Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
"A'a Umma, Ni na isa na ɓata Mali rai? Jeki kedai Allah yakaiki lafiya kuma ki dawo lafiya matata, ai kina ma fita kwanciyata zanyi a daki sai kimdawo". "Da kayiwa kanka ƙiyamullaili" tafaɗa tana maka masa harara kafin tafice ta samu Jamil na kiranta a waje, Jamil dake cikin motar Abba da yanzu ita kaɗai ta rage masa kuma ta zama ta Umma ɗin ya kalleta ganin yanda tasha ado yana cewa, "takawarki lafiya Hajiya Umma, turmi kike shaluguden mahassada, in Jin dai tare zamu shiga wajen bakan nima ki sheda masa yawa buƙatar". Sai data hararesa tana buɗe bayan motar ta shiga sannan tace, "humm wannan ba kalar bokan da kasaba gani bane Jalil, kawai tashi mota muje ɗan akwai tafiya mai nisa gabanmu". Ta ga jikin madubin gaban motar ya kalli mahaifiyarsa yana haɗe fuska kafin yatada motar yabar gidan. Tafiyace sukayi ba ƴar ƙarama ba duba da ƙauyen nada matuƙar nisa dan kusan awanni uku suka kwashe kamin su ƙarasa, tun da suka shigo dajin maguna suke gani irin manyan manyan nan masu wata kalar halitta, dajin Allah ne sosai mai matuƙar duhu suna ta tsallake duwatsuna kafin can sukai ga wani dutse zasu hau Umma ta kalli Jamil tace, "Cire takalminka da rigarka". "rigata kuma Umma? Sai kace..." a ɗan hasale tace, "ƙa'idar wajen nan kenan idan bazaka cireba wuɗannan magunan da kake gani zasu cinyeka tas anan". jikinsa na rawa yacire rigarsa ya riƙe ga hannu yana nata rai, itama cire dankwalinta da takalminta tayi sannan ta shiga jan jiki daga zaune, hakan yasa Jamil yafahinci abunda zaiyi shima, kenan dai tana nufi da jan jiki zasu shiga wajen, ba musu shima ya zauna yabi bayanta suka shiga dajin, duhu sosai suka tarar a wani ƙaramin fili kafin can wata murya ta karaɗesu data matuƙar tsorata Jamil har yana ƙoƙarin miƙewa ya sura da gudu tayi saurin riƙesa ta girgiza masa kai. "Nace miki kidaina kawo mana matsorata a wajen nan, waye shi wannan da sam babu albarka atare dashi! Maza yakife fuskarsa a ƙasa yanzunnan". Jikin Umma na rawa tasa Jamil ya kife fuskarshi ga ƙasa gudun hukuncin boka ya hau kanta, kafin itace wajen suyi wata irin girgiza sannan bokan ya baiyana agabanta yana cewa, "wancan yaron mai addu'a baza mu iya yimasa komai ba, mun faɗa mako kidena kawo mana shi gurin nan inba fushin Allah da la'anarsa kike so su tarwatsamu ba kafin mu isa ga azabar Allah dukan mu, ya koma mana baƙaƙen aljannu da yawa saboda yawan addu'o'in da yakeyi dan haka bazamu iya yimasa komai ba, taimako ɗaya zamuyi Mali, wannan la'anannen ɗan naki ɗan la'ananniyar zamu mashi aikin da zai fi ɗan uwansa kuɗi, Amma idan ya kuskure to tabbas fa zai karɓe tsattsakura hukunci, kenan baƙaƙen aljannu a fusace suke sake saboda ke kika ja aka Turai gun da aka ƙonasu, dan haka ki kawo mana cibiyar kifi da jinin al'adar tururuwa domin na fansheki dan dama ni nake hanasu fuskantarki tunda kafirace ke bawata kariya atare dake, "Aci gaba da basu haƙuri tsinannen, natuna suyafe mani, ga wannan asaya masu abun yanka abasu jini". "Kul hatsabibiya, ba'a jayayya da buƙatar baƙaƙen aljannu, kije ki kawo masu cibiyar kifi da jinin al'adar tururuwa da sukace suna so tunda an biya maki buƙatar mallake mijinki da kuma bautar da kishiyarki, wuɗannan abubuwan dana faɗa maki sune ladar aikinsu ko kuma kihaɗu da fushinsu". Yana gama faɗar haka yayi wata ƙara ya ɓace wajen, Cikin murna Jamil ya kalli Umma da tunaninta ya lula akan inda zata samo cibiyar kifi da kuma jinin al'adar tururuwa yana cewa, "Gaskiya bokan nan yasan aikinsa, kinji fa zanyi arziki har nafi Mutallab, ai Ni sai yau na taɓa samun natsuwa duk malaman nan da nake shiga". Wani sauti irin na ɗari mai tsananin rikitarwa suka sake ji anayinmasu gargaɗi da ba'a fira anan kuma subar wajen tare daba Umma umurnin ta duƙa Jamil ya hau bayanta sufita da rarrafe da baya da baya sannan itacen wajen suka shiga yin girgiza da ƙarfi, ai ba shiri Umma ta duƙa Jamil ya haye bayanta ta shiga rarrafe ta baya da baya har suka fice daga filin dake mamaye da duhu. ******   CTabbas duk wanda yai imani da Allah ya kuma mayar da lamurransa agunsa to zai zame masa waraka da kuma kariya ga dukkanin wata cutarwa aduniyarsa har ma da lahira, dan cikin ikon Allah Jikin Jalil da tánte sukayi sati sunayi masa wancan haɗin na ganyen magaryar da surorin karya sihiri sai gashi jikinsa ya soma yin kyau sosai dan kuwa har masallaci yake zuwa da kansa, kuma ihun da yakeyi da daddare ma yadaina yafara murmurewa dan har abinci yana ci sosai yanzu, shirye yake cikin wata baƙar getzner sai zuba ƙamari yake tamkar ba shi bane ya kwanta ciwo kamar zai mutu. Afrah dake tsaye tare dashi zai ajiyeta makaranta tayi dariya haɗe da cewa Alhamdulillah Ganin yanda yaji sauƙin ya samu lafiya ga wani irin kyau da yayi tace, "Sannu ya jalily, gaskiya cuta ba mutuwa ba kaga yanda kayi kyau kamar ba kai ba?" "Haba!" Yafaɗa yana gyara clip ɗin hannun rigarsa yana jin wani farinciki aransa marar misaltuwa saboda yanda shi da kansa yake jin dadin jikinsa da lafiyar ɗaya samu, hannunta ta sakaɗo cikin nashi tana cewa, "da gaske ya Jalil muje kada mana makara". "To tsinkui ɗina ragguwa kin sha fa kuka da ciwon nan nawa, ashe kina sona haka". "Hmm koma dai meye bazan juri rasaku ba ya Jalil kai da ya Mutallab shiyasa naji tsoro sosai da ciwon nan naka". "Haka ne, yau idan kin dawo ki ƙarasa gida kije ki gaida Abba." Jin maganar tayi a bazata atake kirjinta ya buga tace, "Abba kuma yaya jalil?." "Eh kishirya kije ki gaishesa ko kuma kijirani idan nadawo sai muje tare". Yai maganar in a serious tone yana buɗe motar tare da shiga, turo baki Afrah tai haɗe da cewa, "Zan dai jiraka ɗin gaskiya ni tsoro nakeji." "Tohm babu damuwa shige muje ko". Suka fice dan dama sun riga da sun yiwa tante Sajida sallama, bayan sun ƙarasa makaranta kamin su shiga lecture Aryan ya kirata awaya suka sha fira ya tambayeta ya jikin Jalil ta amsa mashi daya ji sauki tana murmushi tare da ƙara jin ƙaunarsa har cikin ranta saboda yadda yake son ƴan uwanta da ita kanta, tace "Albishirinka". "Goro fari tas matata" "Yau ma tare muka fito ya tafi kasuwa ɗan jikin nasa yayi kyau sosai" "Kai Alhamdulillah MashaaAllah Allah mungode maka Allah yakara masa lafiya." "Ameen Habiby". tafada cikin lanƙwasa muryar da yasa Aryan lumshe idanuwansa, a kullum safiya sake jin ƙaunarta yakeyi a kasan zuciyarsa da duk wani sashe da rouhin jikinsa, ajiyar zuciya ya sauke haɗe da cewa, "Babyna nifa Allah naƙagu muyi aure na gayamiki yakamata ace yanzu ma inada yara, ina bukatarki a kusa dani sosai babyna". "Uhmm to yanzu me kakeso nayi?" "Kiyiwa babban yaya magana please Baby". Zaro idanuwa tayi tare da langaɓe kai tamkar tana gabansa tace, "Bazan iya ba gaskiya Habiby". "Okay okay ni zan masa tunda na kula kunya kike ji, Ni kuma wannan kunyar bana sonta in sha Alla nan gaba kadan zanyi maganinta yadda zata dena takuramu tabarmu musha soyayyar mu". Rufe fuska tayi cike da jin kunya kafin sukayi sallama... #Mutallab Asad #Ƴan Tagwaye #Nana Diso #Billy S Fari MUTALLAB ASAD   (Labari mai taɓa zuciya) Na Billy s fari Nana diso    RUBUTUN ƳAN TAGWAYE KARO NA BIYU      TAFIYAR BIYU TAFI DAYA SHAFI NA HAMSIN DA ƊAYA. Wuɗannan maganganu da mahaifiyar tata tayi mata sune suka baƙanta mata zuciya har takasa kwana saboda zuciyarta dake yimata wani irin raɗaɗi wanda tuna hakan yasa takasa daina kukan nata da takeyi cikin ɗaga muryar, sosai kukan nata daya ishi yayartata yasata miƙewa zaune tana fadin, "wai ke lafiyarki kuwa? Bakida kai ne kika zauna kina wannan kukan kamar na mutuwa kin bi duk kin hanamu bacci?" Banza Aïcha tayi mata har sai da taji mahaifinta ya shigo ɗakin da sandarsa yana coccokala wa tare da bin sautin kukan nata ya isa inda take zaune yana mammakama tayar Tata dake gefenta zaune sandar, "ince dai ba wani abun kikayi mata ba?" "Me zanyi mata mè pèrè? Kawai ta damemu da kuka ta hana mutane bacci ɗan mugunta". "Aicha wani ya dakarmun ke ne?" Ya tambaya yana ƙoƙarin zaunawa ta gefen ɗaya jita zaune, Turo bakinta tayi tana cigaba da kuka tace, "Inma duka ne ai kusan kullum kaine kake jawowa adakeni naga to wallahi ni bazan kara rakaka bara ba idan yaso ku kasheni ku huta tunda kakasa biyamun kuɗin makaranta kuma kana dashi".  "Amma yarinyar nan anyi ja'ira yanzu akan kuɗin makarantar kike wannan uban kukan haka? To Shikenan ai zan biya miki saka kafadunki ki kwanta da sassafe zan baki kuɗin kinji ko?" Washe bakinta tayi tana goge hawayen da yazubo mata tace, "Da gaske kake mà pèrè?" "Eh mana, cewa fa kikayi bazaki sake rakani Bara ba Aïcha! To taya zan ɗauki wannan asarar, gobe da sassafe ki shirya kizo ki karɓa zan biyamiki, ai kinfi wannan datake kwance da bama ganin sisi ta kwana biyu narasa uwar me takeyi yanzu, sannan ke kuma Aïcha kar kiji nace zan biya kudi tunanin duka biyun zan biya mako, to a'a ɗaya zan biya miki ta bokokon nan amma ban iya biya miki na islamiya." Murmushi tayi tace "Nagode da wannan ɗin ma mà pèrè". "Yawwa to akwanta ahuta sai da safe". Yafaɗa tare da miƙewa ya fice daga ɗakin. Washegari tatashi da sassafe ta share ko ina tayi wanke-wanken da batayi ba jiya sannan tasamu gefen da akayiwa suminti ta zauna tana cin sumammen tuwon da mahaifiyarta tayi jiya, tundaga nesa mà mèrè data hangota zaune damɓalɓal a ƙasa take cewa, "Ke Aïcha wai bazaki daina zama aƙasa ba bayan nafaɗa maki ba kyau? Ina kallo Babu takalmi kika tafiya akan suminti kuma shima kinsan na haneki, wai meyasa ku yaran nan ana nuna maku abinda zai karemu daga cutar da kawunanku amma bakwa ganewa zaki tashi ko sai nayi miki mugun duka? So kike kije sai kinyi aure adameni da maganin sanyi infection ya lallata ki ko kisa biyama wanda zai ɗaukeki buƙata? sau nawa zan gayamiki kullum kisaka takalmi kamin kifara aiki? Yanzu kuma kan simuntin kika kafa duwawukanki kika zauna salan sanyi yayi miki illa". "Mà mèrè...." "Zakiyimun shiru kokuwa? Mara hankali kawai daman babanki yacemun kullum kina tafe kinajin fitsari haka kike shiga banɗakin kasuwa da gurare bakya tunanin ɗaukar wata kwayar cutar." "Saboda Allah fa mà mère atsaye nakeyi banayi a tsugunne". " Dallah rufen baki sai kace mai ruɓaɓɓiyar mara daya biyu kin nemi bandaƙi kinaganin kinada kyau ga kira mai kyau to su maza basusan wannan karatun ba idan kika lallata kanki da infection namiji ba kirki zai yimiki ba mazan yanzu ya suka ƙare ma da biyayya da ladabi ina kuma da jiki yasamu lahani?" "Kai mà mèrè tunda dai na tashi kiyi haƙuri bazan kuma ba". "shi kuma takalmin fa? Bakisan sanyi tanan yake shiga ba? Duk talaucin mu ina kokarin siya muku silifas ai, kishige kije ki dakko pant dinki kisamu toka da ruwan zafin can da nace ki dora ki wanke su tas tunda yanzu dai babu halin siyo sabbi sai ayi maganin infection ɗin". "To mà mèrè, Allah yanda kika san abubuwa haka na gyara jiki tare da kula da kai da zakiyi amfani da damar wajen wayarwa da mutane kai tare da haɗa ire-iren magungunan da ranar naji kina faɗawa ƙawarki Allah da kin riƙa samun kuɗi kindena neman kuɗin nan idanuwa a ruf.." kafin taƙarasa rufe baki mà mèrè ta jefota da kofin dake hannunta tana cewa, "to bazan yi ba ɗin dama wannan bakin naki ai baya shiru idan bai maida martanin magana ba". Aïcha na dariya ƙasa-ƙasa ta ajiye kwanon tuwon data gama ci gefe guda bayan ta ɗauraye sannan tashiga ta kwaso panties ɗin nata ta shiga wankewa da toka da ruwan zafi kamar yanda mahaifiyar tata tafaɗa mata, sai data gama sannan ta shanyasu arana". "Kije ki ɗauki magaryarcan dana dafa kiyi tsarki dashi wallahi ko da wasa naƙara jin kin zauna aƙasa ni dake ne". "To mà mèrè bazan kuma ba kiyi hakuri". sai da tagama sannan tayi wanka tafito dakinsu tashiga cikin kayan yayarta ta dakko basilin tashafa sannan tasaka kayan da taga mà mèrè ta ajiye mata ba tare da tayi musu ba, sosai kayan suka karbeta ita kanta sai datace MashaaAllah tabarakallah halitta iya halitta dan kuwa Allah yabata hips da breast sosai, fitowa tayi daman hijjabinta kyaurensu ta ajiyeshi. Kallonta ma mèrè tayi haɗe da cewa mà pèrè, "yau kam bakaga diyarka ba sadaka sai kun ciko aljihu." Aisha dake tsaye kamar tayi kuka tace, "Wallahi wannan shigar babu kyau na gaya muku, ni kabani kuɗin makaranta da kace zaka biya nafara riƙewa kar muje mudawo kace bakasan da zancen ba". "Naji zan baki Aïcha amma naƙara jin kince zakiyi muna wa'azi ni dake ne, shige muje". Yaƙare zancen yana dafa kafaɗarta suka nufi ƙofar fita mà mèrè na biye dasu a soro dan kuwa ta fahimci jiya Aicha tasaka hijjab dan haka sai tabiyosu abaya gano hijjabin tayi da sauri take ta ɗauke tana fadin, "wato jiyama shi kika saka ko Aïcha, wai meyasa ke ana nunamiki gabas kinayin yamma kinfiso kidinga wasu shiga kamar na mahaukaciya duk sa'anin ki da samarinsu ke kuwa duk tsoronki maza sukeyi." Mà pére ɗaya jinfaɗan na ma mèrè ba ƙarewa zaiyi ba yace, "muje Aicha bar fadan mahaifiyar nan taki." Tana ƙunƙuni tabi bayansa tana ƙwalla, da tasan ma mèrè zata ɗauke mata hijabi da bazata saka kayan nan ba wlh, Sai da suka fita sannan tace, "ina kudin makarantar ma pèrè". Aljihunsa ya laluba yace gashinan mu biya ki biya ko?" "Nagode ma pèrè Allah yaganar dakai barar nan ba abunso bace ba." Buga mata sandar yayi agefen hannunta tashiga murzawa tana fadi, "to ba gaskiya nagayamaka ba Ai addu'a nayi maka kuma mai kyau ce".. Baice mata ƙala ba har suka ƙarasa makarantar tashiga tabiya tafito suka dauke hanyar babbar kasuwa gurin manyan gine-ginen da akeyi, tunda suka shigo kasuwar maza ke Binta da kallo suna zuba mata idanuwa, wasu ma ma na gayamata maganar banza ta riƙa jinta atakure tabata daman ƙanƙame jikinta, da haka sukaci gaba da bata su har aka kira sallar la'asar, suna ƙoƙarin fita kasuwar ne wata babbar motar tashiga dallowa ta gefen ɗaya daga cikin makakken ginin da aketa faman yi ta nufi wajensu, ahankali aka sauke glass din motar wannan Alhajin ne na ranar yashiga washe baki yana lashe lebe,  tun daga ƙasa ya turokansa ta window ɗin motar hannunsa na safe da stearing wheel ɗin motar ya shiga kallonta, yana dora idonsa akan ƙugunta yaji wani abu ya fizgesa da karfi, bai sake ruɗewa ba sai da idanuwansa sukayi masa tozali da ƙirjinta dake cike fal dai-dai jikinta, jin yai numfashinsa na ƙoƙarin ɗaukewa bakinsa na rawa yace, "Baba kaine? Sannu da fitowa". yafada yana kashe motar sannan yafito ya nufesu yana tsureta da Mayun idanuwansa masu kama dana ƴan iska kamar yanda take faɗa a zuciyarta, ma pèrè najin muryar Alhaji ya washe baki dan ya gane muryar tasa sosai yace. "Ɗan albarka ashe zamu sake yaɗuwa, kwana biyu?" Alhaji da idanuwansa ke kan Aïcha data haɗe rai tana ɓuya bayan babbar rigar ma pèrè yace, "eh baba nayi tafiya ne, ga tsarabarku a mota ma ɗan ban mance daku ba" "Allah sarki yaro Allah ya maka albarka, Aïcha kina ina banji kin gaishesa ba bale kiyi masa godiya k bakiji me yace ba". "Angode". Tafaɗa ataƙaice tana dallawa Alhajin harara, murmushi ya sakar mata dan shi ji yai kamar tayi masa wani kallon soyayya ne, haka ma yau ya tsaya yana sake yiwa ma pèrè bayanin irin tarin arziƙinsa da abubuwan da zai yimasu indai Aïcha ta amince dashi, jikin ma pèrè da yaji zancen kuɗi na tsima yace, "Aïcha kinji fa, barar nan dena shi zamuyi har da gida zai saya mana, Kinga maza bishi bari na jiraki anan". Ma pèrè ya faɗa yana laluba gun da zai zauna, taimaka masa alhakin yai ya zauna sannan ya fiddo bandir ɗin kuɗi ya saka masa a hannu yana cewa, "baba fara rike wannan naka ne, bari mu shiga mota takarɓo makau tsarabarku". "Ni ba inda zanje wlh". Aïcha tafaɗa tana zaunawa kusa da ma pèrè, bai san lokacin daya ɗauki sandarsa ya shiga maka mata yana cewa, "yau naji dibar albarka, zaki shige ki karɓo mana ne ko kuwa?" "Ƙyaleta baba bari na dauko maku da kaina". Alhajin ya faɗa yana ƙoƙarin juyawa, "kaga tsaya ai wlh bata isa ba, kasa kuɗinka kasiya zuwa kaɗai takarɓa ne bazata iya ba, kina ina kike nace ko nayi maki Allah ya isa". Ya ƙare zancen yana laluben aljihu tare da taura kuɗinsa aciki, Aïcha na hawaye tabi Alhaji da har ya shiga mota ya bude mata gaba yana cewa ta shigo, "Ni dai ka miƙo mani nace" tafaɗa tana turo baki, murmushi yai ɗan kyanta sake kashesa yakeyi ya kwantar da murya haɗe da cewa, "haba Aïcha shigo ki karɓa mana nema akwai kuɗin da zan baki, gashi ina so ma naje nayi maku sayayyar kaya da yawa ki zabo da kanki". "Bana so kariƙe abunka". Muryar ma pèrè taji yana cewa, "Aïcha zan fa yimaki Allah ya isana". Sai data bubbuga ƙafa tana ƙwalla sannan tashiga motar, bata saka ƙafafuwan ta ba sai daya sake roƙonta tana turo baki sannan ta shiga gaɓa ɗaya #Mutallab Asad #Ƴan Tagwaye #Nana Diso #Billy S Fari SHAFI NA HAMSIN DA UKU. *MUTALLAB ASAD*      Arewabook:- billysfari       Paid book ne, N500 via ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A, Gt bank, sai shaidar biya ta +234 704 040 2435 ko +234 809 845 6130 Ga masu son vip post 1k ne. Sauran ma'aikatan ne kowannen su yazo yana haƙi tabbatarwa da Mutumin yagudu. Hakan yasa Mutallab yin gaba batare da yacewa kowa komai ba haka kawai yaji bai yarda da yarinyar ba kuma. Ganin yayi gaba har ya huce matattakalar karshe yasa daya daga ciƙin ma'aikatan kallon Aicha suka ce " shige Kibishi yaƙaiki yagida" sukama suka cigaba da karasa aikinsu. Sosai take kuka duk fuskarta tayi jajir ga gefen fuskarta da Alhajin ya karta hannunta ma ta yanke da flower vase saboda yadda da datsa masa acikin hannunsa. Ko da takarasa yana ciƙin mota ita kuma tana bakin kofar motar takasa karasawa gani takeyi shima zai iyayin Abinda Alhajin ya aikata mata, Cikin zafin kai da masifa yace " zaki shigo motar kokuma sai ƙin karasa bayyanar da fitsarar taki." Hakan yabata damar shiga bayan motar shikuma baice mata komai ba ya kunna motar duk da yadda jiƙinsa yakejinsa ba nasa ba ga yanayin kunci da yaji yashiga wato itama dai yaudararriyar yarinyar ne abaya ai bai ganta da wannan shigar ba yanzu kuma yaganta da mafi kazantar shiga. Ko da ya hau ƙan titi baice mata ina suka dosa ba sau cewa yayi " Ita diyar mutunci Kana ganeta ne ta hanyar suturta jiƙinta, babu ta yarda macce mai mutunci da kima zata banzatar da jikinta kuma tace zata samu daraja ko kema a idanun al'umma talauci ba hujja baniba." Kara sautin kukan tayi tana fadin " Ban kasance daga ciƙin wannan ayarin da kake ambatata dasu ba ban kasance daga ciƙin mutanen dakake jifana dasu ba Ni din bakowa bace ba face mai bin umarnin iyayena Nasance mai gujewa wasu dabi'un Nasu Amma kash Aibatarwa garinr yakasance ina gudun lafazinsu.wallahi Allah iyayena ne suka saka ni saka wannan tufafin, kuma mahaifina yasani bin wannan Alhaji ta hanyar Nuna fushinsa da Ambatar Allah ya'isa idan ban bisa ba." Duƙan sitiyarin yayi yana jan wani burki ya tsayar da motar jin yadda zuciyarsa take masa mugun zafi. " haramun ne agariki kiyiwa iyayenki laifi don ki kare ƙanki su din sun kasance rayuwarmu su din mutanene masu daraja sudin bazasu taɓa ƙaimu ga halaka ba sau ma ga karemu daga halaka karya dasu tana sawa zuciyata tayi zafi ina ne unguwarku." " Nasani bazaka yarda ba nasani zaka kirani da makaryaciya Nasani zakace nafaɗi hakan dan na kare kaina Amma iyayena bakamar iyayen da kasani baniba, sudin mutane da ilimi bai wadace su ba neman duniya ya rinjaye komai Na rayuwarsu, Indai zasu samu kudi to tabbas komai akan daidai yake ko da kuwa haramun ne...takasa karasawa tana kuka.. duk wani sautin kukanta sai yajishi har cikin jiƙinsa sai yajishi har tsakar kansa, yadda jikinsa yashiga zubawa yasashi rufe idanuwa sannan A hankali yace " kiyi shiru banson kukan nan." " Taya zan iya daina kuka? Tayaya? Kasan kuwa Nunawa mahaifiyata nagudu daidai yake da yankani agidan mu yau, ina tabbatar maka tana nan da ruwan magani tana jiran into ta gyarani babu ruwanta da diyarta ta aikata zina ko tayi sabon Allah, kaicon kaddarata kaicon samun iyayen da basajin tsoron haduwarsu da Allah." Sosai jiƙinsa yashiga tsuma yanabin hanyar data gayamasa zata sadasu da gidansu. Ko da suka isa karamin ginin kasar da kana ganinsu kasan talakawa ne sosai, jin karar mota yabawa baba damar saurin fitowa yana fadin " Aicha har kin dawo yabaki kudi dai ko zaki iya fitowa Ko mamanki taxo ta daukeki." Da mugun mamaki Mutallab ya daga idanuwansa yana kallonsa with shock sosai. Mama dataji an akwala mata kira yasata fitowa da gudunta tana faɗin " kunga diyar kirki bari nazo na daukike basai kin wahala ba, ta bude kofar hakan yasa Aicha jara fashewa da kuka maman na fadin " Ke dai bazaki canza haliba yanzu kiduba kiga motar da akawoki saboda Allah ina fatan yabaki kudi dai? Yafarkaki ne kiketa kuka, muje ma Na tanadi magani." Hakan yasa yasa mama ta kalli Mutallab tace " ina kudin nata ne? Tunda ita kamar agajiye take takasa magana." Karo na farko da yadago rinannun idanuwansa da suka canza daga fari zuwa ja." Ahh Ashe shine alhajin sannu Alhaji mungode fa Allah yasaka da Alkhairi naga kaima kamar da gajiyar akanka ko to bakomai sai ka kara dawowa muje ke kuma, yanaga kafar taki bata takawa sosai dan ubanki ki bude baki kigayamin idan ya yagaki da yawa mu kara kayan gyara. Da idanuwa mutallab yabisu zuwa har suka shiga gidan ganin mutane tsalli tsalli na kallon motar yasashi jan motar yafita daga layin" Innalillahi wa'inna illahirrajiun shine abunda yaketa ambata ko da ya fita titi kashe motar yayi jiƙinsa nata rawa kuka nacin karfinsa Innalillahi wa'inna illahirrajiun yanzu akwai irin wannan iyayen? Su suna ganin basuyi dacen mahaifi ba Ashe mahaifinsu mutumin kwaraine akan wannan kazantar da yagani, yaaAllah ya Allah ka zabamin Alkhairinka zan gyarata zuwa abunda zasuyi alfahari da'ita? Yanzu ina son sanin suwanene su? Babbar yaya da shigowar ta kenan daga siyo kifi ta kalli ƴar uwar tata sai taji hawaye da tausayinta shikenan itama sunyi sanadiyar lallacewar rayuwarta kamar yadda sukayi nata. Saukar kukan Aicha tana zama gefen mahaifinta, yasata faɗin mama kunsan zamu mutu kuwa? Mama hakan daidai ne? Hakan soyayya ce?." Mama dake juye ruwan zafi tace zaki iyimun shiru ko sai naso na laƙadamiki duka ne? Eh nace zaki iya bakinkinko sai na gasa miki shi, sha -sha -sha wacce batasan inda ke yimata ciwo ba, in banea shirme da hauka kiga yaro matshi kyakyawa ga kudi kiduba fa kiga har gida yakawoki yayarki fa sai mu mukaje muka dakkota, idan Allah yasa kinyi masa ai auranki zaiyi in kuwa ya aureki ai yayo dace Nifa ƙaf zuri'armu babu wulakantaciyar macce duk da bakar dabi'ar mahaifina rububbin yaransa akeyi saboda gyara da kulawa da kai kunadai ganin ni kadaice na aure talaka amma duk sauran yan uwana ai kunsan wanda suke aure tashi malama kishiga bandaki nakaimiki na gashi da zama cikinsa. " " Ganin idan ta fadi gaskiya mahaifan nata zasu iya yimata baki yasata saurin mikewa tana bata rai tashiga bandaƙin ruwan maganin da tasan mahaifiyar tata ta hada ta zujeyi shi acikin masan tsugunen su sai data gama komai ta fito tashiga daki tasamu yagulalliyar katifarta ta kwanta yayarta data zubo mata abinci ta karaso kusa da ita tana taɓata ganin yayar tata tana kuka itama sai ta fashe da kuka, " sœur (yar'uwa

Chapter 30 of 54