Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 18 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ce sol farin dake da surki surkin ja a cakude dashi.

Sassalkar sumar kanta mai tsaho santsi da kuma cika kadai ta isa ta gaya maka cewa ita din ba BAHAUSHIYA bace,saidai wani yaren daga cikin yarukan da Allah ya albarkaci qasata nigeria dasu.

Kai tsaye zaka iya kiranta da KYAKKYAWA cikin mata dake da kyau a ajin farko,wani baiwar kyau da Allah ya bata tun tana ciki zuwa isowarta duniya,kyan dake iya zama barazana ga rayuwar diya macen da bata samu kyakkyawar tarbiyya ba,ko bata hadu da iyayen qwarai ba,wani irin kyau mai sanyi da tsayawa a rai,wanda ya cakuda da tsafta iya kulawa da kai da kuma gayu sannan ilimi ya hada dukkansu yayi masa ado na musamman.

Towel ne kawai daure a qirjinta,cikin wata irin nutsuwa take takowa har ta iso gaban makeken mudubinta,har ta miqa hannu zata dauki daya daga cikin tsadaddun mayukan shafawarta saita fasa,ta daga kai tana kallon agogon bangon dake manne saman mudubin wanda yayi wata qaramar qara dake nuna awa guda cif ta cika.

Zagayayyun fararen idanunta ta janye daga kan agogon cike da mamaki,saita dauki man ta bude,ta dan tsaya tana dubansa kamar yaune rana ta farko data fara ganinsa,ba zata iya tuna when last da ta bari man shafawarta ya qare ba,hakan yana nufin dole gobe taje shopping kenan,saita lakaci man ta fara shafe lafiyayyar fatarta cikin hanzari,tana yi tana duban wayarta dake ajjiye a gefe.

Kasa daurewa tayi,gani takeyi kamar ta kasa saurin da ya kamata ace tayin,ta jawo wayar tana loda wasu numbers dake alamta ta jima da haddace su,suka cika cif ta danna kira,SOULMATE sunan ya bayyana baro baro kan screen din wayar tata.

User busy ta saka mata,mamaki ya kamata,ta sake maimaita kiran aka sake sanar mata ana amfani da layin,saita aje wayar kawai ta mayar da hankalinta kacokam akan shiryawar da takeyi din,saidai can qasan zuciyarta bata daina mamakin wasu abubuwa da take gani cikin satin nan ba,wanda kai tsaye zata iya kiransu da BAƘIN ABUBUWA.

Kamar ko yaushe ta shirya tsaf cikin wata lafiyayyar rigar bacci da ta saka kudi masu nauyi ta siya duk don saboda ta burge mijin nata,masoyin da duk duniya idan ka dauke iyaye da kuma AFIFA bata da kamarshi,tayi checking kanta da kanta ta tabbatar komai yayi fiye da yadda ADAM keson ganinta a kowanne dare,saita saki qaramin murmushin da ya sanya dimple din dake dukka kumatunta lobawa,ta kawo qaramin baby hijab ta saka,sannan ta dauki wayarta laptop da sauran wasu tarkace da takeson dubawa na sauran aikin office da bata qarasa ba,ta zura slippers a qafarta ta fito.

Sai data kashe kowanne qwai da sauran kayan electronics dake aiki a qasan sannan ta haura saman cikin takun nan nata kamar tafiyar wahainiya,wanda ya zame mata halitta cikin jininta yake.

Ba kowa a falon,sai butar shayin data barshi yana sha a dazun da sautan cups da suka bata,dukka sai data killacesu sannan ta dawo zuwa babbar qofar da zaga sadata da bedroom din nasa,tana mamakin yadda akayi duk motsinta na yau baiji ba.

Da sallama a bakinta ta tura qofar,yana zaune sosai saman lafiyayyen gadon,ya jingina bayansa da fuskar gadon,saman cinyarsa kuwa na'urar laptop ce daya zubawa dukkanin idanunsa,yakuma bata hankalinsa dari bisa dari,koma me yakeyi da alama yaja hankalinsa matuqa.

Sautin muryarta ya sanyashi daga kai a hankali ya watsa mata manyan idanunsa,sai ya fidda qaramin murmushi daga labbansa idanunsa nadan lumshewa saboda yadda ta dauki hankalinsa,har yaji ma komai ya fita daga kansa,shi kansa yasan Allah yayi masa baiwar kyakkyawar mace,Allah ya bashi macen da yasan qarfin ikonsa ko wani qoqarinsa.... dukiyarsa ko iliminsa,wayo da dabara dukka basu isa su bashi SÃAHAR ba face tsananin rabo da kuma irin sa'arsa,wadda tunda ya fara gwagwarmaya a rayuwarsa ya fahimci shi din me sa'ar ne.

Kyawawan idanunta masu zubin gold ta narke masa tana kallonsa cikin salon kallon tuhuma,takuma maqale kafadarta tana kebe baki,sai ya daga hannayensa dukka biyun sama

"Am sorry baby" saita sake kafadarta ta fara takowar saidai har yanzu bata saki fuskarta ba.

Kai tsaye tayi qoqarin shigewa jikinsa sanda ta iso abinda zai zata ba,tana shigewar ne tare da qoqarin kai idanunta kan allon computer dinsa,saidai tun kafin kwanyarta ta gama tantance komai ya saka daya hannun ya rufe system din ba tare daya kasheta ba,yasa daya hannun kuma ya riqota cikin jikinsa sosai yana jifanta da wani irin kallo

"Bansan lokaci ya tafi har haka ba baby" ya qarasa maganar yana kissing goshinta,a shagwabe tace dashi da muryarta dake da wani irin zaqi da taushi

"Duka cikin satin nan haka kake mun,bansan yaushe na koyi bata lokaci akan computer da waya ba...... nidai ka gayamin,ko wata ka samo?". Tsam ya janyeta daga jikinsa yana duban qwayar idanunta,yanayin fuskarsa ya canza daga walwala zuwa wani yanayi na daban,idanunsu suka sarqe waje daya,sai ya girgiza mata kai

"Banason na qara jin wannan kalmar daga bakinki,ina dake ta yaya idanuwana zasu iya ganomin wata macen?,kinsan matsayinki a raina kuwa?,kinsan yadda kike a zuciyata?,beside ma.....mu da muke qoqarin ganin munkai rayuwarmu wani mataki na kwatance......ina nake da lokacin da zan kalli wata diya mace?,wai kina tunanin a duniya ma akwai macen data kai kyanki kuwa?" Kanta ta cusa a qirjinsa dariya tana subuce mata,a duk sanda adam yake gaya mata irin wadan nan kalaman,tana jin kanta acan qololuwar sama,tana jin duk duniya babu macen da ta kaita sa'a,babu macen da tayi dacen mijin qwarai kamarta,tana jin cewa zata iya tsayawa takarar macen da tafi kowacce mace sa'ar miji a duk fadin duniya,zuciyarta kuma na sake nutsewa cikin shauqin son adam da kuma qara amincewa dashi da kuma sallama masa rayuwarta gangar jikinta dama komai data mallaka.

Saman kanta ya dora nasa kan yana shafa sumarta da yake matuqar so yana kuma sake fito mata da abinda yake zuciyarsa a kanta,tayi shuru tana saurarensa,kowacce gaba ta jikinta tana saki cikin zallar shauqin so.

Sun jima a haka kafin ya umarceta ta bashi ruwa a parlor,ta sauka a hankali ta fice tana takawa tana jinta kamar tana yawo a gajimare,yayin da shi kuma ya bita da kallo,yana jin sha'awarta na sake fusgarsa da wani irin shauqi a kanta.

Kafin ta dawo ya kashe system din yama yi ready din kwanciya,ta hauro gadon ta tsiyaya ruwan ta miqa masa.

Sai daya kammala sha sannan ya bata cup din yana cewa

"Wannan watan ya akayi salary dinku yayi delay?" Maida cup din tayi ta ajjiye,sanna ta juyo gunsa

"Sun shigo fa tun kwana uku,kawai na dan ari kudin ne na siya wasu abubuwa dasu,amma gobe nake sa ran zan tura main account din gaba daya".


FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥
[8/24, 2:11 PM] KYAUTA: *H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 35


Fuskarsa tadan canza kadan har hakan ya bayyana qarara

"Me kikayi dasu da yafi abinda yake gabanmu muhimmanci baby?" Kai ta yada gefe tana dan murmushi kadan,adam da gaske yake,so yake yaga tabbatuwar mafarkinsu,ya bawa abin muhimmanci qwarai da gaske fiye da yadda ita din ta bashi,kodon akwai banbancin muhalli gidaje da yanayin rayuwa da dukkaninsu suka fito daga ciki ne?,batason gaya masa Afifa ta arawa,don babu jituwa ko kadan tsakaninsu,don haka tace

"Wasu gyare gyare namu na mata nayi dasu" a tausashe ya kamo hannunta ya sanya cikin nashi yana duban qwayar idanunta

"Idan kikaji ana batun ready made to kece,ke din baki buqatar wata kwaskwarima ko sauran gyara,ko yaushe cikin kyau da daukan hankali kike baby,so please mu maida hankali mu tara abinda muka tara mu gabatar da qudurinmu kafin cikar shekarun da muka dibawa kanmu" kai ta gyada tana dubansa,zuciyarta na qara aminta dashi,ci gabansu yakeso da gasken gaske ita da dukkan abinda zasu zo nan gaba ta tsatsonta,akwai masoyi sama da haka a rayuwa?.

"In sha Allah,hakan bazai kuma faruwa ba" kai ya jinjina yana sakar mata murmushin nan nasa gami da gyada kansa.

Suna shirin kwanciya ya saka hannunsa da sauri ya jawo locker din bedside dinsu ya ciro wani dan kati,sai ya fiddo idanunsa duka waje

"Kaiiiii!" Ya fada yana dafe kai,ta daga idanu tana dubansa sanda take zura santala santalan qafafunta cikin duvet

"Me?" Ta jefa masa tambayar tana kallon yadda ya dafe kai

"Yau ya kamata ace kinje allura,ni dake duka mun sha'afa" ya qarasa maganar yana ritsata da idanu jikinsa adan sanyaye,ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi,tadan juya qwayar idanunta sannan tace

"Shine duka hankalinka ya tashi haka?" Fuskarsa yadan sake hadi da qaramin murmushi sannan yace

"Banaso a samu matsalane baby"

"Matsala kuma?,kamar ba miji da mata ba?,kana tunanin duk babyn da zamu samu a yanzu ba zamu iya daukan nauyinsa ba?" Kansa ya girgixa a nutse ya maida katin saman drower din ya ajjiye yana duban idanunta

"Ba haka nake nufi ba.....amma kinsan komai yana da lokaci,kuma komai idan aka tsarashi yafi zuwa ta dadin rai" iska ta furzar daga bakinta tana dubansa,duk cikin tsarukan adam wannan ne kadai baiyi mata ba,wannan ne kadai takejin rawar zuciya da rashin tsaiwar hankalinta a kansa,har yau har kwanan gobe ta gaza sabawa,ta kasa jin gamsuwa da nutsuwa da hukuncin,duk kuwa da cewa ta gaza musanta masa ko qalubalantarsa,tasan koda tayi yunqurin hakan yana da tarin hujjojin da zai bata da zasu mamaye tunaninta

"Ko baka da wanann halin na tabbatar ina da gatan da bazan rasa komai ba" kansa ya fara girgizawa da sauri

"Noooo.....Allah ya kiyaye,ta yaya hakanma zata faru?,ya za'a yi nabarwa wasu hidimarki?,har abada,meye amfanina baby?,karki qara fadin hakan,inason na nunawa duniya ne i can make it happen,i can do it,we shall live happily,wannan din akwai lokaci na musamman dana tanadarwa zuwansa" kyawawan idanunta na saman fuskarsa tana dan lumshesu da budesu, zuciyar ta na bata mabanbantan ra'ayi,ta yaya zaka tsarawa kanka abinda Allah ne kadai yake da ikon tsarawa bawa?,ta buda baki a hankali zatace wani abu,sai yasa tafin hannunsa ya rufe tausasan labbanta yana girgiza kai,sannan daga bisani ya birkitota jikinsa yana lullubeta da soyayyarsa.

*_W A S H E G A R I_*

Shirye take tsaf cikin wata lafiyayyar lafaya wadda ta kusan zame mata al'ada sanyatan,a duk sanda ta sakata din kuma sai kamanninta su canza,ka rasa fahimtar da wanne yare zata dangantata,wani irin kyau shigar take mata mai daukan hankali.

Golden yellow ce da aka yiwa ado da brown color,dukkan takalmi jaka da dan kunne zuwa sarqa da tayi amfani dasu sunyi matuqar dacewa da shigar tata.

A nutse suke takowa ita da adam din suna hira qasa qasa,sanye yake da joggers pants dogo har qasa da kuma wata shirt me gajeran hannu,hannunsa yana riqe da hand bag dinta,daya hannun nasa kuma yana riqe da key din motarta,cikin kulawa tamkar wani bodyguard dinta.

Da kansa ya bude mata motar ta shiga ta zauna,sannan ya zagaya ya ajjiye mata hand bag din a kujerar me zaman banza,ya kuma durqusa saitin window din yana jifanta da wani narkakken kallo

"Karfe nawa zaki dawo?" Murmushin nan dake qarawa fuskarta kyau da daraja ta saki

"Zan iya kaiwa yammaci,inason na biya ta gidan momee" kai ya jinjina

"Banjin yau zan fita,inaso na huta,naso mu kasance tare,amma ba damuwa,da yammar ki zauna zan shigo gidan saimu wuce tare" kai ta jinjina masa,yayi kissing hannunsa ya hura mata iskar sannan yaja da baya,ta saki murmushi ta maida masa martani,ta kunna motar yaja baya ta tasheta ta fice a gidan a hankali.

Ajiyar zuciya ta saki idanunta nakan titi,kwanya da zuciyarta gaba daya ba abinda take bita sai kyakkyawan xaman dake tsakaninta da adam,wani irin zama me cike da fahimtar juna qauna tausayi da zallar soyayya,iyakar zamansu na shekara biyu ba zata iya tuna ranar data bata masa rai ko ya bata mata ba,kullum ita dashi cikin tattalin junansu suke.

Lallausan sautin wayarta ya katse mata tunaninta,ta dan dubi wayar kadan dake gefanta,sunan BESTIE A ya bayyana kan screen din wayar,ta saki murmushi har qaramin bakinta yana motsawa,ta miqa hannu ta daga wayar ta sakata a handsfree.

"Zaki shigo kuwa?,ko oga adam ya hanaki?" Murmushi ya qwacewa Saahar

"Hooo afifa ta adam....."

"A'ah.....adam dai na saahar,bar wannan zancan" ta katsi numfashinta,da alamu batason zancan

"To shi kam baice komai ba,infact ma ina kan hanya,ina fatan kina gida baki wuce zoo road din ba"

"Eh bankai ga tafiya ba,daman yau sai dare nake da niyyar tafiya"

"Okay saina qaraso" daga haka ta gimtse wayar ta ajeta a gefe tana dora dukka hannuwanta kan sitiyarin ta dafeshi,ta sauke ajiyar zuciya sosai,tana mamakin irin wannan rashin jituwa tsakanin adam da afifan,ta sani adam yana tsananin sonta,yana kuma yin komai don ita da kuma girman qaunar da yake mata,yayin da afifa take challenging duk wani tsari ko shiri na adam din,komai nasa baiyi mata ba,bai kuma dace da tsari da kuma hasashen da takewa rayuwar saahar din ba,saidai dukkaninsu ta yiwa kowa uzuri,ta tabbatar dukkaninsu qaunarta a zukatansu ne ta kawo wannan sabanin a junansu.

Tafiyar mintuna talatin kacal ta sadar da ita da shagari quaters,ta gangara layin dake shimfide da kwalta,gidajensa bisa tsarin da kana kallo kasan kusan dukka mazauna wajen suna da sukuni na rayuwa.

Gida me lamba 0009 ta tsaida motarta ta danna horn,babu jimawa mai gadin gidan ya bayyana,ya kuma dage qofar gidan cikin gaggawa sakamakon gane motar da yayi,ya maida qofar ya rufe bayan shigewarta da sauri yabi bayanta.

Duk da kasancewarsa ya fara manyanta amma hakan bai hanashi bude mata qofa ba yana fadin

"Barka da zuwa uwar dakina" yayi maganar yana dariya,ita dimma murmushi takeyi

"Baaba habu barka kadai,lallai yau nazo a sa'a,kamar kowa yana gidan ko?" Ta fada tana bin rumfar adana motocin dake gidan da kallo,wadda ke dauke da motocin uku na baqi,sauran kuma duka motar mai gidan da matar gidan ne

"Aikuwa duka basu jima da shigowa ba,sunzo alhaji dr ne" idanu ta fiddo adan rude

"Me ya samu abban?"

"Ba komai fa,jiya ne yadan kwana da zazzabi" da sauri ta fita a motar baaba habu ya kulle mata,ta bude jakarta ta cire kudi ta miqa masa

"Ayiwa iyali cefane" hannu biyu yasa ya karba yana kwarara mata godiya,bata tsaya saurarensa ba,don idan da sabo ta saba da godiyar baaba habu da bata qarewa.

"Allah ya tsareki ya kareki daga dukkan abunqi da kuma sharrin me sharri" ya furta yana juya kudin a hannunsa,ya jima baiga mutane masu kirki da karamci ba irin ahalin gidan Dr Mamman girema ba.

"maama" ta fada da hanzarinta sanda take shiga falon,saika dauka sun dauki wasu shekaru basu hadu ba,zallar kewa da kuma qaunar ganin mahaifiyarta ya bayyana muraran a muryarta,kiran kuwa ya iske matar har cikin kitchen dinta dake falon,tayi hanzarin daukar butar shayin data cika da zazzafan baqin tea wanda yasha hadin kayan qamshi masu kwantar da hankali ta fito tana cewa.

Fara tasss kamar diyarta saahar din,doguwa ce itama,amma shekaru da girma sun sanyata tayi jiki,duk da bamai yawa bane amma ya hadiye tsahon nata kaf,saita shiga jerin sahun mata masu matsaikatan tsaho kamar saahar din,kallo daya zakayi mata kasan cewa ta zuba tashen kyau qwarai da gaske zamanin quruciya kamar yadda diyarta a yanzu take.

"Eheeennn....aifa saike saahar,bansan ranar girmanki ba" ta fada murmushi na fita a fuskarta.

ƙanƙameta tayi sosai kamar zata koma cikinta

"I miss you maama"

"Sakeni saahar,kayan ruwan zafi ne a hannuna" sakin nata tayi tana gaidata,sannan ta karbi kayan hannun nata suka jera zuwa falon Dr,cikin sakalci take qorafi

"Yanzun abba baiji dadi ba amma maama a rasa me gayamin,banda Allah ya kawoni?"

"Bafa wani ciwo bane,zazzabi ne da ciwon kai,kuma hakan baya rasa nasaba da stress da rashin hutu"

"Amma ya kamata zuwa yanzu abba ya zauna ya huta,me yake nema Allah yayi masa komai" dan kyabe baki maama tayi

"Naji su yasir na magana akai,ban sani ba ko yanzun zai yarda ya huta din" daidai lokacin da suke isowa qofar falon,maama na gaba saahar din tana biye da ita.

Dattijon da duka duka shekarunsa ba zasu haura hamsin da takwas ba,zaune saman luntsuma luntsuman sofa's dake zagaye da qawataccen falon.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 36


Daga gefansa Aafiya ce durqushe saman qafafunta,matashiyar da suke sa'anni ita da sahar din,baqar fata mai haske gareta sabanin saahar dake fara tasss,saidai komai nasu kusan daya ne,kama daga tsahon da girman jiki,sanye cikin wasu gray material da aka yiwa dinkin riga da skert budaddu,tarkacen takardun abban take hadawa,daga daya hannun nasa kuma yaaya saifullah ne yake zare abun auna bugun zuciyar daya cusa qasan abun awon jinin daya nada a hannun abban,wannan kusan ba sabon abu bane,kusan duk bayan wani lokaci yana yima abban irin wannan gwajin,na hawan jini dana suger saboda kula da lafiyar abban,duk da bashi da komai daga jinin har sugar din,Allah ya bashi cikakkiyar lafiya.

Daga saman daya sofa din kuma yaaya muhyiddeen ne zaune,gefansa yaaya zainul-abideen da suke kira da yaa zain,dukansu hira suke a tsakaninsu,fuskar kowa qunshe cikin walwala da farincikin dake nuna zallar sukunin rayuwa da kwanciyar hankali daya samu matsugunni cikin rayuwar kowannensu.

Hawaye taji yadan tsatstsafo cikin idanunta,sai taji tayi missing gidan dama kowa da kowa,harda rayuwarta ta baya,ada ita keda wannan matsayin,ko yaushe tana daga gefan abban tana kula da buqatunsa,yanzu kuwa aure ya nesantata da komai dama kowa.

A shagwabe ta qarasa shigowa falon,ta kuma isa gaban abban daya tarbeta da dukkan kulawa,abu na farko ta fara qorafi akan rashin sanin rashin lafiyarsa

"Jiya ne kawai amma kinga yadda suka sanyani gaba"

"Me zakizo kiyi to,bayan gamu duk munxo?" Yaaya zain ya fadi,duk da ya girmeta,infact itacema qarama,amma time to time sai ya dan xungureta sunyi fadan sako da sako.

Baki ta tabe ashagwabe

"Ni kaina na sani da abbana kawai"

"Gaskiyarki auta ina bayanki" yaaya muhyiddeen ya fada yana murmushi,ta waiwaya tana sake masa murmushi

"Yauwa yaaya na na kaina" yaaya saifullah ne baice komai ba kasancewarsa shine babba,sai ta waiwaya tana gaidashi bayan ta gaida abban tayi masa sannu da jiki,ta gaida kowa ta waiwaya ga Aafiya

"Babu ko maraba bestie"

"Goyaki kawai zanyi yanzun nan,shine abinda ya rage ki gane nayi murna da zuwanki" dariya duka falon aka saki,don tsakanin Aafiya da saahar babu me shiga.

Shigowar saahar ya sake jinkirta tafiyar yayun nata,a nan suka sake sabon breakfast gaba dayansu,duk kowa ya cika cikinsa a gidansa kafin fitowarsa,basu watse sunbar falon ba sai kusan qarfe daya saura bayan abba Dr yasha maganinsa yadan kwanta.

Suna isa dakin aafiya dake gidan ta fara warware lafayar jikinta gami da warware agogon dake daure a tsintsiyar hannunta

"Bestie....bari nayi alwala nazo ki gyaramin kaina don Allah,ya dameni wallahi kwana biyun nan" idanu Aafiya ta fiddo

"Hala kin manta santsi da tsahon gashinki,sai yaushe zamu gama aikinsa" karyar da wuya tayi

"Haba mana bestie....."ta fada a karye

"Ya na iya dake,ina hutun sallah,idan kin fito sai muyi" Aafiya tayi maganar tana nutsewa cikin sofa din dakin gami da jan wayarta ta soma dannawa.

Tana idar da sallah Aafiya ta fara gyara matan,tanayi suna taba hira,abunda ya daukesu mai tsaho,sanda suka gama data duba agogo saita fidda idanu waje,ita da zataje asibiti allura?,lokaci ya qure tasan yanzun haka nurse din dake mata allurar ta tashi,batason kuma yauma su sake missing allurar kamar jiya,ta fuskanci hankalin adam bazai kwanta ba sai ta tabbatar masa tayin

"Bestie taimaka kiyimin allura mana" sosai ta waiwayo tana duban saahar

"Allura?,baki da lafiya ne?" Aafiya ta jefa mata tambayar dai dai sanda take amsar allurar daga hannun saahar.

Juya allurar ta fara yi tana kuma qoqarin karantar allurar meye,dukka idanunta ta fitar waje,cikin mugun gigita ta watsasu kan fuskar saahar

"Wannan allurar kice?,ko acan pharmacy din sukayi mistake din baki ita?"

Janye idanunta saahar din tayi daga kallon tuhumar da Aafiya keyi mata,bayan ta tsareta da dukkan kallo na idanu da kuma kunnuwanta,sam ta sha'afa cewa wani babban sirri ne,sirri ne da suka tsarashi tsakaninta da adam,bata tunani duk duniya akwai mahaluqin da yasan da wannan babban sirrin idan ka dauke mommee din adam din

"Allurar planning bestie?,tun yaushe kika fara?" Aafiya ta jefawa saahar tambayar tana tsareta da dukkan wani kallo dazai nunawa dan adam tsantsar tuhumar da ake masa mai tsananin qarfi da kaifi.

Shuru saahar tayiwa Aafiya ba tare data amsa mata ba,yayin da Aafiya taci gaba da tsareta da kallon tana jin wani daci yana ratsata har saman harshenta,kwanyarta ta cika da nau'ikan tani iri daban daban,zuciya nata yi mata hasashe kala kala.

Tasan saahar sosai har fiye da yunwar cikinta,shurun da tayi yana tabbatar mata da cewa batayi shirin amsa mata tambayarta ba,kuma muddin ta kafe akan abu,la shakka bata isa ya juyata kota sauya mata ra'ayi ba,don haka ta kwantanta yin barazana gareta ko zata samu taji bayanan da zuciyarta keda muradin ji daga bakin 'yar uwartata. Wannan ya sanya ta miqe tsam da allurar a hannunta tayi qofar fita a dakin.

Cikin wani irin zafin nama da dukkaninsu basusan saahar din tana dashi ba ta miqe,cikin matuqar sa'a ta samu nasarar cafkar hannun Aafiya

"Ina zaki?" Waiwayowa tayi ta watsa mata wani kallo

"Zanje na nunawa maama da abba abinda kike aikatawa kanki"

"Baki da hankali ne?"

"Nice bani da hankali ko kuma kece saahar?" Ta kirayi sunanta kai tsaye abinda ba kasafai take yinsa ba.



Please Login or Register in order to submit comment