Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 29 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta rasa amsar da zata bata,daga bisani Allah ya kimsa mata,ta waiwayo ya dubeta tana sauke ajiyar zuciya

"Ni dake duka muje muyi istikhara,idan mun samu nutsuwa akan abun,zan maara miki baya"

"Kin tabbata da gaske kike?" Murmushi ta saki

"Da gaske nake,amma ki tanadi abinda zaki gayawa su abba,don ni bazan iya musu qarya ba" miqewa tayi daga tsugunon da tayi ta zauna sosai

"Kinfi kowa sanin ba dabi'ata bace,so nima ba qaryar zanyi masa ba".

Akan haka suka samu matsaya ita da afifa din,sannan kuma dukansu suka shiga istikhara din kamar yadda afifa ta shawarcesu. Cikin kwana ukun kuma baki dayansu ita da afifan,kowanne ya samu nutsuwa cikin ransa,rudanin dake ran afifa ya kau,haka dan kokwanton da ita sãahar din kanta takeyi game da aikin sai taji babu shi,taji har cikin ranta zata iya,fatanta daya kada abba yace ba zatayi ba.

*_TOFA😂,me yake shirin faruwa kuma?,GUDUN K'ADDARA sãahar ke shirin yi ko kuwa?,ku biyoni dai muje zuwa_*


Page 58

*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔

Page 58

Kwana biyu kacal Mrs sadeeqa tayi kiranta,ta gaya mata cewa hajiyan tayi accepting nata,saboda haka ta shirya kwana uku masu zuwa zasu zo da mota a dauketa ta kama aikinta.

Taji dadin hakan,amma kuma fargaba ta lullubeta na yadda zata tunkari abban,wuni tayi cikin rashin sukunin,afifa na kallonta taqi bata shawarar komai

"Na gama aikina ai,tunda har nace bazan gayawa abba manufar komai aka aikinki ba"

"Haba bestie"

"Da gaske nake" ta sake jaddada mata,sai daga bisani ta samu qwarin gwiwa,bayan wata idea ta fado mata,ta dauki wayarta da sauri ta fara kiran anty farheen.

"anty,zan sameki yau a gida?"

"Eh ba inda zani yau,akwai wani abu ne?"

"Saina iso kawai" tace da ita,saita ajjiye wayar ta fada toilet kawai ta fara wanka,so take ta gama da kowacce matsala a yau,tayi shirin tafiyarta hankali kwance.

Cikin lokaci qalilan ta shirya cikin wata doguwar rigar abaya qirar qasan oman mai sulbi da kuma tsarin zubin duwatsu masu daukan hankali,fuskarta ta sake wani fresh da wani irin haske me kyau,kalar abayan na charcoal color ya karbi farar fatarta sosai,sassanyan qamshinta na bin kowanne sashe na dakin har zuwa falon da batakai ga fitowa ba.

'Dan abinda take da buqata ta dauka a wata qawatacciyar qaramar jaka me jikin mage,dai dai lokacin da afifa ke kitchen tana duba girkin abbansu da basu aikin gidan suka dora ta dawo dakin,ta murza qofar ta shigo,idanunta akan sãahar

"Madam nanny" ta fada tana murmushi hadi da tabe baki, zagayyun fararen idanunta ta juya tana goya jakar a bayanta

"Yes,daga yau sunana kenan" qaramar dariya afifa tayi tana zama saman stool

"Kinsan Allah zaiyi wuya ma su karbeki as nanny,shin wai ke baki kallon kanki ne?,wace zata daukeki 'yar aiki muddin tana da aure?,wace wawiyar ce?....."

"Don Allah afifa tsaya,kiyimin fatan alkhairi mana,wannan duka fatan tsiyan na meye ne ha'an"

"Baqinciki nakeyi, bestie na zata zama 'yar aiki"

"Okay,that's fine,kici gaba da fada" saita fara zura dogayen qafafunta cikin wani lallausan plate din takalmi

"Ina zakine ma babu ko gayyata?" Ta jefeta da tambayar bayan ta dakata daga danna wayarta

"Gidan yaa muhyi"

"Jirani don Allah na shirya" ta fada tana miqewa da gudu bayan ta cillar da wayar tata ta shige toilet ba tare data tsaya jiran jin abinda sãahar din zata ce ba. Iska me zafi ta fitar,afifa dole saita bata mata lokaci,tanason ta gama komai da wuri ta iske abbanta a gida,ta kalli agogon dake daure a hannunta dan india dan kamfanin Daniel Wellington,saita maida dubanta ga qofar bandakin

"Ki sameni a wajen ummee,don't stay longer please" saita tsugunna ta dauki laptop dinta me tambarin apple ta fice daga dakin.

•••••••••"daga ina kuke halan da yamman nan?" Farheen ta fadi tana zama saman kujera,bayan ta fito musu da plate din snacks,me aikinta dauke da daya try din data shirya musu smoothie,don ita din gwanar girki ce kala kala,fridge dinta kawai idan ka bude zaka samu fresh snacks sosai,a nan din sãahar ta koyi girki masu yawan gaske

"Nanny sãahar ce ta tasomu,ni fa amma gayyar sodi nazo,don bata gayyaceni ba nace ta tsayani mu taho tare" afifa tayi maganar tana duban sãahar daketa ji da rigimar khalipha shi da aleena data qara wayo sosai

"Nanny kuma?" Farheen ta fada tana dan dariya,a zatonta fadan da suka dan saba tabawa ne da shaqiyanci ma juna ya motsa tsakaninta da sãahar din

"Eh mana anty,koda yake dai ance waqa a bakin me ita yafi dadi" ta qarshe zancan tana jawo cup din da smoothie din yake,ta gyaran zaman straw din jiki ta fara zuqa a hankali tana lumshe ido,zaqi da dadinsa yana ratsata

"Uhmmmm,ta yaya don Allah ya muhyi zai iya qara aure ana masa wannan delicious din" qaramar dariya farheen tayi,tasan afifa qwarai badai iya tsokana ba,amma hakan na mata dadi,don babu komai tsakaninta da dangin mijinta face tsantsar girmama juna da zaman lafiya hadi da qaunar juna

"Basu da tabbas fa,iya girki ko qwarewa a wani abun baya hanasu qara aure idan sunso,koda kuwa ke din hurul'eeni ce,saidai kawai dai ki iya din don ki amsa sunanki na mace,sannan saboda lafiyarki yaranki dashi kansa me gidan,yaranki mata kuma ki zame musu makaranta,sannan koda wata zatazo din ya zamana ba'a fiki da komai ba,kin wuce kiyi kwaikwayo saidai keda ita ku goga,kowa ya baje hajarsa" kai sosai afifa take gyadawa cikin gamsuwa,zaiyi wahala ka zauna da farheen baka qaru da ita ba ta kowanne fanni na rayuwa.

"Ke kuma yaushe kika zama nanny?" Ta maida tambayarta ga sãahar,daga kanta tayi,sai kuma ta zaunar da aleena sosai tsakanin qafafunta

"Shi mutum idan gulma tayi masa yawa sai addu'a,da kin barta ta qarshe miki labarin..... bestie naga alama bazaki rufan asiri ba" dariya sosai afifa keyi harda kwanciya cikin kujera,abun yana bata mamaki yadda sãahar lokaci daya ta daukaki batun aikin da zahiri tafi qarfinsa,ita kanta a gidansu 'yan aiki nawa ne?,so amma a yanzun ita bata jin komai akan aikin,tunda suka tsaya sukayi addu'a a tare.

"To nayi miki qarya ne,ba nanny din bace?"

"Ban sani ba.....am anty don Allah alfarma nazo nema" ta qarashe maganar tana maida hankalinta ga farheen

"Ina jinki,Allah yasa bata fi qarfina ba". Komai ta zayyanewa farheen shi,saboda babu 'yar boye boye a tsakaninsu,sannan ta qarashe da cewa

"Matsalata daya abba zaice zaiyi bincike akan inda zani aikin,abu daya nakeson kiyimin,zance masa kin sansu,sannan wata uku kacal zanyi na dawo" shuru farheen tayi tana jinjina kai,tana qaunar sãahar har cikin ranta tamkar qanwarta uwa daya uba daya,zata iyayi mata kowacce alfarma,to amma kuma akwai matuqar girmamawa da ganin mutuncin juna tsakaninta da surukanta,batason tayi musu qarya

"Zan iyayi miki kowacce alfarma,amma bazan iya shaidar abinda bani da tabbaci ba,inason ki bani address dinsu na gani,zan aika ayimin binciken ingancin halayyar mutanen gidan"

"Alright" ba wani jinkiri ta kira Mrs sadeeqa kai tsaye,ta kuma tura mata komai da komai.

Address din ta tura mata,ita kuma ta miqawa farheen wayar. A fili ta karanta address din

"Wannan layin ai kamar layin gidan qawata sauma,bari nayi confirming" khalifa ta tura ya dauko mata wayarta,saita tashi tabar gurin. Duk da hankalin sãahar nakan yaran,amma kuma fiye da rabin tunaninta yana kan farheen data fita a falon.

Ta kusa mintuna ashirin sannan ta fito,ta koma ta zauna a inda ta tashi

"Yanzu kuma ina da qwarin gwiwar bada shaida,layin gidan qawata ne,tasan gidan,sanann me gidan ma tacemin sananne ne sosai,mutumin kirki ne qwarai da ya samu yabo da shaidar al'umma,ko jiya shine wanda ya qaddamar da committee na tsaro na unguwar,kusan ko yaushe suna tare da me gidanta tsakanin sallar magrib da isha'i,duk da ba mazauni bane,yakanyi watanni ma baya gari,yarinyar ce tace bata santa sosai ba,tunda ba inda take fita,amma tace eh tabbas yana da diya guda daya. Ajiyar zuciya sãahar ta sake,sai ta sake jin nutsuwa tana ratsata,yanzun kam ta samu qwarin gwiwar tunkarar abba,muddin farheen tace ta san gidan,tana da yaqinin babu lallai abba ya zurafafa ko yace zai hanata,yana ganin kimarta sosai cikin surukansa.

Ana idar da magriba sãahar din ta miqe

"Zan wuce gida bestie ya za'a yi?"

"Kije kawai,drivern anty farheen sai ya saukeni"

"Ba wata damuwa?"

"Babu miss nanny" harara ta watsa mata,ta dauki qaramar hand bag dinta ta tsugunna tayi kissing aleena a cheeks dinta.

A kan hanya ita kadai tana driving tana tsara zantukan da zata tunkari abba dasu,wani lokacin takanji abban me sauqi ne akan maama,amma tasan muddin abban ya amince,maama din ma komai zaya zo da sauqin in sha Allah.

Mintuna talatin kacal suka kaita gida,saboda tana tuqin tana duba lokaci,tanason ta saita lokacinta dai dai da sanda zata riski abban yana hutawa.

Baaba habu ne mutum na farko daya fara yi mata barka da zuwa bayan ya dage mata gate din gidan ta wuce zuwa ciki,ya iso gaban motar sanda take fitowa

"Barka da zuwa farar d'iya" qaramin murmushi dake qawata fuskarta qwarai ta saki tana fitowa a motar

"Baba habu,baaba rabi ta koya maka ko?" Murmushin dake dauke da dattijanka yayi

"Sunan ya dace da me shine ai,kedai Allah yayi miki albarka keda sauran 'yan uwanki"

"Ameen ya Allah baba habu,Allah ya qara girma" kamar sauran lokuta,bata fiya wucewa ba tare data yi masa alkhairi ba,tun tasowarta yake cikin gidansu yake kuma musu aiki bisa gaskiya da amana,ko sau daya bata taba jin wani yayi kuka a kansa ba,hakanan baaba rabi,ba kasafai gidansu suke sauya me aiki ba,saboda suma masu aikin idan suka fara,basa barin gidan haka siddan saidai mutuwa ko kuma aure.

Hannu biyu yasa ya karba yana godiya,ba kasafai ta fiyason yawan godiyarsa ba,ko ya dinga sanya hannu bibbiyu idan zai karba abu daga wajenta ba,to amma koda zatayi maganar ma bazai canza ba,ya riga ya saba

"Ameen ameen,baba habu ayi min addu'a" ta fadi tana rufe jakarta

"Kullum cikin yi muku nake,amma a yanzun ma bazan fasa ba,Allah ya tabbatar miki da dukkan alkhairi a rayuwarki"

"Ameen ya hayyu ya qayyumu,na gode sosai" cikin wannan girmamawar da mutuntawar ta nufi entrance na gidan,bakinta dauke da

"La haula wala quwwata illa billahil aliyyul azeem" don taga motar abban nata,hakan kuma ya tabbatar mata yana gidan,koda ya fita to masallaci ne kawai.

Falon nasu ba kowa,ta danja qaramin tsaki,ta tsani wannan loneliness din na gidan sam,shi yasa bata cike sati guda a gidan,kwanaki taji maama tana batun zuwa nijer cikin 'yan uwa ta dauko yara biyu mata,batasan inda zancan ya kwana ba har yanzu.

Dakinta ta duba don sanar mata da isowarta amma bata risketa a can ba,saita zarce kitchen tana tafe tana yaba tsafta da kulawar da gidan nasu yake samu,wannan ya sanya ta taso da dabi'a ta masifar tsafta qwarai.

Sallamarta ya sanyata waiwayowa sanda take juye tea a flask

"Daga ina da daren nan?"

"Gidan ya muhyi" ta fadi tana zagayowa ta rungumeta ta baya

"Yau kuma?,sakeni to kada na qone"

"Da kin barta ai hajiya,auta ce fa" cewar lariya me aikinsu

"Wannan gansamar?" Ta fadi dai dai sanda sãahar din ta zagayo ta karbe qaramar rariya da cup din da take tace shayin taci gaba da aikin

"Amma na hanaki tafiyar dare irin haka ko?,abbanku ma kuma bayaso"

"Za'a kiyaye in sha Allah maama"

"To Allah yayi albarka"

"Ameen maama na". Tsaf ta gama hada mata komai sannan suka fito tare bayan taji abban yana masallaci,ita tayi dakinta ita kuma ta wuce sassan abban.

Kayan jikinta ta fidda,ta shiga wanka,ta wanke jikinta da kyau da ruwa me dumi sosai,sai data fara yin sallar isha'i sannan ta shirya cikin riga d wando masu laushi,rigar ta kawo mata har cinya me gajeran hannu,sai wandon shima daya saukar mata har qasa,ta kama gashinta ta hade da pink ribbom sannan ta shafe jikinta da lallausan turarenta. Wani kyau tayi sosai,kayan sun karbeta kamar bana barci ba,idan ka ganta a lokacin zata dauka duka duka shekarunta sha takwas ne zuwa sha tara. Remote din ac ta dauka ta rage qarfinta,ta ajjiye saman bedside table sannan ta dauki hijab dinta me hannu ta saka,ta zira slippers dinta ta fito daga dakin.

Tana takawa qirjinta yana dukan uku uku,addu'o'i fal bakinta,daga jiya zuwa yau ta wani mugun damuwa da aikin,damuwar da ita kanta takanji mamaki,batasan dalili ba,tafi danganta hakan da abubuwa biyu,neman mafaka da kuma tausayin yarinyar da ya sauka tun daga saman zuciyarta har ciki tun jiya.

Da sallama ta shiga parlor din abba,ya amsa mata yana dauke dubansa daga kan zain dake zaune a gabansa ya mayar kanta,ta qaraso cikin nutsuwa tana zama a gefansu. Abban ta fara gaidawa sannan ya zain,sai ta karbi maama dake qoqarin serving nasu abinci ta fara zuba musu,data kammala sai ta koma gefe ta lafe kawai,hankalinta yana rabuwa gida biyu, rabi a hirarsu,rabi kuma tana tauna yadda maganar zata fita a bakinta

"Yadai ummin abba?,akwai labari?" Dr mamman ya fada sanda ya gama tauna lomar abincin dake bakinsa,murmushi ta saki,tayi qas da kanta tana murza yatsunta

"Babu abba"

"Ban yarda ba,bari mu gama cin abincin tukunna" ba abun mamaki bane sam don ya fahimci damuwarta lokaci daya,shi din wani irin mutum ne daya samar da shaquwa da sabo sosai tsakaninsa da iyalinsa,akwai fahimtar juna da kuma sakin fuskar da bai haifar da raini ko rashin girmamawa ba a tsakaninsu ba.

Ba jimawa zain yayi musu sallama ya wuce,falon ya zama daga ita sai abban,don maama ma ta wuce bedroom dinsa tana sanya turaren wuta,wanda hakan din dabi'arta ce,duk da ko yaushe gidan ma gaba daya cikin turare yake,amma muddin abban yana gab da kwanciya sai ta kunna burner ta saka wani turaren,wanda yawanci yana riqe dakin har zuwa safiya,a gurinta sãahar ta koyi wannan,yana qarawa bacci dadi da armashi sosai.

"Ummi na,ma yake faruwa?,kada kiji nauyina,ki gayamin" sake takurewa tayi kadan tana jin fargaba,ta saci kallon abban,abinda ya alamta masa da gaske akwai magana me muhimmanci da takeson gaya masa

"Ehmmm,ina jinki ummi na"

"Abba....." Sai ta kasa ci gaba

"Ina jinki,fell free mana ummi"

"Abba don Allah wata alfarma nazo nema,wadda nake da tabbacin indai ka amince tafi dukkan wani aiki da zanyi kyau da samun lada me tarin yawa,abba.....inason ka saurareni,sannan kayimin alfarma"

"Ina jinki" ya fada yana tattara hankalinsa a kanta.


Page 59

*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔

Page 59

"na samu aiki abba.....amma ba irin aikin da kuke tunani zanyi ba,aiki ne na kula da mara lafiya"

"Kula da mara lafiya kuma?" Ya tambayeta cikin mamaki,kai ta jinjina

"Banda abinki ummi,ai ba sai kinyi da kanki ba,idan kikayi bayani,sai na biya a daukowa mara lafiyan me kula dashi har zuwa sanda Allah zai bashi lafiya" kai ta girgiza alamun a'ah

"Ba jinya bace ta kullum kullum da ake kwance ba,abba yarinya ce marainiya,wadda take fama da epilepsy,tana buqatar kulawa ta wasu watanni daga gurin tsayayyar nanny da zata iya kulawa da ita da kyau"

"Ikon Allah" kawai dr mamman ya fada,ya gyara zamansa yana kallon sãahar din,abinda ya bata damar dorawa

"Zanyi aikin nan abba idan lamuncemin,bawai don neman kudi ba,sabida babu abinda na rasa daga wajenku,zanyi ne kadai saboda kwadayin lada wajen Allah,wanda na tabbatar hatta ku zakuyi tarayya a cikinsa,don Allah abba ka lamuncemin,haka kawai na tsinci kaina cikin kwadayin wannan ladan" kai ya gyada,maganarta gaskiya ne,saidai abun ya masa banbarakwai,diyarsa da aikin nanny a wani gidan?.

"Duk maganarki haka take,to amma banda abun ummin abba,ko biya kikayi akayi kina da wannan ladar ai" zamanta ta gyara

"Abba suna da wadatar da zasu iya biyan kowanne mutum,amma kudi basa iya taba siyan nagarta da cancanta" kai ya jinjina cikin dogon nazari

"Abba bazan jima ba,tana samun lafiya shikenan" ta yanke masa tunaninsa ta hanyar fadin haka. Dole murmushi ya kubce masa saboda yadda tayi maganar cikin kwantar da murya tana langabe kai,da alama da gaske har cikin zuciyarta takeson tayi aikin.

"Shikenan,kiban address,zan sa fahad ya yimin bincike akan nagartar mutanen gidan,don bazan bawa wani cikin yayyenki bama"

"Kana iya tambayar anty farheen,ita ta fara bincikawa ma, neighbors na qawarta ne,kuma Alhmdlh basu da matsala,shi yasa aikin ya sake kwanta min a raina" fadin farheen din ya sake sanyawa hankalinsa ya dan kwanta

"Zan nemeki" ta miqe tayi masa sai da safe ta wuce sashensu.

Washegari da safe taga sauyin fuska daga wajen maama,sai tasha jinin jikinta,abban yana fita kuwa ta kirata,sababi ta fara tare da gaya mata itakam bataga dalilin wannan aikin ba,sosai ta kwantar da kai tana kwatanta mata amma maama tayi biris. Wuni guda ana abu daya har dare,shima abban ya gaza shawo kanta,sai da tayi kiran afifa. Itama afifan qin zuwa tayi da farko,ko da tazo dinma sai ta hadasu duka ta fatattakesu,daga bisani afifan tabi bayan maama,batasan ya suka qarke ba,tadai shigo tana harararta

"Burinki ya cika new nanny" murmushi me kyau ya subucewa fuskarta,yadda tayi maganar ya tabbatar mata da ta shawo mata kan maama,saita rungumeta tana cewa

"Allah ya barmin bestie na" murmushi itama ta saka

"Ba wani dadin baki fa,bawai ance kije ki manta da mahmud ba" baya taja tana hade rai,afifa ta bita da kallo tana jan qwafa,itadai batasan sai yaushe sãahar zata dauka daga kan wannan aqidar ba,tana addu'ar Allah ya kawo mutumin da zai sauya wannan tsattsauran ra'ayin nata.

*****Cikin takun nan nasa me cike da tsantsar qasaita da kuma wani irin aji suke nufar sassan hajiya qarama. Sanye yake da yadin baby cashmere me tsada dan qasar indai,wanda aka tsarawa wani irin dinki shi ba dinkin suit ba hakanan ba style na Pakistan ba,sosai dinkin ya qara masa kyau da kwarjini,ya kuma fidda qirar jikinsa qwarai dake dauke da siffar qarfi,duk inda ya gifta sai ya bada ajiyar sassanyan qamshin turarensa me masifar tsada daya sanya qamshin baya bajewa da wuri. Hnunsa riqe da siririn hannun fadeelan suke takawa zuwa sassan momy qarama,daga kan fuskarta har idanunta shabe shabe suke da hawaye,wanda rabi na shagwaba ne,rabi kuma tana ji har cikin zuciyarta yadda zatayi kewar mahaifin nata. Qasa qasa yake magana da ita tamkar wata babba

"Calm down my angel,ipad dinki na wajen momy qarama,nayi alqawarin kiranki kullum through video calls,i will do my very best na dawo da wuri,new nanny dinki na nan zuwa" kafada ta maqale tana zirara da hawaye

"Nikam banason wata nanny kuma,kai zanbi" murmushi ya saki saman miskilar fuskarnan tasa,sai ya sanya hannuwansa ya dagata ya azata zuwa kafadarsa yana ci gaba da takawa hadi da lallashinta cikin hikima. Duk duniya ita daya yake iya tsaiwa ya lallasa haka,banda a kanta,baisan koda hanyar yadda ake rarrashi ba.

Suna shiga falon momy qarama na fitowa daga kitchen,hannunta riqe da mug dake cike da tea

"Badai har ka fito ba?" Agogonsa ya duba yana amsata

"Am ready to go,banason na wuce haka kada nayi missing flight"

"Gaskiya ne" ta fada tana neman wajen zama,sai shima ya zauna saman daya daga cikin qawatattun kujerun dake falon

"Na sanya jibril yayi magana da mutanen can,za'a kawo food stuff,idan akwai abinda babu ki gaya musu kawai,zan saka elyas yayi transfer ta account dinki,naki ne keda fadeela,shikenan koda wani abu?" Qasaitaccen murmushi ta saki,a duniya idan akwai wadda ta shigo rayuwa a sa'a to tana cikin sahun farko na jerin wadan nan matan,tana jin dadi,kanta kuma yana sake fasuwa a duk sanda toufeeq ke treating nata haka

"Eh to,batun nanny din fadeela ne,yau in sha Allah zatazo,wannan karon ina saka ran an samu wadda zata iya kula mana da fadeelan in sha Allah,duk da naso ka ganta kafin ka wuce" miqewa tsaye yayi

"Ba damuwa,indai tayi miki fine,just ta kula da aikinta shine abun buqata,and then ta fadi nawa takeson salary dinta,every month ko qasa da haka,duk ba damuwa indai zata kula da qa'idoji da sharuda"

"Karka damu in sha Allah" tare suka sake fita da fadeelan,still tana maqale dashi. Kuka ta saka masa sosai security dinsa ya buda masa motar ya shiga,sai da yasa akayi kiean baaba ramatu,da wayau da dabara ta rabata da gurin tana kuka.

Har suka fita a gidan yana jin sautin kukanta cikin kwanyarsa,ya lumshe manyan idanunsa da suka sauya launi saboda wani bacin rai daya sokeshi,sannan ya budesu sosai yana jin wani ciwo cikin ransa,sam wannan ba itace kalar rayuwar daya tsarama kansa da kuma 'ya'yan da zaya haifa ba,wannan din wata bahaguwar rayuwa ce da qaddara ta tsago da ita cikin nasa shirin da tsarin ta kuma wargaza komai

"AMEESHA" sunan da bazai taba gogewa cikin tarihin rayuwarsa ba,koda ace ya fita daga zuciyarsa da dukkan wani abu daya danganceshi. Cikin hanzari ya watsar da tunanin,ta hanyar ciro wayarsa ya laluba wata number da yayi alqawarin kira ya kira din,ya fara amsa wayar cikin wani irin sanyi bayan ya maida bayansa yayi relaxing a jikin kujerar.

Koda ya gama wayar shuru yayi yana juya wayar a hannunsa,kamar wanda take sabuwa ga idanunsa ranar ya fara saninta,yau din gaba daya duk wanda ya kalleshi yasan yanayin komai ne cikin sanyi,yanayin da sam bashi a halittarshi.

Tsaiwar motocin ya janye hankalinsa,ya daga kan nasa yana duban driver dinsa

"What's happening?"

"I don't know sir,but.... lemme check" ya fada,sai driver din ya bude ya fita ya barshi shi da guard dinsa guda daya dake zaune a gaban motar.

Ko minti uku baiyi ba ya dawo da gaggawa

"An samu matsala sir,harith ne ya bige wani tsoho......"

"Ya salam" ya furta da sauri,ba tare da ya bari ya kammala bayaninsa ya bude qofar motar da kanshi ya sanya qafafunsa ya fito wajen,cikin sakanni guard dinnasa dukka suka fito suka take bayansa.

Har a sannan tsohon yana zaune a qasa yanata bala'i,harith din da wadanda suke mota daya suna tsaye a kansa. Tsawa daya ya daka musu cikin bacin rai dukkansu sukaja baya suna sunkuyar da kai,ya ratsa ya tsakaninsu ya isa gaban tsohon,ya duqa zai dagoshi suka matso da nufin karbarsa,ya daga musu hannu alamun dakatarwa,ya tsugunna gaban tsohon bayan ya tadashi sosai.

"Kayi haquri baaba,am very sorry,bada niyya bane na tabbatar,amma kayi mana afuwa gaba daya" dukka wani fushi da fada daga dattijon sai ya sauka,saidai idanunsa suna zube cikin na toufeeq din yana kallonsa,ya saki ajiyar zuciya

"Shikenan,ba komai"

"Ina fata baiji maka ciwo ba ko?" Ya sake fada yana kamashi ya miqar dashi ya tayar dashi tsaye yana kade masa jiki,cikin matuqar martaba da mutuntawa,duk da alamu da suka nuna babu wani sukunin rayuwa me yawa tattare da tsohon

"Ba komai yaro,banji ciwo na,buguwa ce kadan a hannu na"

"Dole a dubaka kada ya zame maka matsala baaba" cancel din mota daya yayi cikin jerin gwanon motocin,yace su miqashi asibiti a dubashi,sannan su kaishi ga iyalinsa, yayi kiran elyas da hannu,y qaraso cikin girmamawa,ya gaya masa abinda yake da buqatar a bawa tsohon

"Okay sir" ya fada a ladabce.

"Yaro!" Yaji muryar tsohon ta kirashi dai dai sanda yake shirin saka qafafunsa a motar,ya tsaya cak ya waiwaya yana dubansa

"Ban taba tsammanin mutum me arziqi har haka zai iya tsaiwa ya saurari talakan da bai mallaki komai kamata ba,na gode qwarai da karamcinka,a duk lokacin da kaji tasowar fushi daga zuciyarka,ka yawaita ambaton A'UZUBILLAHI MINASH SHAIDANIR RAJIM, HASBUNALLAHU LA ILAHA ILLA HUWA ALAIHI TAWAKKALTU WA HUWA RABBUL ARSHIL AZEEM" Shuru toufeeq yayi yana kallonsa har ya shige motar harith ya rufe,ya zagaya ya tayar da motar

"Sir..... it's getting late,we should leave" jikinsa a wani irin mace ya shiga motar yana maimaita kalmomin da dattijon ya gaya masa,daidai sanda jibril ya rufe qofar kira ya shigo wayarsa

"Maji" sunan daya bayyana kenan wanda furtasa ya hade masa da faduwar gaban da baisan dalilin saukarta ba.

Tattaro dukka nutsuwarsa yayi sanda motar ke dagawa ta dauki hanya sosai,cikin muryar da ita daya duk duniya yakewa magana da ita,duk da baisan hakan yana faruwa ba yayi mata sallama,sannan ya gaidata,ta amsa masa da wani irin kulawa

"Ina fadeela tah?" Ta tambayeshi a sanyaye. Wani nauyi yaji ya saukar masa,ya shirya yana hanyar barin qasar,tun da bai shaida mata ba sai a yanzu?,a yanzun ma da itace tayi kiranshi?,yaya zataji idan ya gaya mata hakan?

"Ko baka gida nayi kira da layin da zan sameta?" Ta jefa masa tambayar. Sosai nauyi ya sake kamashi,ya sani tana da wancan layin na baaba ramatu,to amma takan tsallake kowa

Please Login or Register in order to submit comment