Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 30 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tayi kiransa koda lokuttan da take da yaqinin baya tare da fadeelan,tun da jimawa ya fahimci tana hakanne don taji tasa muryar da lafiyarsa,tunda har yanzu hannayenta sun gaza iya koyar daukar wayar suyi kira a nata lambobin da layin domin suji lafiyarta,koda wasa.....koda sau daya......koda da gwaji. Wani al'amarine da yake damun qwaryar zuciyarsa qwarai cike da wata irin damuwa,amma ya gaza ta kowacce fuska.....ya gaza kawo gyara koda qanqani ne.......sau tari yanajin naqasu,gazawa da kuma kasawa,hadi da wata cikakkiyar tayawa me wawakeken girma daga rayuwarsa,amma baisan ta yadda zai gyara ba.....ta ina?,kuma a yaushe?,rashin matallafine ko kuwa?,duka shima bai sani ba.

"Allah ya kiyaye,ya tsare, ubangiji ya bayar da dukka sa'a da kariyarsa,fatan alkhairi" ta fada a taqaice ta kuma gimtse wayar.

Wani abune ya sauko ya daki zuciyarsa,take tayi wani irin rauni,yanajin wata irin kunyarta na mamayarsa, kunyar da dukka d'a na qwarai yakeji a lokacin da yayi wani abu na sabawa ga iyayensa,duk da a karan kansa yasha gayawa kansa shi din ba na gari bane......yanajin wani irin karyewa a tata muryar,kamar wadda kuka ke shirin subucewa,amma duk yadda yaso ya juya zuciyarsa ta bita don taji meye damuwarta ya kasa,sai ya soke hannayensa guri guda yana matsesu da wani irin qarfi,kamar yana shirin ballasu.

⚜️⚜️⚜️ Kebantacce falo ne wanda ke dauke da wasu qasaitattun kujeru da suka zama cikamakin cikar adon falon,bashi da wani girma,amma yana da tsari me matuqar kyau tare da jan hankalin me kallo.

Saman daya daga cikin kujerun falon sãahar ce zaune,cikin kamilalliyar shigarta ta jilbab,wanda yake hade da doguwar rigarsa me dogon hannu,gefe da gefe na dan qaramin hijabin madin rigar a tsage yake,an masa wani irin ado daga bakin tsagar,farar kyakkyawar fuskarta ta fita sosai ta tsakiyar fuskar hijabin da wani irin kwantaccen kyau me daukan hankali.

Tun farko shigowarta gidan take nazarinsa daya bayan daya,ta kowacce fuska gidan ya amsa sunansa,ya kuma sake bayyana mata tarin dukiya tare da arziqin da masu gidan suka mallaka. Ta taso cikin gata soyayya kulawa tsakiyar nasu arziqin da dukiyar,tun daga kan mahaifinta zuwa yayyenta,hakanan dangi na mahaifi da mahaifiya,amma a yau daya,cikin mintunan da basu gaza goma ba kanta yana shirin kwancewa ta zama 'yar qauye cikin gidan.

Ba iya wannan ba,ta lura akwai tarin doka da bin tsari daga dukkan ma'aikatan gidan,kula gami da takatsantsan da tsoron kaucewa qa'ida,tun daga mai gadi,zuwa wadda ta rakota qofar sassan hajiyar gidan,kawo wadda ta kawota wannan falon da take zaune a yanzun tana jiran isowar matar,don ta ganta ta kuma karbeta gami da sake mata bayanin aikinta cikin gidan.

Wayarta na hannunta a lokacin tana shaidawa afifa ta iso,afifan da tace sam ita ba zata iya rakota ta ganta a bigiren 'yar aiki ba,saidai duk da haka batayi fushi ba,tana maqale a online tana bibiyar dukka motsin bestie din tata.

Qarar takalmin da ya fara ratso falon yaja hankalinta,saita kashe data dinta,ta kuma ajjiye wayar tsakanin qafafunta,ta daga kai tana aje dubanta daga guraben da sautin tafiyar yake fitowa.

Guri guda idanunsu suka hadu nata dana hajiya qaramar. Daidaita kallonta ya sakeyi kan fuskar sãahar duk da bata kai ga qarasowa gurin ba,wani abu yana sauka a zuciyarta,tanason ta karanceta irin karatun kallon farko,tanata qoqarin daidaita zuciyarta da taji kamar ta tsaya guri daya,ta gaza wanzar mata da kowanne feeling akan sãahar din,ba kamar yadda takanji ba akan sauran dukka nannys din fadeela na baya da sukabar gidan.


Page 60

*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔

Page 60

Cikin takunta na qasaita da nuna isa ta qaraso,ta dauke filon dake saman kujerar dake fuskantar sãahar din ta zauna,tana maida filon saman cinyarta,bayan ta dora qafarta daya saman daya

"Sãahar ko?" Hajiya qaraman ta jefeta da tambayar sunanta kai tsaye,kai ta gyada mata cikin tabbatarwa gami da furta

"Eh nice,barka da yamma"

"Barka kadai" ta amsa mata tana qare mata kallo a fakaice,zuciyarta cike fal da mamaki irin sassanyan kyan da yarinyar ke dashi,babu alama ko digo dake nuna wahala ko buqata daga jikinta,asalima ko ita din sãahar din fatarta tafi tata nuna jin dadi da hutu,to amma ta wani bangaren tasan zata samu nutsuwa,zata samu sauqi itama,ilimi zallah ya nuna kansa tattare da sãahar din.

Gyara zamanta tayi tana sauke qafafun nata,har yanzu idanunta akan fuskar sãahar din,kyanta yana sake bata mamaki

"Nasan mrs sadeeqa ta gaya miki komai,so amma koda zata gaya mikin ba komai zata iyayi miki bayani ba kamar yadda ni zanyi miki.....da farko kina iya kirana da hajiya ko hajiya qarama ko mommy qarama,kusan nice shugabar gidan nan,kowa da kika gani ya kwana ya tashi cikin gidan nan qarqashin ikona yake,hatta dashi me gidan kansa da abinda ya mallaka ya kuma haifa......aikinki guda daya ne tal cikin gidan nan,kula da jikata tamkar ke kika haifeta,munason ta samu kulawa fiye da yadda zaki bawa kanki kulawa,saboda yanayin ciwonta,bamason kiyi nesa da ita,saidai idan tayi bacci ne, kuma koda kin koma naki dakin zakici gaba da dubata ne gudun faruwar wani abun,wankanta da tsaftarta yana wuyanki,abinda zataci kuma wannan ba dolenki bane" sai Tayi shuru tana maida numfashi. A nutse sãahar ta daga kai tana dubanta tare da nazarin kalamanta,wanda suke cakude da sautin izza a cikinsu

"Fadeela.....ita daya muke da ita,itace sanyin idaniyarmu,farincikinta shine namu, sabawa daya daga cikin ayyukankin nan suna iya zama silar rasa aikinki" ci gaba kawai sãahar tayi da nazarin mommy qarama tana kuma kallonta

"Kin fahimta?" A nutse kuma a hankali ta gyada mata kai

"Da kyau,gidan nan yana da tsari,bawai zama bane kamar na sauran gidaje da kika sani,abu na gaba kowa aikinsa ya sanya a gaba,ba ruwan wani da shiga sabgar wani,ban yarda da zama tsakanin ma'aikata ana hira ba,kowa yayi abinda ya kawoshi ya wuce mazauninsa" shuru ta sakeyi tana kallon yadda sãahar ta kame,ta kuma bata hankali tare da manyan fararen idanunta tana kallonta

"Magana ta qarshe" ta furta tana zama serious sosai

"Nasan kinsan kalar ciwon da yake damun shelelenmu,right?" Kai ta jinjina tana ci gaba da sauraronta

"Yauwa,akwai magunguna da takesha,so gaskiya banason yawan qwayoyin da yake yawan bata,saboda haka duk lokacin da ya dace tasha magani zan shaida miki,kota waya,ko na tako har zuwa sashen da kaina,ban yarda ba ko sau daya ki dauki magani ki bata ba tare da sanina ba" wanann maganar ita ta zowa sãahar din a hagunce,sai ta gyara zamanta itama,ta kuma dora qafarta daya saman daya ba tare da tasan tayi hakan bama

"Amma why not ki yiwa likitan magana,idan zai yiwu da kansa zai fada,zai kuma rage mata,idan wasu kuma za'a yi exchanging dasu duka zai fadi"

"Look!" Hajiya qarama ta fada tana fidda idanunta waje

"Ina cewa ko minti biyar banyi ba da gaya miki rule's na gidan nan,who are you da zaki shiga lamarin da bai shafeki ba daga zuwanki?,na gaya miki hakanne don na taimakeki,bijirewa hakan zai iya shiga list na dalilan rasa aikinki" mamaki ne ya kama sãahar,tadan yamutsa fuska kadan tana juya maganar a ranta,kaf cikin maganar bataga inda tayi wani lafazi da bai dace ba

"Ke ba kowa bace face nanny da zatayi aiki a biyata" zuciyarta da kwanyarta suka tuna mata matsayinta cikin gidan,sai ta zame qafafunta data dora saman na juna a hankali lokacin da taga hajiya qaraman na kallon yadda ta hade qafafun

"Am sorry,zan kiyaye in sha Allah"

"Kin samawa kanki lafiya" ta furta tana sake tsuke fuskarta,saida can qasan ranta tana cike da mamakin yarinyar,kwata kwata batayi kama da masu aiki ba,koda kuwa makaho ne ya shafa zaiji hakan,duk da sun nema well educated amma kuma wannan kamar ajinta ya d'ara wajen.

Waya ta dauka tayi kira na qasa da second goma sha biyar,cikin minti daya tak matar ta iso,daya daga cikin masu aikin gidan,wanda basai ka tambayi hakan ba,saboda uniform da take sanye dashi,ta rusuna cikin girmamawa

"Sabuwar nanny din uktie,a kaita sassansu,ki damqata a hannun baaba ramatu"

"An gama ranki ya dade" ta fada cikin rusunawa,luggage din sãahar din ta dauka tayi gaba,don dukka nanny din data kasance ta fadeela ce a gidan,tana samun wani respect da kyautatawa darajar fadeelan,wannan haka tsarin gidan yake.

Har takai qofa momy qarama na rakata da kallo,batasan me yasa yarinyar ke jan hankalinta har haka ba,yadda take takunta a nutse daya na bin daya kadai yana nuna mata kamar akwai wata extra qasaita a jinin yarinyar

"Sãahar" ta kirayi sunanta da dan kaushi kadan,dakatawa tayi sannan ta waiwayo tana dubanta

"Mrs sadeeqa nada matuqar kirki,tana kuma da darajar da zata baki dukkan wata kima da martabawa a gidan nan,ba tare da ko na miki screening ba na dauki aikin kula da 'YAR SO na baki,ki kula da kyau,kada kuma ki gota iyaka" har yanzu kalaman matar basu daina bata mamaki ba,sai ta saki wan siririn murmushi ta jinjina kai kawai,sannan ta juya a nutsenta tana barin falon,tabi bayan ma'aikaciyar.

Kamar ko yaushe katafaren ni'imtaccen falon nasu a tsaftace yake sannan killace,iskar na'urar sanyaya daki tana busawa ta kowacce kusurwa na falon tana cakuda da qamshin fresheners.

Sau biyu me aikin tana sallama kafin qofar glass ta falo na biyu ta bude,baaba ramatu ta fito cikin kamalarta da carbi a hannu,da alama tana azkar din yammaci ne

"Qaraso mana,ke da baquwa ce?" Tayi tambayar idanunta akan sãahar dake tsaye a baya

"Nanny din fadeela ce hajiya tace a rakota" juyawa baaba ramatu tayi tana duban sãahar,sai kuma ta sakar mata murmushi

"Maraba,sannu da zuwa,Allah yasa tana jin hausarmu" tayi maganar cikin tantamar sãahar din tasan zo na kasheka da hausa. Murmushi ne ya subucewa sãahar din,karon farko tun shigowarta cikin gidan,yadda dattijuwar tayi magana cike da barkwanci yana burgeta

"Ina yini?" Ta fada a nutse don kore shakku daga zuciyar baaba ramatu,a mamakance riqe da baki t juyo ga sãahar

"Ma sha Allah,lafiya alhamdulillah,sannu da zuwa"

"Yauwa sannu" ta maidawa baaba ramatu

"Shigar mata da kayan nata ciki,dazu dazu aka kammala kintsa dakin muje ko 'yata?" tayi maganar da sakakkiyar murya tana yi mata jagora ga tsararren hallway din da zai sadaka da dakunan baccinsu.

Daya daga cikin qofofin dake kulle baaba ramatu ta tura ta shiga tana cewa sãahar

"Bismillah" sai tabi bayanta,bakinta dauke da addu'ar shiga sabon guri ko zama a baqon guri. Daki ne me yalwa wanda yake dauke da qawatattun kayan gado 'yan asalin qasar turkey,komai na dakin kwantacciyar kalar yellow green ne me kyau da daukan hankali,kalolin dake qarawa idanu qarfin gani,dakin nada wani irin tsari me burgewa,bai cika girma ba,hakanan bai cika qanqanta ba.

"To ga dakinki nan,idan kina da buqatar wani abun kina iya magana a kawo miki,aikinki kawai ki kula da fadeela" baaba ramatu ta fada cikin murmushi. Murmushin itama tayi

"Bana buqatar komai,amma ina ita babyn?,inaga ita ya kamata na fara gani ko?" Qaramin murmushi ya sake sauka a fuskar baaba ramatu,haka kawai kallon farko taji sãahar tayi mata,fadeelan bata tana nanny irinta ba,yawancinsu tun daga hanyar shigowarsu gidan zuwa hanyar isowarsu dakin suke rudewa da kalle kalle da kuma santin tarin dukiyar dake jibge a gidan,hakanan duka cikinsu babu wadda ta taba tambayar a kaita gurin wadda tazo gidan aiki dominta,har sai baaba ramatun ta buqaci hakan

"Tana dakinta,tun dazun taqi fitowa rigima takeji,tunda babanta yayi tafiya dazun ya barta take fushi da kowa harda ni dana daukota daga waje,ko abinci taqi ta karba" baaba ramatu ta fadi tana dan dariya.

Kai sãahar ta girgiza tana dan murmushi

"Ayyah,tana kewarsa ne tun yanzu,muje na gani ko zata yarda ta fito" gaba baaba ramatu tayi tana dan yi mata hirar fadeelan,yadda halayyarta da dabi'unta suke. Qofar dakin dake facing ta sãahar din baba ramatun ta tura ta bude, tsararren dakinta cikin kalolin white cream ya bayyana,wani irin daki da yafi kama da dakin hamshaqiyar mace me aure,dakin dake aka sanya masa dukkan wani abu na buqata jin dadi da kayan qawa,wanda hakan bai sanya ya cika tarkace da yawa ba,sai wani irin kyau da tsari na musamman daya bayar,ga tasirin tsafta sosai a tare dashi,ko ina qal qal yana fidda qamshi me dadin gaske.

"Fadeela" baaba ramatu ta ambaci sunanta sanda suke shiga dakin. Tana nade cikin duvet,ko motsi batayi ba

"Ki tashi ga sabuwar me kula dake tazo ganinki" kafadarta ta maqale,ta kuma bubbuga qafafunta

"Bana sonta" idanu baaba ramatu ta zaro waje tana kallon sãahar cikin rashin jin dadin kalaman fadeela,sãahar din da siririyar muryar fadeelan ta sanyata dariya tare da qarin dariyar zallar quruciyar data fuskanta tattare da ita

"Kul na qarajin kince bakiso wani,bakya sonta?"

"Eh ta koma,saboda nima daddy ya tafi...." Ta fadi tana yaye duvet din da sauri,sai kuma ta tsaya cak tana rarraba kallonta akan fuskar sãahar dake jifanta da murmushi. A hankali ta zame duvet din duka daga fuskar tata tana ci gaba da kallon sãahar.

Waiwaya sãahar din tayi ta kallo baaba ramatu

"Baaba a kawo abincin nata"

"To shikenan" ta fadi tana juyawa ta fice daga dakin,cikin ranta tana jin cewa sãahar din zata bada fiye da abinda ake zata.

Bata taka ba taci gaba da kallon fadeela tana murmushi,har sai da yarinyar ta miqe ta zauna sosai da kanta,sannan ta sauke hannuwanta ta taka zuwa bakin gadon ta zauna daga gefanta

"Kiyi haquri" sãahar ta fada tana kallonta,tana iya ganin sanda ta waiwayo da sauri tana kallonta,saita sake mata murmushi

"Ummmm"

"Ba abinda kika yimin fa amma kike cewa nayi haquri"

"A'ah,kince bakya sona,na dauka nayi miki wani abun" kai ta girgiza da sauri,saita shagwabe mata

"Abby ne ya tafi ya barni,bayan yace bazai sake tafiya ba dani ba" siraran hannuwan yarinyar ta kamo tana kallonsu,babu wata qiba sam,kamar bata cin wani abu da zai gina mata jiki,duk da daular da take ciki,saidai kyau da gogewar fata kawai

"Abbynki ba zaiyi qarya ba,lallai uzurin da sai yayi tafiyar ne kuma ba tare da ke ba ya kamashi,but na tabbatar bazai dade sosai ba" murmushi ya qwacewa fadeela

"Shima haka yacemin"

"So....you must trust him" kai fadeela ta jinjina tana murmushi

"Wait.....yanzun kinci abinci?" Kai ta girgiza fuskarta na sake narkewa,ido sãahar ta zaro

"Eehhhh,bakyason abby ya dawo yaga kin zama qatuwa?,baby fadeela ta zama 'yar lukuta?" Dariya fadeelan ta saki,yadda sãahar din ke bubba hannayenta tana mata sign na qiba

"Inaso auntie,inaso"

"Good,chubby fadeela"

"Yes anty,not slimy,a chubby,a daina tsokanata a school"

"Aha,oya gate up" tayi furucin tana miqa mata hannunta,sai tayi hanzarin dora nata hannun,cikin kulawa sãahar ta riqeta sosai ta sauko da ita tana karantar yadda walwala da farinciki ya maye gurbin bacin rai data dawo ta sameta a ciki,wani irin nau'in tausayinta ya sake saukar mata,saita ajjiyeta saman lallausan carfet din dake gaban gadonta,itama ta zauna akai,ta fara diban abincin tana bata a baki.

"Kin iya feeding mutum like my abby" murmushi sãahar tayi

"Really?" Kai ta gyada mata

"Okay,nayi alqawarin zaifi na Abby din naki gaba kadan. Wani dariya me cike da nishadi fadeelan ta saki, sãahar ta tsaya kawai tana kallonta,an gaya mata tana da wuyar sabo sosai,nannys dinta suna jimawa kafin ta fara sakin jikin dasu,duk da ba wani dogon zango sukeyi ba a gidan,amma sai gashi ita lokaci guda ta sake sosai da ita.

uhmmm,ga sabuwar nanny a sheqar da batasan ta waye ba, za'a dore kuwa?,to lokaci shi zai nuna mana,asha hutun weekend lafiya,fatan alkhairi a gareku gaba daya,masu comments ina gani na gode sosai,gurin amsa comment dinne baya dannuwa,but am really appreciating

*HUGUMA*


*_TABARMAR KASHI_*


Page 61

Tsaf ta gyara gurin bayan ta gama bata abincin,duk da akwai wadda ke da alhakin hakan amma bata jira ba,ta shiga toilet dinta ta wanke hannunta,ta zari towel din dake ajiye musamman saboda goge hannu tana gogewa
baaba ramatu ta shigo.
Tayi mamakin yawan abincin da taga taci
"Ke ai baki iya bayarwa ba,new nanny ta fiki iyawa" baki ta kama tana dariya "'yeee,zakici qaniyarki,yau nice ban iya bada abinci ba?,tun kina koyar yadda akecin abincin to ni nake baki don gidanku" dariya ta saki tana buga tsalle a gadon,abinda yasa sãahar murmushi kenan tana dan binta da kallo,abinda ta karanta,yarinyar nada sauqin kai,sanann irin mutanen nan ne masu son abinda zai nishadantar dasu,a yadda ta karanta gasa da minti arba'in a tarayyarsu,tana bugatar kulawa da zata dace da hankalinta.


A dakin ta barsu,ta dauki excuse don ta kintsa kanta da dakinta. Tana shiga ta zare mayafin jikinta ta ajjiye saman gado tana furzar da iska daga bakinta,yarinyar ta shiga ranta lokaci guda fiye da yadda tayi zaton zata kasance,wani abu takeji game da ita a ranta,tana jin kamar daga jininta ta fito.
Sai data gama shirya kayanta a wardrobe tsaf ta fidda komai ta ajjiyeshi a muhallinsa,bath stuff dinta ta kaisu bandaki,sannan ta zare kayan jikinta ta shiga bandaki tayi wanka. Koda ta fito cikin wata doguwar riga ta lallausar auduga ta shirya,ta
gabatar da sallah,zuwa lokacin dakin ya fara
kama qamshin turarukanta masu sanyin
qamshi.

Hijabinta ta zare ta tsaya bakin mudubi
tana taje gashinta,ta gama tana hadeshi akayi
knocking,ta qarasa a nutse ya yafa qaramin
hijab ta bude gofar.
Me dafa abincin sashence,itama sanye da
uniform dinta,saidai su nasu akwai banbancin
color dana sashen hajiya qarama dana sauran
ma'aikatan dake gidan,nasu din fari ne qal da
ratsin bagi

"Its time for dinner maa" ta fada cikin
rusunawa

"Alright,thank you" ta fada cikin sauqin kanta da ba kasafai yake bayyana tattare da ita ba.

Ciki ta koma ta fidda slippers din da aka bata cikin wata jaka,wanda qa'ida ne na dukka ma'aikacin da zai fara aiki cikin gidan,ta sanya a qafafunta,saita kashe wayarta ta jona a charge da nufin sanda zata dawo ya cika,sai tayi kiran dukkan wanda ya kamata,don batason suyi kiranta bayan bata nan,ta maida qaramin hijabin daya sauka har kusan qugunta sannan ta fito a dakin.
Kai tsaye dakin fadeela ta koma,ta sameta sunata rigima da baaba ramatu akan kayan da zata sanya, kowa da yake gidan ya saba da wannan agenda din nasu,sosai take maidata kamar kakarta. Cikin hikima da dabara ta fidda mata wasu kayan,da lallashi ta sakata ta sanyasu,bayan tayi mata alqawarin bata zabin kayan baccin duk da takeson sakawa,sannan suka fito cin abincin ita da fadeela da baaba ramatu.
A gasa sãahar ta sauko musu dasu,sabanin yadda suka saka ci a saman table. Sãahar ta buda abincin tana gare masa kallo. Abinci ne yankunan Europe da Asia,saita ajiye murfin warmer din tana duban fuskokinsu. Ba wani karsashi a fuskar baaba ramatu,amma fadeelan har zumudin a zuba mata takeyi. Damar zubawa ta bawa baaba ramatu,ita kuma ta zubawa fadeela,sannan ta zauna ta bata da kanta kamar wancan lokacin,sai data tabbatar ta qoshi sannan ta zauna sosai,kadan ta tsakura ta ture,don ba jituwa tsakaninta da abinci, especially ma abincin dare, tafi qaunar coffee fiye da komai a rayuwarta.
Suna daki tana shirya fadeelan wadda taketa gogarin bata labarin abby dinta, magana daya biyu saita sakoshi, murmushi kawai sãahar ke binta dashi,tunda batasan komai a kai ba,kawai dai tana ji a zuciyarta cewa yarinyar ta rabauta da uba daya san darajar diyarshi,yake bata dukkan kulawa,ya kuma damu da damuwarta. Ruwa me dumi sosai tayi mata wankan dashi,ta shiryata cikin wasu kayan bacci masu taushi dai dai da shekarunta,ta sake mata gashinta yadda zatafi in dadin kwanciya.

Har wani lumshe idanu fadeela keyi,tana jin dadi sosai a jikinta

"Aunty nanny kin iya wanka wallahi" dole dariyar da saahar batayi niyya ba ta qwace mata,ta rige siraran hannuwan fadeelan

"'Wankan ma akwai wanda yafi wani dadi?" Kai ta gyada

"Sosai,na abby da naki yafi dadi, amma shi abby sai ya daina yimin, waina girma,sai randa na fadi bani da lafiya shine yakemin" ta garasa maganar cikin karyewar murya dake nuna itama tasan halin ciwon da take ciki
"Aunty nanny,abby yace wai zan warke watarana hakane?" Qwalla ce ta cika idanuwan sãahar,saita jawo ta ta zaunar da ita saman cinyoyinta

"In sha Allah, kina addu'a?"
§ . 865 4C16
"' Ai ban iya ba" fuskarta ta dago ta shafa, komai nata siriri,saita saki murmushi
"Zan koya miki,zamu dinga sallah abby's chubby" magaleta tayi tana dariya saboda sunan ya mata dadi. Dai dai lokacin aka turo gofar dakin fadeelan.
Dukkansu suka daga kai suna duban me shigowar,mommy qarama ce,cikin wasu kayan bacci da suka zubu,tayi rolling da wani qaramin mayafi kalar kayan,ikinta sai fidda qasaitaccen qamshi yakeyi. Miqewa fadeela tayi ta isa gurinta,saita miga hannu ta ruqota suka qaraso cikin dakin
"Mummy amma abby bazai kori wannan nanny din ba ko?,ita ina sonta sosai" ta fadi tana dora kanta akan cinyar hajiya garama. Hannu ta dora saman kanta tana shafawa,idanunta akan fuskar säahar
Нд
"'Indai ta kiyaye doka da qa'idoji,sannan ta riqe alkinta ta kula dake yadda akace mata"
"Mommy tana kula dani sosai" tayi maganar da accent na quruciya a muryarta
"Okay,jiki wajen baaba ramatu kice ta baki kayan dana bata ajiya", fellawa tayi da gudu ta fice, saita tattaro hankalinta kan säahar.
Idanu tadan kafeta dashi,wasu lokutan takanji shakka da kokwanto akan yarinyar,tana da wani irin kwarjini da bata ganinsa saman fuskar kaf ma'ikatan gidan sai ita,sannan daga shigowarta zuwa yanzu ta fahimci kwata kwata bata rawar jikin da dukka maaikacin daya shigo gidan yakeyi,kamar zai kwanta a hanyarta tabi ta kansa,dazu data kira mrs sadeega ta gaya mata haka yanayin ta mrs sadeeqa ta gaya mata haka yanayinta yake,bata da son yawa surutu da kuma hayaniya,MISKILA CE.
Ад
miskilar data fadi shi yafi qara kwanta mata,saboda tasan muddin tana da wanna dabi'ar ba zata saba da kowa ba,ba kuma zata zauna tayi hira da kowa ba akan abinda ya shafi gidan ba,aikinta kawai zata yita yi babu waiwaye ba duban kowa.
Wata jaka ta ajjiye mata tana Kallonta
"Ya lafiyar fadeelan?”

"Alhamdulillah" ta amsa mata a taqaice tana kwashe cosmetics din yarinyar data bazasu a gasa

"Madallah,wadannan...
...sune magungunan

ta,zaki dinga bata da safe da rana bayan ta dawo daga school sai da dare idan zata kwanta,kamar yanzun kenan,ba'a son fashi ko daga qafa,ki kula da kyau,ba kowa ake nunawa maganinsu ba,idan ya qare ni kadai zaki gayawa,zan sake kawo wasu,a ciki akwai tablet dinta,u are educated a yadda aka bani information dinki,so koda baki taba amfani da ita ba zaki iya hada mata ita,na sanya an dora komai daya dace a kanta,so amfani kawai zata fara yi da ita" kai ta gyada kawai
"Ki kular mata da tab,na tabbata bakisan darajarta ba,abace me tsada daga kamfani me daraja ta daya a duniya" sam sãahar din batasan murmushi ya subuce mata ba sai da taga hajiya qaraman na kallonta sosal,saita buge da gyada kai
"In sha Allah " ta fada hankali kwance,cikin ranta tana mamaki,haka 'yan aiki sukeji?,haka ake dizgasu? ta godewa Allah data rayu a gidansu taga yadda ake karrama masu aiki,ta godewa Allah da bata taba sha'awar dauko me aiki a ravuwarta ta baya ba,ashe suma suna jin babu dadi idan aka fadi wani kalma na qasqanci a kansu,suma mutanene kamar kowa,a yanzun abinda yasa itan bataji wannan ciwon ba,saboda tasan daga inda ta fito, tablet zata iya cewa dai dai take da 'yartsanar wasanta,batasan nawa ta lalata ba tun kafin tayi hankali,ta yayunta da maaminta kafin ta mallaki nata kala kala.
"Muddin wani abu ya sameta zan cirene cikin albashinki" wata dariyar taso taso mata amma saita danne ta sake gyada kai. Dauke idanunta hajiya qarama tayi daga kanta,tana mamakin yadda maganar bata dameta ba,ta fada ne don ta mata ciwo,amma bata alamun wannan a tare da ita ba.
"Nawa kika yanke salary dinki,monthly ko weekly?" Hajiyan ta fada bayan ta miqe tsaye
"Wannan ba matsala bane,aikin yafi salary din muhimmanci" da sauri ta waiwayo tana dubanta,maganar taba fusgar hankalinta,sai ta dawo da baya tana tsareta da ido

"Ban gane ba,meye alaqarki da yarinya da aikin yafi miki kudin muhimmanci?,ana aiki don kudi ne haka ne?" Kai ta gyada tana lumshe ido. Ta girgiza kanta a nutse
"Ba haka nake nufi ba,shi kula da yaro lada gareshi me tarin yawa,koda ba'a biyaka a nan duniya ba,ladanka na qiyama yana jiranka,abinda ubangiji zai maka sakayya dashi,yafi kudin da za'a baka" qogarin dai daita yanayinta hajiya qaraman tayi tana jinjina kai,sai ta juya ta fice kawai ba tare da tace mata komai ba.
Da kallo ta bita har ta fice,saita dauke dubanta daga kan hanyar tana qoqarin fidda abinda zuicyarta keson suranta mata,ta jawo ledar ta buda kayan da suke ciki. Tashi tayi ta yiwa tab din gurin ajiya me kyau,sannan ta dawo ta zazzage magungunan.

Zama tayi sosai tana binsu da kallo,mamaki yana dan kamata,wasu irin tablet da babu rubutu a jikin robobinsu bare kaga bayanin da kowanne magani ke zuwa dashi. Ta

Please Login or Register in order to submit comment