Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 17 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

haram ce,halal halal ce,Allah yasa mufi qarfin zakatanmu👏🏽👏🏽).

Sau daya tak ya kalleta ya kauda idanunsa,sannan ya gewayeta ya sanya jikinsa zuwa falon

"Sannu da zuwa yaa toufeeq" ta furta tana bin bayansa hadi da binsa da wani mayen kallo,bai amsa mata ba yaci gaba da kutsa kai,masu aikin dake kai kawo a parlor din suka yi masa barka da zuwa sannan suka kauce daga gurin.

"Abban yana samansa" ta fada cikin yauqi da kwarkwasa,wanda sau tari wani lokaci ita kanta batasan hakan tana faruwa ba,tsabar yadda zuciyarta ne ta afu ason samun soyayyarsa.

"Ya toufeeq" ta kira sunansa,waiwayowa yayi ya watsa mata wani irin kallo daya takura zuciyarta guri guda ya sanyata harbawa,saita duqar da kanta qasa tana wasa da yatsunta

"Yaa toufeeq,am sorry for what happened last time,tsautsayi ne in sha Allah hakan bazai sake faruwa ba" qaramin tsaki yaja,yayi gaba ya fara takawa zuwa stairs din dake cikin falon.

Binsa tayi da kallo har ya bacewa ganinta,hannuwanta ta yarfar kamar zata saki kuka,ta tsani wanann miskilancin nasa,yana matuqar dafaata da dagula mata lissafi,sai ta koma ta zauna saman daya daga cikin qayatattun kujerun falon tana dafe da kanta,dai dai sanda daya daga cikin masu aikin gidan ta qaraso cikin rusunawa

"Ranki ya dade,abincin daren,na kammala fa"

"Dalla matsa ki ban guri" ta fada mata cikin tsawa tana jan tsaki

"Allah ya baki haquri" ta fadi tana janye jikinta daga gurin tunda ragowar mutuncinta,tasan tsaf zata iya ci mata zarafi,ta juya ta koma cikin kitchen din,cikin ranta tana Allah ya qara da yadda toufeeq din yake wajiga rayuwarta. Sake daga kai tayi ta dubi stairs din,gurin mommynta takeson zuwa,to amma ta sani,tunda ya iso ko ruwan giya tasha bata isa hawa saman ba har sai ya sauko,saita kwashe qafafunta ta mayar saman kujerar ta kwanta tana dakon fitowarsa,a ranta tana tsara yadda zasu kebe ita dashi ko na minti talatin ne kacal.

Da sallama a bakinsa ya shiga falon bayan dr yayi masa izini,tana duqe tana zuba masa lemo a cup,kakkaurar mace wankan tarwada me tsaho da jiki,wanda kana dubanta zakasan ba hausa fulani bace.

Da fara'a a fuskarta ta dago tana cewa

"Wata sabon gani,kaine yau a gidan namu?" Dan binta yayi kadan da kallo yana mamakin furucinta,A GIDAN NAMU,sai baice mata komai ba,ya taka a nutse ya isa daura da mahaifinsa,kwata kwata baisan me yasa bai taba jin matar ko daukarta da wani daraja ba,duk da tsahon shekarun data kwashe tana amsa sunan MATAR MAHAIFINSA,sannan dai dai da rana daya bata taba gwada masa wani hali ba,amma haka kawai take takenta baiyi masa ba.

"Ina ka baromin kishiyata?" Ta sake fada cikin fadada fara'arta,maimaikon ya amsa mata tambayarta sai ya buge da fadin

"Barka da dare"yayi furucin kamar ba da ita yake ba,yana maida dubansa ga mahaifinsa,cike da kulawa tace

"Barka kadai Muhammad,ya ayyuka,ya akaji da kacaniyar jama'a" ta tambayeshi cikin nuna kulawa.

"Alhamdulillah" ya amsa mata a taqaice,sam bata damu ba,don ta saba da irin wanna halayyar tasa,saita fara kwashe kayan abincin dake gurin tana dubansa

"Me za'a kawo maka?" Kai ya girgiza,baisan sai yaushe zatayi fushi ba ta daina tambayarsa abinda zaici ba duk sanda yazo gidan,bayan tafi kowa sanin baya cin abinci daga hannun kowa kuma a ko ina ba,sai a wasu kebantattun hannuwa da gurare.

"Alhamdulillah,basai na saki hidima ba" murmushi ta kumayi

"A'ah kace dai ba zakaci ba kamar kullum"

"Yi tafiyarki ki rabu dashi,kada Allah yasa yaci din" Dr ahmad ya fada,wanda tunda ya shigo lemonsa yake kurba yana kuma kallon labarai daga NTA network news.


"Zaici ne wataran ai" ta fada da dariyarta tana yin gaba. Sau daya tak kalmar ta shiga kunnensa amma ya gama fahimtar abinda take nufi ba tare da ita tayi zaton zai fahimta din ba.

"Barka da warhaka" ya fada cikin girmamawa,sauke qafafunsa dr ahmad yayi qasa yana ajiye cup din hannunsa gami da bashi amsa duka lokaci guda

"Kai ya kamata a yiwa barka ai,irin wannan aikin da kayi na cin zarafin yarinyar dana nema alfarmar a bani aronta,ka kuma sanya tabar aiki lokaci guda,to kaga kai ka cancanci a yiwa barka" bai barshi yace komai ba dr din ya tsinke da fada,ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba,daga qarshe yace

"Ka ajjiyemin komai daya shafi company dina kaima na sallameka,na gode da iya taimakon daka bani,ka koma bakin taka dukiyar" daga haka ya miqe ya wuce bedroom dinsa yana bar masa falon.

Kasa motsawa yayi daga gurin,yanajin tamkar ya hadiyi zuciya ya mutu,tsahon tasowarsa bayan shudewar matsalolin da suka sanyo kai a rayuwarsu tun zamanin quruciyarsa,bazaice ga lokacin daya zauna yayi masa fada me zafi irin haka ba,sai yanzu?,a dalilin yarinyar?,ya jima a gurin sannan ya miqe a nutse yana sauka qasan,fuskarsa cike fal da fushi da kuma bacin rai,ta zama silar gurbata kyakkyawar alaqar dake tsakaninsa kenan da mahifinsa lokaci guda?.

Suna zaune a falon,hajiya mansura(matar dr ahmad jarma) tare da labiba,ganin yazo zai wucesu ba tare daya kalli kowa a cikinsu ba,kamar ma baisan da zamansu ba hajiya mansura ta magantu

"Harka sauko?,kun gama kenan?" Da so samu ne yayi wucewarsa,to amma ko babu komai ita din mata ce ga mahaifinsa,zata iya cin darajar mahaifin nasa koda qanqani ne

"Eh" ya amsa bayan ya waiwayo yana dubanta hannayensa zube a aljihun rigarsa. Kwarjini ya mata sosai,tadan daburce amma saita maze ta hanyar sakin murmushi

"Ammm,tafiyarku daya da qanwarka,nace ko ta bika saiku tafi tare?" Ido kawai ya lumshe wanda ke nuna ya amsa kenan,ya juya ya fita a falon.

Da mugun gudu ta sauko daga saman kujerar,ko ina na jikinta yana rawa

"Mommy,ki bada kayana gobe usaina ta kaimin"

"Ki tsaya ki tafi da kayarki,goben akwai inda zan aiketa"

"Tsaf zai tafi ya barni idan na tsaya jiran hada kaya" tayi maganar a lokacin ma takai bakin qofa.

Lokacin data isa tuni ya tayar da motar,abinda ya tabbatar mata inda ta qara wasu mintuna saidai tazo ta tarar da wajen wayam. Gaba ta bude zata shiga,cikin kaushin murya yace

"Koma baya!" Jiki a sanyaye ta maida murfin ta rufe,ta koma bayan ta zauna,ranta ba haka yaso ba,taso zaman kusa dashi,ta yadda duk maganar da zatayi masa ta tafi cikin kissa da kuma jan hankali.

"Yaa toufeeq" ta kira sunansa sanda suka dauki hanya sosai

"I don't want to hear anything from you har mu qarasa gida,if not kuma,i will drop you" kallonta ta maida ga titunan da suke wucewar,yadda suka dauki shuru saboda daukewar qafa da ababen hawa sakamakon dare daya fara yi,marufar asirinta yin shurun,don tasan kadan ne daga aikinsa ya sauketan kamar yadda ya furta. Ranta ya quntata sosai,dukka wani plan nata ya rushe,manufar da yasa tacewa Mommy tayi masa magana ya sauketa ma ya tashi a banza.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥






*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
Page 33


Shuru ne ya wanzu cikin motar,sai satar kallonsa da take tayi ta cikin madubin motar a duk sanda zasu gifta wani guri dake da wadatar haske,ji takeyi kamar taje ta rungumeshi tsam tsam ko zata ji sassaucin yadda zuciyarta ke azalzala da qaunarsa,burinta da fatanta a yanzu shine Allah ya mallaka mata toufeeq din kota halin yaya ne ma.

A nasa sashen kuwa hadiyar wani abu ke tauri kawai yakeyi daya tsaya masa a wuya,tabbas ya sake amanna da kaidin mata babba ne,babu abinda ba zasu iya aiwatarwa ba,fada da kalmomin da Dr ya gaggaya masa kawai ke yawo a kunnensa,yayi qwafa can qasa yadan daki sitiyarin motar kadan yana jinjina kai,ji yake dama ya buda idanu ya ganta yanzun a gabansa. Dan qara speed na motar yayi saboda wani faduwar gaba da yaji ya ziyarceshi,wani yanayi ne da yakan samu kansa a ciki muddin wani abu zai afku ga fadeela,sai duka ya samu kansa tunaninsa ya koma gida.

Tun kafi ya kammala parking yace mata ta sauka,ta fidda ido tana ganin yadda motar ke slow bata qarasa tsaiwa ba,saita langabe kai zatayi masa salo

"Yaa toufeeq idan na karye fa?"

"Keep quiet,will you drop ko sai na fiddaki da kaina?" Jin haka ya sanya ba shiri ta tattare ta tsallake,Allah yasa motar a sannan ta kammala tsaiwa, zuciyarta kamar zata fashe saboda baqinciki,batasan me yasa yake tozartata haka ba,tanason tayi zuciya ta kuma yi fushi dashi amma ta kasa,shi din fushinka banza ne,rashinsa banza a wajensa,wannan bacin ran ya sanya tayi wucewarta ba tare data tsaya ta kalli inda baaba ramatu ke zaune ita da fadeela ba,wadda ta damu baaba ramatun ta rakota su fito su jira dad dinta,dole ta taso suka bar nanny dinta a ciki.

Yana fitowa daga motar fadeela din ta miqe da sassarfa tayi gurinsa cikin murnar ganin ya dawo da wuri

"Daddy......dadddd......." Maganar ta kasa fitowa gaba daya,saboda yadda harshenta ya lanqwashe,haruffan suka sarqe cikin na juna,a take kuma kowanne sashe na jikinta ya fara wani irin kakkarwa ta soma lanqwashewa zata kai qasa,kafin takai qasan har ya risketa,ya kuma tallafota ta fada jikinsa ta zube gaba daya,ta fara wata irin jijjiga me qarfin gaske. Duk da cewa ba yau ne ciwonta irin haka ya fara tashi ba,amma har yau har kwanan gobe ya kasa sabawa da irin wannan tashin hankalin da yake tsintar kansa a ciki a duk lokacin da EPILEPSY din fadeela ke fuskanta a rayuwarta ta motsa,komai qwace masa yakeyi,kamar yanzun daya rude gaba daya yana kiran sunanta,wanda zuwa sannan ta zama unconscious.

Tuni baaba ramatu dake qwalla ta kirayi hajiya qarama,ganin dosowarta gurin yasa yayi hanzarin yiwa kansa saiti tare da qoqarin dawowa da kansa dai dai,bai jira isowarsu ba ya dauketa don ya sama mata gurin da zata zama comfortable ya wuce sassansa da ita da wani irin sassarfa yana monitoring numfashinta yadda yake kai kawo yana wani irin riqewa.

Sosai ya kwantar da ita saman lallausar sofa,ya kuma tallafi kanta da pillow me laushi yana kallon numfashinta,a duk sanda take irin wannan abun,sai ya dinga ganin kamar zai rasata,kamar zata tafi ta barshi,hannunsa ya sanya ya juyata barin hannunta na dama don daidaituwar numfashinta da yakeyi kamar zai dauke,yaci gaba da kallonta,yana jin inama ace yana da qarfi ko wata dama da zai iya fidda wannan ciwon daga jikinta?,a ko yaushe saidai ya zauna ya kalleta helpless,har sai ta gama ta dawo hayyacinta.

Maida dubansa ga agogo yayi bayan shudewar wasu mintuna,dai dai sanda hajiya qarama data iso tace

"Ta tashi?" Kai ya girgiza ya jawo wayarsa a gaggauce yana neman number Dr anwar,har yanzu idanunsa nakan agogo yana irga mintunan,bata taba daukar mintuna irin haka ba tare data dawo dai dai ba,abun ya fara daga masa hankali.

Kira daya tak ya daga

"Fadeela ce?" Dr anwar ya fada,saboda layi ne da yasa aka tanadar masa saboda matsala irin wannan

"Gani nan" ya fada kawai

"Kada ka matsa daga inda take,ka barta a right side dinta kaci gaba da monitoring dinta da kuma mintunan"

"Alright" ya fada yana ajjiye wayar da sauri,zuwa lokacin hajiya qarama ta koma kujerar kusa dasu ta zauna,ta hada tagumi hannu bibbiyu tana maimaita kiran sunan Allah cikin nuna tsananin tashin hankali,kauda hankalinsa yayi daga maganganun da takeyi,saboda qara masa tashin hankali da kuma karaya kawai sukeyi. Mintuna biyar kacal Dr anwar ya iso,saboda basu da nisa,layi biyu ne kadai ya rabasu. Shi ya dauketa zuwa clinic na cikin gidan,dab da zasu shiga ta motsa tana bude idanunta a hankali bakinta dauke da sunan

"Daddy" miqa masa ita yayi yace ya qarasa masa da ita ciki,suna hada ido ta saki ajiyar zuciya ta qanqameshi sosai,sai taji zuciyarsa na karyewa,tausayinta da tausayin rayuwarta da kuma tsanar mahaifiyarta data jefata a wannan mummunan yanayin yana sake ratsa kowanne sashe na gangar jikinsa.

Sosai Dr anwar yayi checking dinta don gano abinda yasa jijjigar tata ta dauki lokaci fiye da yadda ta saba,ya ajjiye kayan aikinsa gaba daya yana duban toufeeq,hajiya qarama na zaune daga gefe,baaba ramatu kuma na tsaye daga saman kan fadeelan

"Ya kamata gaskiya a qara ninka kulawar da ake bata,akwai factor's da zasu iya ta'azzara epilepsy din,ta qaru daga adadin mintunan da aka saba yinta" idanunsa da suka sauya launi ya mayar kan baaba ramatu

"Ina fatan nanny dinta tana aikinta?" Dan sunkuyar da kanta tayi,ta fahimci me tambayar tasa take nufi,idan ta bayyana masa gaskiya zai kori yarinyar ne daga bakin aikinta,idan kuma ta boye masa taci amanar mutanen da suka bata yarda,har yanzu batajin yarinyar ta samu kulawa dai dai da wadda Dr anwar ke magana akai,ita din ba komai take iya aiwatarwa ba,kamar kula da magungunan yarinyar da sauran wasu kayan qarin lafiyar,abune na wadanda sukayi karatu,ita kuma bata taba halarta boko ba,iya bakin qoqarinta tanayi wajen kula da fadeela tamkar jikar data fito daga jininta,kowa ya shaida hakan,wasu abubuwan hajiya qaraman ne ya kamata tayisu,to amma ita din ba mazauniya bace,koda mazauniyar ce ma,bata ganin alamun.........

"Ko yaushe ciwon zai iya worsening,me zai hana kayi haquri a jarraba yi mata aiki?" Maganar dr anwar ta katse tunanin baaba rabi. Yayi susa ne a inda yake mata qaiqayi,kullum cikin sallolinta na dare addu'arta tafi qarfi akan ciwon fadeela,Allah ya yanke mata,idan da alkhairi Allah ya fahimtar da mahaifinta mahimmancin aikin nan ayi mata ta huta ta rabu da wannan ciwon,tana matuqar qaunar yarinyar kamar jininta.

"Haba likita?,ya zaka ce haka?"

"Hajiya" baaba ramatu a wannan karon ta sanya baki

"Nima ina ganin abarwa Allah a gwada jarrabawa din,ba'a san inda za'a dace ba"

"Dakata ramatu,ashe baki da hankali kema?" Ta fada cikin fushi

"Ke kinsan ma me ake nufi da yiwa mutum aiki a qwaqwalwa?" Shuru baaba ramatu tayi tana sadda kanta qasa

"Allah ya baki haquri" ta fada a sanyaye tana jin ciwon maganar data yaba mata,shi yasa sai ayi abu dubu cikin gidan bata tofa tata ba,wannan shi ya siya mata kima ya kuma sanya ta dade sosai cikin gidan.

"Relax please" toufeeq dake riqe da hannun fadeela ya fada yana rage girman idonsa,dole hajiya qarama ta koma ta zauna tana huci harda qwafa

"Dr,banason azo ayi abinda zai zama nadama a garemu,kaso mafi rinjaye a aikin nan bashi da tabbas na dawowarta normal,if akayi rashin dace ma abun yana iya qaruwa ko kuma a sake samun wata matsalar bayan ya qarun haka ne?"

"Yes,duka akwai probability na samun hakan"

"Mubar zancan"

"Is ok" kansa ya mayar ga takardar ya sake rubuta mata qarin wasu magungunan ya miqa masa

"Aci gaba da kula da magungunanta da muhallinta,and someone who is very knowledgeable is the one who can takes care of her"

"Thanks" ya furta yana bawa dr anwar din hannu sukayi musabaha sannan yayi musu sallama ya fice.

Matsowa hajiya qarama tayi tana shafa kanta a nutse

"Sannu uktie" daga kai yarinyar tayi ta kalleta,saita sakar mata wani dan malalacin murmushi wanda zai nuna maka jikinta duka ba dadi,qarasowa toufeeq yayi ya bata hannu,ta kama hannunsa ya dagota,ya dauketa cak ya azata a kafadarsa

"Ka bani ita mu wuce sashena ta kwana gurina mana?" Hajiya qarama ta fada

"I can take care of her, don't mind it"

"Okay,ke ramatu,ki tattaro magungunanta ki kawo su,a hado mata da kayan baccinta,ki cewa nanny dinta tazo part dina ta fara mata wanka ta shiryata saina miqo maka ita"

"No,tell her to pack her things,gobe driver ya sauketa a inda aka daukota,she's no longer needed,zan canzata with someone better" yana gama fada ya fara takawa a hankali yana fita daga clinic din,yana jin zuciyarsa kamar zatayi melting down,wani irin yanayi na tsananin kewa da tausayin kawunansu yana tsarga masa.

Shi yayi mata komai kamar yadda yace,ya shiryata cikin fararen kayan bacci masu taushi,ya bata abinci taci,tana ci ta kalleshi da fararen idanunta

"Dad,kaima kaci" kai ya girgiza yana qoqarin sauke murmushi akan fuskarsa

"I can't eat" sai ta bata fuska ta rufe nata bakin,ya fahimci me take nufi don haka yace

"Later angel"

"Sure?" Sai ya gyada mata kai yana lumshe ido.

Ci gaba yayi da kula da ita,har bacci yayi awon gaba da ita,ya zauna a gefanta yana qare mata kallo cike da tausayi,zuciyarsa na gaya masa ya ajjiye komai da komai,ya zauna yayita kula da ita tsahon rayuwarsu.

Qarar wayarsa ta katse masa tunanin daya zurfafa a ciki,yanzun yake shirin kasheta, saboda baya buqatar wata hayaniya kuma,ajiyar zuciya ce ta qwace masa sansa yaga sunan MAJI yana yawo saman screen dinsa,sai ya daga wayar a sanyaye ya kaarata a kunne hadi da yin sallama da muryarsa da tayi laushi qwarai

"Bakayi bacci ba?" Ta tambayeshi bayan sun gaisa da hausarta da ta gauraya da sirkin larabci,cikin wani yanayi na nauyin qirji da kuma tausayi dake can qasan zuciyarta yana cinta

"Yanzu nake shiri"

"Ina fadeela?"

"Tayi bacci" shuru na rashin sabo ya gifta a tsakaninsu sannan tace

"Ka yawaita addu'a tare da miqawa Allah al'amuranka,kana buqatar matar aure ta gari kamar yadda fadeela take buqatar UWA" shuru yayi yana saurarenta,ta saba yi masa wannan maganar dake kama da wasiyya,amma kuma a yaudin tayi masa maganar da bata taba yi masa irinta ba. Shurun da yaji yasa ya gane kiran ya yanke sai kawai ya ajjiye wayar gefe,ya zame daga gefan fadeelan ya kwanta rub da ciki yana sauke idanunsa akan innocent baby face dinta.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥


[8/24, 2:11 PM] KYAUTA: *H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 34


******Tamkar wadda aka yiwa dukan tsiya haka take dawowa cikin dakin,duk wani karsashi data fita dashi babu shi afifa sam bata lura da sauyin yanayinta ba,saboda lokacin da ta dawo din tana amsa waya ne,tana gamawa kuma ta dora mata da hirar da sukeyi dazun kafin ya fita

"Epilepsy duk bahaushen asali yana mata kallon farfadiya,ciwon da aka dangantashi da aljanu,amma kuma mu a likitance ba aikin aljanu bane,aikin daga gazawar qwaqwalwa ne,na gaya miki dalilan dazu da irin yadda akeson a basu kulawa.....yanzu kuma bari kiga w......" Maqale mata maganar tayi,saboda waiwayowa da tayi taga sãahar din dafe da kanta hannu bibbiyu. Da sauri ta ajjiye system din hannunta dake dauke da zanen qwaqwalwa ta nufi sãahar din

"Me yake faruwa?,kin fita lafiya kuma saiki dawomin a haka?" Ta fada tana dafa kafadarta. Kanta ta dago da idanunta da suka cika da qwalla,cikin matuqar sarewa da mutuwar jiki tace

"Inajin kamar na fara gajiya da rayuwar nan"

"Me kuma ya faru haka ana zaune qalau?,ko yaa muhyi dinne?" Kai ta gyada tana sharce qwallar data ziraro mata

"Shine,yana maganar na sake duba akan hukuncin ajjiye aikina,ni kuma wallahi Allah afifa bazan taba iya sake taka kamfanin MT jarma da sunan ma'aikaciya ba,bazan iya daukan cin fuska ko cin kashi daga gurin kowanne d'a namiji ba a yanzu,na fuskanci iya abinda zan iya dauka,ina buqatar nutsuwa,inason nayi nesa daga dukkan wani namiji da abinda ya danganceshi,wai har kun manta da irin abinda na fuskanta ne?" Kai afifa ta girgiza,ta kama hannuwan sãahar din dukka biyun

"Cool down mana bestie,taya zamu manta da wadan nan baqaqen ranakun a rayuwarmu?,yaa muhyi ba cewa yayi ki koma ba lallai,cewa yayi kiyi tunani, kina iya cewa ba zaki iya komawa ba ya baki uzuri,na tabbatar bazai sake cewa komai ba,please kada ki ja ciwon kanki ya tashi,calm down bestie" kai ta jinjina tana jin sassauci natsuwa na saukar mata kadan kadan,sai ta lumshe ido ta dafa hannun afifa

"Thank you for always being with me afifa" murmushi ta saki tana jin tausayi da qaunar 'yar uwarta

"Ba buqatar ki godemin,domin kamar na aikata dole na ne.....yanzu ki kwanta kawai,dare ya farayi,gobe zan qarasa miki bayanin" bata musawa afifan ba,don a yanzun itama ba abinda take buqata irin ta zauna silent ko hayaqin da takeji cikin kanta zai sauka.

Ta kwanta ne kawai ta kuma rufe ido,amma duk wani motsi na afifa tana jinsa,har afifan ta gama abinda zatayi ta rage musu hasken fitilar dakin zuwa kala me duhu ta kwanta.

Cikin duhun dakin idanunta keta walainiya,ba abinda ke gilmawa qwaqwalwata irin abinda ya faru da ita,rayuwarta ta baya data shude kamar zuwa da tafiyar ruwan sama,ta runtse idanunta da kyau tana girgiza kai,saboda bata shirya tuna irin wannan abun ba cikin daren daya fara nisa,saidai duk yadda takai ga toshe tunanin sai daya fara dawo mata da kansa.


*_WACECE SÃAHAR?,ME YA FARU DA ITA?,ku biyoni muje mu gani_*

*NAMIJI tabarmar k'ashi*

Madaidaicin gida ne dake dauke da dakunan bacci manya guda biyu a qasa,da kuma mayalwacin parlor dake dauke da dukkan wani nau'i na kayayyakin da rayuwa ke buqata ga masu qarfi da kuma wadatar abun hannu.

Qawataccen dining area da aka zubawa dining me kyau da daukar idanu na gilashi,da kuma qofar qawataccen kitchen din mamallakiyar gidan, kitchen din daya tara dukkan wani abu daya kamata ace akwaishi ga kitchen din diya mace.

Tun daga manyan hotunan masu gidan dake manne a bango hudu na gidan kadai ya isa ya gaya maka irin gidan daka shigo,hotunane da aka daukesu bisa tsari da burgewa,gogewa da kuma sanin ilimin zamani,hotunan dake fallasa zallar soyayya qauna kulawa da kuma shaquwa tsantsa daga idanun mutanen da siffofinsu ke manne jikin taswirar.

Duk da akwao banbancin siffa da kyau daga barayin mutumin dake jikin hoton zuwa ga matar dake tare dashi,amma wannan bazai zama cikas zuwa ga burgewar da zasu yiwa zuciyarka ba,hakanan bai zama cikas ga bayyanuwar soyayyar dake idanun kowannensu ba.

Komai na falon a kammale yake a tsaftace hakanan a kintse,cikin wata irin tsafta kulawa da kuma sassanyan qamshin dake gauraye da sanyin ac din dake karakina cikin falon da kuma kewayensa,wani irin yanayi daka iya karyar da zuciyar dake da rauni,ya kuma bawa kowacce irin rai nutsuwa da gamsuwa.

Daga saman gidan shima Parlor ne dauke da bedroom guda daya,saidai yafi dukka bedrooms din gidan girma da yalwa,shine kuma yake a mazaunin master bedroom,saidai shi parlor din baikai girman na qasa ba,saidai yana da jan hankali da alatu sosai har kamar ma yaso yafi falon qasan,hakan kuma baya rasa nasaba da kasancewarsa falon me gidan,wanda daga shi sai matarsa ke mu'amalantar sa.

Cikin daya daga cikin bedrooms na gidan,dakin baccin dake da wani irin tsari da aka shiryashi cikin unique colors,qofa guda daya tal dake cikin dakin baccin ta bude a hankali.

Sambaleliyar matashiya ce ta fito,doguwa mai matsakaicin tsaho,murjajjen jikin da ya hana bayyanuwar tsahonta,ya sanya tsahon ya zamana ado a gareta,fara

Please Login or Register in order to submit comment