Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
wasa nakeyi maki". Tare da samun ɗaya daga cikin kujerun dake a gefensa ya zauna dan yau ba kowa a palourn, littafin hannunta ya karɓa dan yasan bazai rasa Assignment ne zata kai masa ya nuna mata ba, calculation ne field ɗin daya fi gwanewa don haka yana dubawa yayi mata alama data zo ta zauna a hannun kujerar da yake akai, bai yimata Assignment ɗin ba sai dai ya shiga nunnuna mata yanda zatayi haɗe da yimata bayani, bayan ya tabbatar ta gane sosai yasa taciro paper tafarayi agefe ya gani, Sosai yaji daɗin yanda tayi shi daidai ƙwaya ɗaya kaɗai tayi kuskure, nan ma bayani ya sake yimata sannan ta sake gyara wanda tayi kuskuren ta nuna masa, "Excellent Auta ki ƙara ƙoƙari, math da kike gani yafi komai sauƙi kawai tsoronsa da student ke sakawa zuciyarsu yasa suke ganin yafi kowane subjects wahala, ina Jiddah take ne?". "Tana ɗakin Umma". "Ok tashi kije idan kin gama sai ki kwanta saboda kisamu ki tashi dawuri gobe, ungo wannan kije kici". Ya miƙa mata ledar ƙwan dake hannunsa tare da miƙewa, tasa hannu biyu ta karɓa tana cewa, "Nagode Ya Mutallab Allah ya saka da alkhairi yasa kasamu babban aiki". Yayi murmushi haɗe da shafa kanta sannan yace, "Amin Afrah sai da safe ko? Kitabbatar kinyi addu'a kuma kin kwanta da arwala". "In Sha Allah Yaya sai da safe". Tafaɗa itama tare da juyawa ta nufi ɗakinta shi kuma ya fice daga palourn, dai-dai zata haura kan benen sai ga Jiddah tafito tare da Ummanta suna dariya, suna ganin Afrah annurin dake kan fuskokinsu ya ɗauke, Ummah tace, "Yawwa Jidda kitafi ki kwanta dare yayi yanzu, gobe kya ida bani labarin samarin naki, ai bansan haka kike da farin jini ba sai yau da kika faɗa mani zancen yaron nan ɗan gidan commissioner, dole na sake sa a rubuto maki suratul Yusufa saboda kisamu mijin kece reni da shiga rana, tun yanzu fa kenan shekara sha bakwai ina da kin zama cikakkiyar budurwa? Ai nasan sai ƴaƴan Senate da gwamnoni ko Jiddah na?". Dariya Jiddah ta ƙyalƙyale da ita tana cewa, "Allah Ummata". "Ah to ke bakiga alama ba tun yanzu har kin fara samun masoya? Ai kyakkyawar juma'a tun daga larabarta ake ganewa, su o'o da ba farin jini bakiga har yau ba mashinshini duk da shegen kyannan nata ba?". Kallon Afrah dake saurarensu tayi kamar bata ji ba dan har takusa hayewa abunta Jiddah tayi haɗe da cewa, "Ai wallahi Umma na tsani kyawon yarinyar can, haka fa ko a school lokacin ayita cewa wai tafini kyau". "Ƙyalesu meye amfanin kyau ba farin jini?" Sukasa dariya tare kafin Umma ta rakata har ɗakinta da ba addu'a ba kakkaɓe gadon kawai ta haye Umma ta kashe mata wutar ɗakin tana faɗin, "Good night my dota". Ta amsa mata da "Good night Mom". Tana sake shigewa cikin lafiyayyar katifar dake kan gadon tare da jan duvet ta lulluɓe tana rafka wata uwar hamma kafin bacci ya ɗauketa yayi awon gaba da ita. *********** Mahma mahaifiyar Meenal kuwa kasa bacci tayi daren da suka dawo birthdayparty ɗin Meenal, data rufe idanuwa babu abinda take hangowa sai lokacin da Dady ke sakawa Mommy cake a baki da irin tsadaddar suturar dake jikinta, kai da kawo ta dingayi tsakar ɗakin nata wani irin baƙin ciki na taso mata a wuya don gaba ɗaya banda gaisawar da sukayi da Dady yi yayi tamkar bai sanda ita a wajen ba, a tsammaninta tunda su suka haifi ƴarsu ita dashi to su zasuyi ruwa da tsaki a wajen, amma sai yaga ya dauki matarsa ya sanya a gurbin da itace ya kamata ya saka, abun takaicin ma ko ɗan cake ɗin ita bata samu ƴar tata ta saka mata abaki ba, kenan hakan nanufin ba tada wani muhimmanci acikin rayuwarsa da duk wani abu daya shafesa in ba ƴaƴanta ba? Tamkar wata taɓaɓɓiya tace, "Ina! Wallahi hakan baza ta saɓu ba, tare muka sha wahalar rayuwa dashi, sai yanzu ace wata tazo tafini moriyar arziƙinsa? To wallahi bazai yihu ba dole cikin biyu ayi guda". Yanda take surutun tamkar maiyi da wani yasa grandama ta jiyota daga ɗakinta tafito ta sameta a tsaye sai Safa da marwa takeyi, kallon-kallo suka yiwa juna Mahma ta ɗauke ki tana cewa, "Bazan bar Abban su Meenal da waccan matar ba Hajiya, na tsaneta gabaɗaya wallahi". "Dama waya faɗa maki barno gabas take, lokacin da ana nuna maki annabi ba rufe idanuwa kikeyi ba kina ɗaukar komai wasa, ai yau kinga ya nuna maki matsayin da matarsa take dashi agunsa, da tuni kin ɗauki mataki da duk hakan bata faru ba, ita kuma wannan sakaryar narasa meke damunta da har yau takasa ƙulla makircin da zaisa tafita tabar gidan ke kuma ya maidake ɗakinki ki zauna da ƴaƴanki, kallo ɗaya zakiyi masa ki fahimci matarnan tariga data gama dashi.." haka grandama ta zauna tayita mata fanfo tare da shirya mata abubuwan daya kamata suyi nan gaba tare da taimakon Meenal. Sanin da Mahma tayi akwai gajiya tare da ƴar tata ta hidimar Birthday ɗin nata yasa washe gari bata nemeta ba sai da daddare tayita kiran wayarta lokacin tana tare da AAB amma da yake silent take bata ji ba har sai data iso gida, lokacin Mommy na palourn tana kai da kawo ta kasa kwantawa ganin Meenal ɗin bata gida don koda ta duba ɗakinta ɗazu ta samu batananhar tafita, tayita kiran lambarta itama da taga har ƙarfe 12 tayi bata dawo ba itama bata ɗaga ba, wata irin ajiyar zuciya ta sauke lokacin da Meenal ta shigo palourn tana waya da mahaifiyarta da taga kiranta lokacin data iso gida shine takira tana cemata tabari zata kirata anjima tare da ƙoƙarin raɓawa ta gefen Mommy zata wuce. "Meenal daga ina kike adaidai wannan lokaci? kinsan ƙarfe nawa kuwa? Ɗaya saura minti biyu ace kina ƴa mace bakya cikin gidanku wannan wace irin rayuwace kike son ɗaukarwa kanki da bazata ɓulle maki ba?" Mahma dake kan layi tana jin abinda Mommy ke faɗa sai tafasa tsinke kiran tana saurarensu kawai, Meenal kuwa jefa wayar tayi acikin handbag ɗinta sannan ta tako zuwa gaban Mommy da ranta ke aɓace dan har ga Allah taji matuƙar tashin hankali ganin lokacin da Meenal ɗin takai bata dawo gida ba, duk da dai dama takan kai tara goma bata gida wasu lokutan amma bata taɓa kaiwa irin wannan lokacin ba da ƙarfe ɗaya na dare ke neman rufewa, cike da fitsara Meenal ta kalli Mommy tace, "Rayuwarki ko tawa? Banyi niyar dawowa gidan bane sai yanzu ko akwai wanda ya isa ya hanani da zakizo gabana kina yimun ihu bayan ke ba kowa bace face ɗiyar talakawa da ubana ya taimaka mata kuke ci ƙarƙashin sa keda iyayenki, to idan tunaninki kikirani karuwa karki fara domin ke fini kama da karuwan!" Runtse idanuwa Mommy keyi kalmar na dakar mata zuciya a zafafe ta e "What? Meenal..". Bata ƙarasa ba Meenal tayi saurin dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu tana cewa, "wait! You heard me well, kuma bari nafara baki amsarki tambayrki tafarko da kika ce daga ina nike, to ina hotel tare da Bestie na, ko kina da matsala ne idan ma acan na kwana? Ina dai rayuwata kike magana akai ko? To idan an lalata taki rayuwar ce aka lalata? ko da yake ku ƴaƴan talakawa akan kuɗi babu abunda bazaku iyayi ba shiyasa kike tunanin zanje inyi irin rayuwar da kikayi...." kafin taƙarasa rufe baki Mommy ta ɗauketa da mari haɗe da cewa" ke awa zaki jefeni da kalmar karuwa?" Cikin rashin kunya kamin tarufe baki meenal tayo kanta tana ƙoƙarin marinta itama, cikin zafin nama tariƙe mata hannunta tana ƙara sauke mata wani lafiyayyen marin da sai da yakaita ƙasa tare da cewa, "Ƙaryarki Meenal ki tsaya dai-dai matsayinki kada kice zaki shiga nawa, I am not your mate you most respect me in this house baki isa kice zaki mareni ba! Rayuwa kuma duk da takice amma dole kiyi yanda Yakamata acikin gidan nan don bazan zuba maki idanuwa ba tunda haihuwar ki akayi bake kika haifemu ba". *LAST FREE PAGES* *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 #Mutallab Asad #Ƴan Tagwaye #Billy S Fari #Nana Diso. *MUTALLAB ASAD* *PAID BOOK #500* *TAGWAYE BIYAR.* NA *BILLY S FARI* & *NANA DISO* 16. Daidai lokacin Dady yafito daga ɗakinsa jin wani irin ihu da Meenal ta daka tare da jifa da handbag ɗinta agefe ta cire siririn mayafinta data aza kanta ta sakeyi kan Mommy, da sauri kafin taƙarasa ya riƙota ta shiga fizge-fizge tana faɗin, "Wallahi Dady bazan yarda ba saina rama maren data yimani tunda ba ita tahaifeni ba kuma ita ba uwata bace". Akiɗime Dady yace, "What! Tamareki  da tayi maki me Mansura?" Yayi maganar cikin ɓacin rai yana kallon Mommy da ranta itama yakai ƙololuwar ɓaci don yau ashirye take dako me Dadyn yazo, sakin Meenal yayi yayo kanta yana nunata da hannu jikinsa har na wani irin ɓari haɗe da ciccira yace "Ashe bance kifita rayuwar ƴata ba? Akan me zaki mareta ina ruwanki da inda taje ko ita ɗin ƙaramar yarinya ce da zaki takurata aduk lokacin fita da kuma dawowarta?" Mommy ce tayi masa wani kallo mai cike da takaici da baƙin ciki tace" wannan ce yarinya? Wannan ce yarinya? Kai a atunaninka wannan sangartawar da kake yimata ta itace tarbiya? To ka faɗamun menene amfani na a gidan nan idan Meenal baza taji maganata ba ko ɗorasu akan hanya madaidaiciya ba? kenan duk ƙoƙarin da nakeyi akansu kai bazaka dena kallonsa a matsayin takura ba?ace yarinya balagaggiya kamar meenal kana barinta tanayin abunda taga dama mai kyau ko mara kyau kuma kace yarinya ce, a haka har ta kalleni tacemin karuwa tana ƙoƙarin ɗaukar hannu tace zata mareni shima yarinta ce? To bari kaji na rantse bazan ƙara ɗauka ba nagaji wallahi, Nagaji da wannan wulaƙancin yayi yawa". Ta ƙare zancen cike da takaici tanaa kallon yanda Meenal tafaɗi ƙasa tana rusar kuka tamkar wacce aka cirewa rai, kukan nata ya sake birkita Dady gabaɗaya ya ruɗe hankalinsa ya tashi ba tare da wani dogon tunani ba yacewa Mommy, "Koma meye naji amma na baki mintuna goma kifice mani daga gida banson in sake ganinki, mintuna goma nace kin ji na faɗa maki ko?". Ya faɗa a tsawace ganin har lokacin Mommy bata motsa daga inda take tsaye ba dan tsoron Allah ya gama kasheta gaɓar ɗaya, ganin kuka na shirin ɓalle mata yasa tayi saurin barin wajen da gudu hawaye na zubo mata yayinda shi kuma Dady ya shiga lallashin Meenal dake kuka tana cewa sai ta rama marin da Mommy tayi mata. Cikin rikicewa da ƙidemewa yashiga bata haƙuri yana cewa, "Sorry Meenal bakiga nace ta tafi ba? Ko so kikeyi kitayar mani da hankali". Mommy kuwa tana shiga ɗakinta ta fashe da kuka kamar kamar ranta zai fita, aranta cewa takeyi yau ko gidannan ne yarage mata a duniya sai tabar shi cikin daren nan. Jakarta kawai ta ɗauka haɗe da hijjabinta tafito, Dady dake tsaye tamkar an dasa shi lokacin da tafito daga cikin ɗakin yana kallonta sai yaji gabaɗaya zuciyarsa ta gama karaya tana wani bugawa da sauri da sauri, dan tunda yake da Mommy yasha faɗa mata hakan amma bata taɓa gwada tafiya ba sai yau, zuba mata ido yayi yaga shin da gaske takeyi tafiya zatayi ko kuwa da wasa take? Amma kafin yafito duniyar tunanin da yakeyi sa ganin yayi ta buɗe kofar palourn tafita. Meenal na ganin haka ta saki wani murmushi haɗe da faɗin, "Dadyna ka ƙyaleta daman ta'ishemu, wannan hukuncin naka shine dai-dai ita" Kallonta yayi da idonsa da suka sauya launi kafin ya ɗaga ƙafafuwan sa daƙyar yayi hanyar waje da sauri, ganin ta kusa kaiwa ƙarshen gate ya sashi saurin ɗaga ƙafafuwansa, cikin taƙar da bata wuce biyar ba ya isa wajenta tare da riƙo hannunta yana sauke ajiyar zuciya tare da girgiza mata kai, "Haba Mansura yanzu tafiya zakiyi kibarni akan ɗan wannan abun? Bakya ganin Meenal yarinya ce har yanzu tana buƙatar a lallaɓata? Haba Mansurah don Allah kada kitafi kibarni". yafaɗa cikin musayar tausayi har launin idanuwansa na canzawa. Fizge hannunta tayi tace "Kayiwa kanka adalci Dady ta ina Meenal take yarinya? Ta ina tazama yarinyar da har yanzu za'a ci gaba da lallaɓawa tana abubuwan daba dai-dai? To Ni bazan iya ba zantafi nabarka da ɗiyarka kamar yanda ka buƙata sai ta zauna gidan mahaifinta cikin kwanciyar hankali, amma  bazai yihu su hanani kwanciyar hankali ba acikin gidannan dan ina son kyautatawarsu? Nice duk lokacin da nace ta gyara shikenan sai abu yazama issue kullum cikin wulakantanci saboda yaranka?, wallahi nagaji bazan iya a kawai kazauna da abunka", Ta sake yi gaba abunta tana share ƙwalla, sai daya sauke ajiyar zuciya sannan yace, "Listen mansurah! Meenal itace kaɗai 'yata macce kuma ina tsananin sonta sosai amma duk ƙaunar da nake mata bazan iya auranta ba, matsayinki daban nata daban saboda haka kidena tunanin zata iya maye mani gurbinki acikin gidan nan?". "Da alama ita hakan take tunani tunda ka bata dama shiyasa take tunanin na aureka saboda kuɗinka sannan ina zaune anan dan na wulaƙantasu don haka ƙara natafi nabar masu gidansu." Sake marairaicewa Dady daya rasa yanda zaiyi da Mommy data birkice masa yau yayi haɗe da cewa "Haba darling please kiyi hakuri i will handle this bazata ƙara kaiwa dare ba zan yimata magana kin ji" Yafaɗa yana jawo hannunta, ganin ya kasa fahimtar duka ƙorafukkan data jero masa gashi sai magiya yakeyi yana bata haƙuri yasa kawai ta haƙura ɗin ya janyota a jikinsa suka shige ciki, bai tsaya ko'ina da ita ba sai ɗakinsa yayi mata masauki abakin gado yana cewa, "Don Allah Mansura kiyi haƙuri kinsan ina sonki". Yafaɗa yana zama akusa da ita tare da cire mata hijjabinta. Ƙasa tayi dakai tana sauke ajiyar zuciya ya riƙo hannunta yana ɗan murzawa a hankali alamun lallashi sannan yaci gaba da cewa, "Waye zai yarda ya rasa mata kamarki Mansura duba da yadda kike tsaftacemin daƙina, yadda kika gyaramin gadona ga iya sarrafa ƙamshin ta ɗaki, banɗaki, kayanmu da jikinmu duka kin tanadar masu ƙamshi na musamman da ako yaushe bama rabuwa dashi, haba gimbiya wane ni idan babu ke mansurah?". Ɗagowa tayi tana zuba masa narkakkun idanuwanta data sha kuka, cikin wani salo irin na soyayya da kuma shauƙi abunka da mata da miji sai Allah tace, "Ba wani Dadyn Meenal kawai daɗin baki ne zaka yimani". Murmushi ya saki tare da rumƙe hannunta sannan yace, "Wallahi Mansura Tsaftarki kaɗai bazata bari in iya rabuwa dake ba domin tana sakamin nutsuwa, fisabilillahi dubi fa yadda kika luluye bedsheet ɗin nan akan gadon nan sai kace tare aka haliccesa da katifar? Dubi yanayin jikinki da tashin ƙamshin dake fita aciki, hakan kaɗai na sakamin shauƙi akanki da kuma begenki". Ba shiri Mommy ta saki murmushi tana jin wani farinciki na shigarta, wannan shi ake cewa zuma da maɗaci, lokaci ɗaya ya ɓaƙanta mata ya kuma sake faranta mata alokaci ɗaya, yadda yaga ta saki yasa cikin wani salo da da don nuna mata irin zazzafar ƙaunar da yakeyi mata ya shiga birkita mata lissafi da wani sabon darasin daya gigita, lokaci ɗaya ya rabata da sutturarta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin dake fita daga cikin inner wears ɗin nata dake a tsaftace tamakar ba daga cikin cikinta suka fito ba, murmushi ya saki yana cigaba da aika mata da saƙonni tare da tuno mahaifiyar Meenal da wani sa'in ma warin inner wears ɗinta kaɗai ke hana masa natsuwa acikin ɗakin yaji gaba ɗaya ya tsargu, wani murmushin ya saki ce da jin daɗi kafin su shiga farantawa junansu. Bayan sun gama samun natsuwa Daddy ya kalli Mommy yace, "Allah ya faranta maki Mansura? komai naki  na musamman ne, kina ƙoƙarin kulamin da kanki ta hanyar tsaftace pant jikinki da inner wears ɗinki ba tare da kin barsu da wari ko bashi ba, Allah ma ya sani ina son tsabta da ƙamshi a rayuwata ta kowane irin yanayi, wannan dalilin yasa kika sake maƙalewa a zuciyar nan tawa". Shiru Mommy tayi tana saurarensa yayin da shi kuma ya shiga tuna shekarun daya zauna da mahaifiyarsu Meenal, ta soshi kamar ba gobe amma ƙasa ta na ɗaya daga cikin abinda ya rabashi da ita, dan hatta pant ɗinta da sauran inner wears ako yaushe jiƙe yake jinsu ko yaji suna hamami, idan yayi mata magana kuma sai tace ya aibatata ko kuma yana cimata fuska, gabaɗaya kasa gane yanayin warin jikin da takeyi yake, shi ba warin albasa ba shi ba normal wari da zai bar mutum ya numfasa ba, askin mara dana hammata kuwa gaba ɗaya ba tada lokacinsa, uwa uba gashin kanta da ba'a magana dan ako yaushe ya da ƙare yake ba gyara. Ganin Dady ya sake lulawa wata duniyar tunanin yasa Mommy tashiga sake aika masa da wani salon daya kusa tsayar da bugawar numfashinsa, wanda wannan ma wani sirri ne da akullum kwanan duniya yake alfahari da ita wajen sarrafa shimfiɗarta. HMM.. TO ƳAR UWA, KIN DAI JI DA KUNNUWANKI, TSAFTA DA GYARA BA'A YARA KAƊAI KO ƳAN MATA AKA SANTA BA, SUMA IYAYEN YARA YANA DA KYAU SU KIYAYE DOMIN FARANTAWA MAZAJENSU, YAYA DAƘINKI YAKE? YAYA ZANIN GADONKI YAKE? DANGIRMAN ALLAH IDAN KINSAN DA DATTI YANZUN NAN KI SHIGA KI SHARE KI GYARA GADON KI KI DAME GADONKI WANNAN SHINE ASSIGNMENT ƊINMU NA FARKO GAREKI. ASSIGNMENT NA BIYU😅 YAYA BANDAKINKI YAKE? SHIN YANA ZARNIN FITSARI KO QARNI KO KUMA WARI? AJIYE WAYARKI MAZA JE KI GYARA TUKUNA KI DAWO DOMIN KAUCEWA MASIFAR DAKE CIKIN RASHIN WANKE BANDAKI DA KUMA KWAYOYIN CUTAR DA YAKE HAIFARWA, DOMIN BA INFECTION KAƊAI BA HATTA SOYAYYA ƘAZAMIN BANDAKI YANA KASHEWA🤣 ƘAZANTAR BANDAKI YANA LALLATA NI'IMAR MACCE, TARA PAD KO AUDUGA ACIKIN BANDAKIN KI NA IYA JANYO IDAN MAI GIDANKI YA GANI YA TSANEKI YA KUMA YA DINGA JIN KAZANTAR JIKINKI, DON HAKA A RIKA FITARWA WAJE ANA TSAFTACE MUHALLI 🙄 *IDAN KUMA BA HAKA BA TAYAYA INFECTION BAZAI KAMAKI BA? TAYAYA MIJINKI BAZAIJI KIN SHIRE MASA BA ANYA KUWA KE CIKAKKIYAR MACCE CE? YAR UWATA AHAKA KIKE MACCE BAYAN KINSAN KAZANTA CE JINI TAYAYA ZAKI DINGA AJIYESHI ABANDAKI? TAYAYA ZAKI HAIFAR DA SOYAYYA A ZUCIYAR MIJINKI? INA SO YANZU KI TSAYA KIGA WACECE KE, IDAN KE ƘAZA MACE TO MAZA KI GYARA, ASSIGNMENT NA UKU😜 SHIN KINA WANKE INNER WEARS ƊINKI? KINA WANKE WANDONKI KULLUM KO MAIMAITAWA KIKEYI? KINSAN KAZANTAR WANDO TANA HAIFAR DA INFECTION? KINSAN DATTIN GABANKI YANA HAIFAR DA KURAJE? KINSAN RAGOWAR RUWAN TSARKIN KI YANA SAKAMIKI DOYIN GABA? YAWAN DANSHI AGABANKI NA RUWAN TSARKI YANASAKA WARIN GABA TSANANTA! MATSATSEN WANDO YANA SAKA KAIKAYIN GABA DA CIRA, MAZA AJIYE WAYA JEKI TSAFTACE WANDONKI DA INNER WEARS TA HANYAR WANKE SU DA RUWAN ZAFI A KUMA SHANYA ARANA DON KASHE ƘWAYOYIN CUTA🙌 ASSIGNMENT NA HUƊU🙈 YAUSHE RABON KI DA ASKE GASHIN MARARKI? NACE ZO KI FAƊA MANI DA GASHI AMARARKI? KINSAN WANNAN GASHIN NA MARAR TAKI YANA HANAKI NI'IMA? KIN SAN WANNAN GASHIN NA ZUBAR MAKI DA KIMA A IDANUWAN MAIGIDA IDAN YAYI YAWA? DON ALLAH AJIYE WAYA IDAN KINA DASHI YAU BA GOBE BA KIJE KIYI SHAVING KI DAWO KI BANI LABARI🥱 ZAKI IYA YIN SHAVING DA ABUNDA KIKE DASHI DON SAMUN CIKAKKIYAR NATSUWA SHAVER CE REZA CE. HODA CE CREAM NE DUK WANDA KIKE DASHI HAJIYA MUNA SO KIJE KI ASKE GASHIN NAN🤣. MARARKI TANA KAIKAYI IDAN KINYI SHAVING? MARARKI TANA KORAJI? TO MATSO KUSA ƳAR UWATA DAGA YAU KIN DAINA JIN HAKAN BAYAN KIN ASKE GASHIN GABANKI KISAMU ZAITUN KO MAN KWAKWA KO MAN ALAYADI SAI KISHAFA AGURIN DA KIKAYI ASKIN WASHEGARI MA KI SHAFA KI SHAFA TSAHON KWANA UKU KE DA KURAJEN ASKI KO KAIKAYI SAI DAI IDAN KINDAINA WANNAN IN SHA ALLAH. #Mutallab Asad #Ƴan Tagwaye #Billy S Fari #Nana Diso. *17* *MUTALLAB ASAD* Arewabook:- billysfari Paid book ne, N500 via ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A, Gt bank, sai shaidar biya ta +234 704 040 2435 ko +234 809 845 6130 Ga masu son vip post 1k ne. # ƳANTAGWAYE BIYAR #MUTALLAB ASAD ________ *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 ____ Yadda Meenal taga Mommy tafita sai data daka tsalle tare da ɗaukar handbag ɗinta ta haye sama zuwa ɗakinta, tana shiga ta ciro wayarta takira Mamah da alokacin ke zaune tare da grandama cike da farinciki tana labarta mata abinda taji ya faru daga cikin wayar Meenal, tana ɗagawa cikin nishaɗi take cewa, "Mamah albishirinki?" Sai da Mamah ta kalli grandama sannan ta saki murmushi tana cewa, "Goro fari tastas ƴata". "Yau dai tafaru ta ƙare Mamah ya yasaketa mun huta, yanzu haka ya bita baya kuma na tabbata korar kare yayi mata mai haɗe da wulakanci don sai yace kar gateman ya sake bari ta shigo masa gida". "Kai Masha Allah, ko keda Meenal kiran dana tayi maki kenan kisan ciwon kanki, kina ganin irin cin fuskar da mahaifinki yayi mana awajen Birthday ɗinki saboda Munafurcin matar nan". "Oh my God Mamah yanzu ai komai ya ƙare ko ba haka ba?" Ta faɗa tana ɓata fuska jin Mamah zata ɗauki laifin mahaifin nata, taɓe baki Mamah tayi don ta fahimci Meenal ɗin haushi taji shiyasa ta katseta, "eh Shikenan Meenal Allah yayi maki albarka kinyi daidai yau kin nuna Mani kin haihu acikina, ai naso Dadyn bai iso wajen ba ki rama marin da tayi Mali idan ma dambe zakuyi kuyi, kinga daga lokacin ai girma ya faɗi a wajenta sai na jiki". Mamah tafaɗa cike da son sake hurewa ƴar tata kunne, haka sukaci gaba da fira har sai da Meenal ta gaji ta kashe wayarta tana yimasu sai da safe. Suna gama waya kiran bestie na shigowa amma da yake haushin abinda yayi mata take ji sai tayi banza dashi kawai ta gyara kwanciyarta. Haka ya ƙarashi kiransa har ya gaji ya haƙura, washe gari Meenal bata tashi bacci ba sai ƙarfe goma sannan ta shiga toilet, cikinta tafara ragewa sannan ta ɗauro arwala ta shiga ranka sallolin jiya la'asar, magrib da kuma isha'i data tuna batayi ba sannan tayi sallar asuba, tana gamawa batare da ta tsaya yin wanka ba balle kuma brush ta sauka ƙasa, ba kowa a palourn kasancewar yau Dady ya hana Mommy fitowa kamar yanda ta saba su haɗa breakfast da masu kari yace ta kwanta tahuta, ɗan haka umurni kawai tafito tabasu na abubuwan da za'a dafa sannan ta juya takoma taa kwanta kamar yanda ya buƙata. Meenal kuwa rashin ganin Mommyn ya tabbatar mata da cewa bata kwana gidan ba, dan haka cikin da jin daɗi da kuma farinciki marar misaltuwa a zuciyarta ta nufi kitchen dan yunwa take ji sosai jiya data dawo bataci abinci ba. Umurni taba mai aikin da har takammala komai akan takawo mata breakfast a dining cikin girmamawa da kuma shakkun rashin mutuncin Meenal ɗin ta shaida mata da komai na akan dining jere a kammala yanzu lunch ne zata haɗa, Meenal bata jira taƙarasa maganar ba kawai ta juya ta nufi wajen dining table ɗin, Ganin yadda mai aikin ta shirya abincin kusan kala huɗu kamar dai yadda ta saba ya sata kwala mata kira, da gudu ta iso wajen ta durƙusa agabanta tana faɗin, "Gani ranki shi daɗi.." bata ƙarara rufe baki ba Meenal tace, "Ke dalla Malama rufemun baki, halama baki san acicin gidannan

Chapter 10 of 54