Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 16 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yakeyi,saika dauka yanzu yanzu ta gama fesa turarukan nata,kabbasa ce me dan karen qamshi data dade da bin jikinta,bayan body mist da sauran turaren kaya da take using dasu masu dan karen tsada da kyau,tana iya kashe ko nawa ne ta siya turare,ba kamar sauran tarkacen makeup ba da har yau saidai a siya mata,don ba wani damunta sukayi ba,gwara gwara powder ma.

Tare suka taho da miss sameera,suna dan tattaunawa akan abinda ya shafi aikinsu. Dab da zasu gifta office dinsa idanunta ya sauka a kansu,can qasan ranta tayi qwafa gami da duke kanta,don ko ta qofar office din bason gifatawa takeyi ba bare wani abu ya kaita,har ya hadata mu'alama da mamallakinsa.

Babban hall din company a nan ta taras da ma'aikata masu yawa,kowa yana saman kujerarun da aka warwatsa a gurin, gurin sama na musamman aka bata ta zauna tana maida hankalinta ga babban allon majigin dake iya nuna yadda kowanne abokin aiki ke qoqarin yin kutse a na'urar dan uwansa amma wancan yana tosheshi. Tun bata jima da zama ba wasan ya dauki hankalinta sosai,bama ita kadai ba,kusan duk wanda yake wajen abun ya matuqar qayatar dashi,mayun na'ura aka hada team dinsu guda kowa yana qoqarin baje fasaharsa.

Sosai wasan ya dauki zafi,ya kuma dauki hankula,har haka ya sabbaba tashin 'yar hayaniya a hall din saboda ana gab da gangara a wasan.

Ba zato ba tsammani sai gashi ya bayyana a gurin,da yawa basu lura da shigowar sa ba,har sai daya fara zuwa tsakiyar hall din,sannan kowa ya fara shiga taitayinsa,cikin girmamawa kowa ya fara duqar da kansa yana miqa masa gaisuwa. Ko gaisuwar mutum daya bai amsa ba,yaci gaba da takowa ciki,cikin izza da qasaitarsa,hannayensa zube a aljihun suit dinsa,fuskarnan a dinke tsaf kamar ko yaushe,murtukewar kuma da bata taba hana bayyanuwar kyansa.

Bai tsaya ba har ya isa ga kujerar da CSO yake tsaye a gabanta,yadan russuna cikin girmamawa

"You are welcome sir" ya fada a ladabce,yana mamakin yadda akayi yasan da game din,bayan basu tura takardar gayyata office dinsa ba. An rasa zaququrin da zai tura ne saboda zallar shakkarsa da sukeyi,dukkansu jikkinansu sun basu bazai dauki wannan da muhimmanci ba bare ya halarta.

Idanunsa masu kaifi ya zube masa yana jifansa da kallon da ya sanyashi qas da kansa,cikin husky voice dinsa data qara wani zurfi da bacin rai a cikinta yace

"what nonsense are you doing here?" Kadan ya dago ya saci kallonsa,yadan sosa kansa sannan yace a ladabce

"Ba shirme bane sir,and It's not a joke, it's a game to strengthen the security team"

"Who gave you permission to do it?,a tsakiyar ranakun aiki saboda rashin sanin muhimmancin ayyukanku?"

"Sorry sir,munyi requesting wa office din president,da muka samu tabbacin zuwanta munyi tunanin wannan ya wadatar......". Ambatar sunanta yasa ya gama fahimtar inda komai ya dosa,tunda ya shigo da safen yaci karo da sabbbin ma'aikatan da baisan da zamansu ba dama,yaga kuma aikace aikace masu yawa da shi yasan bai sanya hannu don a gabatar dasu ba,saboda yana da nashi plan din da yakeson ya kammala a qaddamar dasu duka a tare kuma lokaci daya.

Waiwaya yayi yana duban sashen da take,tana zaune akan seat dinta,har zuwa yanzu bata tashi ba,hakanan bata motsa ba,tana ci gaba da latsa system din gabanta,duk da cewa an dakatar da komai amma ta shiga wani sashe daban,zakayi tsammanin batasan me yake faruwa cikin hall din ba.

Kafeta yayi da idanu,ransa yana sake baci,wato she doesn't care?,me yasa Dr zai saurin aminta da ita ne ma wai?,meye dalili?,baisan sharrin mata ba,they can do whatever don suga sun shiga jikinka,sun samu aminci da yardarka,sannan daga bisani su cutar da kai,bayan dogon lokacin da suka dauka tare da kai,bazai sake barin haka ta faru ba!,har abada!!.

Matsawa yayi gaba kadan yana fuskantarta,cikin izza ya motsa bakinsa yana magana da ita da wani irin zafi

"Where did you get all this courage mr president?,me yasa kikeson ki dinga yin gaban kanki bayan baki cancanci hakan ba?" Cikin matuqar mamaki ta daga kai,kanta tsaye ta saka idanunta cikin nasa birkitattun idanuwan wadanda ke cike fal da memories masu zafi dake sake zafafa kansa

"What are you trying to say?" Ta tambayeshi itama kai tsaye

"Kin fahimci komai,dukka wadan nan abubuwan da kike gudanarwa me hakan yake nufi?,baqin fuskar ma'aikata da kika kwaso babu cikakken bincike tantancewa ko tattaunawa da wadanda suke da haqqi da abun,me hakan yake nufi?" Wani irin kallo ta jefa masa,zuwa lokacin tana jin takai geji,ta kuma gaji da sauraron maganganunsa masu kama da ya shirya ci mata mutunci,saita miqe tana fuskantarsa kai tsaye cikin rashin tsoro da kuma rashin shakka,saidai kafin tace komai muryar sajjad ta mamaye gurin.

Tun sanda ya shiga office dinsa saima data tura masa information na cewa ana can ana game din,a nufinta na b'ata sãahar da kuma kawo rigima a tsakaninsu,tace masa ya fita zuwa hall din yaji hankalinsa bai kwanta ba da fitar tasa ba,saboda tun daren jiya yasan cikin mugun bacin rai yake,saboda kiransa da NADEEYA tayi ta gaya masa saqo daga AMEESHA,ita kanta nadeeyan tayi nadamar kiran,ta dauka komai yana zuwa ya wuce,ta zaci zuciyarsa ta sassauto ashe ba haka bane,ta tafka kuskuren daya dami zuicyarta,tun jiya kuma take kiransa amma har zuwa yanzun bai daga wayar ba,abinda yasa ko kamfanin da zafi zafinsa ya iso yau,sai Allah kuma ya kade azal bata sauka kan kowa ba har ya isa office dinsa,shi yasa yanzun da yaji ya fita sai yabi bayansa,don shi yasan da game din,ya jima ma zaune cikin hall din yana kallon yadda suke abun cikin gwaninta sa qayatarwa.

"everybody outside please!" Nan da nan employees din kawunansu ke a qasa cikin d'ari d'ari da rashin jin dadin maganganun da yake gayawa president din tasu suka fara qoqarin fita cikin gaggawa,kamar basu da buqatar dama gani da jin abinda yakeyi matan,banda wasu tsiraru cikin mata da basu so hakan ba,dama su din ta shige musu hanci da qudundune,tako ina ta sha gabansu,sun rasa yadda zasu fatota,ciki harda saima dake lafe a bakin qofa.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥






[8/23, 6:15 PM] KYAUTA: *H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma


Page 31


Da hanzari sajjad ya tari numfashinsa,don bayason yace komai kada al'amuran su qarasa jagulewa

"Please toufeeq Calm down,don't make harsh words" bai ko waiwayo ba ko ya saurareshi ba ya tako zuwa gabanta,ya bada kusanci sosai a tsakaninsu irin wanda bai taba yi ba. Ranqwafawa yayi yayi mata rumfa saman kanta yana dubanta

"Nawa ne kasonki?!" Ya fada da wata irin kakkausar murya. A birkice take kallonsa,sosai maganarsa ta daketa,sai yanzu ta fahimci inda ya sanya gaba ma gaba daya,yana nufin wani ha'inci ta qulla ko ko meye?,kamar yasan me take tunani saiya sauqaqe mata ta hanyar sake bayyana mata abinda yake nufi

"Nace nawa ne share dinki?,tsakanin kawo ma'aikata da sauran ayyukan!,nawa kika tsara samu!,nawa kika samu!,ki gayamin zan ninka miki,amma ki fita daga rayuwarmu!" Duk da cewa bata shirya zubda hawayenta ba amma ta gagara riqesa,a take ya zarto daga idanunta ya sauka saman lallausan fuskarta da bata iya riqe komai ma ballantana ruwan hawaye saboda santsi da sulbinta,ta kafeshi sosai da ido kamar wadda ta warke daga ciwon makanta,cikin matsanancin fushi tace

"wanne irin mutum ne kai mara kirki?,mara iya mu'amala?,wanda baisan kima da martabar dan adam ba?,me yasa dukka zancanka kudi!,me yasa kake hangen kudi sune gaba da komai?,kana tunanin aiki daku na nufin in zama baiwa?,ko mara 'yanci?,ko kuma aiki daku na nufin zan mallaki wata dukiya?saboda kun mallaki yanke talauci?,Mr Muhammad.........idan baka sani ba yau ka sani,banyi aiki daku bisa radin kaina ko kuma don ina nema ba.....nayi aiki daku ne bisa dole da kuma takura neman alfarma da kuma ganin kimar yaaya na, karamcin mahaifinka kuma ya zama silar wanzuwata a nan gurin......baka da matsayin da zan nema sa hannunka akan ayyukan kamfanin nan,duk abinda kake tunanin na aikata.....yes na aikata din,na samu kaso me tsoka wanda hankali bazai dauka ba,na tara arziqin da yafi na mansa musaa dukka a jikinku,do your worst,I don't care or fear......ba dai dukka taqamarka kora ga ma'aikaci ba?,zaka iske resigning letter dinku a wajen sameera,ka riqe tsiyarka ka bawa wanda kaga dama" ta qarasa fada kuka sosai yana qwace mata,sannan ta soma fita daga hall din da sassarfa kuka na sake qwace mata.

Da sassarfa sajjad yabi bayanta shi da mr hamza,saidai cikin rashin sa'a ta rufe office din,a yanayin da take sun tabbatar ba zata sauraresu ba,sai suka barwa miss sameera dake tsaye saqon idan fa bude ko tazo fita don Allah kar ta barta,ta tsaidata ta sanar dasu.

A office ya sameshi yana kai kawo,ya cika ya batse kamar zai fashe

"Burinka ya cika,hankalinka kuma ya kwanta" sajjad ya fadi shima cikin bacin rai

"Stop sajjad,don't aggravate my anger,bakaji me ta fada bane?,I will surely punish her" ya qarasa fada yana dukan bayan kujera da hannunsa a zafafe. Kallonsa kawai sajjad yakeyi,yama rasa abun fada,wanne irin tashin hankali ne haka suka tashi dashi yau,sai kawai ya zaro wayarsa ya fara dialing number Dr.

Tana kuka tana rubuta resigning letter din,bawai tana kuka kan barinta aiki bane, a'ah,tozartata da yayi a gaban mutanen da suke ganinta da kima da mutunci,maganganun daya gaya mata,wanda shine mutum na biyu a duniya daya taba gaya mata magana masu zafi irin haka. Ta kammala rubutawa kai tsaye ta turawa sameera,tace bayan ta tura musu a rubuce tayi printing as hard copy,ta riga ta yanke har abada ita da companyn,bama iya kamfanin kadai ba,duk wani aiki da yayi kamanceceniya da wanann ta barshi har abada.

Da hanzari take tattara dukka wasu kaya da suke da alaqa da ita tana hadasu a wata jaka,ta taka zata cire wata calendar dinta kanta yayi mummunan sarawa,ta koma da baya babu shiri ta dafe kanta da hannayenta biyu tana kiran sunan Allah,idan batayi wasa ba alamu sun nuna ciwon kan da taketa gujewa motsawarsa a yau zai motsa din. Batason ciwon ya sameta a nan,don haka ta bude qofar,ta leqa ta kira sameera. Yanayin da taga uwargidan nata ya sanya hankalinta tashi,nuni tayi mata da iya kayan data samu cirewa ta miqa mata key tace ta saka mata a mota. Sameeran na fita ta miqe da qyar,ta yafa mayafinta ta zura takalminta ta taka a hankali tana ficewa daga office din,zuciyarta na karyewa,wani sashen na zuciyar tata tana ban kwana da dukka abinda ya shafi MT JARMA,bankwana na har abada.

_uhmmm,ko shin da gaske bankwanar ne?,ko kuma akwai sauran kallo?,masu karatu,ku gyara zama da kyau,akwai fa sauran kallo,zamu shiga gaba ta biyu na labarin,gaba me matuqar muhimmanci,muje zuwa_🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️


Da kallon mamaki maama kin bita sanda ta shiga gidan

"Ke kuma me ya faru na ganki a gida a irin wannan lokacin?" Idanunta fal da hawaye da taketa qoqarin shanyewa tace

"Ba komai maama"

"Qarya kike ban yarda ba" ta fada tana tattara hankalinta a kanta tare da barin duk abinda takeyi. Hawaye ne ya zarto a fuskar sãahar din,tasa bayan hannunta ta share

"Na ajjiye aiki maama" fuska tadan baata kadan

"Dalili dame?" Kai kawai ta shiga girgizawa,bakinta ya kasa furta komai,tana jin daci da ciwon abinda yayi mata har saman harshenta,ga kanta da yake sara mata sosai kamar zai rabe gida biyu

"Jeki,Allah ya kyauta" maama ta fadi saboda yadda taga ta gaza furta komai,koma meye tasan zataji idan yayunta ko afifa sukazo.

Komai ta zube a qasan daki ta isa gado ta kwanta rub da ciki tana fashewa da kukan da takeson saki tun dazun, idanunta a lumshe tana bitar maganganun daya yayyaba mata,tayi nadama da dana sanin sanin kamfanin ma gaba daya bare wasu mutane dake da alaqa dashi.

Sai data shafe kusan awa daya sanann ta laluba magani tasha, tayi kuma sallar azahar don tasan zaiyi wuya batayi bacci ba,idan kuma tayin lokacin yana iya kubce mata. Kamar yadda ta zata din kuwa,lokaci kadan baccin yayi awan gaba da ita,saidai dukka cikin barcin ba komai sai mafarkai,wadanda dukka toufeeq ne a ciki da tarin cin mutunci da cin zarafinsa a gareta.

Knocking din baaba rabi ne ya tayar da ita

"Hajiya tace ki fito hakanan kici abincin rana"

"To" ta amsa mata,ta sa hannu ta shafi fuskarta,tana tuna yadda ya zabga mata mari a mafarki,kwatan kwacin marin da ta taba ji ya zabgawa wata,kai ta girgiza ta miqe a hankali ta wuce bandaki. Alwala ta dauro,sannan ta dawo ta cire kayan jikinta. Wata sof cotton shirt ta saka me gajeran hannu royal blue,me adon furanni da gold colour,sai spaghetti skirt daya dace da rigar,tasa comb ta sake gyara gashinta daya hargitse saboda baccin da tayi,ta qara turare a jikinta ta dauki wayarta dake da tarin miscall ta kashe ba tare data tsaya duba kiran waye da waye ba,ta tabbatar dai harda kiran dan anace mahmud a ciki.

A parlor ta samesu,maama da baaba rabi dake gyara freezer din parlor din

"Barka da fitowa farar d'iya" ta fada tana murmushi

"Barka baaba rabi,ya aikin?

"Alhamdulillah "

"Ma sha Allah " ta fadi tana qarasawa kusa maama ta zauna,wadda har yanzun binta take da kallo

"Me za'a kawo miki?" Baaba rabi ta tambaya

"Barshi baaba,zan dan huta ne kadan sannan naci abincin,zan zuba da kaina" ta amsa mata tana daukar remote ta canza channel.

Bayan wucewar baaba rabin kallonta maama tayi

"Kunyi waya da yayanki ne?" Saida gabanta yadan fadi,tasan yaaya muhyiddeen take magana a kai tabbas,batason ko sau daya ya roqeta ta koma aikin nan,don ba zata iya ba muddin wannan mutumin yana a cikin kamfanin

"Bamuyi ba,ko ya kira din inajin bacci nake a sannan" kai ta kada

"Me ya sanya kika ajjiye aiki sãahar?" Shuru ne ya biyo baya na 'yan sakanni,tanata qoqarin hadiye bacin ranta sannan ta motsa bakinta

"Bazan iya ba maama,dansa bashi da kirki sam,baya ganin kima da girman kowa,duk wata mace dake aiki a kamfanin kallon baiwa yake mata,ko wata mara daraja da batasan martabar kanta ba" shuru maama ta danyi sanann ta numfasa

"Amma dai kinsan qarfe daya baya amo ko?,kuma ko meye halin mutum sai k........." Qarar wayarta ya katse mata maganar,sai t maida hankalinta a kai ta daga wayar ta sanyata a free.

Dr mamman girema ne,wanda kafin su gama wayar sun sanya sãahar din cikin tunani,tabbas inda dukka maza irin mahaifinta ne,su kuma mata duka zasu kasance kamar mahaifiyarta ba ko tantama da ba'a samu mutuwar aure ba,koda an samu din ma saboda sabanin da baya wucewa tsakanin bayi,to zaiyi matuqar qaranci.

Tuwon alkama yace yanaso miyar danyar kubewa,batason ta zauna tayita zaman tuna mutumin da a wajenta bashi da wani amfani sam,banza ma ta fishi,don haka sai ta wuce ta debi abincinta taci,tana kammalawa ta shiga kitchen da kanta ta dorawa abban nata tuwon.

Tunda akayi sallar magariba taji yaa muhyi din tare da abba suka shigo gidan ta qule a daki taqi yarda ta fito,saidai ana gama sallar isha'i saiga maama da kanta

"Ki dauki abincin can ki kaiwa abbanku,zan shiga wanka" hakanan ta miqe jiki a sabule,ta fidda hijabinta ta maida gurbinsa da dan qarami ta fito ta debi kayan abincin ta wuce sassan Dr mamman.

A ladabce ta zauna ta gaidasu dukkansu,don yau kafin ta fita basu hadu da abban ba,ta zauna sosai ta fara serving nasu duka su biyun da suketa tattaunawa akan harkokin da suka shafi kasuwancin da suke na hadin gwiwa a tsakaninsu. Ta ajjiye musu komai tana shirin miqewa abba daya gama wanke hannunsa yace

"Dawo ki zauna mana ummin abba" murmushi kadan tayi,ta dawo ta zauna din,sai da ya fara cin abincin sannan yace

"Me ya faru ne yau a MT JARMA?" Kanta ta sunkuyar tana jin rauninta yana dawowa,kamar yanzun abun yake faruwa,amma dole ta bude baki tayi magana da harshen da zasu fahimceta

"Na ajiiye aiki yau abba,ku yimin afuwa abba kai da yaa muhyi na rashin neman sahalewarku kafin aiwatar da hakan,abun yazo a gaggauce ne,sannan kuma a gabar da bazai bada damar yin hakan ba"

"Me ya faru?" Abban ya sake jefa mata tambayar. Bata rufe komai ba ta zayyane musu,tun haduwarsu ta farko har zuwa abinda ya wakana yau din. Ta qarashe maganar tana hawayen takaici.

Ga mamakinta sai taga abban ya saki murmushi yana girgiza kai

"Dake dashi dukka quruciya ce take damunku da kuma zafin kai,tare da wasu memories da suketa hunting rayuwarku,shikenan dai,bakin alqalami ya riga ya bushe,dr jarma ya kirani da kansa,yace bazai tilastaki ba akan ajjiye aiki da kikayi,yace a baki haquri a madadinsa da dukka ma'aikatan,sannan ya tura kudi a baki saboda hobbasar da kikayi kika daga kamfaninsa zuwa matakin gaba,kika gyara matsalar da suke fuskanta kaso sittin cikin d'ari" ya qarashe fadi yana duban fuskarta. Batace komai ba sai kai data girgiza,taji dadi da bai nema alfarmar lallai ta koma ba,don bataso ya roqeta abinda ba zata sake iyayi masa shi ba.

"Dama aiki ba dole bane,aure ne dole" abban ya sake fadi,maganar data bugeta sosai,ta kuma sakata dago kanta da sauri ta kalli abban,shima idanunsa yana kanta,ya jinjina kai alamun tabbatar mata da hakan

"Tunda taqi tsayawa ta fahimci kowa abba bazaiyiwu taci gaba da zama babu auren kuma ba aikin ba,Allah baya barin bawa babu aikin yi,akwai irin aikin da takeso din abba,idan na dawo daga tafiyar nan ta wata daya zuwa biyun nan zan applying mata" kai ya sake jinjinawa yana tsame hannunsa daga tuwon

"Banqi ta taka ba,amma duk da haka ta maida kai ta fidda miji,saboda lokaci tafiya yakeyi,kuma har yanzu ke din yarinya ce qanqanuwa ballantana kice kin girmi yin aure a yanzu". Gaba daya babu abinda maganganunsu sukayi sai dagula mata lissafi,dan ciwon kan data samu ya ragu sosai ya dinga qoqarin dawowa saboda damuwa,ga gidan babu kowa bare ta samu me debe mata kewa,tanaso tayi magana da anty farheen to amma tasan tabbas yaa muhyi yana gidan,don tafiyar tasa sai zuwa wani satin,sai kawai ta hada kayanta a washegari tabi afifan nata zooroad.

Ranar da taje qin cewa afifan komai tayi,itama bata matsanta ba sukaci gaba da hutunsu,har sai data huce,ranar suna ta raka afifa gyaran farce da fuskarta,suna hanya tana driving ta bata labari. Sosai afifa bataji dadin ajjiye aikin ba,duk da itama taji ba dadi akan yadda abun ya faru tsakaninta da toufeeq din,saidai itama ta gaya mata

"Ba kowanne namiji ke iya fuskantar mace ya bata uzuri ba,ya kuma banbance rashin kunya da tsaiwa akan haqqinta ba,bare mutum irin MT da Allah ya yiwa baiwar kyau kudi da ilimi da kwarjini....."

"To hell with his kudi da kwarjinin,ya dauka ina cikin shirgin wawayen 'yammatansa ne da zan dauki irin wannan?,ki daina yabonsa please kina batamin rai afifa.....bakisan wayeshi bane,saboda baki taba mu'amala dashi ba,he was arrogant beyond belief,good look don't always signal kindness" dariya afifa tayi

"Wato kin fahimci kyansa ya janye hankalina sosai ko?"

"chapter close a beg" yatsunta biyu ta sanya tayi signal na zipping bakinta,bata kuma sake cewa komai din ba,sai suka shiga wata hirar ta daban.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥
[8/23, 6:15 PM] KYAUTA: *H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma


Page 32


*********K'arfe kusan takwas ne na dare,saman titin dake wadace da fitilu yake tuqin yau da kansa,kuma shi daya,abinda ba kasafai yake faruwa ba. Sanye yake da wata maroon and golden hoodie captan abaya na maza saqar qasa turkiyya,dogon hannu gareta,ya saki hular a bayansa,hakan ya bawa kyakkyawar fuskarsa damar fitowa sosai,cike da wannan turbunewar da kuma rashin fara'a daya zame masa dabi'a.

Kiran dr jarma ne ya fito dashi,don yana zaune shida fadeela a part dinsa suna buga game data tubure itakam yau tare zasuyi,da qyar ya lallabata ya maidata gurin nanny dinta sannan ya fito,tare da alqawarin zai dawo da wuri su qarasa. Baisan kiran na meye ba,amma alamu sun nuna a gaggauce yake neman nasa.

Cikin rukunin gidajen dake sharada NNDC QUARTER,mayalwacin layin dake shimfide da kwalta da kuma fitilu a jere reras,kowanne gini dake layin abun kallo ne,wannan yana wane wancan,a haka yaci gaba da tafiya bayan ya ragewa motar gudu,da alama ya kusa isowa gidan daya nufaci zuwa.

K'ofar wani mansion house dake dauke da ginin bene hawa biyu ya tsaya,ya danna hon na farko, kafin yayi na biyu security din dake sanye da baqaqen uniform da suke kama dana police ya buda masa qofar,a nutse ya sanya hancin motar zuwa cikin makekiyar harabar gidan. Biyu daga cikin security dinne suka bude masa qofar cikin girmamawa da qauna me tarin yawa suke gaidashi,ya amsa musu yana rufe motar,ya jefa key din a aljihun rigar tasa,ba tare daya ciro hannuwan nasa ba yaci gaba da takawa zuwa cikin kamar maijin sanyi. Bawai sanyi yakeji ba,kawai yana jin wani iri ne da yanayin yadda dr din ya kirashi.

Kai tsaye ya kutsa zuwa hanyar da zata sadashi da falon gidan,ya tsaya yayi knocking,duk da cewa gidan mahaifinsa ne,amma hakan ba sakashi shiga kai tsaye ba,duk sanda yazo gidan sai ya tsaya ya nemi izini don cikar dokar addinin musulunci.

K'ofar aka bude,labiba ce,sanye da wata doguwar riga da tasha tattara daga qirji,ta bude daga qasa sosai,kanta cike da qananun kitso da gashin doki,sao farata zaqo zaqo data sanyawa hannayenta tamkar wata dabbar daji,amma ita a gurinta hakan ado ne na wayayyun mata masu aji(wallahi wallahi wallahi muddin kinsan daya daga cikin wadan nan abubuwan dabi'unki ne to kiyi gaggawar dainawa tun kina raye kina da lafiya,qarin gashi haramunne koda mijinki zaki yiwa,ko meye zaki sanyashi a kitsonki a qara miki tsahon gashinki haramunne,hakanan saka farce shima haramunne,haramunne haramunne,koda faratan hannunki bai halasta ki tarasu ki barsu baki yanke ba,haramunne barin farce yayi zaqo zaqo bare har kije ki biya kudi a dora miki shi,kina 'yar adam amma kinason kiyi kamanceceniya da dabba?,suke da wanann siffa ta akaifa ko qumba masu tsaho,acikin tsarki na addinin musulunci,bansa aske gashin maara dana hammata harda yankan farce sai yiwa yara shayi(kaciya), ma'aiki baya taba fadar magana wallahi wallahi ta tashi a banza,idan yace abu haramunne mu yarda mubi,ba wani kwaskwarima da malaman zamani masu son zuciya zasuyi ma maganarsa ta koma halak,haram

Please Login or Register in order to submit comment