Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 49 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fita a kitchen din shima.

Sassan nasa babu kowa kamar ko yaushe,bedroom dinsa ya wuce,ya soma zare kayan jikinsa cikin wata muguwar kasala,ya zauna yana zare takalmansa idanunsa suka sauka aka robar maganin.
Hannu yasa ya sake daukota yana juyawa,sai ya maida ya miqe yana dauko system dinsa daga inda ya ajiye ya kunnata,akwai result da zai karba yau game da maganin daga gurin Dr anwar,don haka yabar system din tana daidaita ya wuce toilet don yayi wanka kafin ya fito.

"HUGUMA*


'_TABARMAR KASHI*

Book 02Page 29

Sai da ya gama shiryawa tsaf cikin wasu lausasan pyjamas bagaqe a yau amadadin farare da yafi amfani dasu komai ya zauna luf a jikinsa,yaja stool ya zauna vana duba system dinsa.

Dukka hankalinsa va bayar akan bayanan da Dr anwar ya turo masa. Lokaci daya yaji wani gumi yana tsatstsafo masa,yasa hannunsa a tausashe ya share yana dungule hannunsa ya rufe bakinsa yana tsurawa system din ido

"'Yaya akayi maganin ya kasance daga hannun haliva qarama? me yasa maganin da bai kasance na lalurar fadeelan ba amma take shansa? me hakan ke nufi?" Ya viwa kansa tambayar yana jin hankalinsa yana tashi

"Take it easy" wata zuciyar ta gaya masa

"'Kayi bincike wisely" aka sake nanata masa. Miqewa yayi yana fita a bedroom din nasa a hankali, ya ciro wayarsa da ya bari a parlor ya fara kiran layin nadeeya. Bugu daya ta daga

"Yaa moha"

"Me sunan matar nan baga wata gajeriya me jiki dake aiki a sassan momy?" Dan shuru kadan nadeeya tayi sannan tace

"Ko adama?" Kai ya gyada

"Yes, kiyimin kiranta, amma banason kowa yasan na nemeta"

"To yaaya" ta fadi tana ajiye wayar, saita dubi su sãahar wanda suke zaune zasu fara cin abinci

"Ina zuwa AUNTY N" kai ta gyada mata,saita koma daki ta dauki mayafinta ta fice.

Tun daga yadda ta shiga parlor din zakasan a mugun razane take,ko ina na jikinta rawa yakeyi,gumi kuwa ya gama jiga mata jiki sharkaf. Yau ta shiga masifar da me fiddata sai Allah, dazun nan hajiyan ta gama yi mata kakkausar jan kunne kamar yadda ta saba a duk lokacin da aka karbo maganin, saidai kuma jan kunnen yau din yafi na kullum, kamar tasan abinda ya faru a hanyarta na kawo mata maganin. Da hannu ya yiwa nadeeya nuni akan ta tafi,ba musu ta juya,cikin zuciyarta tana taya adama alhini,ko wanne tsautsayi ne yasa ta shiga gonar toufeeq din? wanne irin laifi tayi masa haka?.

Tun kafin yace ta zauna gafafunta suka kasa daukarta, saita sulale tayi zaman dirshan a gurin. Kallo daya yayi mata ta fashe da kuka, tama mance da wani jan kunne na hajiya qaraman

"Wallahi bansan komai a kai ba indai batun magungunan ne" idanunsa kawai ya zuba mata yana mamakin rudewar da tayi. Sake debo rantsuwa tayi

"Na rantse da ikon Allah bansan komai ba"

“Tun yaushe ake kawo maganin?" Ya jefa mata tambayar
Shekara biyu…shekara biyu a cikin ta uku* ta bashi
amse kowanne sashe na jinta yana kakkarwa. Wani irin zafi idanunsa yaji sun fara yi masa, abinda zuciyarsa ke hasaso masa har bayaso sukai ga kwanyarsa bare ta sauya masa su ga dayan sashen na zuciyar tasa

*ki hada kayanki gaba daya,na sallameki daga aiki a gidan nan" abindia ya fada kenan. Faduwa tayi a gurin tana hurwa tana kuka sosai, saboda tasan muddin tabar aiki a gidan asirinta ya tonu,mutane masu yawan gaske ne suke neman damar yin aiki a gidan amma basu samu ba

Tsawa ya buga mata wanda ta sanya ba shiri ta tattara zaninta ta fice tana kuka. Shuru yayi yana maida jikinsa ga kujerar idanunsa a lumshe

"To maganin meye?" Tambayar da Dr anwar dinma bai bashi amsa ba, yace masa baida alaqa sam da ciwon fadeelan, suna kuma ci gaba da bincike.

"Wanne magani kenan ake bata yanxu?" Tambayar da tazo kansa kenan,ya kuma miqe a nutse ya sanya flip flops slippers dinsa yana baro sashen.

Tuni ta gama cin nata abincin ita da fadeelan, nadeeya ce tayi saura,don haka suka barta a falon suka wuce daki don ta shiryata ta bata maganinta tasha. Toilet ta kaita, kamar ko yaushe yanzu ta fara canza pattern na wankanta, zata hada mata kayan wankan gaba daya,tayi mata tsarki ta wanke mata bayanta da sauran inda hannunta bazai kai ba,sauran kuma saita tsaya tana kallonta tayi da kanta, tanayi tana gyara mata har su kammala. Sanda yayi sallama dakin basuji shi ba,suna bandakin tanata tsokanar fadeelan saboda yau ta dage bayan nata ma zata wanke da kanta.

A nutse ya garasa shigowa,ya maida murfin qofar ya rufe, idanunsa suka sauka akan dressing table din fadeelan inda kayan baccinta maganin nata da sauran tarkacen kayan nata suke.

Kai tsaye ya dauki robar maganin yana dubawa,sak irin maganin da yasan yana siyowa da kudinsa va damgashi ga hajiva garama har na tsahon watanni shid,bayan wata shidan kuwa baya taba batan lissafi zai sake kawo wani na wata shidan. Bude robar yayi ya zazzago maganin. Shine asin da asin babu banbamci, sai ya maida murfin maganin ya rufe ya maidashi inda vake vana fadin

"Hasbunallahu wani'imal wakil" wane sashe na zuciyarsa kuma na tambayar sa,waye yake bata kudin siyan maganin?. Lokaci daya komai ya rikice masa,lissafi yaso qwace masa,ga hajiyan da wani magani sabanin wanda ake baiwa fadeelan, ita kuma gata da irin maganin fadeelan ba tare da yasan waye yake siya ba.

Komawa yayi ya zauna saman sofa bed,har ta gama wankan suka fito tana tsane mata gashinta da hoodie towel din data rataya mata saman kanta.

"Abby...." Fadeela ta fadi, abinda ya jawo hankalin sãahar sal tadan ja da baya tana boye jikinta a qofar.

"Abbyyy..." Maganar yarinyar ta magale mata a maqoshi,a hankali yatsun hannunta dana gafafunta suka fara motsawa suna shacking. Dukkaninsu suka fahimci abinda ke shirin faruwa da ita,lokaci guda kuma kowanne ya taso da mugun hanzari suka nufo fadeelan,shi ta gaba sãahar ta baya,suka kuma isa gareta lokaci guda tare da rarumota cikin jikinsu saboda kada tayi mummunar faduwar da zata ji ciwo.

Shi yayi nasarar rungume fadeelan,yayin da säahar ta saki wani irin kuka mara sauti cikin narkewar zuciya tana kiran sunan fadeela

"Shshshsh" ya fada yana dora yatsansa saman lips dinsa duk da cewa shima cikin tashin hankalin yake

"Stop crying" ya sake fada da muryarsa da taynkaushi.va mige a nutse ya kaita saman sofa bed ya kwantar da ita sosai yana ambaton sunan Allah a ransa. Ta dauki tsahon kwanaki masu dama rabon da ta samu wannan attack din,kusan zai iya cewa harma ya manta,ya kuma tsammaci lalurar ta tafi kenan. Idanunsa suna kan agogo yana yana lissafa adadin mintunan kamar yadda ya saba,yayin da sautin kukan säahar ke shiga masa kunnuwa,sai ya dinga jin kamar ana soka masa allura cikin qwaqwalwarsa,wani irin ciwon kai ya fara saukar masa kadan kadan har cikin idanunsa.

Wannan karon bata gara ba akan mintunan data saba yi, ta bude idanunta a hankali tana kallonsu.

"Aunty N,faduwa nayi ko? ‚na dauka na warke na daina faduwa" furucin da ya sanya sãahar tsananta kukanta,hawaye masu yawa suka jige mata fuska ta kasa controlling dinsu, gaba daya hannuwanta suna cikin na fadeela ta rigeta tsam

"Zaki daina daughter, zaki daina in sha Allah very soon, in sha Allah,in sha Allah, i promise" duk da yadda kansa yake sarawa hakan bai hanashi dubanta ba,bai taba ganin hawayenta da kukanta ba kamar yau, kamar ma ta fishi shiga tashin hankali. A nutse ta mige ta dauko tissue ta dawo ta zauna a gefanta tana share mata majinar data zuba daga bakinta hade da yawu. Hannu fadeelan ta miga tana share mata fuska

"Ki daina kuka anty N,na dauka na warke ne, amma ai na saba" migewa tsaye yayi yana saka hannunsa a aljihun wandonsa kansa yana sake sarawa,yanajin kalaman fadeela har cikin zuciyarsa,yana jin kamar ya gaza.

_WASHEGARL


Cikin jikinta fadeelan ta kwana a daren jiya,da safe ma tace yau ba school, tunda juma'a ce ta zauna a gida ta haqura. Da safer tayi mata duk abinda ya kamata, duk da cewa Zuciyarta babu dadi,haka gangar jikinta babu kuzari, amma haka ta daure ta koma sashensu.
Me share share ta samu yana aikinsa,kamar yadda toufeeq din ya maidashi akin sassafe, shida zuwa bakwai ya gama komai,idan kuma ya makara saidai ya bari kuma sai bayan sun fita office. Gefe yaja yana sadda kansa gasa sanda yaji sallamarta

"Good morning maa" ya fada ba tare daya kalleta ba

"Morning"' ta amsa masa tana wucewa. Samun kanta tayi da kallon gofar dakin nasa, ba alamun da mutum a ciki,duk da cewa daman kusan kullum kamar haka qofar yake, amma yau sai taji abun yadan ja hankalinta, duk da haka ta watsar ta isa nata dakin tana shiryawa a hanzarce don kada tayi late.

Ta zarta lokacin shirin nata, amma ga mamakinta har ta kammala shiryawa ta fito bataji wanann sassanyan qamshin nasa da duk safiya yake gaya mata kammala shirin boss din ba. Ta iso parlor babu kowa, dama jacob ne zaka samu ya raya falon da qamshin abincinsa, shima tunda yaje gida wanna yayi qaura. Yankewa tayi ta fita farfajiyar gidan saidai kafin ma ta qarasa duka taga babu motocin da suke fita din ko guda daya

"Good morning madam,ya jikin oga din?" Muryar jibril dake magana cikin girmamawa ya furta. Da dan sauri ta waiwayo

"Jikin oga kuma?" Ta tambayi kanta da kanta,ta tambayi jibril din kamar zubewar kimarta ne, saita amshe kawai

"Jiki da sauqi alhmdlh"

"Allah ya qara afuwa"

"Ameen" ta amsashi. Qafafunta babu qarfi sam ta koma ciki, taja burki a falon ta tsaya tana tunanin meye abunyi?, at last taga babu wani abu da ya rage illa ta shiga dakin da kanta.

"HUGUMA*


"_TABARMAR KASHI_'

Book 02 Page 30


Sau biyu tana dora hannunta akan handle din tana janyewa. Tana tunanin yadda zata shiga dakinsa yau a karon farko, tana kuma tunani da tsoron kada ya fasarata.

To amma kuma zuwan ya zame mata tamkar wajibi,don kowa a gidan da zai buqaci jin yanayin lafiyarsa ita zai fara tuntunba daga bakinta kuma za'a so aji komai. Uwa uba fadeela, data tashi ta tabbata abby din zata nema.

Kuma ko babu komai rama alkhairi sai dan halak, shine mutum na farko daya fara kulawa da kuma lura da sauyawarta lokacin da ciwon kanta ya motsa.
Sama sama ta soma jin kamar muryar meenal daga falonsu,wanda daga shi sai hallway din da kuma bedrooms dinsu. Bata sake tunani na biyu ba ta murda gofar kawai ta shige. Dai dai lokacin da yake kwance cikin duvet, bai jima da komawa ya kwanta ba,saboda a jiyan bai samu wani cikakken bacci ba,gaba daya idanunsa ne suka soye yanata hada lissafin da bai samu nutsuwa a kansa ba sai da zuciyarsa ga bashi gamsuwa da rinjaye akan bangare guda. Koda ya samu baccin sai tashi farkawa ba sai qarfe shida na safe, alfijir ya fara ketowa sosai. A razane ya sauko, hanzarin da ya sanya kanshi sarawa ya rige kan yana takawa a hankali ya wuce toilet. Alwala ya daura ya zauna yayi sallarsa,ya duba first aid kit ya balli maganin ciwon kai yasha. Yana gama lazumin ya lallaba ya koma gadon yana sake qudunduna a duvet din. Idanunsa ya lumshe a hankali,yanayin da vake tsintar kansa kowacce asuba ya fara sauka ga jikinsa, abinda bai taba tunani ba saboda ganin yadda ya kwana yana fama da tunani bacin rai da kuma ciwon kai.

Matse jikinsa yayi guri daya vana lumshe idanunsa,abun mamaki sai ga hotonta kar cikin duhun idanunsa sanye da farar gown dinta me qaramin hannutsigar jikinsa ta zuba lokacin da ya tuna yadda jikinta ya gogi nasa,sai ya runtse idonsa da kyau ya juya yayi rub da ciki yana gangame pillow da hannunsa tare da ambatar sunan Allah a sarari.

Duk yadda yayi zaton na wasu mintuna ne zuwa awa komai zaiyi narke masa amma abun ya wuce tunaninsa,maganin ciwon kan da yasha sai yakeiin kamar maganin wani garin garfi ya sha bana ciwon kai. Sake tura kansa yayi cikin duvet din yana kiran sunan Allah gasa qasa,jikinsa yayi dumi sosai ,sai hucin numfashinsa da ya cika duvet din wanda ke gauraye da sassanyan night scent dinsa,da ya rufe idanunsa ita yake gani cikin mabanbantan yanayin da yake ganinta, idan kuma ya bude idon nanma ba sauqi, abun kamar wani tsafi ko sihiri.

Kamar cikin mafarki yaji tattausar muryarta tana yin sallama cikin dakin. Tsai da numfashinsa yayi na wucin gadi yana cike da mamaki da kuma tantama, idanunsa a rufe ruf ba tare daya motsa ba, kunnuwansa suna jiyo takunta cikin lallausan carfet din dake dakin duk da takun nata baya bada sauti.
Koda bata zurafafa kalle kalle a bedroom din baiya iska da gamshin da yake fiddawa kadai ya isa gaya mata na musamamn ne fiye da kowanne daki dake gidan.

Wasu irin furniture na alfarma masu tafiya da hankali, luxury curtains da suka mamave dakin suka sanvashi ya sake zama wani luf luf da babu lallai ka iva tantance dare ne ko kuwa rana?. Akwai wadatar hasken fitilu a dakin har kusan color biyu,farin qwai da kuma light blue sai suka hadu suka bada wata kwantacciyar kala me kvau a kowanne sashe na dakin,frames manya manya dake dauke da ayoyin tsari ne a kowacce kusurwa ta dakin. A kallon da tayi masa sai jikinta ya bata bacci vakeyi,abinda zataso tayi shine komawa,to amma zuwa lokacin ta jiyo muryar haseena daga bakin gofar dakin, zuwa lokacin ma har ta fara knocking.

Yau daya tak taji wani abu ya taba zuciyarta,wanda bata dorashi a mizanib komai ba sai na haushin rashin hankali da rashin kamun kan meenal din

"'Yau zataga qarshen fitsar" ta gayawa kanta d kanta,don haka sai t wuce bakin gadon kai tsaye ta zauna kusa dashi. A yadda ta zauna kawai sai da tsigar jikinsa ta zuba,ya runtse idonsa ta cikin duvet din yana sauke numfashi a hankali.

Zubawa lallausan creamy white duvet din idanu tayi tana sauraren knocking din da meenl ke ci gaba da

"Koda yayyanka uwa daya uba daya, bai cancanci kazo dakinsu a irin wannan lokacin ba,ko ita da ta taso a mazaunin auta yar lelen yayyenta,har suka gama rayuwarsu cikin gudan ko da safe maama bata bari taje a wannan lokacin. A nutse ta daga kanta jin ta fara murda gofar, tana nufin shigowa zatayi kenan? ta rantse yau saita nuna mata iyakarta, don haka ba tare da tunanin komai ba ta dage duvet din ta tura kanta gaba daya har zuwa rabin bayanta a ciki, abinda ya bawa numfashinsu d qamshin su damar gauraya guri day kuma lokaci daya,kowa ya zuqi hucin numfashin dan uwansa har cikin huhunsa.

Idanunsa ya lumshe yana jin yadda numfashinta ke sauke yana garawa duvet din dumi, ko sau daya bai motsa ba,har zuwa sanda aka tura qofar aka budeta.

Mugun bugawa zuciyarta tayi, saboda ganin qafafun mutum biyu cikin duvet daya, take zuciyarta ta ayyana nata ga abinda sukeyi

"Na shiga uku!" Ta fada da garfi tana sakin qofar, ta kuma juya da hanzari ta fice.

Qaramin tsaki säahar ta saki bayan ta tabbatar da ficewarta,sannan ta yungura zata miqe tana qogarin yaye duvet din. Hannunsa ya sanya ya zagaye wuyanta da kyau,a hankali yana warware idanunsa ya saukesu fes cikin nata

"Ina zaki?" Ya furta a hankali cikin salon rada da wani irin taushi yana kallon zara zara din gashin idonta dana girarta,wani abu yana tsarga masa saboda ya samu kusanci da ita fiye da yadda ya taba samu tsahon sanin da yayi mata a rayuwarsa,ainihin kamanninta hadi da cute face dinta yau ta zama kusa da shi sosai fiye da ko yaushe jarababben qamshin nan nata gaba daya ya cika duvet din. Tsigar jikinta ce ta tashi saboda iskar daya baza mata saman fuskarta,kasa magana tayi sai ma gogarin sake migewa da takeyi saidai babu dama saboda ya tare ta da hannunsa

"Ina zakije nace? bake kika kawo kanki ba?" Ya sake fada yana lumshe idanunsa dake kan fuskarta,yana jin yadda komai na jikinsa ya fara wani irin aiki.

Gabanta ne ya fadi,sai yanzu ta fahimci wautar data tafka,ta sauke idanunta cikin toro da d'ari d'ari ga gangar jikinsa. A tube yake babu riga,sai tarin lallausat gargasar data cika girjinsa me santsi da laushi, gabanta ya sake faduwa ta maida idanunta ta kulle gam,qirar jikinsa toro yake bata, saboda jikinsa ya ginu da wasu irin muscles dake nuna yadda ya baiwa motsa jiki muhimmanci

"Me kikazo yimin?" Ya sake fada muryarsa na sake karyewa da yin laushi, labbanta dake walainiyar lipstick suna fusgar hankalinsa,yana jij kamar ya cinyesu

"Bab.....ba komai, just nazo ne gaya maka na gama shirin fita,saik kum......

"Sai kuma na baki sha'awa ko?, kikaji kinason ki rungume ni?" Ya garasa fada yana dage dukka girarsa sama. Ido ta fidda waje,abinda take gudu kenan zai manna mata sharri

"Allah ya kiyaye,meye abun sha'awar a nan?"

"Oh really?, dama kince babu maza a gidan nan ai ko?"

Shaf ta mance da maganar sai yanzu, amma ganin yana son raina mata wayo saita fara quna quni tana son qwatar kanta

"Banyi garya ba.....ka sakeni" ta fadi tana son janye hannunsa amma ko gezau, tako ina ya tsareta tas.va ma sake matso da ita sosai cikin jikinsa.

Sai data soma gajiya sannan ya zare hannun nasa,yana jin yadda jikinsa yake fidda gumi saboda saukar zazzabin nasa da kuma yanayin da yakejin jikin nasa a ciki. Da hanzari ta zare kanta daga duvet din tana nishi, tuni dankwalinta ya zame daga kanta, tana gyara yafen mayafinta ya yaye duvet din saman kansa yana dubanta gasa qasa

"Coffee please" ya fadi har yanzu muryarsa na cikin wani irin rauni

"'Ina kwana?" Ta fada cikin zafin rai da yadda gaba daya ya janyo ta yamutse

"Alhamdulillah" ya amsa mata a taqaice yana maida kansa cikin duvet din, don babu abinda ganinta yake qara masa sai shiga wani irin yanayi dake sanyashi birkicewa.

"Idan kika wuce baki kawomin ba sai kin gane baki da wayau" ya fada qasa qasa, kamar yasan shirinta kenan.

Baki ta tura gaba kamar ta fasa kuka,shi kam ba'a masa abin arzigi sam,inda tasan irin wannan cakumar zaiyi mata da ba shakka bata shigo dakinsa ba.
Tayi mamaki sosai sanda ta bude gofar dakin ta samu haseena zaune a gurin. Kallon kallo suka yiwa junansu,sai haseena din ta mige tsam ta kewaye säahar ga mamakinta sai ta kama handle din gofar ta tura ta shige.

Karon farko. wani abu mai nauyi ya tsaya mata saman zuciyarta, tabi qofar da tuni haseena din ta maidata ta rufe da kallo, sai taji ta kasa daga qafafunta

"Shin meye nawa?" Ta yiwa kanta tambayar, tanason garyata kanta da kanta game da damuwa da takaicin da taji a ranta. Kai ta girgiza tana son tabbatarwa kanta cewa ba komai bane ba kuma abinda ya shafeta bane don haka ta soma takawa tana wucewa kitchen din.

Duka duka mintuna biyar sun isheta ta kammala hadawa, wasa wasa sai gashi tana dosar minti goma tana dawurwura cikin kitchen din, kadan kadan wani irin bacin rai ya soma hayewa zuciyarta,wanda ya janye dukka wata nutsuwa da walwalarta,sai data zuba coffe powder din spoon uku sannan ta tuna yayi yawa, ta zare dot din ta zubar tana sake hada wani. A hankali ta saki spoon din sugar ta koma da baya ta jingina da kitchen cabinet din, tamkar yayewar hijabi ta hango abinda ya faru da ita shekarun baya. Adam take gani fes saman gadonta na aure tare da wata,lokacin da ta kamasu a zahiri,yaci gaba da duban qwayar idanunta ba tare da ya bar abinda yakeyi din ba. Sakin cokalin tayi a qasa,kamar wadda aka fusga ta nufi hanyar kitchen din tana in kanta kamar zai fashe lokaci guda zuciyarta na sake haska mata shigar haseena dakinsa cikin wata banzar rigar bacci da wani gantalallen mayafi dan mitsitsi.

Da wani irin qarfi ta buda qofar dakin, abinda ya jawo hankalinsu kenan su duka biyun,shi da yake zaune saman gadon da haseena dake tsaye a qasa amma dab da gadon hawaye suna wanke mata fuska. A hankali idonta ya sauka akan jikinsa da babu riga,sai ginannen qirjinsa dake bayyane, saboda duvet din ya dawo iya cinvarsa zuwa gafafunsa

"Bacemin a gun" ya fada a tsawace, sai haseena ta juya da sassarfa tana fita a dakin, sautin kukan da taketa cinyewa yana qwace mata. Jiri jiri ta soma ji,tana jin tsawar har cikin kwanyarta itama, fara takawa tayi zuwa gefansa don ta lalubi wayarta da kuma dankwalinta tabar masa dakin itama

"Where is my coffee?" Ya tambayeta da muryarsa deep inside fushi yana azalzalarsa

"Ban dafa ba" ta bashi amsa kai tsaye tana jin kamar zuciyarta zata tsage. Idonsa ya lumshe kana ya budesu,yana hangen tsiwar nan fal idanunta

"Har yanzu ban koya miki darasi ba shi yasa baki fasa yimin rashin kunya ba......

"Me yasa zaki barta ta shigomin daki a cikin yanayin da nake ciki?,idan da a tsaye ta ganni kinsan abinda zai faru?"

"Sai kayi mata abinda kace kana yiwa mata, tunda dama budurwa ce ina kyautata zaton indai bawai ka karba yadda kace kana karba ba,qila shine dalilin bibiyar.....waima meye nawa a ciki?,live your life, bani da case" ta bashi amsa da wani irin zafi har cikin ranta tana in qunar da batasan dalilinta ba, kalamansa kuma suna dawo mata.

Kamar ta yanki zuciyarsa da reza haka yaji,wani irin fushi ya taso masa, ita batasan dukka laifukan ta ba? ta yaya zata dinga bari mata suna samun access dashi ta kowacce hanya?,a kirashi a waya ta bashi su,su shigar masa office su shigar masa sashe harma ta fita ta barwa yarinyar sashensa? yarinyar da ko falonsa na farko bai taba bari ta shiga ba yau gata cikin bedroom dinsa a lokacin da yake cikin wani yanayi?, banda Allah yasa yana kwance tasan iya dadin zubar da mutuncinsa zaiyi?, koda bai shirya aurenta ba wanna zai zama sanadin da dole ya aureta. Maganganunta suka sanyashi jin he is nothing, bazai qyaleta ba yau sai ya nuna mata
BAMBAMCIN DAKE TSAKANINSU.


"Kema yau zanyi miki abinda nake musun, kinga daga nan zaki gane dalilin da yasa suke bibiyar tawa" Ya fada yana sanya hannunsa yayi mata kyakkyawar fuzgar da bata dire ko a ina ba sai saman jikinsa. Dukkan jikinta ne ya dauki rawa lokacin da suka samu sadarwa tsakanin ilkinsu a sannan ta gane me yake nufi da yace ya godewa Allah data sameshi a zaune. Cikin kwanyarta taji kamar zata zauce sanda ya riqe fuskarta da kyau a tsakiyar tafin hannunsa,ya kuma hade bakunansu guri daya.
"HUGUMA*

*_TABARMAR KASHI_

Book 02 Page 31

Duk yadda tayi zaton zai mata mugunta da labbanta yanda yayi mata wancan karon ba haka bane, cikin wani irin taushi da tsananin qwarewa waien iya sanin kalolin kisses yake sumbatarta hadi da lashe lips dinta zuwa harshenta dama ilahirin bakinta gaba daya,cikin second biyar yanayin fitar numfashinsa va fara canzawa da wani irin gudu har girjinsa yana dagawa.
Lausasan hannuwanta da sukayi wani mugun sanyi ta aza saman nasa hannun dake kan fuskarta tana gogarin turewa saidai ko gezau baima ji me takeyi ba, yaji dai saukar wani sassanyan abu me laushi akan hannunsa,wanda ya qara saukar masa da wani yanayi cikin kowanne sashe na jikinsa ya kuma gara masa qaimi.

Sai daya tsotse bakinta iya yadda ransa yayi masa,ya kuma tabbatar da mutuwar jikinta da kyau sannan ya juyeta zuwa saman gadon,ya kuma zame mata rumfa, bai sake mata bakin ba duk da haka,sai hannuwansa da ya zame a hankali ya zurasu ta gasan rigarta. Daidai cibiyarta suka sauka,ya fara yawo dasu tun daga nan yana haurowa sama, yana nufar ababen harinsa na tsahon lokaci,wanda a yau yakejin kamar numfashinsa zai fita saboda son isa garesu. Ci gaba yayi da hawa sama da hannuwan nasa,yana isa yaji akwai babban shamaki tsakanin hannun nasa da su,sai ya dagata cikin zafin nama yana neman zip din rigar. Baisha wahala ba saboda zip din gaba ne da rigar, tana jin garar zipping din rigar tasa dukka hannuwanta ta damqe hannun nasa idanunta na malalar da hawaye tana girgiza masa kai,sam bata shiryawa wannan rayuwar ba

"'Kada ka karya yarjejeniya......kada kayi cin amana" fararen idanun da suka juve zuwa ruwan goro ya lumshe,CIN AMANA?,SHI DA SADAKI YA BIYA YA AURETA A HANNUN WALIYYANTA DA SHAIDU?.
Maganar data furta sai ta zama kamar zuga cikin kunnuwansa, ya tabbatar idan bai tabbatarwa yarinyar ta halasta a gareshi ba wannan bakin nata bazai mutu ba,ba kuma zata daina gaya masa maganganun da basu da tushe a wajen kowa ba tamkar hayarta yayo ba aure aka daura musu ba. Jaa daya ya yiwa zip din sai gashi ya balleshi gaba daya har qarfen ya fice daga jikin zip din fara tas din fatarta ta bayyana da dukiyar

Please Login or Register in order to submit comment