Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 69 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

duk da Dr jarma vaso kafewa akan ba za'a koma da ita cikinsu ba

"Abba yayi gaskiya maji, ki barta kawai" toufeea ya fada cikin I don't care manner. Dubansu tayi duka su biyun

"Inajin babu wani hukunci da kuka isa kuyi mata kamar wannan da Allah yayi mata,ba lafiya babu dukiya diyar da takevin fadi tashin tara komai da mallakar komai saboda ita ta kashe kanta da kanta, banda Allah wa ya isa ya hukuntata haka?, saboda haka ku barta taji da nata, kuci gaba da fatan ku bar sararin duniya lafiya,kada Allah ya jarabceku da son zukatanku har takai ku aikata abinda ta aikata din" wannan maganar ta sanyaya musu jiki dukkansu saidai har yanzu TOUFEEQ bayason koda kallon fuskarta,gashi ita din ta nace da kallonsa bakinta dake zubda miyau yanata motsi, da alama akwai maganganun da take fadi amma ba'a iya jin ma me take cewar.

Abinda yayi gudu kusan shi ya faru,bayan isarsu gidan gain gawar haseena ya sanya hajiya garama tayita kwarara ihu,ihun da iya shi kadai ke fita ake iya jinsa, amma muddin magana zatayi komai baya fita.
Wanann shi ya daga hankalin sãahar sosai, uwa uba mutuwar data tabbata haseenan tayi,ya sake saka mata tsoron Allah da kuma tsoron duniya, da gaske budurwar wawa ce, kuma babu mayaudariyar aba irin duniyar yanxun nan zata daura aure da kai,yanzun nan zata sakeka,waccae shekarar iwar haka hajiya qarama din nata tsara yadda wannan shekarar zata kasance mata cike da cikar burikanta da haskowa kanta tarin nasarori da kuma ci gaban rayuwa,amma a ayanzun sai gata a kanannade cikin keken guragu, ba gafa ba hannu babu baki,ba lafiyar ma dukanta,babu dukiya ba miji babu diya,lallai ba shakka babu abinda yafi aikata alkhairi dadi a rayuwa,KOWA YAYI NA GARI KANSA kamar yadda bahaushe yake fada, kuma hakan take.

Ganin tana neman birkice masa sai va dauketa
gaba daya ya kaita bristol ya kama royal suit kamar yadda ga saba sukayi zamansu a can. Katafaren gidan da yake kan ginawa ya tayar da qarasa ginin,cikin. sati guda komai ya kammala. Babu abinda suka dauke daga wancan tsohon gidan sai suturar jikinsu. Ana ya goben zasu tare ya kaita gida yace ta kwana wajen maama

"Zaki zama full house wife, idan kika shiga MY KINGDOM ban miki alqawarin fita ko yaushe ba,ki kula da ni ki kula da abinda zaki haifa min for the rest of our lives shine burina".

Ranar da zasu tare din dr iarma na zaune a parlor dinsa suna yin dinner tare maji na serving nasu ya kalleshi

"'Diyarka kadai zaka dauka nima dauke tawa diyar zanyi"

Dr jarma yace da toufeeq. Kansa ya daga yana duban maji ko zata shiga maganar sai yaga ta fuske, da suka hada ido sai ta kauda kai

"Ai gaskiya ya gaya maka,ka sakata a gaba ba batun aure bayan ta gama isa munzali har tana shirin wucewa aurar da ita zamuyi muma"

"'Kodai kunason ku shaqata ne maji?" Ya fada qasa qasa yadda Dr bazaiji ba.

Spoon din hannunta ta jefa masa tana cewa

"'Qaniyarka,me yasa ka maidani kakarka ne?" Dariya ya saki yana kaucewa

"Afwa ni ba wani abu nake nufi bafa".

"Bar dan nema, ka dauka tsufa mutuwa ce?" Dariyar da yake rigewa ya saki yana hada hannunsa guri daya

"Ayimin afuwa,na tuba". Har qasan zuciyarsa yakejin rayuwarsa ta sauya, yana mugun jin dadi idan yazo yaga maji da Dr a tare guri guda suna hidimtawa juna da sunan miji da mata

_(kowanne yaro a duniya bashi da burin da ya wuce wannan, dukkan yaran da uwayensu ke wani gida suna auren wani tabbas don basu da yadda zasuyi ne amma inda ace son ransu ne ko gaddara ta basu damar rubuta abinda zai wanzu a rayuwarsa,da zasu rubuta tabbatuwar iyayensu guri guda, babu abin alfahari irin ka tashi kaga mahaifiyarka tayi rayuwa kuma ta rasu cikin dakin auren mahaifinka, saidai idan ba yadda ka iya da yadda Allah ya tsara maka qaddararaka, yan uwana mata,mu qara haquri akan wanda muke dashi kan zamanmu gidan mazajenmu, MAZA)MATA a duk sanda rayuka suka baci, muka yanke shawarar rabuwa da junanmu,mu dinga saka tunanin makomar 'ya'yanmu akan gaba kafin komai,Allah ya zaunar damu lafiya ya gara mana haguri da mazajenmu, suma Allah ya qara musu haquri da juriyar zama damu)_

Sai data shiga gidan ta tabbatar gidan yaci sunansa MT JARMA KINGDOM,wani irin fasali da tsarin ginin gidan turawa akayi, kowanne sashe na gidan idan ka kalla zakasan cewa lallai da gaske gidan na masoya ne, an kumayi tanadin wanzar. da soyayya me dimbin yawa a gidan,da rayuwa me cike da ma'ana da sanyayar da zukata.

Wata ravuwa da ko a mafarki dukkansu basu taba zaton akwaita a duniyar ma'aurata ba suka shiga shimfidawa cikin gidan, dukkansu kowa yasan irin bacin rai baqinciki da karayar zuciyar da ya samu,wanann ya qara musu qaimi wajen kula da juna matuqa da gaske.

TOUFEEQ wani irin gold ne a cikin duhu,wanda sai me sa'a ce qwarai zata takashi. Tun asali namiji ne daya amsa sunan NAMIJI bawai muna maza ba, idan nace
NAMIJI ba ina nufin a halitta kawai ba,a'ah, irin mazan da sukayi qaranci a yanzun, wanda yake buda hannayensa ya kuma bude kafadunsa don ya tallafe dukkan nauyi da bugatar iyalinsa,ya bata lokacinsa a kansu,ya nuna musu zallar madarar qauna da kulawa,yayi gyara cikin hikima da iya sarrafa harshe idan anyi laifi ya kuma bada uzuri me nisan gaske a garesu. Ya yarda da maganar annabi da yake fadin mu din an haliccemu daga gashin haqargari na, ko ayi haquri damu aji dadi damu a haka a karkacen da muke, ko kuma ace sai an migar damu, miqar damu kuma yana nufin karya mu,karyamu shine rabuwa damu.

Gefan sãahar kuwa ko daya ciki bata bari va hanata bashi dukka wata kulawa data kamata ba,gasa da wata guda ta gama fahimtar halayya da dukka dabi'unsa wanda batakai ga fahimta din ba. Tayi kuka tayi kuka a sujjada har batasan iya adadi ba bayan data fahimci musayar alkhairin da ubangiji yayi mata,tayi sadaka me tarin yawa dukka tana godewa Allah da bai wofantar da wahalarta ba yayi mata kyakkyawar sakayyar da a nata ganin bata cancanci haka ba, girman rahama jin gai da kuma tausayin bayinsa ne yasa ya mallaka mata toufeeq din. Kamar yadda yake a tsarinta tun can baya,yanzun ma bata wani yarda ta dauki me aiki ba,tanason samun ladan gidanta da hannunta. Daga harabar gida garden na gida da sauran hidimomin gida akwai ma'aikatan da sukeyi acan waie ta cikin gida kuma baba ramatu suka taho da ita,' yar amanarsu,itake gyaran dakuna da bangaran säahar din yayin da säahar din ke rige da ragamar kula da hatta da cup din ruwan da toufeeq zai sha bata dorawa kowa ba. Yayi mitar ta dinga zama tana hutawa shi ya yafe amma tace sammm, saidai idan ya dawo ko yana gida shike tayata su kammala komai tare.

Dalili na biyu da yasa bata dauka me aiki ba,tana ganin a yanzun fadeela ta fara tasawa,shekara takwas tana sanvata fara kovar wasu abubuwan, batason gata da dukiyar mahaifinta ya sanya ta tashi a SANGARTACCIYAR MACE. Yarinyar ita kanta qaunar ace vi abu kaza takevi.don haka ta taso da wani irin qwazo, idan ka ganta tare da sãahar baka isa duk qwaqwarka kace ba ita ta haifeta ba.


Cikin hukuncin Allah cikinta ke girma cikin goshin lafiya,tun a sannan yaso ya kwashe iyalansa subar gasar saboda harkokin business dinsa amma maji tace bata varda ba girma takeyi vanzun tana da bugatar rayuwa cikin ahalinta wanda abaya bata samu wanna damar ba, uwa uba ma bata yarda ya daukar mata yarinya da
'yan jikokinta ba jirgi yana gantali dasu. Yadda tayi lafazin son zama cikin iyalin nata ya taba zuciyarsa qwarai, don haka ya haqura shima ya tattara tafiyar ya watsar, duk da yasan zamansa guri daya a nigeria bazaiyiwu ba,saboda yabar kasuwancinsa a wasu qasashen, don ma bashi da haufi ya hadu da directors 'yan amana,sannan kuma kusan komai dashi akeyi ta na'ura, koda meeting ne dashi akeyi ta conference call.

*****Wani irin gawataccen daki ne da aka yiwa tsari
2) me kyau da wasu irin books shield na glass da wani irin garfe me haske da daukan idanu. An gawata dakin da nau'in kuieru biyu, sofas masu taushi da kuma lounge chairs da suka dace da paint curtains da carfet na dakin.

Takardu ne masu tarin yawa a gabansa da yaketa signing tare da karanta rubutun jikin was daga ciki.
Kana ganinsa zakasan he was so busy hankalinsa kuma yayi nisa sosai.

A hankali aka turo qofar dakin,säahar ta bayyana cikin wasu silk nightgown farare tas in and top,gashinta me tsaho da sheqi yana daure a siririn band da baka ko rya ganinsa saboda cikar da gashin ya qarayi. Ta aje wani irin kyau idan ka dauke tulelen cikinta da take tallafe dashi saboda nauyin da yayi matan, fuskarta a tsuke take sosai, babu alamun walwala ko kadan a tattare da ita.

Sam bai ankara da shigowarta ba sai sheshsheqar kukanta ya ji. Fatali yayi da takardun cinvarsa va mige da sauri yana dubanta,sai kuma ya fara takowa zuwa inda taja ta toge fuskarsa ciks da damuwa

"Ya salam, ya isa cutie tell me me kuma ya faru?" Sake fashe masa tayi da kuka,abinda ya sake rikitashi gaba daya,ya kamo hannunta ya rige sosai cikin nasa ya fara janta ciki a tausashe amma saita cake

"Ka sakeni tunda yanzun baka sona,har suna ma ka canzamin,saboda tsabar baka sona yanzu kake tsokanata da wani cutie,bayan fuskata duka ta kumbura, kyauna dama kakeso ba ni ba,yanzu kuma na zama mummuna ka daina yayi na" matugar juriya kadai yayi bai fashe da dariya ba, saboda yanzun nan cibi zai zama qari. Tunda cikinta ya fara nauyi ta zama mafadaciya,komai akayi mata ba'a kyauta mata ba,ba'ayi mata dai dai ba,ga dan banzan tsarguwa, ko kallonta ya cikayi sai tace muninta yake kalla

"Wallahi kinji Allah kenan, inda zaki zauna a haka zanso hakan bayan kyan da kika qara har tacen wajen ma ko?, ba'a magana" kunyarta har yau tana nan, maganar tasa ta sanyata dauke kanta murmushi na shirin kubcemata, amma tsabar qwarewa a rigima saita fuske

"Ban yarda ba, inda hakanne ai ba zaka barni ina jiranka ba,ni kadai almost one hour?" Wannan karon dai sai da dariyar ta qwace masa,yasa hannu ya juyo da fuskarta yana cewa

"A'ah…ayimin afuwa,ashe duka wannan fushin abun
ake nema?,aikam aiki dai ya gare mun samu babban aiki"

ya fadi yana jin dadi qasan ransa. Shi kam ya daga mata gafa ne saboda cikin kwanaki ukun kamar yaga bata jin dadi sosai, tun ranar data dawo daga sunan afifa wadda ta haifa baby giri dinta qatuwa wadda taci sunan SHIFA(MAJI), suna kiranta da AHLAM, shi dai wannan ciki •) ya biyashi dari bisa dari.

Ko taku daya bai bari ta garasa ba ya dauki abarsa
ya wuce da ita fadarsa, yana tafe yana tsokanarta

"You gain weight moonbeam"

"Kaine ka jawomin" ta fada tana mintsininsa a tsakiyar qirji, tasan yana tsokanarta ne don yasan batason yace tayi nauyi.

Yana alfahari da ita gwarai ta wannan fannin, duk hanyoyin faranta rai ta sansu. Idanunsa a lumshe yana tina irin farinciki da gamsuwar da take bashi yaji tadan tureshi kadan tana guna guni,kunne ya saka da kyau

"He acts like he's the smallest thing in the world but he's freaking huge" dariva ce me garamin sauti ta subuce masa,ya daga fuskanshi yana kallon tata

"Eheenn,wanann grumbling din bashi da ma'ana,kin fada ne don ki rama nace kin qara nauyi, after all ma sai da kika gama kwashe dadin?, kwadayayya?" Kukan kissa ta sakar masa tana dan kai masa duka, shi kuma ya bita da gwalo yana boye kansa cikin boobs dinta. Sai data gaji ta barshi jin tayi shuru sai yakai hannunsa ya shafi gefan fuskarta

"What happened?"

"Am hungry" ta fadi cikin salon ban tausayi. Tashi yayi sosai yadda zai iya ganin fuskarta,da gaske ta bashi tausayi, tana wahala da cikin sosal,bai sani ba ko haka kowacce mace keyi?, ameesha dai baiga bakan daga gareta ba

"But you just eat.

"Need something sweet,am craving" dariya ta bashi,sai yasa yatsusa yadan rufe rabin fuskarsa yana zuba mata ido

"Uhunnn" ta fadi tana kallonsa itama. Da gaske ya fuskanci yau rigimar ce a kanta, don ledar data matsa yayi mata siyayya ma gata a yashe a gasa, da kanta tavi list din komai amma bataci komai din a ciki ba. Baison rigimar tayi tsaho, don haka yayi wuf ya tashi yana dagata

"Go bath"

"Noooo hottie"

"Dole indai kinason maqulashe". Kumatunsa ta riqe da hannunta daya tana jaa

"Having someone who can handle all your moods is such a blessing" hannun ya sunkuya yayi kissing yana murmushi.


Zafafabiyar

"HUGUMA*


_TABARMAR KASHI*


Book 02 Page 71

Tare suka shirya shi da ita, ta saka doguwar rigar abaya wanda yanzun sune suturarta saboda girman cikinta,shi kuma ya Sanya kaftan abaya sassauga suka fice.

"Ina muka nufa?"

"Pizza zanci" ta fada tana tande baki. Dole ta bashi dariya sosai

"Wadan nan babies,wanne irin kwadayayya suka maida ke?"

"Ask them" ta fada kawai tana nuna masa tsinin cikinta wayarta na hannunta tana qoqarin kunnata.
Gurin saida pizza me kyau tsafta da inganci va kaita cikin nasarawa GRA

"A nan fa zamuci" ta fada tana neman gurin zama

"Oh god" ya fada a hankali, mamaki yana sake kasheki, da gaske ake cewa dole ka sake yin karatu na musamman akan mace idan tana da juna biyu, wawayen maza sai suyita cusgunawa matansu a irin wanan yanayin su dauka kome iskanci ke sawa suyi. Tunda yake da ita bai-taba gani ta zauna cin abinci cikin mutane da yawa bama bare waje sai yanzu.

Hakanan yaja tasa kujerar shima ya
) zauna,ya jira waitress ya bata order.
Dukan pizza din ya tura mata,yana kallon yadda take ci hannu baka hannu qwarya

..Hmmm.

...i love you"

"Baby iam finished"

"Alright" ya fadi yana miqewa

"Moha…...i wanna discuss something with you please mana" ta fadi tana narke murya tare da tara hawaye a idanunta. Tare suka waiwaya suka kalleta shi da sãahar din, kasa ci gaba da kallonta tayi saboda wani irin kallo da taga tana jifan toufeeq din dashi, ta dauke kanta gefe tana gogarin hadiye wani mugun kishi da ya taso mata, bata taba zaton tana da kishi irin wannan ba sai yanzu.

Mamakin zallar garfin hali ko gegashewar zuciya zaice irin ta ameesha ke kai kawo a ran toufeeq, bai taba zaton har gaban abada zata iya tararsa da zancan ban haguri bama bare batun ya koma sonta har akai ga zancan ta koma tana amsa sunan MATARSA. ransa yaji wani wani irin baci, duk sansa ya kalli fuskarta sai va tuna zunubinta,sai yaga komai muraran shimfide saman fuskarta muraran kamar a lokacin kunnuwanta suke jive masa abinda yaji din.

Karo na biyu säahar ta gaza jurar kallon da tayi imani har yanzu ameesha na jinfan toufeeq din nata dashi,sai ta waiyawa tana mata wani qasgantaccen kallo

"Da kamun kai da cikakkiyar nutsuwa akasan diya mace, bin d'a namiji ba nata bane, ki tagaita kallonki a kansa wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa he's mine ever and ever"

Kalaman sun taba ameesha sosai, dole ta waiwayo ta zubawa säahar idanu,kallon fuskar säahar din taketa gudun yi din batasan me yasa a duk sanda ta kalleta ba sai taji kamar ita nata ajin baiki ba, duk sanda ta dubeta sai taji kamar har abada toufeeq bazai iva sake kallon kowacce diya mace yaji ta burgeshi ba, duk sanda ta kalleta tana jin cewa tsananin rabo da kuma tausayi ya mallaka mata toufeeq a baya,duk sanda ta kalli qualities din da sãahar din ta hada sai taji kamar ta rasa toufeeq har abada,mafi munin tunin da batason tunashi wanann ne kuma ya sanya taqi giving up,wata yudararriyar zuciyar tana gaya maya cewa ZAKIYI NASARA,SHI ME TAUSAYI NE.

Taku biyu yayi ya kamota cikin jikinsa qasan ransa yanajin farinciki yana ratsashi, har yanzun classy säahar din nan tasa tana nan babu abinda ya canzata,me tsananin kamun kai da jin takaicin yadda mata da yawa suka zama was marasa aji da sanin ciwon kansu

"Yes‚iam your's,lam all yours,let's go" ya fadi yana dauka mata wayarta tana jingine a jikinsa suna takawa a nutse.

Zallar kishin da ya gani cikin idanunta bai taba ganin irinsa ba kaman yau,mota ya bude mata ta shiga,ya kunna mata Ac ya kuma daura mata seatbelt ya dage dukkan glasses din

"Ina zuwa, kada ki fito" ya fada yana rufe mata qofofin sannnan ya juya yana barin wajen.

Tanason tace masa ina zaije? yazo kawai su tafi amma ta kasa,minti daya biyu har biyar shuru, take zucivarta ta fara raya mata qila ma ya shanya ne kawai vana wajen tsohuwar matarsa suna soyewa.

Wannan tunanin ya kumbura zuciyarta,sai kawai ta fashe da kuka,take mararta tayi wani mugun motsawa da matsanancin civo.

Ransa fes yake dawowa ga motar,ya tabbatar yau vau kawo garshen case din ameesha,yayi imani daga rana irin ta yau ba zata sake marmarin hada hanya da shi ba indai da zuciya a qirjinta. Zasu biya su dauko fadeela da yanzun maji keson qwaceta itama, tuntuni yakeson ta dawo gida säahar ke hanashi daukota

"Zaka iya kallon idon maji kace kazo daukar 'yarka?"

"B wani madam, kema fa nasan kaara kawai kikey" murmushi kadai takeyi bata taba yarda ta amsashi ba.
Yana bude motar sautin kukanta ya sauka a kunnensa

"Subhanallah" ya fadi da sauri yana dagota saboda vadda ta zauna din ya tabbatar ta takure da yawa

*Ka daina tabani, marata kamar zata tsinke,babu dadi, ka koma wajen tsohuwar matarka ka gyaleni naii da ciwona" bai sake ce mata komai ba sai kawai ya tayar da motar, cikin wani mugun speed ya fice da motar daga harabar asibitin.

Kafin sukai asibitin ciwon ya sake tsananta.
Luckily suka tarar da Dr raheema na shirin fita daga duty, dubawar farko taga haihuwa ce, kuma gadan gadan tazo don takai 4cm.

Ya rude gaba daya saboda yadda yaga tana juyi a tana riqe komai da qarfinta na gaske sai ya daga masa hankali. Ya rasa waye zaima fara kira?,sai kawai ya kira maji.

Hankalinta yadan daga, saboda burinta a duniya na garshe taga tulin jikoki daga jikin diyoyinta guda biyu,tunda ita Allah bai gaddareta da samun tarin

'ya'ya masu yawa ba, ta daure zuciyarta cikin nutsuwa tace

"Ma sha Allah, Allah ya raba lafiya,Kun dauko kayan haihuwar ne?"

"Daga gurin pizza nagudar ta tashi"

"Ashsha wanne irin sakarci ne haka Muhammad? ka dinga yawo ya yarinyar mutane da tsohon ciki?,waye yace maka ana fita anyhow da tsohon ciki?" Kai kawai ya girgizawa,maji ba zata fahimta,yanzun inda bai fito da ita ba da yanzun tana gida suna dambarwa

"Ka yiwa baaba ramatu magana,gani nan isowa nima" katse wayar yayi kawai ya kira baaba ramatu din. Maama maji ta kira, amma saboda kara irin tata,duk kuwa da cewa säahar din auta ce, autar ma da ake fatan ganin abinda zata haifa amma cikin alkunya tace

"Haba maji, kina gurin ai ba sai nazo ba" sosai maii keiin dadin yadda dr girema da maama ke bata girma da damqa mata säahar halak malak, saidai duk da haka ta roqi tazo din a haka suka rabu.

Cikin abinda bai wuce mintuna talatin ba sai gasu a asibitin. Maji, anty farheen, anty sumaira, raihanatu wadda tazo musu hutu ne(cousin din adam da su dr girema suka turata karatu,bayan dawowarta sun laluba ainihin dangin mahaifinta sun maidata hannunsu, sun kuma yi mata kaykkyawan rigo,sun barwa momee itane dama saboda ta dage zata rigeta da amana, suka barta suna ganin kamar 'yar 'yaruwarta ce ba zata cutar da ita ba yanzun haka shirin bikinta akeyi) sai fadeela data kasa ta tsare itakam vau zatayi 'yan ganne. Kwatsam saiga afifa ita dake da danyen jego ta saka sajjad din a gaba sai da suka taho. Sosai maji ta dinga fada,tace ya dauketa su koma amma ya bawa majin haquri, tayi algawarin bestie dinta tana sauka zasu koma,tunda ance takai kusan 7cm ma. Yadda ta marairaice yasa ta bawa maji tausayi,sai ta qyaleta kawai suka zauna kowa yana fatan samun labari me dadi. Oga toufeeq kuwa basusan ina ya shiga bama,don basu sake ganin fuskarsa ba ma.


• Zafafabiyar

"HUGUMA*


•TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 72


Awa daya da wasu mintuna daya daga cikin nurses din dake labour room din suka fito.

"Hajiya d'iyarku ta sauka, amma bazan fadi abinda aka samu ba sai an bani goron albishir" ta fada tana murmushi

Caaa sukayo mata,har abun ya bata dariya yadda taga suna zumudi. Tun kafin maji taji abinda aka samu ta balle jakarta ta fidda rafas na 'yan 100 sabbi kar ta migawa nurse din

"Sauka lafiyar ma da kikace tayi ya wadatar,ga goron albishir dinki" fuskarta ce ta fadada sosai da fara'a tana juya kudin,kafin ta sake cewa komai afifa ta bude tata iakar ta ciro 'van dari biyar biyar ta damqa mata
"Kun samu 'yan samari mazaje" nurse din tayi saurin fada tana rige kudin cikin farincikin tagomashin da ta samu a yau din.

Baaba ramatu ce ta rangada guda cikin tsantsar farinciki

"'Ma sha Allah,alhamdulillah" ta rufe da fadin hakan.
Cikin ganganin lokaci gurin ya kaure da hayaniyar farinciki. Sai sannan aka fara cigiyar toufeeq. Murmushi.Sajjad ya saki

"Oga fa inajin yana masallaci, bari na duboshi" ya fadi yana miqewa ya fice daga gurin.

Sanda sajjad din ya shigo yana zaman tahiya na garshe. Ya zauna daga gefansa har ya sallame, cikin fargaba ya waiwayo yana dubansa, amma murmushin da ya gani saman fuskar sajjad din ya sassauta tsoronsa

"'Yallabai anata qiyamullaili ko? sai kazo to ta babies sun iso”
"Really?" Ya fada yana fidda ido

"Ahaf, kai dai ka tanadi goron albishir dina" ya fada yana migewa. Ai kafin sajjad yakai bakin qofa har ya riskeshi ya ma wuceshi.

Cikin wata irin sassarfa yake takawa,wani farinciki da karsashi suna ratsashi. Duka basu a veranda din, sai hayaniyar su da yake jiyowa daga dakin hutu.

A nurse ya bude gofar dakin, tashin farko idanunsa suka sauka kan fuskarta. Tana zaune sosai abinta saman gadon tana kurbar tea me zafi da kauri, sam ba zakace itace tasha wannan gwagwarmayar ba. Wani irin sassanyan farinciki ne yake ratsa kowacce gaba ta jikinta, tun daga ainihin zuciyarta har zuwa kan fuskarta.
A sace take kallon yaran, tana tasbihu ga ubangijin da ya maidata vara biyun data barar bayan ya maida mata su sai ya sauya musu da nagartaccen uba na gwarai,wanda zasuyi alfahari da fitowa ta tsatsonsa. Komai na duniya idan ubangiji yayi akwai hikima a ciki, haka siddan baya hukunta komai ba tare da dalili ba. A sannan taji babu dadi matuga game da rasa cikinta har taji kamar duk duniya ita daya ke cikin qunci da takurar zuciya,ashe duka ubangiji ya hukunta hakan ne saboda tanadin sauyi mafi alkhairin da yayi mata.
Qamshinsa shine ya fara janye hankalinta,duk da jama'ar dake dakin amma hakan bai hanata shanshano shi ba. Daga kai tayi, idanunsu suka gauraya da na juna,sai ya lumshe mata nasa idanun yana sakar mata wani tattausan murmushi gami da hada hannunsa yay! mata jiniina. Kai ta sunkuyar tana jin nauyinsa data tuna abinda ya faru awannin dazu,sai shima ya kau da kan nashi ya fara takowa cikin dakin bakinsa dauke da sallama.

Hankali kuma sai yayo kansa,kowa yana qoqarin masa barka yana amshewa yau dai duk yadda yakai ga turbune fuska lafiyayyen murmushin nan nasa yaqi boyuwa,a haka har ya qarasa gaban gadonta.

Kuiera nadeeya ta bashi, sai ya jawota gaban gadon ya dora gafarsa kawai akai, fili yake da bugata su bashi,saboda kyakkyawar runguma ce yake gain tafi dacewa da ita. Idanunsa cikin nata yana jin kamar zasu narke su zama abu guda. Cikin hikimar manya maji da baaba ramatu suka mige zasu fice, abinda ya sanya nadeeya fadeela anty farheen da anty samreen suma bin bayansu. Afifa ce dake cikin babban mayafi tana baiwa baby nono ita da sajjad basu fita din ba. A gefansu nadeeya ta jere yaran tana cewa

"Maji din ta fita ai, saiki sake ki qare wa kayanki kallo antyN" ta fadi cikin dariyar tokana tana yin gofa da sauri gudun kada toufeeq din yakai masga.

Hannunsa ya mige ya rige tafin hannunta cikin nashi yana ci gaba da yi mata wannan tattausan kallon

"Yanzu Madam kishi kadai dama ya isa tayar da naquda har a haihu?" Ya fadi cikin salon tsokana kadan. Kai ta langabe tana kallonsa tana kuma satar kallon afifa,ta tabbatar idan afifa taji ta shiga uku da tsokana.

Murmushi ya sake mata yana kanne mata ido d'aya.

"Idan nace sannunki Allah yayi miki albarka batayi kadan ba?" Kai ta gyada cikin murmushi tana kallonsa itama

"Ida nace na gode qwarai, Allah ya sanya mahaifanki cikin aljanna madaukakiya shima baiyi kadan ba?" Nan ma kai ta jinjina tana murmushi zuciyarta cike fal da mahaukaciyar

Please Login or Register in order to submit comment