Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
daga tashina kawai kin rufeni da fada." Cikin zafin rai da nuna bacin ranta tace " Kakirani da mara ilimin mana kawai Amma saboda Allah jiya jiyan nan akawoni kana zancen wata akan gadona acikin dakina." " A hakali ya rungumota yanafadin kiyi hakuri kinji bansan Nayi ba." " Amma dai kacemun fa bakwa tare." Rungumeta yayi sosai Ajikinsa yana dan shinshinar gefen wuyanta lumshi idanunsa yayi yana fadin" Inson kamshi Meenal." Bai ankaraba yaji tafashe da kuka tana fadin " Dan kasan nafisonka shine kake wulakantani ko? Har kafara mafarki kana ambatar masoyiyarka." Dan sakinta yayi yana kallon yadda take kuka sosai Riko hannunta yayi yace " soulmate Bantaba ce miki bazan kara aure ba Amma Nayi miki Alkawarin babu saki tsakanin mu da yardar Allah Amma bazan taba yimiki Alkawarin bazanyi aure ba." sautin kukan Nata takara tana kallonsa." yaushe akayi auran mu har kafara bijiromin da zamcen kishiya wallahi bazan iya hadaka da kowacce irin macce ba." Kallonta yayi yana faɗin " Kidaina kukan meenal menene nakuka?". Fuzge hannunta tayi tana faɗin Ni ka cikani, daman ance maza munafukai ne ai tafaɗa tana ficewa daga daƙin." Duk yadda yaso ya danne zuciyar akan yimasa zafi da takeyi Amma yakasa haƙan yabashi damar tashi tsaye yana dan jingina jiƙinsa da garun daƙin haɗe da ɗan ciza labbansa Ya Allah yafaɗa cike da bacin rai kamin kuma yayi yunkurin barin daƙin har yafito yanajin sautin kuƙanta adaya daƙin nata hakan yasa yabar part din nata gaba daya yaNufi part dinsa.    Sosai tashiga raira kuka again nata jin alamun yabar bangaren nata yasata saurin fitowa tana Nufar daƙin nata da yazama kamar bana sabuwar amarya ba Duba da Yadda ya ɓaci Duk da kaya hatta bra ɗinta tana kasan daƙin, jin karar wayarta tana ringing yasata Ta nufi kan mirror ta dauka. Sautin Kukanta shine Abunda yafara duƙan kunnen mumy cike da Tashin Hankali tace " Meenal lafiya innalilahi wainna illahirrajiun. " " Mumy daman haka maza suke? Dazu fa da muka koma bacci da safe yadinga ambatar wata yarinya wai Aicha aciƙin mafarkinsa mumy Har da cewa Zan kasance dake na har Abada Aicha ina tare dake." " Ke danAllah Nutsu mana, lafiyarki kuwa meenal? A bacci fa kike magana?." " Wallahi mumy da gaske nakeyi kuma na tambayeshi wacece ita wai baimun Alkawarin bazai kara aure ba ai mumy when akayi bikina? Kwana daya? Mumy ace har yafara maganar Aure." " Haba meenal kada kishi ya rufemiki idanu mana kina yanke hukunci abunda yake a baɗini, mafarki ai ba gaskiya baniba kuma kikasan me yagani har yake faɗin haka! Banason sha shanci ki goge hawayenki kije kibashi hakuri ki Nuna kamar bakiji, yanzune lokacin da zaki Nuna masa kulawarki." Cikin kuka tace " Mumy?" " Karkice komai kiyi yadda nace miki kinji kina dai ganin cikin suttura da rufin Asirin da kika samu ko? To ki godewa Allah." Cikin shashekar kuka tace " Mumy zan iya mutuwa idan yayimun kishiya wallahi mumy zan mutu ne."  Tafaɗa tana kuka sosai. Kashe wayar mumy kawai tayi dan tasan meenal da kafiya bama akan abunda takeso. Kashe wayar Nata ke da wuya taga kiran wata Numba kamar ta dazu tana kara kira. Karawa tayi tace " Hello." " Diyata lafiya naji muryarki haka? Meke faruwane Allah yasa ba wani illar yayi miki ba?." " Umma Wai kishiya yace zaiyimun." " Kishiyar lafiya daina kuka kinji maza shirya kisa yakawoki sai kice masa zaki zo ki gaida babansa kada kuma kice masa muna waya dan zai iya hanaki Nikuma nayi miki Alkawarin zan baki maganin da babu maccen data isa ta Aure yarona kinji." Murmushin da batayi tsammani ba taji ya subuce mata kamin kuma tace " Da gaske umma?." Tabbas kuwa diyata." To ganinan zuwa tafada tana saurin jan hijjabinta tayi kasa, ko data isa part dinsa yana cikin bedroom dinsa da yagaji da haduwa duba da komai naciki farine. Palour din ta kallah Afrah datagani zaune ta kallah ta nunata tana fadin " Afrah ko?" " Afwan Anty Meenal ina wuni." Cike da dan nuna takama tace " lafiya kuma har cikin palour kike shigowa ina laifin ki tsaya acan kasa set room yazo yasameki." Da mamaki Afrah ta kalleta sai ma tacigaba da danna wayarta bata kulata ba." Mutallab da fitowarsa kenan cikin white shadda yatsaya na binta da kallo yana kokarin daura agogansa yace " Kamar yadda bakida shamaki da bangarena haka afrah ma batadashi dan haka ki iya bakinki banson haka." " Aikuwa tanadashi tunda ai ba matarka bace ba." A dan kausashe yace " Meenal." Sai kuma tayi luff tana faɗin " Sorry." Afrah kuma tayi hanyar fita Alamun kuka yana kokarin cin karfinta.  A Hankali yace " Afrah dawo." Jiyowa tayi fuskarta dauke da hawaye riko hannunta yayi yana goge hawayen meenal dake gefe tana kallonsu tace " Yanzu askim." " Meenal wannan kanwata ce farincikina Bazan lamunci ki wulakan ita ba kamar yadda ita bazan lamunta ta rainaki ba, banason karajin kowanne wulakancin magana akanta ko sauran ahalina." Kallonsa tayi tace " Kayi hakuri." Afrah kuma tace " Babu komai, sai ta danyi murmushi tace " Yaya kayi kyau." Murmushi yayi yace " Allah?" Da dan fara'arta tace ko anty meenal. Itama daga mata kai kawai tayo dan ta lura soyayyar tasu ba yadda take tunani bace ba. Sai da afrah ta fita sannan ya Nufo inda take, jawota yayi yana kallon idanuwanta Da ya haifar mata mutuwar jiki atake, cikin wani calm voice yace " Am Sorry dear." " Okay." Cikin wani salo yashiga matso da baƙinta daf da nashi, a hankali yashiga sumbatar bakinta tsigar jiƙinsa na mimmikewa. Cikin salo Na Nigerian kiss wanda yake cike da rashin gwanancewa meenal ta tsaya kaikam inda Mutallab yashiga jan harshenta yana sarrafasu a hankali a hankali, yadda taja baya yasashi dan binta yana kara rungumota haɗe da sauke mata wasu zafaffan Numfashi." " Ni danAllah kasakeni Gurin Abba nakeso kakaini mu gaisa." Da idanuwa ya bita yana shafa mata wuyanta." " Nifa kana kashemun jiki tafada kamar zatayi kuka." Jin wayarta tafara kara yasata dagawa tana fadin " Mumyna." Ki sakko kasa ga Masu kawomiki gara nan Sun kawo." " Tohm mumy, Askim wai ga masu kawo gara nan sun kawo." Cikin wata kasalalliyar murya yace " Okay yana dan saita ƙanshi yayi hanyar sauka kasa itama tabishi.    Tante ƙinga wulakancin da matar yaya tayimun. " Uhmm Ai ni yadda naji wasu cikin yan uwanta suna mata wata shaida sai jikina ya mutu." " Ai wallahi kama kaina zanyi babu ruwana da'ita harda wai me isa nashigo palour din yaya fa." " Allah dai yabasu zaman lpya mu muna nan mai zai haɗamu da'ita.      Dariyar da Umma taƙeyi a daƙin ne yasaka Asiya shigowa tana faɗin " Umma lafiya? ." " Wallahi kan batun yarinyar nan ne Ashe lamarin nata zaizo mana da sauki." " Me tayi umma?" Kijimun jakar yarinya har ta yarda dani wai zan bata maganin da baza'ayi mata kishiya ba." Dariya Asiya tayi tace " Aikam nima dai nadago aikin nan yayi dan gidan zan koma." " Aiki kuma yanzu zan fara hadomin garwashi yanzun nan. Cikin kankanin lokaci Asiya ta hada ta mikawa Umma. Sai data karba sannan ta bar daƙin zuwa daƙin duhun Nata a hankali ta tsugunna karkashin gadon tajawo kwaryar Tana budewa ta jefa Nama wasu kwari kamar bera suka cinye, wani magani tasaka tashiga ihu tana faɗin " Meenal Meenal Meenal Nasaki kinsaku Na hanaki ƙin hanu, Na mallakeki har Abada Sai Nace Zakiyi Sai Nace zaki Bari Meenal Meenal ta karasa tana mai cillah wani Naman ciki."   *******    qu'est-ce que tu fais aïcha ? (Me kikeyi ne aicha?) A hankali ta dago ƙanta tace " j'ai mal à la tête (ina fama da ciwon kai ne)." Mugun tsaki mama taja tace " aikin ki kenan bakida lafiya kina nufin abincin siyarwar wazai siyar?" Mikewa tayi tace Amma mama a kofar gida zan tsaya ko?" Tundugarar mata da kai tayi tace " Lokacin da kike faman zagaye da uban naki a kofar gida kukeyin bara? Nace kofar gida kukeyi? Naga zaga gari kukeyi. Batare da nacewa mama komai ba Na dauki kular abincin daya na dorata ƙaina daya kuma na riketa Nayi hanyar fita ko dana fito yaran duk sun shirya zasu tafi makaranta, sabon hawaye ne ya wanke mun fuskata, wata kokawar tafi karfinka duk yadda naso nayi ilimi Amma hakan ya gagara ina kallon wasu daga cikin yaran kawu suka sakamin dariya suka fita. Wannan shine karo na farko danaji wani abu ya tsaya min araina ina kallonsu duk sukayi makarantar gomnati nikuma nasamu gefen wata bishiya na zauna, jin Ana kiran sunana yasanya na juya ina fadin " Nice kawu." " Aicha, tu as un petit ami ? (Aicha kinada saurayi)?. Daga kai na nayi nace " je n'ai pas d'oncle (banidashi kawu). " To ni gaskiya narasa yadda zanyi dama ace kinada wani saurayin ne sai kice masa yafito kawai nayi miki aure idan bahaka ba hassan sai tata azabtar dake wallahi ki duba kiga tallah ta aikoki." " Kawu kada kadamu zanyi inshaa Allahu bazakaji Matsala daga gurina ba." " To Allah yataimaka yayi gaba." Nikuma nan nashiga zabga gyangyadina bayan nadanyi baccin ne Na dauki kular nashiga kasuwa cikin hukuncin Allah tas akasiye haƙan yabani damar daukar Naira dari biyu nasiya pant duk da nasan mama zata iya zaneni akan hakan Amma kuma banajin zan iya zama da wando guda daya, Allah ya jikan mahaifita duk matsi da talaucin da muke ciki bata was gurin ganin mun rasa wandon sakawa kokuma takalmi dan tana yawan faɗar gaban macce yana lallace idan tana amfani da rubabban wando, tafiyace Nayita sosai kamin Na isa zuwa Gidan ko dana isa Na tarar da wani yayana wato dan mama dayake soja ne yadawo kowanne ciƙin yan uwan yana kusa dashi tunda nashigo ya zuba min idanu, gaisheshi nayi nakarasa kusa da mama nace " Sannu da gida mama gashi. Karba tayi batare da ta irgaba ta zura acikin jakarta, sai kitashi malama kibar nan ko kinzo kinsakamu gaba. Cikin wata katuwar murya Naji ance " Mama inason yarinyar nan a auramin ita gaskiya." Da mamaki najiyo ina kallonsa... SHAFI NA SABA'IN. *MUTALLAB ASAD*      Arewabook:- billysfari       Paid book ne, N500 via ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A, Gt bank, sai shaidar biya ta +234 704 040 2435 ko +234 809 845 6130 Ga masu son vip post 1k ne.    Daga mata gira daya yace " Ai mama bansan munada kyakyawa haka acikin dangina ba." Tsaki mama taja tace " haba mukhtar me zakayi da wannan yarinyar ai gwara mairamunka." " Saboda me mama." " Kai baka gani gata matsiyaciya ga jahilci ga tallah ga bara ai sai kajawowa yaranka wata masifar kama bar batunta." " A hakan nakesonta Mama Kuma ita mairamu zan aureta ai." Nidai ban amince ba wallahi tafada tana mikewa ta bar gurin. Ni kuma gabana ne yashiga waduwa dan harga Allah bana kaunar Mukhtar irin mazan nan ne da basa boye kwadayinsu ga mata, hawaye ne naji yazubomin mutuwar iyayena sai ta tsayamin Arai yauma ga yar'uwata bata raye. " Keje ki azan wuta ki wanke kwanukana ga kayan Mukhtar can suma ki wankesu." " To mama." Har kusan karfe 11 ina wankewa na gyara gurin nayi kokarin yin sallar isha'i daga nan kuma Na bingere da bacci, cikin dare kawai sai naji ana shafani hakan bakaramin dagamun hanjaki yayi ba nayi saurin mikewa Nan naga yaya mukhtar a kusa dani yana washe mun baki, jikina har rawa yakeyi nace masa " Me kakeyi Anan? DanAllah karka cutamin." Wani shu'umin kallo yayi mata sannan yariko hannunta, " Nakasa bacci Aicha Ko rufe idanuwana nayi ke nake gani, surarki tahana jikina da gangar jikina samun salami danAllah ki amince da Soyayyata ni ba cuta miki zanyi ba." Ɓacin rai ne ya tasomin sai kuma natuna duk abunda zanyi nice zan kwana aciki dab kuwa nasan muguntarsa zai iya zaneni sai nace masa "zaka iya aurar ƴar tallah?." Kallonta yayi yace " me zai hana na'iya auranki? Kada fa ki manta kanwata kike sannan inaso in fiddake daga wannan ƙangin da kike ciki na mahaifiyata." Duk da jiƙinta bai bata gaskiya yake gayamata ba sai ta daga ƙanta sama alamun ta amince. " indai har da gaske kakeyi ba yaudarata zakayi ba to Nikuma Na amince." Wani fitinannen kallo ya aika mata sannan yace " Kwanta kiyi baccinki Allah ya kula dake." Murmushi tayi haɗe da fadin nagode sosai sannan ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya cike da maraici Na iyayenta." Mukhtar na fitowa kuma yasaka dariya yana fadin" Yarinya kenan bakisan wuta ba sai ƙin taƙa me zanyi da matsiyaciya irinki? Ai lallabaki zanyi in samu abunda nakeso nakara gaba." Da Asuba tana tashi tashiga gyara gurin sannan ta surfa waken ta dora musu dumamen kafin nan ta Nufi inda mama take dan karbar kudin markaɗe, kamin takarasa ne taji muryar Mukhtar yana faɗin" Ai abokina ina gayamaka nayi babban kamu agida wannan karan har na yaudareta ma yau da daddare zai afka mata insamu biyan bukatata, bakaga yadda nake sha'awarta ba. Wani mugun ajiyar zuciya Aicha taja tana komawa da baya saurin shigewa bandaki tayi tana sakin wani zazzafan kuka da sai da yasa hawaye masu zafi suka shiga zubo mata, Yaa Allah shine Abunda ta fada acikin ranta wannan wacce kalar masifa ce. Sosai ta dauki lokaci tana kuka sai dataji mama tafara kiranta ta wanke fuskarta da ruwan butar tafito. " gidan uban wa kika tsaya sai rana tayi ƙinsamu munyi kwantai?" Cillomata Naira dari tayi tace " Gashinan sai ki hanzarta gurin abunda nasakaki." Mukhtar dake fitowa daga ciƙin dakin yace " Ƙanwata ko nazo natayaki." Cike da takaicinsa da haushinsa tace " bana bukata." Katayata uban me? Sukaji muryar Mama tana faɗi dallah shige kabani guri." Sosa kansa yayi ya koma ciƙin daƙin. Aicha kuma tashiga fito da komai da zatayi soya sai da ta aza wuta sannan taji sallama agefenta amsawa tayi tana faɗin " yaya isa kaine?" " Nine Aicha tun jiya nake faɗin zanzo zanzo Amma Allah bai bani iko ba yanaganki gaban kasko gashi lokacin makaranta yayi." Hawayen fuskarta ta goge tace " Ai kosai nake siyarwa da mama da safe da yamma kuma nake mata Tallan abinci." Sunkuyar da ƙansa yayi yace " ƙai innalilahi wainna illahirrajiun wannan rayuwa da abun tsoro take wato duk sun ƙada yara su suntafi makaranta ke kuma ga wahalar da ake sakaki." " To yaya zanyi yaya isah da ta koreni ai gwara nayi mata hakan." " Allah yabaki miji nagari kiyi aurenki yanzu dai ga wannan dubu dari da hamsin ne kudin siyayyar da marigayiya tayi ne daman nakwashe na siyar gasu nan na haɗamiki su kirike a hannunki ko?." Kallonsa tayi cike da girmamawa tace " yaya isa ayi sadakarsu kawai." " saboda me bayan ƙinfi kowa bukatarsu?." " Share hawayenta tayi tace " tsoro nakeyi inda zan ajiyesu." " Yanzu duk ba wannan ba kaya yakamata adinka miki da abubuwan yammata in yaso canjin ki ajiye agurinki zan cire dubu hamsin in yi miki siyayya sai nakawo sai kice musu kanwar mahaifiyarki ta aiko miki dashi ko?." Ayi haka yaya isa?" " Dole ayi haka Aicha kiduba ki fa MashaaAllah amma shigarki kwatakwata batada ma'ana babu suturar arzuki gwara adan tsinto miki akwai balki dinnan ta gidan hayar nan naga tsayinku daya har jikinma zansiyo kayan sai ta dinka miki kala goma ai sun isa ko?" Murmushi tayi tace " Yaya isa Allah yayi maka sakayya nagode." " Babu godiya Aicha ƙarbi wannan ki zauna kici kamin kifara tuyar ko? Kwai ne da shayi da burodi inshaa Allahu tunda naga inda kike har da dare zanna aiko miki dashi Allah ya jikan iyaye." " Ameen yaya isa Nagode ta faɗa tana karba hadi da fara shan shayin, tausayi tabashi ganin yadda jiƙinta yake rawa ko ba'a sanar masa ba yasan tana cikin azabtuwa da yunwa." Nikam ince Amini tazo kuwa?" Sai datagama shan shayin sannan tace " Baitazo ba kasanfa mahaifinta bayasan alaqarmu da juna." " To Allah yasawaka bari naje ni sai nadawo." " Allah yakiyaye Hanya Nagode." Tana cikin shan shayin kawu yazo sai data gaidashi sannan yasamu guri yazauna." Aicha ina kika samu wannan babban burodin?" Batare data fara bashi amsa ba ta raba building ta mika masa sannan yace " isa ne yakawomin kawu." Sai da yakarba yafaraci sannan yace " Kai Amma Mungode sosai, daman maganar mukhtar ce yanzu danadawo gida yake sanarmin wai kun daidaita yanasonki." Zubawa kawu ido tayi sannan tace " kawu dangirman Allah kada ka amince Ni wallahi banasonsa." " To daman Aicha ko kinasonsa dan kingansa kamar ke akyau zan hanaki gwara Allah yakawo miki wani ko isa dinnr ma yasamu ya aureki." Murmushi tayi tace " Nagode kawu." Sannan tashiga soya kosan." *********** A'a maraba Diyar tawa ce tafe haka? Umma tafaɗa tana washe baki haɗe da jawo hannun meenal tazauna kusa da'ita. " Barka da asuba Abba." A dan zabure ya ƙalle Mutallab yace " Barƙanmu." Itama meenal tagaishe sa ya amsa sannan ta gaida umma. " To tashi muje ciki ko mafi gaisawa, Abbansu bari mushiga ciki gasu Asiya can jidda ma dayake nan ta kwana. Da mamaki mutallab yabisu Amma haka kawai yaji tsigar jiƙinsa ta Mike alamun akwai lauje cikin naɗi kenan. Sai da Abba ya waiwaya baya sannan yace " Ya kasuwar ya kokari? Kasha hidima Allah kaima yafiddakai kunyar lahira." " Ameen Abba Akwai abunda kuke buƙatane?" Shiru yadanyi kamin yace " Kudin hannuna ne dai bashida yawa." Murmushi mutallab yayi ya zura hannunsa aciƙin aljihunsa yaciro bandir din ƴan dubu daya ya mika masa. " Dauka yayi yace " Allah yasaka da Alkhairi. Zaka barta Anan ne kokuma tare zaku tafi." Zan shiga kasuwa ne Abba idan nadawo na dauketa." " Nidai kamar nace katafi da'ita mutallab." " Abba idan akayi haka ai sai umma taga ko dan ba'ita ta haifeni ba ko?" " Eh toh gaskiya hakane. Asiya ƙinzuba kuwa Umma tafaɗa da ƙarfi yayin da suke shiga bangarenta. Asiya dake zaune tayi saurin barbada maganin kan kujerar sannan ta koma ta zauna. Jidda dake gefe guda taci kukanta tagaji ta kallesu taja tsaki saboda takaicinsu takeji umma takasa magance mata matsalar mijinta tunda sukayi auren ko zuwa gidan baiyiba, shiyasa itama tayi tawowarta jiya da daddare. Antynmu ce sannu da zuwa Asiya tafada meenal ce ta washe baki dan ita gaba daya ma sai taji wannan matar tafi mumy sonta yadda take riritata, ko dazu data gaisa da tante batayi mata wannan girmamawar ba." Nagode meenal tafada." Tana zama ƙan kujerar batare da bismillah ba, ko data zauna din sai data riƙe ƙanta nawasu mintuna kamin kuma taji ya saki. Umma kuma tasaka murmushi tace " Lafiya dai ko diyata?" "Umma lafiya." " Ke asiya Mike maza kike ki zubo mata abinci mana." " Yanzu kinajina?" Daga mata kai tayi tace " Eh umma" Kinga mutallab dinnan idan kika biye tatashi zaluntarki zaiyi tun yanzu yafara maganar aure ina ga gaba? Tun yanzu zaki tashi tsaye kishiga yaƙi agidanki, daga yan uwansa har wannan matar kada ki raga musu, harshi mutallab din." " To umma daman ai ban ragawa Afrah ba yau da safe." " Shima idan takama kiyi masa rashin mutunci shine zaku zauna daidai, jiya ya kusanceki kuwa?" Murmushi tayi tana dan sinna kai tace " Eh umma." To inaso kiyimun wani aiki dashi zamuyi amfani ahanashi yimiki kishiya." " Umma komenene zanyi wallahi." " Maniyyinsa nakeso ki kwasomin ki kawomin." Ciki da rashin tsoro ko mamaki tace " sperms?" Daga kanta tayi tace " Eh shi." " To tayaya zan iya kwasowq?" Miko mata wani jan yanki tayi tace " Gashinan zaki shafa ajikinsa kawai sai ki ajiye a kawomin zanyi miki aikin da macce ma idan tagansa tsoronsa zataji." Murna sosai meenal tayi. Ko da ya isa kasuwar sai da yazagaya duk wasu branch dinsa ya tabbatar lafiya sannan ya danyo musu siyayya yadawo gidan san da yashiga yabawa Abba gasassun kajin kamin yace meenal din taxo. Har waje umma tarakata kamin kumatace " Allah yakiyaye sai najiki." " Tohm umma nagode sosai. Sai data shiga motar sannan ya ƙalleta yana ɗanyi mata murmushi " Har yanzu fushin Ake dani?" Murmushi tayi tace " A'a babu fushin danakeyi kawai dai ina mamakin cin Amana irin na maza." Baice mata koami ba har suka karasa cikin gidan yadda tabar kayanta haka tatarar dasu dab babu wanda ta sanar ankawo kayan gara nan ta dauki wayarta takira Umma " Umma ga kayan gara ankawo ko zakizo kigani." Murmushi umma tayi harda shewa sannan tace " Ganinan zuwa tafe." Mutallab dake tsaye yanajin ikon Allah yace " Umma naji ƙinkira meenal." " To wa kakeson in ƙira sama da'ita?." Bakiga tante agidan ba?" Karamin tsaki taja tace " Tunda dai na gidan ubanane ai banga dalilin kiranta ba umma naga damar kira kuma nakirata." Baice komai ba yashige part dinsa itama tayi shigewa bangarenta miyar da mumy ta aiko mata takallah tana faɗin wata miya babu abinci saboda ba diyarta bace ba, Nan takara kiran Umma akan akawomata abinci tace zata tawo mata dashi, ko datashiga daƙinta gaba daya bedsheet dinta da kayanta ga bra ga pant duk akasa ga takalma data watso tsaki taja tayi shigewarta wani bedroom din ta kwanta tashiga chatting. Yadda ƙansa yayi masa nauyi sai yaji inama ba meenal ce tafaɗi maganar nan ba, dazu tagayawa afrah magana yanzu kuma tante? Sai yatuna maganar idress na faɗin " wannan yarinyar banso kasameta ba Mutallab wallahi ba tsararka bace ba kwatakwata ba nasanta daɗewa duk wani abu da zatadaina gaba zata iya cigaba Amma dai ina maka fatan Alkhairi. Wayarsa ya dauka yakira numbarta daga wa tayi tace " yaya akayi ne?" Cikin sanyin murya yace " yunwa nakeji." "To menene zanmaka banda abinci naga ga babarka can kakirata takawo maka mana." " Meenal meenal menene haka?" " Tsaki taja sannan tace " Babu abinci." Takashe wayar tana faɗin " Ai wallahi da wuta wuta zanbika bawai kaga ina sonka ba bazan dauki mulkarwa ba. Numbar afrah yakirawo yace " Afrah zansamu abinci?" " Eh yaya bari har shayi sai nadafa maka." " Tohm Nagode yafada yana kashe wayar haɗe da dafe ƙansa da yashiga Sara masa, cikin mintuna da bazasu gaza 5 ba sai ga afrah ta kawo masa palonsa sai data zuba masa sannan ta koma, sosai yaci shinkafa da miyar kamin kuma ya miƙe yaNufi masallaci, a filin gidan yaga Umma tanata kason Kayan garar baice komai ba yafita dan yasaka Aransa guda daya bazaiyi amfani dashi agidansa ba haka su tante. Jalil ne yashigo gidan mamaki ne yakusa kashe shi saboda yadda yaga Umma na kaso." A hankali ya juya kawai yafita dan inhar yashigo zasu iya samun matsala dashi. MUTALLAB ASAD   (labari mai taɓa zuciya) Na Billy s fari Nana diso      RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.    TAFIYAR BIYU TAFI DAYA   SHAFI NA SABA'IN DA ƊAYA. Rabo irin na galari Umma ta yiwa kayan garar ta kwashe kaso ɗaya bisa uku tace akai can gidansu, kashi ɗaya kuma ta kwashe tace akaiwa Jamil, shi kuma kashi ɗaya tace a kwashe a shiga ciki dashi shine kason Mutallab, daga Afrah har tánte Sajida babu wanda yabi takan abinda Umma keyi har ta gama, don tunda tánte Sajida tafito taga yadda Umma ta baje tana kasafin kayan bata sake fitowa ba balle ma tasan irin wainar data toya, tare da Mutallab Jalil suka shigo gidan bayan dawowarsa daga masallaci daya same shi anan waje wurin masu gadi suna fira, suna shiga masu aikace-aikace a gidan Mutallab ɗin na shiga da kason shi da Umma tasa su kwashe su shiga dasu ciki, "kai Bala ku dakata." Mutallab ya faɗa tare da ƙarasawa wajen yana kallon Umma, yace "Amm Umma ina ga kawai ki wuce da sauran kayan ba buƙatar su anan tunda akwaisu enough a store." "Ayi haka Mutallab, ai

Chapter 40 of 54