Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tayi magana Mommy tamiƙe tana cewa, "Haba Alhaji wace irin magana ce wannan? Taya zaka hanata shigowa bayan ƴaƴanta na cikin gidan wannan sam bai kamata ba, kuma bakaga meenal din batada lafiya ba tana buƙatar dumin mahaifiyarta Ai, sannu da zuwa Mahma karaso daga ciƙi" mumy tafada tana murmushi hadi da ɗan Nufota. Ɗago kai Mahma tayi ranta a ɗan ɓace tace, "waye ya kasa dake? Kibarni nayi dashi ai yafiki sanin ƴaƴana nacikin gidan tunda tare dashi na haifesu, koma meye ai kece munafukar dake nema ta shiga tsakaninmu tunda kece silar dakatar dani shigowa gidan, ɗan haka idan wancan karon kinyi nasara to wannan karon baki isa ba saboda gida na ƴaƴana ne babu wanda ya isa ya hanani shigowa cikinsa". Tana ƙare faɗar hakan tawuce fuuu ta haye sama zuwa ɗakin Meenal ya Kamal yabita baya da akwatinta." Duk da mumy taji zafi Amma sai kawai tayi Murmushi batace komai ba sai binta da ƙallo da tayi. Duƙar dakai Dady yayi cikin matsanancin ɓacin rai ya ɗago kai yana kallon Mommy data kasa furta ko a har Mahma tabar wajen yace, "Kin gani ko? Abinda nake so na hana faruwarsa kenan amma kika dakatar dani". Karka damu dadyn meenal babu komai, ai baƙonka Annabinka Ni bandauketa da komai ba Allah yagani kuma ai ƴarta tazo dubawa kuma a musulunce ba'a hanata ba, indai ta nine kar wannan abun yadameka, in sha Allah har tatafi bazan yanka mata ba". Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya sake kallonta yace, "Shikenan Allah yai maki albarka, amma kina ganin da akwati fa tazo, hakan kenan na nufin zata kwana ne". "Ko kwana nawa zatayi Alhaji tayi bakomai, fata dai Allah yaba Meenal ɗin lafiya". "Amin ya rabbi". Dady yafaɗa yana barin wajen don dama yagama breakfast ɗin. *********** Boka maganar ka gaskiya ce Amma inaso kayimun Aikin da yaronnan nan zaifara bin mata yanzu bana ta ubansa dan nagama dashi wallahi ko kara Na ajiye bazai taba tsallakawa ba inason yazama dan iskan nagasken gaske. " hu hu hu he angama angama amma bazamu iya shiga jiƙinsa ba dan kona mana aljanu yaƙeyi yana yawan Azkar da Ambata Allah yanzu ma baya kasar ai." Da mamaki umma tajiyo tace " Baya kasarfa kace?" " Akwai Alamun haka Yanzu dai Munasom baƙaken akuyoyi gida 4 sai bakar maggi guda biyu zamuyi Aiki Akansa ta yarda idan yaga macce sai yayi kamar ya afka mata." " Nabiyaka bokana nagama gashinan Asiya dukkan wani abu da ake bukata zan dawo bayan sati daya." Ga wannan layar kisaka A cikin fulan mijinki zaki samesa fiye da da, wannan kuma kisa masa aruwan wanka yayi kinsan Aljanunmu sunajin dadin shiga jiƙinsa tunda baya ambaton Allah ko karatun Alkur'ani bayayi." " Angama boka Nabiyaka tafada tana tafiya da baya da baya. ****** Tunda su Afrah suka tafi jalil sai yau yasamu sukayi waya duba da basu saita layinsu da wuri ba, sunyi magana sosai akan kasuwa kamin kuma afrah tashiga bashi labarin Madina da rauda da gurin tahirin da sukaje, sunje ma bakiya Nan yayi ta yimusu Addu'a har yana fadin yaya mutallab kayimun Addu'ar mata tagari danAllah. " Ina yimaka ai Jalil ina, ina tante? Bani mu gaisa."mika mata wayar jalil yayi suka gaisa itama tace yayi addu'a fa sosai Afrah ma tayi addu'ar miji nagari, yace mata insha Allahu duk sunayi aryan yazo kuwa?" Wallahi yaya har gidansu naje wai yayi tafiya ina tunanin ko gurin aikin nasa ne suka turashi wani gurin ko?" " Eh to zai iya yihuwa container sun sauka ko?" Eh yaya gobe zasu dakko hanya." " To Allah ya iso dasu lafiya a cire kudi kaje kayiwa su Abba siyayyar kayan abinci." " Su abba kuma yaya saboda.." Banson jin komai kayi yadda nace kuma ka dora masa kudin cefani dubu dari biyu akai." Duk da yaji babu dadi cikin ransa amma haka ya amsa masa sunayin sallama. *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *MUTALLAB ASAD* *PAID BOOK #500* *TAGWAYE BIYAR.* NA *NANA DISO** & *BILLY S FARI* 39.   Tafiyace mai dan tazara kadan takawoni gida, sallama na rangada sannan nashiga, ganin Mama tafara hararata yasa nayi saurin canza fuska na nufita " S'il te plaît, ne me bats pas, que veux-tu que je fasse pour toi ( DanAllah karki dakeni me kikeso inyi miki?)" Muryar baba taji yana faɗin " Ince Banhanaki zuwa makarantar nan ba? Na lura su suke huremiki kunne." Yaya dake gefe ce tace " Ai idan baku hanata ba watarana sai ta kafirtaku, kuma kizo kibiyani abincina da kikaji ko da zaneki wallahi." " To ke yanzu ba abun arnan kikeyi ba? Dubu karin gashi ga farce da matsatsun kaya duk sura a bayyani S'il vous plaît changer (danAllah kicanza) ." Jin zata fusgoni yasani yin bayan Mama." " Aicha Ni sa'ankine banza mai kama da mahaukata dubi shigarki." " Gwarani kama nakeyi da mahaukata kefa? Arniya kike kama dasu." Jin saukar marin da mama tayi mata yasata saurin barin gurin hakan yabawa yaya babba damar riketa tashiga duƙanta." " Dakarmin fitsararrar yarinyar nan sosai yadda gobe zata shiga taitayinta." " Jin yadda ake dukanta yasata saurin durkusawa tana kokarin guduwa amma duba da yar uwartata tafita karfi yasa bata samu damar guduwa ba, jin yadda ake duƙanta yasa hankalin baba dan tashi yace " Barta haka karki nakasata mudaina fita bara yihakuri ki kyaleta da halinta." Jin an sassauta mata duka tace " Allah yana kallonki wallahi kuma shine mai sakayya kuma ban faɗi karya ba ai bakya shigar rashin da'a." Ki kiyayeni wallahi Aicha idan na rikeki bakijin da sauki, dauki bokitin ruwan kije ki jidomana." Sosai take kuka tasan daman baza'a taba goyan bayanta ba jin yadda kowannensu ke mata faɗa yasata saurin daukar robar ruwa tayi hanyar tuka tuka, ko dataje tatarar da layi duba da anfi daukar ruwa da daddare sai dataci rabin layi sannan ta hango lami daga can karshe suntawo da'ita da nata ayarin ganin Aicha tsaye yasasu kyalkyalewa da dariya suna faɗin" kunga sarakan bara da maula ke mai bara zo kikarbi sadaka." lami tafaɗa tana kyalkyalewa da dariya. Wani ne alayi yace wai har yanzu babanta bai daina bara ba?" " wannan tsohon mai dankaran son abun duniya tayaya zai daina ai yananan maula sai wacce tayi gaba." " Jarababben tsoho daman ance idan kafara ai baka dainawa yanzu haka diyar tasa yake siyarwa ake bashi kudi." " To daman bakaga yayarta ba? Ai cikakkiyar ƴar iskace to kana ganin ita bata fita barara ita kuwa kanwar kasan nawa take siyarwa." Duka gurin aka saka dariya wannan shine karo na farko da akaga Aicha ta kaure da dambe itada lami, sosai ta hau kan lami tayi mata dan banzan duka, sannan takara dafaɗin " Ubanki ai ke kawalci yakeyi gwara nawa bara yakeyi kuma duk ranar dana karajin sunan grande soeur(babbar yaya) kokuma babana ko ni bakinki sai na karyaki tafada tana daukar ruwanta tayi gaba, sai alok'acin kuka mai karfi yazo mata dan baba yariga yabata musu sunan ahali. ********    Washegari yaƙama Laraba Mutallab yahaɗa musu komai da suke bukata agidan hatta kayan abinci yasiyo, Yanzuma yana kwance ƙangado duba da jirginsu bazai tashi ba sai wajejen karfe biyar Na yamma yauma yatashi da wata muguwar kasala wacce ta haifar masa da miƙewar tsigar jiƙinsa dan yau hatta yanayinsa yasan ya canza sosai, dan bayan sallar Asubahi baisamu yakoma bacci ba sai muraji'a dayayi yayi lissafin kayansu da suka karaso. Wayarsa ce tafara ringing ganin babu kowa ciƙin dakin dan tun safiya Jalil yafita kasuwan. Tana daf da tsinkewa yadaga yana karawa a kunnesa. Saukar kalmar da yajine yasa yaji Wani sanyayyen feeling yana ziyartarsa " uhmm Amincin Allah yatabbata Agareka yayana dan Allah kada ka katsemin wayata na yarda zamuyi zumunci na yaya da ƙanwa." Baisan sanda murmushi yasuɓuce masa ba jin yadda taƙe kashe murya " Ina kwana kana lpya?" Takara jiyo masa maganar tana murmushi." " ina lafiya meenal ƙin haɗani da Abbanki yaƙirani yanata daɗa ko?" " DanAllah DanAnnabi kayi hakuri tafada da alamar firgici atattare da'ita." " To yagida yafada." Ciƙin alamun shagwaba datazame mata jiƙi tace " Banida lafiya fa ina kwance a asubuti " " Subhanallahi Allah yabaki lafiya." " To danAllah nadinga kiranka? Zaka dinga dauka? Allah zan gyara dabi'a ta zan kuma dinga sallah." Cikin mamaki yace " Au Sallar ma bakyayi?" " A'a wallahi inayi amma hadewa nakeyi daga yau zan daina daman mumy tacemin babu kyau." " To yayi kyau." " To bakayimun addu'a ba." " Allah yashiryeki yafada sautin gajiya da magana da'ita yana bayyana." " Kahuta lafiya anjima zankiraka Nagode Allah yakara maka lpya." Dariya kawai yaji ta suɓuce masa bayan takashe wayar tashi yayi yasamu yayi wanka yasaka wani yard mara nauyi sannan yafito. Ko sanda yafito suna zaune suna ƙaryawa. " jalil har kadawo?" " yaya Report Na manta shiyasa natsaya ina karyawa." ma mère soeur bonjour (ina kwana anty ) " dariya duk sukayi daman kanaji har yanzu?" " tante inaji sosaifa jalil ma yanaji." Afrah ce tace " Nima yaya Allah ina ɗanji fa har nayarwa." Jalil ne ya harareta yace " arrête de mentir (kidaina karya)." " je ne mens pas (Ba karya nakeyi ba." Damamaki sosai suka kalleta sannu da aiki Tante (aunty). " Sannun mu ɗan Albarka ya Niya kuma? Allah yakaiku lafiya." " ameen tante." Da kanta tazuba masa abincin." Har yagama ci babu wanda yayi magana sai da yagama sannan tante tace " Nikam danAlbarka kanadai sadaka ko?" Kallon ta yayi sai da yakarasa shan shayin sannan yace " Inayi Tante sosaima ɗan duk container sai mun ware mata." " Yauwa MashaaAllah idan da hali ko malamai kuna sakawa suna muku sauka da addu'a ko? Da ɗan neman maganin tsari dan wannan lamarin mahaifin anku banajin yin ƙansa ne duk da mahaifiyar ku ma batason harkar malan nan Amma tunda duniyar tazama abun tsoro ko na tsari ne." " tante dukanmu bama wasa da addu'a addu'oin safen nan dana yamma muna kokarin yinsu tante sannan sadakama bama wasa da'ita ko afrah nace tayi sauka tante zata iya malaman nan idan kabiye musu sai sukaika harkar halaka wallahi dayawansu makaryata ne, inshaa Allahu zamu kara dagewa da addua fiye da da Tante kundaiji ko jalil." " inshaa Allahu zamu kara dagewa." " Ƙunsan yanzu mutum abun tsorone sai ka kiyaye sosai saboda hassada da idanu dan ma naga ƙun iya taƙunku." Murmushi yayi sannan yace " bari Naje kamin anjima akwai abubuwan da zan karasa. ******    Sai wajejen ƙarfe 2 sannan Aka sallami meenal yau jinta taƙe kamar an mata tukwici saboda Abun kaunarta ya amsa wayarta, kwance take akan gadonta alamun turowar kofa yasata daga ƙanta, yaya kamal tagani tsaye yana kallonta." Ya jiƙin naki meenaluwa? Ko dayake ciwon so ke damunki ba rashin lafiya ba." Karasowa yayi yazauna yana kamo hannunta. Meenaluwata dan Allah ki kulani mana." To bakai baniba." " kiyi hakuri matar mutallab yafada yana dariya rungumeshi tayi ta bayanta tace yauwa jamil dina yanzu Kayi magana zansa dady yacanza maka wayar yau dinnan." Dariya yayi yace au kin dauka ke kadaice ƴar dady to ai yacanza mana har mumy jiya." " Shine ni ba'a canzamin ba ta taɓe baki tana hararsa, shigowar mumy ciƙin daƙinne yasa Meenal taɓe baki alamun kuka tace " Mumy babuni aka canza waya? " " To saƙeshi kai jamil jika zamuyi magana da diyata " " Ohh yaushe aka ɗinki haka like serious yafada yana dariya." Hankadashi Meenal tayi tace " menene naka aciki ko mumy." " Itama murmushi tayi cike da tausayin meenal din duk fitsararta da girman kan nata soyayya tana neman taɓa mata kanta. Wayarta ta rarumo tace " Mumyna kinga dazu nakira Yayana asubuti yaɗauka har yanamin murmushi wallahi jina nakeyi yau nafi kowa lucky." A hankali mumy ta kira sunanta tace " Meenal? Please calm down take it easy wannan soyayyar da kikeyiwa yaron nan tayi yawa Meenal kema kija ajikin mana ƙinga ke macece." Hawayen da bata shirya saukarsu ba taji tace " Mumy zafin ƙaunar Mutallab kullum kara huruwa yakeyi ajiƙina, mumyna soyayya tanada zafi tana dace tanada dafi tanada radadi mumyna, nakasa narasa na rikice akan Mutallab Asad abaya banyarda da so ba amma yanzu ina tsoron so dan kuwa ya maidani wawiya mumyna." " To Allah yashiga lamarin meenal yanzu dai ƙinga kince kin canza ko?" Eh mumyna yauma da wuri nayi sallar azahar." " To mashaa Allahu haka nakesonji, yanzu dai kinsan Kamal ba muharraminki bani bako? To banson nakara ganin yana taba jikinki ko kina taba nasa ƙinga mijinki bazaiso yaga matarsa tana irin wannan abubuwan ba sannan rungume rungumen naku yayi yawa ita sha'awa batada mafadi shi namijine shaidan bazai duba ke kanwarsa bace ba, ba fata nakeyi ba Amma daga yanzu ki hanashi shigowa daƙinki sai kin basa izini sannan wannan shafar da yake miki ki hanashi kinji? Mu al'adarmu kunya ta koyar damu." " Mumy Allah bazan karayi ba bazan karaba nadaina ni ko magana ma kadan zan dinga yimasa." " meenal Nutsu ba magana nace kidaina yimasa ba." " Nagane mumy nadaina komai kikace kuma kayana duk zan canzasu Yayana yace bayason macce mai irin shigar da nakeyi." " Aikam dai za'a sha aiki duk kayanki ai banaji akwai wacce ba fitted ba ko?" Mumyna babu duk sun kamani." " To zan gayawa dady gobe zai muje siyayya." " To mumy anjima nakira Mutallab?" Jiyowa tayi tana kallon yadda tayi maganar, sai taji kwalla ta ciko mata idanuwa wai meenal ce haka? Kai dafin so daban yake." Batare da tabata amsaba tace tana zuwa tafita. ******* Cikin wata matsananciyar damuwa dake cin zuciyarsa yake cewa "Inaso zaka yimun Aiki". "Akan wa?" Sai da yayi murmushi a zuciyarsa yana cewa tabbas dole wannan karon na hukuntaka hukunci mafi muni da zai azabtar dakai takowace fuska kafin ya fiddo hoto ya nuna masa yana cewa, "Akan wannan". Azabure saurayin yace "Wannan ai Ubagidana ne". "Ba matsalata bane, asalima sanin hakan yasa na nemeka da wannan aikin, idan ka amince zan baka 1m". Zaro idanuwa saurayin yayi jikinsa na rawa jin yawan kuɗin da za'a basa yace, "Bakada damuwa na amince zanyi kuma ina tabbatar maka da babu mai ganomu balle a fahimci wani abun". "Hakan nada kyau, kayi komai cikin natsuwa da kuma tsari sannan ka kuma iya takunka, bani account ɗinka zan saka maka kuɗin ka yanzu, abinda nake so dakai kafin gobe ka tabbatar kayi duk abinda ka gani a rubuce cikin wannan takardar". Ya ƙare zancen yana miƙo masa wani envelop yaci gaba da cewa, "ina so naji labarin kukansa gobe". ************ Babban filine na garin nasu matafiya kowanne da jaƙarsa ahannunsa kasancewar tasu batada wani nauyi yasaka ya mutallab daukar daya Afrah ma daya.  kowanne tsaye a layi anfara hawa jirgi afrah sai zare idanuwa takeyi murna ta isheta wai yau itace zataje saudia yaaAllah tafada murmushi na suɓuce mata, ko da suka shiga Egypt airline din first class ne inda suka zauna. " yayana Nagode Afrah yafada tana kara kallonsa." " Karki manta dai kiyi Addu'ar matafiya kinji, "Tohm yayana." ****** Barka da safiya Abba wai kayi baki jidda tafada tana daga tsaye, umma ce tace " To kice masa yashigo mana ba sai katashi ba yi zamanka Abba." Cikin rashin zabi yasamu guri ya kara zama. Sallamar dady ce tasashi dan gyara zama yana shigowa." Afwan Alhaji Saad na katse maka hutawa." "A'a babu komai barka da zuwa da fatan dai lafiya ko?" " Ina lafiya Abokina soyayyar ɗanka na kokarin zarar da diyata." Umma ce tace " Barka dazuwa Alhaji." " Sannu  hajiya barka da gida iyalin lafiya." " Alhamdulillah. " " MashaaAllah nace Nazo kan maganar meenal da Mutallab danAllah abokina kataimaka Nafahimci yaron nan yaron arzukine yaron kirkine wannan shine irin mijin da yakamata diyata tasamu." " Me zakayi da ɗan banzan nan? Yanzu haka na koreshi dashi da kanninsa daga gidana bana iya zama dasu." " Alhaji Asad anya kana cikin hankalinka? Ka koreshi? Yaro kamar mutallab? Sai da karfi yasameka sannan zakace wai ka sallameshi? Haba Alhaji Mutallab hakan inaganin ba daidai baniba, ai idan akwai ɗan da yakamata ace ka koreshi to jamil ne dan shine ɗan dake bukatar hukunci da horo, gaskiya gidanka da gyara kadinga ambaton Allah." Umma ce ta harareshi ta kasan idonta." " mu wuni lafia." Kajimun maganar banza da wofi? Abba wannan ba abokin kirki baniba ka rabu dashi." " Tohm Umma narabu dashi Mutallab kuma baya dawowa gidana wallahi kuma jamil ma zankara masa jari."   **** Yadda take faman kiran wayarsa babu ƙakkautawa amma akashe yasa hankalinta tashi " Meenal are you okay?" " Dady wayar Mutallab bata shiga danAllah ko lafiya tafada kwallah na kokarin bayyana fuskarta." " Shiru yayi shidai dady yacigaba da cin abincinsa saboda yasha alwashin danne ransa akan wannan batun." Kukan meenal da sukaji nr yasasu kara kallonta cikin sanyin murya tace " Yaa Allah kasa yana lafiaya." Innalillahi wa inna ilaihirrajiun mumy kina tunanin wannan abun babu iska?"   " Nima wallahi abun yafara bani tsoro dadyn meenal." " meenal kidaina kuka kinji inshaa Allahu yana lafiya kinji mumy tafaɗa." Mumyna naje nayi sallah nayi masa addu'a?" Hawaye da yafara biyo fuskar dady yasa shi ajiye abincin yatashi yashiga bangarensa ganin haka mumy tabishi tace " Dadyn meenal kuka?" " Nakasa zuciyata takasa zafin da raina kemin ganin diyata tanason abu amma nakasa mallaka mata ada idan akacemin akwai abunda kudi bazai siyaba zan karyatane wallahi, meenal Na kuka kamar yarinya tana kokarin zarewa me zanyi danAllah yanzu? Bakin cikin danake ciki yazanyi yafada kuka na kokarin cin ƙarfinsa." " Addu'a zamucigaba dayi dadyn meenal inshaa Allahu komai zai daidaita kaji kadaina kuka danAllah. #Mutallab Asad #Tagwaye Biyar #Nana Diso #Billy S Fari MUTALLAB ASAD MUTALLAB      (labari mai taɓa zuciya) Na Billy s fari Nana diso      RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.    TAFIYAR BIYU TAFI DAYA   SHAFI NA ARBA'IN DA UKU. Fira suka sha sosai cike da kewar juna dan tunda ta tafi sau ɗaya kacal sukayi waya, tana so tayi bacci amma kasancewar bata son ta ɓata masa rai yawa taci gaba da biye masa suka sha soyayyarsu kafin can baccin yayi gaba da ita, jin alamun sauke lumfashin da takeyi a hankali ya tabbatarwa da Aryan cewa tayi bacci, ɗan haka yai murmushi tare da kai wayar abakinsa  yai kissing ɗin ta yana imagining tamkar a forehead ɗin Afrah ɗinsa yai hakan sannan ya kashe wayar yana sauke wata irin sanyayyar ajiyar zuciya cike da farinciki sannan ya gyara kwanciyarsa. Washe gari. Tsaye Aïcha suke abakin babbar tashar mota jikinta sanye da wata burgujejiyar riga kanta kuma tasaka masa wani mayafi duk da yanayin shigar datayi ba mai ɗaukar hankali bace ko kuma ƙayatarwa hakan bai hana bayyanuwar kyawun da Allah yayi mata ba, mahaifinta ne dake dafe da kafaɗarta hannunsa ɗaya riƙe da sanda yashiga faɗin "Aidez nous s'il vous plaît fisabilillahi (kutaimaka mana fisabilillahi), Aïcha ya naji kinyi shiru da bakinki banji kina barar ba, zan fa yimaki Allah ya isa idan kika ja mana rashin ciniki yau!" Cikin hanzari ta jiyo tana kallon mahaifin nata jin kalmar daya faɗa kamin ta buɗe bakinta kamar zatayi kuka tafara barar kamar yanda ya buƙata, "Ku bamu saboda manzon Allah, sadaka fisabilillahi ƴan uwa musulmi". Murmushin jin daɗi mà père yai jin yanda zazzaƙar Muryar tata ke tashi wajen yin barar kafin suka shiga zagaya motocin dake lodi  suna cigaba da barar tasu, take kuwa cikin ikon Allah sai gashi sun fara samun kuɗi dan kuwa duk inda suka zaga jin yadda Aïcha ke barar tana cewa abasu saboda Annabi Muhammad s.a.w sai ya ɗauki sadakar ya basu. Sai da suka zagaye duka layin dake cikin tashar motar gabaɗaya sannan Aïcha ta samu waje ta tsanya tana kallon mahaifin nata take cewa, "posez-vous s'il vous plaît, j'ai essayé (kazauna nidai nagaji)". Idanuwa mahaifin nata ya shiga jujjuyawa yana miƙa hannu yana don taɓa inda take haɗe da cewa, "Naga ranar da zaki zama jaruma Aïcha wallahi ragwancin nan naki yayi yawa wallahi". Turo bakinta tayi tace, "Tafiyar da mukayi cikin tashar nan da biyan kuɗi akeyi zata kai Naira 150, sannan kaf tashar nan fa mun zagayeta amma kacemin raguwa bayan tun da duku-dukun safiya muka fito yanzu gashi har rana ta tayi". Tsaki yaja yana ajiye sandarsa tare da laluba inda zai zauna ya zauna. Ganin wata haɗaɗɗiyar mota Aïcha tayi na nufowa gurinsu, take ta riga da gudu ko masu kamen barane sukazo, tunowa da mahaifinta yanada ƙarancin gani yasata dawowa tana faɗin, "Mà père sauri ka miƙe ga masu kame nan, gasu nan fa mà père ka tashi mugudu kada su kame mu". Taƙare maganar a tsorace tana rirriƙe mahaifinta ganin motar tariga data ƙaraso wajensu, Allah sarki ɗa da mahaifi yana jin haka ya shiga dukan iska da sandarsa yana riƙeta shima cike da son bata kariya duk da shima jikinsa rawa yakeyi yana ƙoƙarin miƙewa, ganin kyakkyawar motar tayi packing agurin yasata jan mahaifin nata zasu gudu. Daga cikin motar babban mutumin ne ya sauke Glass ɗin gefensu ya leƙo yana cewa, "Ƴar budurwa ina zuwa?". Ganin hankalinta gaba ɗaya baya kansa neman hanyar guduwa takeyi ya sashi fahimtar cewa ta tsorata ne, ɗan haka ya sake duƙo kansa yanda zata gashi daidai yana cewa, "Tsaya mana, nifa ba mai kame bane gurin babanki nazo". Ras Aïcha taji gabanta ya faɗi jin abinda yafaɗa dan tabbas a kallo ɗaya tafahimci irin alhazan nanne da ba'a yau suka saba bibiyarta ba dan su ɓata mata rayuwa, cike da tsana ta dalla masa harara tana cewa, "Dieu te regarde (ALLAH yana kallonka)". Sannan tana hannun mà père sukayi gaba, kashe motar tashi yayi yafito yana mai biyosu da sauri ɗan sun miƙa hanya, gabansu ya sha ya tsaya agabanta, mà père dake faman sauke ajiyar zuciya ya kalla kafin ya maido kallon nasa agareta yana yimata wani shu'umin kallo, gefen mà père ta sake ɓoyewa ganin kallon da yake yimata, lashe ƙasa bakinsa yai kafin yace, "Baba gurinka nazo akan batun yar nan taka ko zaka bani ita saboda na jima ina sonta, duk lokacin dana ganta sai naji naƙara tsunduma soyayyarta". Tsabar kwaɗayi take mà père ya manta da halin da yake ciki na tsoro ya shiga washe baki haɗe da cewa, "Kana da kuɗi yaro? in dai kana dasu zan baka ita". "Mene mà père! Wai kaga wannan mutumen ne? To Wallahilazim babu inda zanje, haba mà père wai me yasa kakeyin haka ne idan sadaka zai bamu yabamu yayi gaba abunsa". Alhaji da yaji abinda mahaifin nata yace sai hakan ya bashi damar riƙo hannunta yana wani shafa mata ta fusge hannunta tana cewa, "Tir dakai! Ƙaton banza ƙaton wofi, da ƴaƴanka kake yiwa ƴar wasu hakan to Allah ya isa, azzalumi ban yafeba". tafaɗa tanayi gefe kaɗan. A ruɗe mà père ya shiga cewa, "Dan Allah dan Allah kayi haƙuri Alhaji kada katafiyarka, kasan yarinya ce sai kayi mata uzuri".Alhajin da idanuwansa suka kaɗa sukayi jajir saboda tsabar jaraba yai murmushi haɗe da cewa, "Bakomai baba, kanada wannan lafiyayyar yarinyar kazauna kana bara? ni ina sonta kuma nayi maka alƙawarin siya muku gida, mota da dukkan abubuwan rayuwa indai zaka mallaka mani ita". "To to ai shikenan ma na baka ita". Mà père ya faɗa fuskarsa cike da fara'a, Kuka Aïcha ta fashe dashi amma duk da hakan bai damu ba, Alhajin kuwa dake ganin ya samu yadda yake so wajen mahaifinta sai cewa kawai yayi "biyoni mota ƴar budurwa ko?". Yadda Aïcha ta sake rirriƙe mafere yasa shi cewa, "Aïcha me isa bakya neman Albarka ta ne? Bazaki bishi kuje ba sai na ɓata miki rai?" "Bazan je ba mà père, wato indai akan kuɗi ne babu abunda bazaka iya ba? Kasan shine? Ko so kakeyi ya gudu dani? To má pére idan ɗan iska ne fa na bishi ya ɓata mani rayuwa?". Sandar hannunsa ya juyo zai buga mata yana cewa, "ke dai kidinga

Chapter 24 of 54