Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 43 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nasa,baisan yadda akayi ba suka sauka saman fuskarta.
Tsaf ta gama fahimtar manufarsa ta soke tafiyar,koda baiyi hakan ba ita sai tasan yadda ta bulowa maganar ta rushe,don ko dogon zama ba zata iya yi dashi ba bare doguwar tafiya ta satittika,idan kowa baisan me ya dawo da ita gidan ba,ita da shi duka sai sun sani. Cikin jikinta tai idanun nasa saman fuskarta,wani abu ne da ita kanta batasan ta yadda yake faruwa ba,a duk sanda yake kallonta sai taji a jikinta,tun haduwarsu ta farko. Nata kewayayyun idanun masu cikar eye lashes ta daga,sai suka hadu guri daya da nasa,sai ya basar yana shirin kau da kallonsa,saidai kuma hararar data watsa masa ya sanyashi kasa aiwatar da hakan. Take ransa ya sosu,mamaki kuma ya cikashi. Ita ba abinda ta iya daga tsaki sai harara?,me yasa ta maidashi kamar sa'anta,da gaske dai ya fuskanci sai yayi maganinta ya saita zamanta.
Tarko ya sanya mata da idanun nasa,saidai tunda ta harareshin bata sake waiwayowa sashensa ba,hasalima ta maida hankalinta kan maji dake magana da ita qasa qasa.

Migewa yayi cikin nutsuwar nan tasa yana ware hannun rigarsa da nufin fita yabar musu dakin,saboda yadda maji din ke magana da ita kamae bataso yaji ne. knocking qofar akayi,maji dake gab da säahar wadda kanta ke a sunkuye tace

"A shigo" A hankali aka murda handle din gofar aka turo aka shigo tare da sallama.

Ba maji kawai ba,hatta toufeeq yayi mamaki qwarai da ganin mahaifinsa dr mahmud kai tsaye cikin dakin. Tsakanin toufeeq da sãahar ne kadai aka amsa sallamar banda maji da ta dauke kanta gefe kamar bata ga shigowarsa ba,ta kuma tsuke fuskarta,wannan kyakkyawan murmushin dake saman fuskarta ya bace bat. Sanye yake da wani irin yadin cashmere da aka yiwa dinkin manya,riga da wando 'yar ciki me dogon hannu,sai wata a sama kamar gown ta maza me gajeran hannu
Tun daga rigar cikin wandon da kuma gown din aikin hannu na sarauta aka zauna aka zuba masa me matugar daukan hankali da masifar tsada,saman kansa hular dara ce maroon color. Ya sake fitowa sak mahmud din data sani shekarun baya da suka shude,matashin saurayin da ya zuba tashen kyau da farinjinin
'yammata wanda take da imanin a yanzu shi toufeeq ya debo,abu daya ya dakushe wannan a wancan lokacin,akwai wadatar kunya me tarin yawa ga 'yammatan wancan qarnin ba kamar yanzu ba.

Gurin zama toufeeq ke gyara masa,amma dukka idanunsa da hankalinsa suna kan majin,wadda ita dinma babu abinda ya sauya daga gareta tsahon shekaru ashirin da bakwai da suka shude sai shekaru kawai da suka dan nuna kansu kadan.


* HAJIVA OARAMA_*


Tunda gari ya waye bata zauna ba,sai data tabbatar an kammala shirya breakfast na alfarma a babban dining din dake sassanta,bayan an kimtsa ko ina ta tabbatar komai yayi yadda ya kamata sannan ta shiga wanka ta shirya kanta cikin wani Swarovski lace dake ta fidda walwalin Swarovski crystal dake manne a kowanne pattern na lace din.


Ta riga ta sani ma,koda bata fadi ba kamar wancan auren nasa,a nan zasuyi breakfast shida matarsa kafin ya shiga kowanne sashe na gidan,don haka ta shirya ta koma falo ta dauki wayarta tare da saka me aikinta ta canza mata channel tanata dakon shigowarsu. Tun tana chart a wayarta don rage lokaci har ta gama lissafe lissafenta ta maida hankalinta ga tv tana dan bibiyar program din da akeyi din.
Sannu sannu ta fahimci lokaci yana tafiya,ta duba wayarta ko zata ga kiran toufeeq amma babu komai,mamaki yadan kamata,to me yake faruwa? aure dai ba na soyayya bane bare tace itace ta hanasu fitowa. Zuciyarta nata yi mata kokwanto ko yana wajen uwarshi?to amma batajin hakan zata faru,saboda sam babu wannan sabon a tsakaninsu,hasalima yaushe rabonsa da ita da har zai iya wuceta ita ya tafi gurinta? har ta dauki wayar zata kira taji alamun bude gate din gidan,dai dai shigowar 'yar aikinta,sai ta maida dubanta kanta

"Waye ya shigo?"

"Boss ne" ta amsa mata cikin girma mawa,maida wayar tayi ta ajiye ta fasa kiran toufeeq din,don tayi amanna nan din Dr jarman zai fara shigowa,kuma dole toufeeq din ya biyoshi.

Duk bayan minti daya sai ta kalli agogo amma bataji shigowar yayan nata ba kamar yadda ya saba yi a duk sanda ya kawo ziyara gidan,duk da cewa abune mawuyaci ka ganshi a gidan. Zuwa lokacin haqurinta ya gaza,ta kasa jurewa,sal ta miqe tsaye tana gyara daurin dankwalinta hadi da qwalawa me aikinta kira tace ta rigo mata wayarta ta biyota da ita.

Tabbas Dr jarma ne ya shigo,don ga galla gallan motocinsa da vake amfani dasu nan guda hudun a fake a parking lot na gidan.

Abun ya sake daure mata kaita maida dubanta ga sassansu fadeela. Gabanta ne taji yadan fadi,saboda jikinta ya gama bata yana can,don son tabbatarwa saita nufi sashen kawai kai tsaye.

A parlor din farko ta samu baaba ramatu tana qarasa kintsa dan abinda bai gama gyaruwa ba a sashen, kasancewar yadda tsafta ta ratsa kowa cikin gidan harta da ma'aikata maza da mata,basa barin koda tsinke a waje bare qura

"Yaaya ya shigo?" Ta tambayi baaba ramatu kai tsaye

"Eh suna ciki"

"Shi da wa?" Ta tambayeta fuskarta adan
yamutse

"Toufeeq amarya da alhaji sai hajiya maji"

"Danqari" ta furta har yana furucin nata yana fitowa fili. Daga kai baaba ramatu tayi ta kalleta,suka hada ido,sai hajiya qaraman ta basar kamar ba ita tayi maganar ba,ta sanya kai ga hanyar da zata kaita qaramin falon sassan gidan wanda daga can sai hallway na bedrooms dinsu. Kai baaba ramatu ta girgiza

"Allah ya kyauta" ta furta qasa qasa taci gaba da aikinta, zuciyarta cike fal da mamakin dabi'un fauziyyan da har yau suka gaza sauyawa.
Ganin idanun TOUFEEQ da sãahar dake a mazaunin suruka yanzu a gurinta shine kadai abinda ya sanya ta gaidashi da harshen larabci a taqaice,kamar yadda suka saba shekarun baya da suka shude. Wannan abunne yayi masa mugun fami hadi da tuna masa wani lokaci can baya. Majin ta mige zata fice tana
cewa "'dan kun gama Khadija ki sameni a falo mu qarasa ko?"

"Da kinyi haquri kin koma kin zauna akwai maganar da zamuyi" Dr jarma din ya fada a tausashe,wanda shi kansa baisan da haka yayi maganar ba. Cak hajiya qarama ta tsaya tana jin qirjinta yana bugun uku uku,sautin da yayanta yayi magana da maji din a yanzu,wani tsohon sauti ne da yake mata amfani dashi a shekarun baya idan yana son lallashinta.
Wai meye yake faruwa ne?,sannan wacce magana ce da yau yayan nata ya hada iyalinsa,harda bare aurowar jiya amma ita babu ita aciki? koma meye za'a tattauna din ba zata iya Jurewa a tattauna ba tare da ita ba. Sai data dorawa fuskarta fara'ar dole sannan ta buda qofar dakin hade da yin sallama. Maii itace ta farko da idanunsu suka fara haduwa waje daya. Dauke kai maji din tayi kamar yadda ta yiwa dr jarma din da a yanxun ma ya samu nasarar dawo da ita ya zaunar duk saboda idanun mutum biyun dai,toufeeq da SÄAHAR
Sam bata ko gaunar jin muryar fauziyya a rayuwarta bare ganin gilmawarta,itace silar da har yanzu take zaune ba tare da wata gagarumar katangar dake qara cikasa daraja da kimar diya mace ba wato AURE,ko tuna abubuwan da fauziyya tayi mata a rayuwa batason yi,amma duk da haka tana godiya ga
Allah da ya bata wasu damarmakin,duk da wasu sun subuce mata,amma still har yanzu tana rige da lambar mutum ta farko data zamewa fauzivya qadangaren bakin tulu,tsare tsarenta suketa tafiyar wahainiya,wasunsu ma su gurgunce ba tare da sun cimma gaci ba

"Ashe duk kuna nan,abun na ahali ne,ko mu koma?" Ta fada da sigar tambaya.

"A'ah,qaraso mana,you are the part of duk tattaunawar da za'a yi din" dr jarma ha fada yana fidda gyara zamansa,har yanzu idonsa na kan maji din wadda ta baiwa banza ajiyarsu shida 'yaruwar tasa.

Guri ta samu ta zauna a tsakaninsu,a sanann majin ji tayi kamar ta miqe ta fice a wajen,to amma kuma yin hakan kamar bada qofa ne ga fauziyya,so far kuma ita din tana jin a shirye take akan sake maido yaranta ilkinta,wanann na daya daga cikin boyayyun dalilan da yasa batabi ayarin family dinta da sukazo biki sun koma tare ba.

Kamar yadda suka saba toufeeq ya gaidata,tayi gogarin gagaro murmushi

"'Lafiya lau ango,idonka kenan?" Gaisuwar da sãahar ta migo ita ta katse tuhumar da take masa ta sigar tambaya a fakaice. Wani irin shu'umin kallo tayi mata,tadan kada qafarta kadan

"Amarsu,lafiya ya kwanan baqunta?,koda yake
ma ai 'yar gida ce na manta" ta furta tana sakin wani murmushi me dauke da ma'anoni da dama,gasan ranta kuma zuciyarta ke
sake cika da alwashi da algawura iri iri akan sãahar din,sai ta biya baqincikin da ta sanya ta kwana dashi a jiya sanadiyyar maida mata maaganganun da tayi. Maida dubanta tayi ga
yayan nata Dr jarma tana gaidashi.

*HUGUMA*


* TABARMAR KASHI_

Book 02Page 17

Amsa mata yayi yana tambayarta hidimar da aka qare jiya

"Alhamdulillah, duk da wata tana tafe in sha
Allah nan kusa,saura kwanaki shida kacal meenal ta dawo,karatu ya qare sai aure in sha Allah" tayi maganar tana murmushi,kai dr mahmud ya jinjina

"To Allah ya zaba abinda yafi alkhairi"

"Ameen ameen,tuwona mai na in sha Allah" da kyau sagon ya isa kunnuwan maji,sai ta saki wani qaramin murmushi tana sake juya kanta gefe. Fauziyya ta riga ta makara,tayi makarar da bazata sake yin sammako ba daga nan har illa ma sha Allah,ta rigata isa gaban Allah,ta rigata kuma shiga kotun Allah,ranar yanke hukunci kawai take jira.

Hamdala dr jarma yayi sannan ya fara da yiwa toufeeq nasiha hadi da tunasar dashi nauvin da ya rataya a wuyansa

"Amana ce ita muka karbo maka,sai kayi qoqarin sauke haqqin Allah a wuyanka,duk da cewa ba wai yau ka fara aure ba" shikam gaba daya wa'azin dr jarma mamayarsa kawai yakeyi,duka abubuwan da yake lissafa masa a yanzun kamar an buga masa gudumar mantuwa,sai yanzun da yake masa bita suke dawo masa a kai, gaskiya ya fada,babu yadda za'a yi suyi wasa da Allah,shi kuma aure koda wasa akeyi,koda wasa aka daurashi to ya dauru kenan. Sai yaji lema tana tsatstsafowa daga gaban goshin sa yasa tafin hannunsa ya gogeta. Kan sãahar ya koma,itama yayi mata abida duka zai gayawa nadeeya,sai da ya kammala sannan yace

"Komai na kamfanina ya gama dai daita kamar yadda nake zato sanadin tubalin ginin aikin daku kuka farashi,so saboda haka nayi hiring naku duk da ban tuntubi ra'ayinku ba,zaku je kuyi conclusion na aikin da ku kuka kafa harsashinsa na wata guda,ku tabbatar da gyaruwar komai din,saiku miga ragamar ga sabbin shugabannin da zan nada kuyi tafiyarku,zaka riqe matsayinka na CEO,ke kuma diyata zaki taimaka masa ne a matsayi
PA dinsa saboda ya samu saugi da saurin kammala komai kada na riqeku da yawa a company din,hutun sati biyu kacal gareku na hutun aure kafin ku fara aikin"

Kusan a tare suka kalleshi,sai ya
sakarwa kowannensu murmushi yana gyada kai alamun tabbatarwa. Maida kansu sukayi ba tare da kowa ya iya musa masa ba,saidai ba abinda qirjin sãahar keyi sai bada wani fat fat. Ya tana qogarin nesanta kanta dashi amma al'amura nason sake kawo kusanci a tsakaninsu?

Duk yadda hajiya qarama taso daurewa ta gaza,suyar maganar takeji har tsakiyar zuciyarta,tayi gyaran murya sannan tace

"Amma yaaya, kana ganin hakan ya dace kuwa?,ya zaa yi harka ta dukiyar iyali a dauko bare a sakata a ciki?, next week haseena zata dawo,sai nake ganin ita tafi dacewa da wannan matsayin" sosai zuciyar maji keson maidawa fauziyya martani amma ta dakata taji wace amsa mahmud zai bayar? ya canza ko har yanzu ita ke riqe da akalar steering na rayuwarsa kamar yadda yake faruwa a baya?

Dan qaramin murmushi ya saki sannan
yace

"Banda abinki fauziyya,ya zaa yi mutum ga matarsa ta sunnah kuma da ita aka fara aikin,tasan makamar aikin sosai sannan a ajjiyeshi a hadashi da wadda ba matarsa ba?" Mamaki ya kama haiiya caramar hadi da rudani, dama sãahar din ma'aikaciyar MT JARMA GLOBAL ce?,me ya kawota aiki cikin gidan?,anya anya ba turota akayi ba?,dukka wadan nan abubuwan dake faruwa ba shiri bane ba kuwa?.

"Yaaya,naga tuwona mai na mukeson ayi,hakan ai zai gara musu ma fahimtar juna yadda komai zaizo da sauqi ko?" Ba maji data karanci fauziyya shekaru masu yawa ba take kallonta fes a tafin hannunta ba,hatta dr jarma yayi mamakin yadda take iya furta wannan maganar a gaban saahar,amaryar da kwananta daya tal a gidan miji akewa zancan kawowa kishiya nan da wasu watanni KO satittika?. Toufeeq ne mutum na farko da ya fara miqewa,don ya gaji da jin soki burutsun hajiya qaraman. Ba tun yau ba ta sani shima ya sani,ba kowacce magana tata yake iya bawa muhimmanci ba tun dazun da taketa zubarta baima gama fahimtar inda ta dosa ba sai yanzu,ta barshi yaji da danyan hukuncin da abban ya yanke masa na komawa company har na wata daya,kuma wai shi da yarinyar da ta riga tabar company din a gaban kowa,a yanzun zasu koma shi da ita a mazaunin miji da mata?.
Iska kawai yake furzarwa a bakinsa,ya akayi komai yakeson ya dinga juyewa daga ainihin yadda qwaqwalwarsa ke wassafa masa zai tafi?, matsalar hajiya qarama da dukka maganganunta bai daukesu a bakin komai ba,don ita kanta haseena din da take magana a kanta bai dauketa wata cikakkiyar mace ba bare wani wasan kwaikwayon hajiyan ya tabbata,damuwarsa yanzun yadda yarinvar ke gara kusantoshi cikin lamuransa,ya gama da case din maji na tafiya honey moon ashe wani yana tafe. Qaramin tsaki yaja,sai ya sauya akalarsa zuwa dakin fadeela ya dubata,yana jin baccin da akace tana yi din yayi yawa,yasan ba kasafai ta fiya baccin safe ba.
Baice da kowa komai ba ya taka a hankali ya fice daga dakin,maji ta waiwaya ga sãahar da kunya ta hanata motsawa

"Tashi kibi mijinki kinji, Allah ya yiwa aurenku albarka,ya tsone idon asara da hassada qyashi mugunta d mugun abu". Cikin ranta sai data yiwa maji addu'a sosai data bata damar barin wajen. Ajiyar zuciya me sanyi ta sauke tana lumshe idanunta,tanason ta zauna tayi bitar abubuwan da suka farun amma kanta ya dauki zafi,ba yanzu take da bugatar hakan ba, saita waiwaya sassan dakin fadeela tana duban qofar dakin,qaramin murmushi ta saki,tunda tazo gidan bataga fadeelan ba,tayi kuma kewarta sosai,don ba kadan ba tana jin yarinyar qwaral a zuciyarta,sai ta soma takawa zuwa dakin itama ba tare da tasan yana ciki ba.

Da gaske baccinta take lakadan hankali kwance,da alama tayi nisa sosai kuma tana jin dadin hakan,a tausashe ya zauna daga gefanta ya sanya hannu ya kama hannuwan ta yana kalla,kusan komai nasa ta daukeshi banda kamannin fuska da wani lokacin take yanayinsa,wani lokacin kuma yanayi take da maji. Sake damqe hannun nata yayi a tausashe yana sauke numfashi me zurfi daga hunhunsa,ko meye yake faruwa yanzun da shi ta sanadinta ne,lalurarta jarrabawa ce a gurinsa daya tabbatar akwai abinda Allah ke nufi a gareshi,kuma koma meye yana fatan ya zame masa kaffara da nasarar rayuwa.

Cikin jikinsa yaji alamun an bude gofar,da yake dakin ba wadatar haske nadeeya ta kashe mata kowanne fitila sansa zasu fita sal ya sanya bata hangeshi a gurin ba sam.
Ta gefen idanu yake dubanta sanda take takowa cikin dakin,sassanyan turarenta yana kwararowa tare da cika dakin. Sanda ta ganshi already ta iso tsakiyar dakin,taja ta tsaya dai dai sanda ta mige a nutse,saita juya da nufin fita a dakin,don ba zata iya zama dashi daki guda ba.

Batasan ta ina ya iso ba,batasan yaushe yayi dogon takun da ya rigata isa bakin qofa ba,ta dai ganshi yana maida key din jikin gofar yana kullewa. Batason ta nuna tsoro ko firgita,sai tayi kamar bata ga abinda yakeyi din ba,taci gaba da takawa zuwa bakin qofar,ta
Kama key din zata bude,wanne tudu wanne gangare sai ji tayi an mata wata wawiyar fusga an ajiyeta tsakiyar dakin. Yadda ta tsorata yasa gudun numfashinta ya qaru sosai,ta fidda idanunta waie tana kallonsa sosai sanda yake tsaye a gabanta hannuwansa cikin alihun wandonsa,ya zuba mata narkakkun idanunsa dake cike fal da bacin rai. Qara taku yayi gaba ya fara hade Gap din dake a tsakaninsu,sai ta fara ja da baya tana dubansa cikin zallar mamaki

"Meye haka?,ka bani hanya na wuce" ta fadi ganin ta qure bangon babu kuma sauran inda zata sake goce masa. Kamar da kurma take magana,bai fasa nufota ba yana dubanta da tsimammun idanunsa,miskilar fuskar nan tasa a mugun hade cikin rashin walwala. Idanunta ta mayar ta runtse sanda ya qaraso dab da ita taku daya kacal zaiyi ya hade da ita. Cak ya tsaya yana kallon yadda fuskarta ta soma yin ja,soft lips dinta suke shacking kamar tanason furta wani abu daga dan mitsitsin bakinta na rashin kunya amma tsoron da taji ta kasa fadin komai. Sannu a hankali idanunsa suka sauka kan qirjinta da yake a cike sosai a kuma tsaye,bugun zuciyarta na nuna alamun ya qaru ta yadda qirjin nata yake sama da gasa da sauri,ya lumshe idanunsa saboda yadda dumin numfashinta dake gauraye da qamshin jikinta ke sauka a wuyansa,wani abu yaji kaman ya fusgeshi,sai yayi taku uku baya a hankali yana jin jikinsa yana saki. Irin wannan yanayin ya taba ganinsa sau kusan hudu cikin mafarkinsa,sak kamar irin haka,irin wannan dukiyar fulanin da yasha kai hannu zai taba amma mafarkin ya katse a dai dai wannan lokacin,ko a yanzun sai daya murza hannuwansa dake cikin aljihunsa da kyau,yaja numfashi sosai yana son daidaita kansa,cikin husky voice dinnan tasa dake da wani irin kwarjini yace

"Open your eyes" a hankali ta fara bude idanun nata har ta kammala budesu gaba daya

"Ke wacce irin mara kunya ce?,ban gaya miki banason tsaki ba,kinyimin tsaki kin harareni me navi miki? ni sa'anki ne? ko don na aureki shine garamar qwaqwalwarki take gaya miki yanzun dai dai muke kamar yadda take gaya miki a baya?" Ya jefa mata tambayar yana tsareta da kallon nan nasa me ladabtar da kowa ba tare da yayi magana ba. Kalaman da ya gaya mata sai suka tunzurata,ta danne tsoratar da tayi din ta sake galla masa harara

"Waye yace ka dinga shiga gonata?,ba haka mukayi da kai ba,munyi da kai kowa zaiyi rayuwarsa ne ba yare da ya shiga rayuwar dan uwansa ba..
tunda nazo kagan na.
bata ida garasawa ba saboda wata muguwar ba zata da yayi mata,dumu dumu ta tsinci harshensa cikin tsakiyar bakinta wanda shine ya toshe sauran maganganun da tayi niyyar gaggaya masa. Wani irin zuqa yakewa bakin nata yana hadawa sa lips dinta cikin wani irin salo da zata iya cewa ta mugunta ce kawai.
Cikin sakanni gaba daya kwanyarta ta birkice da tsananin tsoro gami da firgicin abinda yake faruwa din. Kaf rayuwarta babu mutumin data taba hada baki dashi irin haka baki cikin baki,gefe guda kuma yadda labbanta suka dauki radadi ta gama saddaqarwa sun tsage ne kawai. Duk yadda take tunanin zata iya tureshi ta kasa,sai kawai hawayen da suka tarar mata suka budewa kansu da kansu hanya suka fara sauka,danshinsu ya gangaro zuwa kumatunta ya fara taba skin na fuskarsa.

A hankali yaja da baya qafafunsa na wani irin sanyi da laushi,ya kalleta lokacin da take dugewa a waien tana cusa kanta tsakanin gafafunta tana sakin kuka a hankali don kada ta tashi fadeela dake baccinta batasan ma wainar da ake toyawa ba, yatsuntsa biyu saman lips din nata da ko da bata kallesu ba tasan sun tasa sosai

"Idan wancan karon na takeki wannan karon bakin tsiwar zan cinye gaba daya,kuma bani zan hadiye ba karnuka zan sa a kaiwa,as from today karki sake cewa zaki sakamin wata doka taki,nine gaba dake so nine me sanya kowacce doka nayi niyya,ko zaman dadiro nake da mace bata isa ta kafamin doka ba bare sadakina na biya,ki aje a ranki bazan taba neman komai daga gurinki ba idan ma shi kikewa,don nafi qarfinsa,ko yanzun bakina da kika lasa saikin biya hakan" daga wannan ya juya a hankali ya fita a dakin.

"HUGUMA*


* TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 18

Hawaye sosai takeyi tana shafa labban nata da suke mata zugi, anya ba baki afifa tayi mata ba? ‚idan ba haka ba me yasa yake mata kwarjini har haka?
"Martabar aure" amsar da zucivarta ta sake nanata mata kenan kamar yadda afifa ta gaya mata. Motsin fadee ne ya sanyata saurin share fuskarta da daidaita kanta. Ai tana hada idanu da sãahar din ta wantsalo gaba daya daga saman gadon ta qanqameta tana kiran

"Anty N,good morning" rungumeta itama tayi sosai cikin jikinta,a hankali takejin wani farinciki, bacin ran dake lullube a zuciyarta ya dinga zagwanyewa. Sun jima a haka sannan ta dagata tana kallonta

"Chubby fadeela ina wanka?" Kai ta langabe a shagwabe

"Sai kinzo ke zakiyimin" dariya tadan saki

"Kin fara girma fa,muje na gani" sai ta riqe hannunta suka wuce toilet din.

Sanda suka fito tana tsane mata jikinta aka tura gofar aka shigo. Baaba ramatu ce suna hada ido da sãahar ta tambayeta

"Ya akayi baaba" dab da ita ta iso, ta dan waiwaya ta kalli bakin gofa ta tabbatar a rufe take sannan ta warware bakin zaninta, wata leda ta ciro tayi saurin migawa sahar,sai sãahar din tasa hannu ta karba tana jinjina kai

"Kome ya tafi dai dai, tun bayan tafiyarki wannan magungunan take sha, ina lissafawa a cikin wadancan ina cirewa ina zubarwa kamar vadda kika kwatanta min, amma an samu matsala daga dawowar hajiya" baaba ramatu ta fada fuskarta tana canzawa, tadan sharce gumi, sãahar ta zuba mata ido gabanta yana faduwa

"Matsalar me baaba?"

"Daga dawowar matar nan da kanta take sanya fadeela a gaba da magungunan nan,yau kwana biyu nata take bata tana sha,duk wata hanya da zanbi na kauda afkuwar hakan wallahi nayi amma baiyuwu ba" baaba ramatu ta fada hawaye yana cika mata ido, tana jin bacin rai har cikin ranta na vadda tsahon shekaru tana zaune ana wasu abubuwan amma rashin ilimin zamani yasa bata fahimta. Sosai säahar taji hankalinta yayi mugun tashi,ta dinga jinjina kai tana jin tsohon bacin ranta yana motsawa, a lokacin ta'addancin da adam yayi mata sa qwayoyin magani ne suka dinga dawo mata, ba zata bari ba kuwa haka ya faru tare da innocent fadeela ba

"Zan yiwa tufkar hanci" ta fada a sarari, cikin zuciyarta tana jin zatayi amfani da nata power din da take dashi a yanzu na matar uban fadeela, duk da bawai tana tutiya da wannan matsayin bane.

Kwanaki biyun da maji ta qara cikin gidan säahar gurinta take wuni, tun daga ranar basu kuma haduwa da toufeeq ba saidai a wajen maji,idan ya shigo din ba wani dogon zama yakeyi ba,sosai ta fuskanci abubuwa da yawa,kamar rashin sabo da sakewa tsakaninsa da maji din,duk majin tana bakin qoqarin gain ta jashi a jikinta amma wasu abubuwan basu yiwuwa. Gurinsu maji take yini tare da fadee dinta ga nadeeya,rana ta uku majin ta gama shirin tafiyarta,a safiyar da zasu wuce
airport, dukkansu suna gaban motar da zasu wuce da
rakiyar nadeeya fadeela da toufeeq.

Su libril ke shirya komai,toufeeq din yana sassansa
bai kammala fitowa ba,suna tsaye dukkansu gaban
motar cikin alhinin tafiyar maji,ji sukeyi kamar su hanata
tafiyar, säahar a cikin jiki da zuciyarta takejin babu dadi
qwarai. Hannun säahar maii ta kamo tana murmushi

"Karki damu d'iyata,bazan dauki dogon lokaci ba zan
dawo, dawowar da nake kyautata zaton zan jima ban
koma Algeria ba,akwai kasuwancin da na fara
processing nasa a nan, bana tunanin zan wuce wata uku
ko biyu ma ban dawo ba" wannan albishir din shi yafi
komai faranta ran säahar, ta rige hannun maji sosai tana
murmushi dai dai lokacin da yake takowa zuwa gurin.
Sanye yake da wani baby cashmere da aka yiwa
lafiyayyen dinki wanda yabi jikinsa ya dace da
yanayinsa, ya kuma fitar da structure dinsa sosai yau din
ya saka hula saman kanshi, abinda sãahar din bata taba
gani ba kenan,hakan sai ya sake canza fuskanshi,ya fito
a cikakken shuwa dinsa ya tashi daga launin larabawan
Algeria. Ido suka hada,sai ta janye daga kallonsa tana
hade rai,can gasan ransa ya murmusa a karon farko
bayan da ya karanci wani abu saman fuskarta. Ta kalleshi
ne ba tare da kowa ya tilasta mata ba,amma kuma bayan ya ganta tana kallon nasa sai ranta ya baci tana tuhumar
kanta da kanta. Yau kwana biyu cur bai ganta ba,baisan
a wanne bigire zai sakata ba, amma tuni ya fara karantar
wasu halayen nata,bayan tsiwar da ya samu ya rage mata run randa ya yuwa labbanta wawan kamu,ya fahimci tana kafiya taurin kai da tsaiwa akan ra'ayinta.
Zarmewa idanunsa sukayi da kallon labbanta,sun koma normal,wasu irin soft and tiny lips, masu wani irin pinky color me dan duhu. Idonsa yayi hanzarin daukewa yana lumshe idanunsa tare da budewa duka lokaci guda cikin kaucewa

Please Login or Register in order to submit comment