke, nagode Allah yaƙara maka lafiya ya tsareka.." tun kafin ta ƙarara rufe baki Umma da takaicin yanda Afrah tayi maganar cikin girmama mahaifinnata ya rufe ta tace, "Ai kuwa sai dai kiyi hakuri baza su zauna kina cutar su ba haka kurum, tunda ke karatun ba da gaske kikeyi ba to su kama sai abinda ya turewa buzu naɗi, muguwa kawai". "Ya isa haka, tashi kije Afrah". Abba ya faɗa tare da dakatar da umma ga batutuwa da takeyi don sam ba haka taso abun ya kasance ba, har Afara takai bakin ƙofa Abban hakura sunanta, wani irin takaici ne ya sake dunƙule zuciyar umma don sam bata don yarinyar ta kuma tsaneta sosai, "Ki dafomin tea mai kayan spices wanda kikeyi kiyi maza ki kawomin". Abba yafaɗa yana kallonta, "Tohm Abba". Ta faɗa haɗe da juyawa da sauri, Umma kuwa dake cike da baƙin cikin rashin nasararta na ganin ta jefa yarinyar a ƙunci abinda tasa ayimata tayi kwafa tana tsittsine masu ita da ƴan uwanta aranta, duk da tayi nasara akansu ta fuskoki da dama amma wannan shegiyar biyayyar da suke yiwa mahaifin nasu dake baƙanta mata rai ta rasa yanda zata rabasu da ita ta yadda zasu fanɗare masa ya koresu daga ciki gidan gaba ɗaya. Afrah kuwa tana fitowa sashen Abba ta ƙarasa babban kitchen ɗinsu, kettle ta ɗakko ta ƙarfe ta wanketa sannan ta ɗakko blender ta saka cup ɗin niƙan gari ta zuba citta da kaninfari da cinnamon ta saka cardamom ta saka rosemary ta ɗan niƙasu sama-sama ta zuba a cikin kettle ɗin, can bayan gidan nasu ta zagaya gurin flowers ta tsinko Mint leaves da Lemon grass da scent leaf ta dawo kitchen ɗin ta zubasu acikin kettle ɗin suma sannan ta ɗakko Lipton ta saka  ta zuba ruwa ta ɗora akan gas, shashin su ya Mutallab ta nufa kafin ya ƙarasa dahuwa tana ƙoƙarin ɓoye damuwar dake kan fuskarta, duk da ɗakin nada ɗan girma amma kana kallon nasu khalil da ɗan uwansa dake gefe da daya sha gyara zaka fahimci tazarar banbancin da mahaifin nasu ya nuna ƙarara a tsakaninsu, don jiya-jiya ba da nisa bama aka canza musu kayan gadon amma yayun nata babu komai acikin ɗakin nasu bayan ƙatuwar katifa da ƙaramar wardrobe, Suma tun kayan mahaifiyarsu ne data rasu Umma ta bada shawarar a saka masu su cikin ɗalibai don kar mahaifin nasu ya saya masu wasu, a hankali ta shiga bubbuga ƙofar haɗe da cewa, "in shigo?" ya Mutallab da fitowarsa wanka kenan ya gama shiryawa cikin ƙananan kaya da suka matuƙar karɓarsa yace, "shigo mana". Yana ɗaura agogo a tsintsiyar hannunsa, turaƙofar tayi ta shiga bakinta ɗauke da sallama, ɗago kai yayi ya kalleta haɗe da cewa, "Auta har kinji sauƙin? Yanzu nake cewa na biya na dubi jikin naki". Murmushi tayi fuskarta a cunkushe ta tsaya bakin ƙofa tana tacewa, "na ji saukin sosai yaya, ina wuni?" "Lafiya klw ya jikin?" "Alhamdulillah" ta faɗa tana sauke ajiyar zuciya haɗe da sadda kanta ƙasa tayi shiru, "Menene Afrah?" Mutallab ya faɗa ganin yanda ta su ne kai ƙasa takasa magana, abinda sam ba ɗabi'arta bane indai a gabansa take tofa ta dinga yi masa surutu ne har sai ya gaji, kamar wadda ke jira ta fashe da kuka tana cewa, "Yaya me yasa Abbanmu tsanemu? Me nayi masa daya cireni a school ɗin da mukeyi ya maidani Academy?" Gabanta ya tako ya riƙo hannuwanta ya zaunar da ita a gefen katifarsu ya ɗora hannayensu akan fuskarta ya goge mata hawaye dake zubowa yana cewa, "Wannan ai ba komai bane Afrah, su iyaye aduk lokacin da kika ga sun yiwa ƴaƴansu abu mai daɗi ko al'adun haka duka sunayi ne saboda suna son sa, ina ga yanayin jikin naki yasa Abba yayi tunanin sauya maki makarantar da tafi kusa ga gida saboda abun yazo maki da sauƙi, abun buƙata kawai shine ki dage kiyi karatu domin duk inda kike matuƙar kika sa himma kukayi ƙoƙari to zaki samu fiye da ilimin da kike tsammani, fata kawai Allah yasa hakan yazame miki alkhairi kin ji ko?" Ya ƙarshe zancen yana kallon cikin idanuwanta haɗe da jan kumatunta, goge hawayenki kafin mutumen ki ya shigo yanzun nan ya fara tsarguwarki, Murmushi ta saki tana share ƙwallan sai ga Jalil ya shigo, cikin sigar tsokana ya mangaremata kai yana faɗin,"ya akayi tsinkui kike kuka naga fuskarki tayi ja kamar angasa buredi". Ɗan turo baki tayi tana maka masa harara haɗe da cewa, "yaya ka ganshi ko?" "Manta dashi, dama shi inda yafi gwanewa kenan". Kamar an tsikareta ta miƙe tana cewa, "wayyo yaya bari natafi nabaro tea ɗin Abba akan wuta". Tafice da sauri ba tare data jira amsar da zai bata ba, a ƙasan zuciyarta kuwa taji abinda ya faru ɗin tamkar ba komai ba, tabbas yayanta jarumi ne da ako ina zata iya nuna shi, kuma shine asalin ƙwarin guiwar da ako yaushe take ji mutane na faɗa a matsayin katanga ga kowace irin matsala, duk shekarun nan da suke fuskantar abubuwa kala-kala agidan mahaifin nasu bai taɓa ingizasu su aikata wani abun marar kyau ga mahaifinsu ko kuma matansa ba sai dai yace suyi haƙuri tare da basu kalaman ƙarfafa guiwa. da haka ta ƙarasa kitchen ta sauke kettle ɗin daruwan shayin ta wanke tea cup ta ɗakko zuma ta ɗora a ƙaramin tray ta nufi shashin Abba, har lokacin Umma na gefe da suna taɓa fira, tana ganin ta ta ɗauke fuska. "Sai yanzu kika ga damar haɗo masa shayin kika kawo?" Ba tare data tankata ba ta ajiye tray ɗin a gaban Abba dake faɗar, "Ina ga ai tama manta dani shi yasa taje tayi zamanninta". "Abbana ban isa ba dan Allah kayi haƙuri, na bari ganyayyakin dana saka ne su dahu sosai tukuna...". Bata ƙarasa ba Umma tace, "To ai sai ki tashi kitafi zaki farawa mutane iyayi"... Mutallab Asad #Tagwaye Biyar #Nana Diso #Billy S Fari. _ Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only Zaki biya ta wannan account ɗin👇🏻 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *MUTALLAB ASAD MUTALLAB*                 (MAM) NA BILLY S FARI & NANA DISO    *SHAFI NA BAKWAI.* _RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU._ _TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA_ Batare da Mutallab yace komai ba ya miƙe jiki a sanyaye ya ɗan ranƙwafa cikin girmamawa yace "Abba kayi haƙuri, ban faɗi kowacce kalma ba dan na ɓata maka rai, Allah ya huci zuciyarka seda safe". da kallo Abba yabi bayansa a zuciyarsa yana jin kamar ya aikata wani abun ba daidai ba akan gudan jinin nasa da ada kaf zai iya cewa cikin ƴaƴansa yafi jin ƙaunarsa a zuciyarsa, amma a yanzu sai yake ganin tamkar yaron na shige masa hanci tare da son nuna masa bai isa a gareshi ba, a ƙallah ya kwashe mintuna biyar yana kallon hanyar dayabi ya wuce kafin ya ɗauƙe kansa yana sauke wata irin ajiyar zuciya dake nuni da tabbas akwai abunda yakeji acan ƙasan zuciyarsa game da ɗan nasa, sai dai bazai iya cewa gako meye ba, hanyar da zata sadashi da ɗakinsa ya nufa bayan tafito daga sashen na Abba, kai tsaye toilet ya faɗa haɗe da gabatar da uzurin daya haifar masa da shiga toilet ɗin sannan ya watso ruwa, koda ya fito bai tsaya yin komai ba yasaka kayan baccinsa kawai tare da ɗauke wayoyinsa dake kan gadon ya ajiyesu saman bedside wanda ya ƙawatu da wata irin kyakkyawar fitila akai,kan gadon daya sha lallausan bedsheet fari ƙal ya haye yana sauke ajiyar zuciya tare da rage dukkanin hasken dake cikin daƙin yayi kwanciyarsa batare daya damu da karkaɗe kan gadon ba. (Kamar dai yadda yazo mana acikin koyarwar fiyayyan halitta Annabi Muhammad (saw) cikin hadisan sa cewa yana da kyau idan mutum yazo kwanciyar bacci to ya karkaɗe shimfiɗar baccinsa sannan ya ambaci sunan Allah ya kwanta don samawa kai kariya daga sharrin duk wani abun halitta na aljani da kuma mutum". Sai dai shi Abba tsananin wayewa da ganin rashin dalilin yin hakan kasancewar ako yaushe wajen a tsaftace kuma a gyare yake yasa sam bai ɗauki hakan da muhimmanci ba saboda sakaci da yake dashi na riƙon ibada da sauransu, wannan kuma shine silar da ako yaushe akecin galaba akansa ba tare ɗaya sani ba, hannyaensa ya rungume a tsakiyar ƙirjinsa fuskarsa na kallon rufin ɗakin yana son tunano wasu abubuwan da yake gani yanayi kamar ba daidai ba acikin rayuwarsa sai dai yakasa aikata hakan, gyara kwanciyarsa yayi yaƙara nutsewa cikin ƙayataccen gadon nasa da zai iya ɗaukar mutum biyar cike da tunanin rashin ƙarasowar Umma data ce masa zata je ta kimtsa ta dawo, bai kai ga ƙarasa tunanin ba yaji tayi sallama. Juyowa yayi a natse yana kallonta cike da ƙaunar da baisan yawan adadin da yakeyi mata ba ya miƙa mata hannu yana cewa "Ina kika shigane tun ɗazu baki dawo ba har yaron nan yazo yana nema ya birkita mani tunani", Murmushi Umma ta saki tare da samun gefen gadon ta zauna tana mai kallon cikin idanuwan Abba tace "wa kenan?" "Waye fa banda Mutallab". "To Alhaji ai ɗanka ne kunfi kusa, duk da nasan dai zancen ƴar uwarsa ne zai zo maka dashi kuma maganar gaskiya bazai yiyu a biye mata ba tana jawowa ƴan uwanta duka a makaranta, na rasa wane irin ma kunnen ƙashine da Afrah don nayi mata faɗa akan haka ba adadi amma tayi burus dani saboda tana ganin ban isa gareta ba tunda bani na haifeta ba, don haka a ganina canza mata makarantar shine maslaha ko don hutar da kuɗinka da kaketa narkewa a banza a wofi amma amma ta kasa natsuwa tamaida hankali tayi abinda ya kamata". "Aiki barni dasu yanzu nasa ƙafar wando ɗaya dasu daga ita har yayun nata, magana kuma na riga na gama bazan canza ba balle su maidani ƙaramin mutum, yaran gaba ɗaya yanzu mamakin rashin tarbiyarsu nakeyi, shiyasa nacire ran zasu samu wani cigaba a rayuwa balle su amfaneni? Mtsss Allah dai ya kyauta".Cike da makirci Umma ta kallesa tana murmushin ganin koda yaushe itace mainasara ta tashi ta ɗakko ruwa cikin fridge ɗinsa tare da cups ɗaya dake kai ta dawo ta zauna kusa dashi ta buɗe gorar ta tsiyaya masa ta miƙa masa tana cewa, "Afwan Abbansu karka saka damuwarsu a ranka kazo wani ciwo yasaka kwanciya mu shiga uku saboda ba muda wata gata sama dakai aduniya, idan har su basu buƙatarka to mu muna buƙatarka saboda haka kadena ɓata ranka da matsaltsalunsu". Ajiyar zuciya Abba ya sauke bayan ya shanye ruwan dake cikin cup ɗin tas yana kallonta, hannunta ya kamo yana Murmushi yace, "Shiyasa a kullum nake ƙara jin soyayyarki da ƙaunarki a zuciyata Hajiya Zainabu, badon shuɗaɗɗen tarihin rayuwata ya gama wanzuwa acikin ƙundin ƙaddarorina da aka rubuta ba da tabbas na shafe rayuwa da kowace macce aduniya idan bake ba". Wani daɗi ne ya kama Umma tana sake yabawa malamin da take kallo a matsayin jigo kuma maga isar al'amurran rayuwarta akoda yaushe, fari tayi da idanuwa kafin tace, "Kaji Alhaji da wani zance, ni dai mubar wannan magana tunda bakin alƙalami yariga daya bushe, tun ɗazu nake ta ƙoƙarin na samu zuwa wajenka saboda nasan kana jirana sai ga Jamil ya iso yana faɗa mani cewa ka aika masu da kayan abinci a gida kuma ka tura masa kuɗi masu yawa ɗazu da kuka gama maganar sauyin makarantar Afrah yanata faman godiya da addu'a bisa wannan ɗawainiya da kake yimasa shi da iyalansa tun lokacin aure har zuwa yanzu da an tara ƴaƴa, Allah ya saka da alkhairi Alhaji nima ina taya shi godiya". Ɗan kauda kanshi yayi gefe yana ajiye cup ɗin hannunsa kafin ya juyo yana kallonta, "Kin jiki da wata magana Hajiya, to idan ban yimasa ba wa yake so na yiwa? Shifa ɗana ne dana fara samun kalmar farincikin da kowane mahaifi ke fara samu a lokacin da Allah ya fara bashi kyautar haihuwa, to meye bazan iya yimasa ba shi da duka iyalin daya mallaka? Babu shi don haka yadena wannan godiyar bana so, kema kuma shine kika biye masa kika zo kina yimani godiyar". "Haba Alhaji yabon gwani ai ya zama dole, in dai ba so kakeyi na zama butulu ba kaza ci ki goge bakinki ai dole nima na gode maka don hidimar tayi yawa, shiyasa ma daya zo min da zancen wai Sadeeq nacan yanayi masu rigimar sai an kaishi America yayi karatu nace su bashi haƙuri bazai yiyu ba abun yayi yawa na kuma hana yazo ya gaya maka". Sake da baki Abbake kallonta jin abinda take faɗa ɗa har taƙarasa, ko bai faɗa mata ba yasan tasan matsayin jikan nasa Sadeeq a wajensa, jinsa yakeyi cikin ransa sosai saboda shine aka fara haifa masa a matsayin jikansa na farko amma har take faɗa wannan zance, ko nawa ne a duniya zai iya kashe masa ba tare ɗaya damu da hakan ba, sai daya ɗan ɗaure fuska sannan yace "Kada ki sake yimani hakan akan ɗana da duk wani abu daya shafesa, kin manta matsayin Sadeeq ne a wajena da irin tarin ƙaunar da nakeyi masa?" "Ba haka bane Alhaji, hidimar ce..." "Ya Isa haka Hajiya ina Sadeeq jikana ne ko? To kisanar da Jamil a fara shirye-shiryen zuwan duk makarantar da Sadeeq yake so zan kai shi kuma zan ɗauki nauyin komai da ake buƙata". Cikin maɗaukakin farinciki akan yanda Abba yaba maganar jikan nasa muhimmanci jikan nata ta kwantar da murya cikin iya ƙwarewa da salo makirci tace, "Kayi haƙuri Abba naga ka ɓata rai, ganin nayi Afrah ma.." take ya katse ta da cewa, "Afrah daban Sadeeq kuma daban, don haka bana so kada ki sake yanke mini irin wannan hukunci don ni a gurbin ɗa na ɗauki Sadeeq ba jika ba." Murmushi Umma takoma saki ganin ta sake samun nasara akaro na biyu tace", "Madallah da dattijon kirki, mijina abin alfaharina, Allah yaƙara arziki, ayi haƙuri Abba hakan bazata sake faruwa ba in Sha Allah, da safe zan sanarwa Jamil ɗin saƙonka, angode Sosai." Murmushi yayi yana ƙarajin sonta har cikin ransa kamin kuma ya ɗan gyara kwanciyarsa tare da rufe idonsa dan samun nutsuwar bacci. Shi kuwa Mutallab cikin natsuwa yafito daga ɓangaren Abba ya shiga cikin gidan don son sake kwantarwa da Afrah hankali akan zancen makarantar tata tayi haƙuri ta maida komai ba komai ba. A babban palourn gidan yaja burki ya tsaya daga bakin ƙofa yana kallon inda zai hango Afrah cikin ƴan uwan nasa dake zaune aciki suna kallo bayan yayi Sallama, hakan yasa suka ɗago idanuwa suna kallonsa ba tare da sun amsa sallamar ba kamin kuma su maida hankalinsu akan abinda sukeyi, wani irin tsaki Aunty Amarya da ganin Mutallab ke sata jin kamar taga mutuwarta ta saki tare da kauda kanta gefe, inda sabo ya saba don haka ba tare daya damu ba ya ƙaraso ciki don baiga Afrah a wajen ba, "Sannu da dare Anty". Cikin girmamawa ya faɗa duk da yasan ba lallaine ta amsa ba tare da ɗauke idanuwansa akanta ya maida duka hankalinsa awajen Jiddah, Aunty Amarya kuwa ba tare data iya ɓoye tsantsan tsanarta agaresa ba ta watsa masa wani banzan kallo tare da miƙewa tabar palourn, ko ajikinsa kuma hakan bai damesa ba ya kalli Jidda dake zaune tana dannar iPad ɗin dake hannunta yace, "ke Jidda ina afrah?" Ko ƙarasa rufe baki baiyi ba yaga su Khalid sun miƙe sunbi bayan mahaifiyarsu suna ƙoƙarin barin palourn kamar wuɗanda suka ga wani mugun abu, dama mahaifiyarsu ta gama hure masu kunnuwa tare da nuna masu rashin ganin girman yayan nasu da saka masu tsanarsa, Mutallab da dama a hasale yake dasu na renon daya ga suna son kawo masa don tunda ya shigo ba wanda ya hausawa acikinsu sai ma kallonsa da sukayi suka kwashesa suka watsar gefe ya daka masu wata uwar tsawa, "Gidan ubanwa zaku je? Ku dawo ku zauna". Tare da maida kallonsa ga Jiddah yana sake maimaita mata tambayar daya yimata itama, turo baki tayi kafin tace, "Ina na

Chapter 4 of 54