Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 64 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abubuwa da yawa tattare dake da suke bani tabbacin na samo gold din da nake nema,you gave me a million reasons to love you,zaki yimin nima alfarma?" Ya fada yana riqe yatsun hannunta hopefully. Iconta ta lumshe kana ta budesu, shin idan tace bata sonsa ma a yanzu bata yiva kanta gundumemiyar garya ba? ya riga ya wuce da dukka tunaninta da muddin tace zata iya rayuwa babu shi tayi qarya matuga da gaske yayi mata wani irin ba zata ya qwace komai data mallaka,ya dandana mata meye ainihin so na gaske meye ainihin hidimar miji wa matarsa bawai hidimar mata ga mijinta ba,ya koya mata yadda zata so kuma a sota, bawai ya koya mata yadda zata soshi bane zallar bashi da intention na maida mata wannan zallar soyayyar kamar yadda adam yay ba

"Am ready to be your paradise" ta fadi da mafi dadin muryarta me taushi, sautin da ya ratsa masa kunne,ya kuma kashe kowanne fargaba bacin rai da damuwarsa dukka a lokaci guda,ya fidda wani kyakkyawan murmushi daga saman fuskarsa irin wanda bata taba gani ba

"Kice i love you Muhammad toufeeg, that's all I want to hear daga wannan dan mitsitsin bakin me tsiwa" ya furta yana kallon lips dinta da suka fara motsa shi yana masifar sonsu,suna daya daga cikin abubuwan dake motsashi a kanta,shi kadai yasan taushi da zaginsu.

Kunya ta kamata sai ta kisa fuskarta kan hannunsa dake rige da nata hannun

"Pleaaaaaaaassssseee.…say it mana" ya fadi mata a
mugun shagwabe har sai dataji kamar zata shide.

"Say it mana" ya sake fada har yana zamowa daga saman stool din, sai gashi durqushe saman gwiwoyinsa a gabanta

"Its what I want to hear SAHR karki haramta min,na rogeki ki fadi abinda kikeji a kaina tell me you love me.. only true love can heal all the wounds of the past" Kasa riqe kanta da zuciyarta tayi, idanunta a lumshe ta motsa bakinta

"You are the missing link of my heart, you are the best thing that ever happened to me I LOVE YOU AND I CAN'T LIVE WITHOUT YOU"

"Ya salam!, harda gari" Ya furta muryarsa na rawa,ya riqe hannunta da kyau yana dan jijigashi with so excitement

"Can you say that again?, I want to relieve the feeling" idanunta ta bude tarrr wanna karon ta zube masa,sai kuma ta janye su a nutse tana jin nauyinsa. Da sauri ya kamo fuskartata ya dawo da ita saitinsa

"Look at me once again with those bold beautiful eyes and say it please SAHR" juya qwayar idon tayi cikin nasa idon a rarrabe kamar me koyon magana ta sake maimaitawa din.

Jikinsa duka ya gama amsawa, sai ya mige cak vana garasawa saman gadon vana fadin

"How i wish i could listen to those words again and again,you deserved a kiss" bai sake bata second chance ba ya shiga aike mata da zazzafan sago,lips din nan dake tafiya dashi da kuma albarkatun jikinta bai daga musu gafa ko sau daya ba. A karon farko itama ta fara maida masa da martani, abinda ya taka muhimmiyar gudunmawa wajen haukatasu gaba daya shi da ita.

Sanda taji tana gogarin kaiwa wani waje saita riqd hannunsa numfashinta yana rarrabewa,da rinannun idanunsa ya kafeta shima nasa numfashin yana tsere da kyau

"You are halal for me jininki bai haramta min ke ba duk da ma dai fake jini ne,naga komai" ya fada yana matsar da hannunta gefe ya kuma ci gaba da abinda yakeyi,bakinta ya mutu murus ba abinda ya rage mata illa bada kai bori ya hau.


"_HAJIYA QARAMA_*

Wani mawuyacin dare ne a gareta wanda kaf tsahonsa bata samu bacci ba. Tana kallon nadeeya ta shirya ta kwanta abinta, tunda tayi mata sannu sau daya bata gara waiwayarta ba,duk da abun yadan bata mamaki saboda duk sanda take lalura tana tsaiwa a kanta fiye da abinda haseena zata yi mata, amma yau ta nuna halin ko in kula a kanta. Ba wannan bane damuwarta, damuwarta a yanzun shine kan yadda komai yake lalace mata, anya mutuwar bokanta bata da alaqa da lalacewar aikinta? tunda hatta da gawarta da akayi musu ayyukan tare a wancan lokacin,duk da ita tana zuwa sabunta aikin amma itama yanzun hakan ruwa yanata qarewa dan kada ne.

Qafe hudu da rabi na asuba sago ya shigo wayarta,a mugun razane ta mige hannunta na rawa wayar na neman faduwa a hannun nata, maimaita kiran

"Na shiga uku, innalillahi, na shiga uku" shine abinda ya tayar da nadeeya daga baccinta

"Me ya faru?" Ta tambaya a rude saboda ganin yanayin da hajiya qaraman ta shiga. Bata iya amsa mata ba sai hawaye data fara yi,abinda nadeeyan bata taba gani ba, don haka ta mige ta bude qofar ta tafi taso Abbanta.

Maji na zaune saman abun sallah har ya tashi ya bude mata gofar tayi masa bayani suka rankaya suka fice.

"Lafiyarki fauziyya?" Dr jarma ya tambayeta

"Yaava,plaza ta gaba daya wuta ta cinye ta" ta fada tana sakin kuka me ciwon zuciya. Guri ya samu ya zauna yana maimaita innalillahi wa inna ilaihi raji'un shima. Dukka shagunanta ne a ciki da ta zuba kaya iri daban daban ake saida mata,wadanda ta bada haya basufi kaso daya cikin hudu ba.

Da ayar ya samu ya lallabata ta tsaida kukan

"'Kada ki damu, za'a san abinda za'a yi in sha Allah" wannan magana tasa ta dadada mata qwarai, tasan zata rage asara sosal daga wajensa,shi yasa ma bata gaya masa babu kaya masu yawa a dukka shagunan ba,don an kammala ciniki da lissafin shekara ta maqare duk wata dukiya tata a account, tana shirin zana tayi kasafi tayo order na dukka kayayyakin shagon nata a sake sabon zubi da lissafi sai kuma ga wannan tafiyar ta Germany ta taso mata.

Awa biyar tsakani, da safe likita yana dubata dr jarma na gefe suna magana da nadeeya kira ya shigo mata wayarta. Da daga wayar da fasa kukanta hadi da fusge hannunta duka cikin minti guda tana sake fasa kukan

"Daya plaza din tawa data ragemin yaaya wadda tafi kowacce girma,itama ta gone tun daga sama har casanta yaaya‚na shiga uku,wanne irin ibtila'i ne haka?"
Dr jarma yadan rufe idonsa kadan ya bude yana kiran sunan Allah, kansa yana sara masa da wani irin ciwo,gaba daya jiya bai samu isashen bacci ba wajen rarrashin maji data tubure masa kamar bata taba gainsa ba a rayuwa yanzun kuma ga matsalolin fauziyya daya na bin daya da wanne zaiji?
"Kiyi haquri ki kwantar da hankalinki,kinga yanzun nan likita ke maganar jininki bai sauka ba duk da magungunan da suka baki,zaki iya samun matsala kowacce lokaci muddin kikaci gaba da wanann abun"
"Ya kamata na koma gida yaaya na bincika meke faruwa, manyan plazas har biyu yau babu ko daya?"
"Karkiyi sabo fauziyya,Allah yana iya jarabtar bawa a duk lokacin da yaga dama bawai sai da dalili ba". Tsam nadeeya da haka kawai takejin takaicin yadda take sharban kuka kamar yarinya qarama ta miqe tana fita qasan ranta tana jan qaramin tsaki.


Zafafabiyar

"HUGUMA*


*_TABARMAR KASHI_*


Book 02 Page 59


*****Tunda gari ya waye ta fara maganar tafiyarsu
asibiti,yana cikin duvet yana wani almurin bacci da
sãahar din tasan na neman magana ne kawai, don sau
uku tana kamashi yana binta da kallo tana kai kawon
nata shirin tafiyar. Koda ta kammala gabansa ta
iso, idanunta a qasa a kuma shagwabe tana lanqwasa
yatsun hannunta

"Please na gama fa,kai nake jira" kallon qasan ido yakeyi mata zakayi zaton baccin yakeyi har yanzu, tayi masifar kyau,shigar da tayi ta karbeta,inda yana da hali wani abu shapeless zai samu ya lullubeta ta yadda babu me iya genta har balle yaga tudun qirjinta ko na mazaunanta

"A bani coffee to" ya fada muryarsa can gasa

"Okay" ta fadi da hanzari tana juyawa. Mini coffee maker ta kunna ta hada masa irin wanda yakeso har two cups, duk abinda takeyi din yana kallonta yana dariya qasan ransa, tare da tuno abinda ta jiyar dashi daren jiya wanda shi kam bai taba sanin akwai wannan abun ba.

Gabansa ta iso ta tsaya da mini tray tana cewa

"Ga coffee din" dan Jim yayi kamar bai jita ba,sai kuma ya miqe yana yaye duvet din,ya zauna sosai saman gadon ya miga mata hannu yana kallonta. Tray din duka ta miga masa, hannu yasa ya karba,da hanzari ya ajjiye shi saman bedside table dai dai sanda ta juya ya saka hannunsa ya kamota,fincikota yayi a tausashe sai gata gaba daya cikin jikinsa

"Me yasa baki da wayo kullum,ni da nace ki bani hot coffee saiki bani cold coffee?" Ya fada yana riqe da fuskarta yana kallon cikin idanunta. Zare masa manyan fararen idanunta tayi tana cewa

"Sai dava tafasa fa sosai,ka duba ka gani"

It was not hotter than you,and ba wani hot coffee da ya fiki,i like hot shower,a regular shower but with me in it"

"Don Allah,na yiwa fadeela alqawari zamu iso da wuri"
Tsayawa yayi da abinda yake shirin yi, yana dubanta da jirkitattun idanunsa

"'Me yasa zaki hukunci bayan kinsan idan baban fadeela yana guri rayuwarki da lokacinki duka nasa ne?" A yadda ta hangi fitina fal idanunsa tasan muddin bata lallabashi ba tsaf zai iya soke fitar ma

"Sorry i make a mistake but bazan sake ba" ta fada tana hada hannuwanta guri daya tana dan boye murmushin. fuskarta saboda yadda ta fahimci tayi masifar yi masa yankan hanzari. Kansa yadan juyar gefe guda

"Na fahimci idan akan fadeela ne zaki iya komai shine kikemin wannan 'var murvar don kawai a cuceni ko? yayi….. na yarda,but i need a kiss please"

"Tashin hankali" ta fadi qasa qasa,tasan kiss a gurinsa kamar wani mabudi ne na bude shi

"Eheen, baki shirya fita asibiti ba?" Ya tambayeta yana taba lips nashi da yatsansa. Yana gama fadi ta hade bakunansu ta fara masa yadda yakeso din, saidai daga garshe shi ya karba ragamar. Yadda ta zata din kuwa fara wuce gona da iri yayi, ta kama hannunsa ta riqe tsam don ba damar yin magana da baki, ya fahimci me takeson fada ya daga kansa yana dubanta

"Am sorry for being too forward but your lips make me wonder what the rest of you would taste like da safen nan". Bai bata dama ba ya warware shirinta tsaf yayi yadda yadda ransa yakeso . Bayan ya kammala ya sauka ya sauka ya barta yana mata dariyar cewar da takeyi

"Ka karya algawari " cikin kukan kissa da shagwaba

"Eh ai dama indai nine ta wannan fannin na dade da zama rules breaker, but duk da haka am sorry my
MOONBEAM" sai yayi kissing nata a tausashe ya wuce toilet.

Har ya fito tana kwance, ya zaci zai samu ta shiga daya daya toilet din dake parlor ta shirya, qarasowa yayi gabanta fuskarta na rufe cikin pillow

"Hello ko kina son gari ne?" Hararar wasa ta jefa masa
sannan ta sake qunshe kanta,can qasa tace

"Marata ce takemin ciwo*

"Ya salam* ya fada vana tayar da ita. Da gasken take don sosai ta rigeshi tana cije lips

"Let me help you kiyi wankan mu wuce asibitin sai kiga
likita ko?". Duk yadda taso dojewa bai fita ya barta ba,sai da tayi wankan ta fito ta shirya duka a gabansa,ga kunya ga ciwo,shi kuwa ya murje idanunsa,saima wani mayen kallo da yake bin ko ina na jikinta dashi har ta gama shiryawa

"Ko na sake warming maka coffee din,bakasha ba" kai
ya girgiza yana murmushi

"'Nooo,I got the better ai sukutun da guda daga wajenki”

kunyarsa ta sakata kau da kai, bayajin kunyat baro zance baro baro, sai sun fita kuma waje kaga ya kame kamar ba shine me b'arin zancan nan ba.

Sun samu an gama yiwa fadeela komai daya
Kamata, tasha magani an gyara mata jikinta,sai zaman jiransu. Sanda suka shigo kamar zata koma cikinsu,sosai farinciki ya cikata,ga abby dinta ga aunty N,duk inda ta waiwaya sune.

Basu wuce awa dava da isowa ba afifa da sajjad
suka iso. Sanda suka shigo sahar na saman gadon daga gefan fadeela tana bata fruit yayin da ogan yake zaune saman kujera a gaban gadon hannunsa goye a qirji ya tsaresu da kallo.

Migewa yayi ya bawa sajad hannu sukayi musabaha,afifa ta matsa kusa dasu bayan sun gaisa da toufeeq tana duba jikin fadeelan,shima sajjad din ya dubata,sai suka juya suka fice suna magana a tsakaninsu.

Ba jimawa suka dawo,a lokacin ta gama batan tana zaune daga gefanta tana tayata karanta wasu abubuwa da likitan dake kula da sashen magana na qwaqwalwa ya bata. A tausashe yake jifanta da wani irin kallo har ya qaraso daf dasu. Afifa ta kula,sai taja jikinta baya tana boye dariya qasan ranta.

"Moonbeam" ya furta gasa gasa yana dubanta. Kunya ta kamata jin ya maimaita sunan da ya sanya matan a gabansu afifa, ta daga idonta a hankali ta dubeshi, hakan yakeso sai ya marairaice mata

"Ki barwa su sajjad din ita kizo muje kiga likitan" kai ta jinjina, ta sakarwa fadeela dan qaramin littafin tana zamowa daga saman gadon. Kafin ta qaraso ya sanya hannu ya saita mata takalmanta, kunya da nauyinsu. sajjad ta sake kamata,ta zira takalman a nutse tana dawurwura na abinda zatace da afifa

"A dawo lafiya" kawai taji afifan tace sai bata ce komai ba tayi gaba kamar yadda toufeeq ya bugata.

"Dan tsaya" yace da ita bayan sun fito, ta tsaya cak ya qaraso kusa da ita, sai ya lalubi hannunta ya saka a nasa

"Yauwa to muna iya tafiya,naga alaman turawannan suma mayun mata ne" ya fadi yana wani tsare gida,abinda ya sanya qaramin murmushi ya kubce mata,sai taji dadi gasan ranta, karon farko kenan da taga haka daga wajen mijinta. Abinda adam bai taba damuwa yayi ba kenan, hasalima shi duk inda zasu shiga qoqari yakeyi aga kyanta,yana alfahari sosai da kyan da take dashi.

Ko cikin office din yana tsaye daga bayan kujerarta kamar wani bodyguard ita kuma tana a zaune.
Qwararriyar gynecologist ce da take a wani department daban a asibitin cikakkiyar musulma ce, abinda ya qara masa nutsuwa kenan,säahar tayi mata bayani dalla dalla da harshen turanci

"Ina zargin wani abu" likitar mai yawan fara'a da kirki ta fada bayan ta gama yi mata tambayoyi tare da duba report nata.

Scanning ta fara dayi mata cikin nutsuwa, kai kawai take gyadawa murmushi na fita a fuskarta,sai ta sanya hannu ta kirayi toufeeq tana tsaida na'urar kan wasu abubuwa guda biyu masu suffar wake ko gananun ayaba

"Kalli babies dinka" ta fada tana masa nuni da allon computer din da hannu. Ido sosai ya zubawa abun da take nuna masan,zuciyarsa na dan bugawa cikin wani irin zumudi da rikicewar tunani

"Ban fahimta ba likita" ya amsa mata shima, sai tayi murmushi tana sauke na'urar scanning din daga saman marar säahar

"Yanzu zanyi maka bayani,sauko madam" wannan karon kasa tsaiwa vayi va samu kujerar dake facing din säahar din ya zauna vana bawa likitan dukka attention dinsa

"Alamu sun nuna babies uku ne a mahaifarta,guda daya ne ye fita, yanzun haka akwai sauran guda biyu" daga shi har säahar din ji sukayi kamar jinin jikinsu ya daskare,ji yayi kaman kunnuwansa basu ji masa dai dai ba

"Karkiyimin irin wannan wasan likita, saboda bazan iya jurewa ba kic wasa ne daga baya" ya fada yana jin duniyarsa na kewayawa dash cikin wani madaukakin farinciki

"Ba wasa bane sir,shi yasa na kiraka na nuna maka su" kasa jurewa yayi saboda farincikin da yayi masa yawa,sai yaji kamar zuciyarsa ba zata iya dauka ba,don haka ya zamo saman gwiwoyinsa ya kamo hannun sãahar ya rige da kyau yana dorashi saman qirjinsa, idanunsa a lumshe yana ambatar sunayen Allah. Itama kasa rige kanta tayiyadda hannunta yakejin tsananin bugun zuciyarsa sai taji kamar a tafin hannunta zuciyar tasa take

"Wannan babban sakamakon ba zata da ubangiji yayi mana,duk da mudin ba wasu bayi bane masu tsananin biyayya ba a gareshi, bansan meye zanyi da zai sake sanyawa ubangijr ya sake yarda dani ya kuma aminta
dani ba ina da bugatar irin wannan falalar daga ubangiji
na a duk kowacce shekara idan zai bani, Alhamdulillahil
lazi lam yattakiz walada walam yakun lahu sharikun fil
mulki walam yakun lahu waliyyum minazzulli wa kabbirhu
takhbira" ya fada vana kifa hannun nasa a tafin
hannunta idanunsa na ciccikowa da gwallar da bayaso ta
zubo din,wannan hawayen yafison ya zubdasu a gaban
ubangijinsa don nuna tsantsar godiya a gareshi.
Sai da dr marhooma tayi gyaran murya sannan
ya tuna tana a wajen,don yayi nisa wajen lallashin säahar
da nata idanun suka kasa rige nasu ruwan hawayen

"Akwai bayanin da ya dace nayi muku" ta fadi tana gyara zamanta

"Amma likita,dama mata irina suna iya samun cikij 'yan
uku?" Tambayar da säahar taketa juyawa a ranta kenan ta kuma kasa rigeta. Murmushi dr marhooma tayi

"Kyautar Allah ce yana iya baiwa duk wanda
yaso,musamman idan a danginki akwai history na haifan
twins ko triple din, sannan yawanci matan da suka doshi
shekara talatin ko suka gota sunfi yiwuwar samun haife
haifen 'yan biyu ko uku ko hudu ma,duk da masu qasa
da hakan ma suna samu musamman wadanda ya zama musu kamar gado, lokacin da mace te saki qwai wato ovulation idan aka dace da gwan namiji ya hadu da nata @wan, maimakon ta gyangyashe qwai guda daya sai ta gyangyashe biyu uku ko hudu ko sama da haka,wani kuma yana rabuwa ne yayin gangarawa cikin ainihin qwaryar mahaifa sai a samu irin hakan, hikimar Allah ce duka yanayin yadda yaso a sanda yaso" dukkansu sun gamsu tsoron tare da tabbatar da afkuwar ikonsa suka shigesu, yayi ajiyarsa a muhalli daya,ya kuma fidda wanda bashi da rabon taka duniya,ya tsare sauran wadanda yaso suci gaba da wanzuwa

"Kamar yadda wancan likitan ya fada muku, tabbas mahaifarta tana da rauni, saboda haka zamuyi mata daurin mahaifa, sannan zamu bata bead rest wanda shi ko a gida zata iya yin abinta, saidai tana bugatar yallabai adan daga mata qafa don Allah daga yawan bugatu" ta gada tana sauke dubanta akan TOUFEEQ.
Murmushi kawai ya saki yana debe dubansa ya maida kan sahar, suka hada idanu sai ya kashe mata ido daya, yayi qasa sosai da muryarsa cikin harshen hausa yadda dr marhooma ba zataji ba yace

"Raguwa ce ke wallah, dama neman mafaka kike,to ai dai ba'a hanani shan dumin babies dina ba ko?" Ido ta lumshe tana sakar masa murmushi, sai yaja ajiyar zuciya

"Wannan lumshe idon kawai na tsokanan magana ne saboda kinga bazan iya fanshewa ba?" Siriryar dariya ce ta kubce mata,sai tasa hannu kawai ta rufe bakinta tana kwantar da kanta gefe guda.


Zafafabiyar
"HUGUMA*

_TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 60


"'Excuse me" Dr marhooma ta fada tana tashi hadi da fita daga office din. Da gyar ya zare idonsa daga kanta
kamar zata bace masa idan yabar kallonta ya fidda
wayarsa yana jin qirjinsa har yanzu cike da farinciki,ya
rasa dawa zai fara wanna maganar, idan ya kira sajjad
yasan tabbas! Tsiya zaita masa, infact ma zai addabeshi
ne ya buwayeshi, qila har sai dr yayi musu tsakani ma.
Maji dinsa ce ta fara fado masa a rai, fuskarsa na fidda
murmushi ya soma neman layinta yana qiyasta irin
farincikin da labari zai bawa zuciyarta.

Tun da safe yake aikin lallashinta har sukayi
breakfast sukayi shirin wucewa asibiti shi da ita,sai nan nan yakeyi da ita da al'amuranta yayin da ita kuma take basarwa a shekarun ita kadai tasan yadda ta rayu, cikin baqinciki da daci da qunar rai, inda Allah ya taqaita wahalarta ita din me yawan addu'a ce, bata wasa sam da addu' a,amma abune mai matugar ciwo ka bawa mutum rayuwarka ka zauna dashi fisabilillahi amma ya jefeka da miyagun kalmomi,yasa hannu ya tankwabe dukkan wata kyautatawa taka ya kuma yi maka kallon maciyin amana.

Ko yanzun data gama saka komai cikin handbag dinta caraf yayi ya kama hannun jakar ya riqe, ta waiwaya ta kalleshi ya marairaice mata gaba daya,sai taga ya koma mata mahmud dinta zam a zamanin quruciya da samartaka

"A saussautamin mana shifa ta,ko don idanun yaran nan‚banason su fahimci abinda yake faruwa"

"Sakarmin jakata,meye ya rage dama wanda basu san ka viwa uwarsu ba"

"Bakina bazai gaji da neman afuwa ba" ta fuskanci ba sakar mata jakar zaiyi ba,ita sai ta sakar masa tayo gaba ya biyota a baya. Dakin su nadeeya suka wuce don duba hajiya garama.

Nadeeya na fesa turarenta itama ta gama shirinta sukayi sallama suka shigo. Tana zaune saman gado, idanu da kuma fuskarta dukka sun wani qoje,dare daya Allah ya saukar mata da wani irin rudani da razani daya sake firgita nutsuwarta ya kuma hana jininta saukowa kamar yadda likitan yakeso.

Da sauri ta kauda kanta daga kallon maji, cikin ranta tana jin yadda ta muzanta, majin kuma na mata wani kwarjini da cika mata ido. Tayi kyau sosai cikin wata doguwar riga data dorawa madaidaicin hijabi, fuskarta da jikinta suna nuna nutsuwa kwanciyar hankali da kuma cikakkiyar kamalarta,abubuwan da ta tabbatar itadin ta rasa dukkansu.

Cikakkiyar sallama majin tayi wadda ta sanyawa hajiya garama faduwar gaba, bata ma iya amsawa ba sai nadeeya ce ta amsa, ranta na mata wani irin dadi. Ashe dama haka tarayyar iyaye biyu yake? a duk sanda taga maji da Dr a tare, sai taji kamar an sabunta mata duniyarta,ita ta yiwa majin da Dr gurin zama,sanann ta koma gefe tana hada tarkacenta cikin jaka.

Da dr suka fara gaisawa, gaba daya ta zama wani iri, ciwo kam ciwo yana mintsinin zuciyarta,iya kallon maji da Dr kawaj a mazaunin miji da mata a karo na biyu kadai ya usheta masifa da tashin hankali.

"Sannu da jiki" maji tace da ita a taqaice tana maida hankalykan wayarta da kira ya shigo. Qasa qasa hajiya garama din ta amsa, hankalinta nakan maji amma idanunta akan Dr suke da yake tambayarta tasha magani da abinci.

Murmushi ya subuce mata ganin toufeeq ne
yake Kira
"Assalamualaikum, Muhammad" maji ta fada tana murmushi. Kiran sunan kawai ya sanya hajiya qarama faduwar gaba,ya kuma gara sanyata maida hankalinta kan maji cike da mamakin toufeeq ne yake kira? ita ta mance ma lokaci na garshe rabon da yayi kiranta
"Lafiya alhamdulillah....too.... Ma sha Allah,ma sha
Allah,gamu nan a hanya muma zamu iso" saita katse wavar bakinta na furta
"Alhamdulillah zahiran wa bad'inan" Sai ta sauke wayar daga kunnenta tana murmushi sannan kuma ta mige
"Zan jiraka cikin taxi, marasa lafiyan sun garu" daga kai
Dr jarma yayi ya kalleta
"Waye kuma ba lafiya?" Murmushi ta kuma saki
"Surukarka zasu yiwa daurin mahaifa, Allah dai yayi cikin me zama ne, ba duka bane suka fita" muraran farincikin
Dr iarma ya kasa boyuwa

"'Ma sha Allah,nima yanzu zan fito" yace da mail

"'Allah ya kiyaye gaba fauziyya" maji ta fada tana ficewa abinta. Tsabar bagincikin da yake sussukar zuciyarta kasa cewa komai tavi. Ga mamakinta shima dr jarma din migewa yayi

"Zamuje wuce asibitin, daga nan akwai inda nakeso muje ni da maji din, inaga nadeeya ke ki zauna da ita kada a barta ita kadai,idan akwai wani damuwa saiki kirani" dr jarma ya fada.

"Don Allah abba zan biku, zaman hotel babu dadi wallahi" nadeeya ta fadi kamar zata saki kuka
"Jeki nima bana bugatar zaman naki" hajiya garama ta fada a qufule zuciyarta kamar zata fado gasa, cikin kwana biyu kacal ta fahimci yarinyar gaba daya ta canza itama, kamar bata Santa ba,duk wata damuwa da kulawa da take bata koda tana zazzabine yanzu babu shi

"'Ni nace ki zauna nadeeya,ya za'a bar mara lafiya shi kadal?"

"Taje yaya, kaima ka tafi bare ita" ta fadi tana jin kamar zata saki kuka

Tuni nadeeya tayi gaba abinta, don bata tsaya bama bare ta gane yadda suka qare da abban nata. Kasa zama guri daya hajiya qarama tayi, takai ta kawo ita kadai yau itace a wulaqance haka?,cikin dakin hotel bayan tana fama da ciwo? yau itace ba wanda yake daukan maganarta da muhimmanci bare ace za'a yi amfani da ita? anya batayi sake ba? zaman me ma takeyi ne wai a Germany? bayan matsaloli na shirin rufto mata su murqushe dukkanin nasararta?.

Ba'a jima ba suka gama mata daurin mahaifar aka dawo da ita daki, saidai sun roqi alfarma an dawo da ita department din su fadeela kusa da dakin fadeelan saboda abubuwa sufi yi musu sauqi. Yana riqe da hannunta tsam kamar za'a qwace masa ita,maji da Dr suka turo gofar suka shigo dakin.

Qoqarin yunqurawa takeyi ta tashi maji tace

"Yi kwanciyar ki d'iyata" ta iso bakin gadon. Sai a sannan toufeeq ya zame hannun nasa daga nata,ya matsa baya yana yiwa Dr jarma barka da isowa, qasan ranshi yana mamakin yadda suketa zirga zirga shi da maji din, gefe guda kuma ko yaushe ya gansu tare sai yaji zuciyarsa ta zurafafa da addu'ar dawowarsu da dinkewarsu a mazaunin ma' aurata kamar kowanne iyaye.

A kunvace ta gaida maji, majin ta hamsa
mata, sannan gasa qasa take mata tambayoyin da suka gara saka säahar cikin jin nauyinta. Duban toufeeq maji tayi

"Yaushe zasu sallameta?"

"Zuwa anjima suka ce,zatayi bed rest ne kawai koda a gida ne"

"Yavi kyau, zan wuce da ita gurina" maji

Please Login or Register in order to submit comment