Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 21 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

saki,sai ya dawo ya tsugunna a gabanta

"Bayan ke babu wata,idan akwai ma Allah yasa ta makance ta gurgunce koma ta mutu....."baki ta kama tana dariya

"Nidai ba ruwa na,irin wannan mummunan fata haka"

"Eh kuma har zuciyata na fada ba,bazan wuce hour dayan ba zan dawo in sha Allah" ya fada yana miqewa da dan hanzari sanda wayarsa ta qara yin qara alamun ana sake kiransa. Hakanan ta samu kanta da binsa da kallo har ya fice.

A nan falon taci gaba da zama tana kallon wani film da mbc2 suke haskawa,film ne daya shafi soldiers battle,tana son irin films din sosai.

Kamar daga sama taji qarar waya,a mamakance ta waiwaya tana duban daga inda sound din ke fita. Wayar adam ce a wajen,tadan zubawa wayar ido tana mamakin yadda akayi yau ya manta wayarsa,shi da kwana biyun nan baya sake da waya,ko yaushe tana hannunsa,bini bini ya dauka ya duba,har wani sabon suna ta saka masa saboda maitar riqe waya daya koya,ko cikin dare idan ta farka da yake a kwanakin nan bata fiya kwana da qoshin lafiya ba sai ta ganshi riqe da waya,tun tana daukan abun da wasa har taga ya zama gaske,tayi masa complain sai yace akwai wata sabuwar harka ne da yakeson ya gwada shiga,so ana wayar masa dakai ne yadda business din yake,wanda kuma yake masa bayanin ba qasar nan yake ba,yana china, akwai tazarar 7hrs tsakaninmu,darensu shine ranarmu,lokacin shi kuma yana office bazaiyu ya maida hankali ba akan waya ya ajiye aiki,ranarsu kuma shine darenmu,a sannan shi yana da chance nayin chart,shi yasa yake tashi a daren.

Ta gamsu,saboda ya yarda da adam din,bata taba kamashi da wani laifi da zai sanya zuciyarta tayi ɗar ko rawa a kansa ba.

Kira bayan kira haka ya dinga shigowa,hakanan taji qarar wayar ta dameta,saita yanke shawarar sanyata a silent,don ita din ba gwanar daga masa waya bace,koda za'a kira wayarsa sau dubu bazata waiwaya ta kalleta ba,ada har qorafin hakan yake mata

"Idan kirane mai muhimmanci ko kuma samuwa ce kinga shikenan ta wucemu" dariya kawai takeyi,saboda bata jin zata iya,tana da dabi'a na tsame kai daga abinda ba huruminta bane bai kuma shafeta ba.

Da sauri ta koma ta zauna sanda ta miqe da nufin cimma inda wayar take saboda wani hadadden ciwon mara na tashin hankali da taji ya soketa,ta runtse idanunta ta kuma dafe mararta da kyau tana kiran sunan Allah tana jujjuya kanta saboda azaba. Akalla ta kusa kwashe minti biyar a haka tana juya kanta hagu da dama,gefe guda kuma qarar wayar naci gaba da cika mata kunnuwa. Ta bude idanunta a hankali bayan ciwon ya lafa tana share gumin daya tsatstsafo mata a goshi,qafafunta babu cikakken qwari ta miqe ta nufi wayar.

Tana isa wayar ta danyi blinking light alamun shigowar saqo,ba inda idanunta suka sauka sai kan fuskar wayar. Da sauri ta zare idanunta daga fuskar wayar tana lumshe su,gabanta na wani irin dokawa labbanta na furta

"Ya hayyu ya qayyumu bi rahmatika astagis" tana fatan ta bude idanunta taga ba abinda suka gane mata bane da farko. Saidai a wannan karon data sake bude idanun nata abinda ta gani ya zarta wanda ta gani da farko,dukkan jikinta ya dauki rawa,taji a sannan bata da sauran zabi da ya wuce ta dauki wayar.

Tana daukan wayar qafafunta suka gaza daukarta,dole ta zame ta koma da baya ta zauna saman kujera, hannuwanta kamar ba zasu iya riqe wayar da kyau ba,ta fara qoqarin gwada password din dake kan wayar.

Duk password din da ta saka sai yace mata wrong,daga qarshe ta gwada saka qarshen number wayarsa,a take ta bude,saqon da bai gama fitowa ba ya bayyana muraran.

K'azaman kalmomi masu munin gani bare kuma kunnuwa su iya jumurin sauraronsu,wani gumi mai zafi ya shiga tsatstsafo mata ta kowacce kafar gashi dake jikinta,zuciyarta ta ninka bugunta kamar zatayi tsalle ta fito daga qirjinta,kanta yayi wata irin sarawa ta fara gani dishi dishi sanda ta fara bin charts din dake inbox din da number wayar da babu suna a kanta. Wasu irin qazaman saqonni da ko ita da take halalin adam bata tunanin sun taba musayar irinsu a tsakaninsu,hotuna na kowanne sashe na jikin yarinyar,harda muhallin da ko mahaifiyar yarinyar tana tunanin zaiyi wuya ta sake katarin ganinsa tun bayan da shari'a ta hau kanta. Ganin abun take kamar al'mara,ganin abun takeyi kamar ba adam dinta bane,kamar ma ba wayarsa bace,ba abinda ke kaikawo cikin kwanya da zuciyarta da sunan adam din da kuma fuskarsa. Video na qarshe da idanunta suka gaza kalla wayar ta sulale a hannunta ta fadi tare da wani hadadden ciwon mara da bata taba jin makamancinsa ba,sai kawai ta cure a wajen tana jin numfashinta na shirin barin gangar jikinta.

Wannan yayi dai dai da bude qofar falon da adam din yayi cikin gaggawa,har yayi nisa ya tuna yabar wayarsa,duk da yasan baida matsala,kuma bashi da haufi matarsa bata taba wayarsa,amma haka kawai yau din yaji ya kasa samun nutsuwa,yaji bashi da gamsuwar tafiya,dole ya juyo da kan motarsa ya dawo ya dauki wayar sannan ya koma.

Sam bai lura da inda ya aje wayar ba,idanunsa akan saahar dake cure guri daya kamar alkaki suka fara sauka. Da hanzari ya qaraso yana kiran sunanta,duk da azabar ciwon da takeji a mararta amma hakan bai hanata daga kai ta watsa masa wani kallo da jajayen idanunta ba. Sosai yasha jinin jikinsa amma zuciyarsa na gaya masa komai normal ne,ya miqa hannu gareta,ta tattara dukka ragowar qarfinta ta miqe tana jin mararta kamar zata rabe biyu

"Kada ka yarda ka tabani,karka qaraso inda nake......" Bata kai ga qarasawa ba numfashinta ya soma sarqewa,tana jin wani abu me dumi ya ratso ta jikinta ya soma bin qafafunta yana gangarowa,duk da yanayin gushewar hankali da take kan gabar yi,amma hakan bai hanata qoqarin ganin abinda ke faruwa da ita ba,idanunsu shi da ita suka sauka lokaci daya akan jinin dake malala saman tiles din falon,bai jira cewarta ba ya qarasa gareta da hanzari yana riqeta,zuwa lokacin itama tuni ta qarasa ficewa daga hayyacinta,saboda qarin tashin hankalin fitar jinin da ta gani daga jikinta.[8/29, 2:05 PM] KYAUTA: *H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 41


*******Daga lokacin data fahimci cewa ta farka,ta dawo cikin duniyar da batayi tsammanin dawowarta ciki ba,sai ta fara qoqarin bude idanunta don ta tabbatar da inda take din. A lokacin da kwanyarta ta fara yi mata bitar al'amari na qarshe daya faru da ita saita rasa dukka qwarin gwiwa karsashi da kuma sha'awar bude idanun nata,ta sake runtse idanun nata cikin jin zafi,wani abu me tsini na sukar qirjinta kamar an fiddo zuciyarta an shanyata tsakiyar qwalleliyar rana.

Hannunta data daga a hankali takai saman cikinta ta shafa bayan ta tuna yadda taga jini yana bin qafafunta a kallo na qarshe data yiwa jikinta. "Saahar,kin farka ne,sannu" muryar anty labiba matar yaa saif dake zaune a gabanta ya ratsa kunnuwanta,bayan zuwa yin salla da maama ita da afifa suka fita yi. "Sannu saahar" anty labiba ta fada tana riqe hannunta dake saman cikin
"Ki daina motsa hannun, cannula din dake hannunki zata goce" ta fada cikin matsanancin jin tausayinta,daga yadda taga tana shafa cikin lallai shine abu na farko daya fara zuwa mata kenan a rai bayan ta farfado din,wanda tuni ya fice daga jikinta ta cikin jinin data dinga fitarwa me yawan gaske.

Tare maama suka shigo ita da afifa,dukkansu rige rigen isowa gareta sukeyi

"Menene abun kukan kuma?,Allahn daya baki shi zai sake baki wani" abinda maama ta fada kenan cikin muryar lallashi,a nata zaton saahar din ta fuskanci babu cikin a jikinta.

A mugun karye ta daga kai ta kalli maaman,xancan yayi mugun dukanta,wasu tawagar hawayen masu zafi suka kunno kai,saita maida idanunta kawai ta lumshe,abinda ya bawa hawayen damar saukowa da kyau.

Tsahon zaman da sukayi tare da ita suna lallashinta idanunta na a rufe ba tare data iya budesu ba,taji ciwo sosai na rasa gudan jininta da tayi,amma a yanzun hankalinta yafi karkata ga mummunan ganin data yi a wayar adam din. Ciki tasan ubangijin da ya bata shi zai sake bata wani,ko a kusa ko a nesa kamar yadda ya kawo mata wannan,to amma kuma wannan baqon al'amari daya shigo rayuwar adam fa?,wanda kai tsaye zata iya kiransa da neman mace koda bata ce neman mata kai tsaye ba,iya maganganunsu kawai ya gama gaya mata adam ya jima da yarinyar,sunyi mugun sabo,kuma sun saba kasancewa da juna da irin mu'amalar dake iya wakana tsakanin ma'aurata
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta furta har ta fito fili ba tare data ankara ba,sai sautin muryar maama da tace

"Yauwa,ita zakiyita maimaitawa" sake motsa bakinta tayi a karo na biyu tana sake maimaita kalmar,hawayen na sake bin kuncinta.

A matuqar sanyaye afifa ke sanya tissue tana dauke mata hawayen,saahar dinta jaruma ce da take da wani irin juriya dakiya da kuma cinye abu,irin tashin hankalin da take gani dimuwa da halin qunci sai take ganin kamar ya zarta yadda ya kamata ace an gani a fuskar macen data jima bata samu haihuwa ba ta hadu da miscarriage,saidai bata ga wani abu guda daya da zai dasa mata kowanne irin zargi a zuciyarta ba bare ta sanya ayar tambaya.

Dai dai lokacin likitan yayi knocking qofar ya kuma tura ya shigo shida wata nurse dake riqe da file na saahar din

"Yauwa ta farka?"

"Ta farka dr" anty labiba ta amsa masa

"Ma sha Allah" ya fada yana tsaiwa daga gefan saahar din

"Sannu ko?" Ya sake fada yana duban fuskarta,sai a sannan ta bude idanunta a hankali da suka tasa saboda hawayen daketa fita daga cikinsu akai akai

"Ya da kuka kuma madam?,sorry for the lost.....kiyi addu'a,next year kamar war haka sai kiganki saman gadon nan rungume da babynki alive and healthier" idanunta ta mayar kawai ta lumshe,abinda takeji cikin zuciya da qirjinta ta tabbatar babu me iya fahimta,da rufaffun idanuwan nata ta amsawa likita dukka tambayoyin sa,sai ya rufe file din nata yadan dubi afifa

"Idan me gidanta ya shigo a turomin shi,inason magana dashi kafin na fita duty"

"Okay,in sha Allah" ta amsawa likitan bayan ta daga kanta daga wayar da take dannawa, zuciyarta duka babu dadi,duk sanda daya daga cikinsu ya shiga damuwa ko tashin hankali,kusan su biyu suke raba wannan damuwar da dukka sakamakon da zai biyo baya.

Yanayin yadda taga kukanta yana tabasu tare da sake sanyasu damuwa ya saka dole ta tattara abinta ta cinye ta hadiye tana kiran sunayen Allah can qasan ranta,don ita kadai tasan qunci da bala'in da zuciyarta take ciki,dukkansu sun sanyata a gaba kowanne tambayarta yake me takeso?,me yake damunta?,bisa taimakon afifa da anty labiba ta shiga bandaki ta gyara jikinta tayi wanka,ta fito afifa ta shiryata sannan ta zauna yaa zaid yana ajjiye mata plate din abinci a gefanta

"Banason naga komai a cikinsa" wani marayan busashen murmushi ta saki,ta karyar dakai zuciyarta na karyewa,bata jin a yau maqogoranta zaiyi wani amfani,don bata tsammanin akwai wani abu me tauri kamar abinci da zai iya wucewa ta gurin saboda tsabar quntacewa da gurin yayi. Ganin da gaske ba zata iya cin abincin ba dole suka haqura,afifa ta hada mata kakkauran tea,ita da yaa zaid suka sanyata a gaba,aka samu tasha rabin cup,ta buqaci zata kwanta,shuru take da buqata,kadaici takeson samu ko zatayi wani tunani me amfani kan bala'in dake tunkaro rayuwar aurenta koma kai tsaye tace ya tunkarota,tashin hankali da musibar da ko wanne lokaci hankalinta ke tashi, tsigar jikinta ke zubawa idan taga wata mace cikin irinsa,yau gashi AKAN KANTA.....tamkar almara......tamkar cikin tarikicen tarkacen mafarkai,saidai kash......wannan din a zahiri ne,gaskiya ne,ba mafarki hikaya ko tatsuniya ko almara bace.

Dukkaninsu sun dauka bacci ne ya sake dauketa,don haka yaa saif da yaa muhyi suka dauki iyalansu suka wuce gida,ya zaid shima ya wuce bayan maama ta sanyashi ya dauki masu aikin gidan biyu da suke tare anan tace su tsaya su karbo abincin dare,hamisu driver ya dawo dasu zuwa magrib.

Shuru dakin yayi,daga afifa dake faman research a wani website sai maama dake jan carbi counter,sallamar adam dake gaba momee na biye dashi shi ya ratsa shurun da dakin yayi.

Har tsakiyar kanta taji saukar muryar adam din,bata motsa daga yadda take ba har suka qarasa shigowa,tana jin sanda maama ke gaisawa da momee cikin surukuta tare da bata kujerar zama,yayin da adam ya matso dab da gadonta,ya miqa hannunsa a hankali ya sanya shi cikin nata yana kallon kyakkyawar fuskarta data fada tayi wani fayau da ita.

Ji tayi kamar ya manna mata wuta,da da hali abinda tafiso a yanzun shine ta zare hannunta daga cikin nasa,to amma bata son tayi wani abu da zai fuskanci idanunta biyu,don bata shirya kallon fuskarsa ba a yanzu.

Kamar afifa ta shiga zuciyarta sai kuwa ta isarwa da adam din saqon likita,ya zame hannunsa ya juya ya fita zuwa office din likitan.

Ya sameshi yana shirin fita daga duty,to amma shigowar adam din ya sanyashi tsayawa da hada takardunsa da yakeyi ya masa izinin zama,ya zauna kujerar da take fuskantar dr,ya bashi hannu sukayi musabaha. Gyaran murya kadan yayi sannan yace

"Kaine me gidan saahar girema ko?" Kai ya jinjina yana dubansa

"Ma sha Allah,kasan cewa zubewar cikinta nada alaqa da shan tablet na zubda ciki?" Sosai fuskar adam din ta nuna zallar mamaki da alhini

"Tablet kuma dr?,haka kuka gani?" Kai ya jinjina masa cikin yanayi na tabbatarwa

"Yes,and after that ma.....mahaifarta ta dan samu rauni gaskiya sanadiyyar injection na planning da kuma wannan tablet din masu qarfi da tasha"

"Nasan da zancan injection,infact ma da yardarta aka fara"

"But haihuwarta nawa?" Likitan ya jefa masa tambayar yana kallonsa cikin mamaki

"Ko daya,duka duka ba bamu cika two years da aure ba until now" mamaki qarara ya bayyana kan fuskar likitan

"Amma....sorry mr adam,waye ya baku wannan shawarar?,bakusan allurar planning koda ka haihu bata masu haihuwa daya ko biyu bane?" Iska adam ya furzar daga bakinsa,dr yadan lumshe ido sannan yace

"Am sorry kada na zaqe da yawa,duk da cikin aikinmu ne mu bada shawara ga hanyar da zata bulle ma mara lafiyarmu don samun ingantacciyar lafiya kuma cikakkiya......a likitance kada ta sake ta'ammali da wani qwaya ko allura na zubda ciki ko hana haihuwa,don a yanzu haka mahaifarta ta samu rauni sosai,koda a gaba fa sake samun ciki sai an bashi special care matuqar inason juna biyunta yayi surviving har zuwa haihuwa" shuru adam yayi yana gyada kai,kafin ya sauke ajiyar zuciya yana kallon likitan

"Akwai wanda yasan dukka wadan nan bayanan?" Kansa ya girgixa cikin halin ko in kula

"Babu,but sister dinta taso taji wani abu daga gareni,so amma kuma tunda kaine ka kawota kuma kaine mijinta, that's why bance komai ba,coz kaine kafi cancanta mu tattauna maganar da kai"

"Okay dr,na gode,inason please kada wanda yasan da wannan,zanyi qoqari in sha Allah na kiyaye lafiyarta,zan kuma bincika abinda ya kawo wadan nan matsalolin"

"Hakan yayi kyau" daga haka sukayi sallama da likitan ya baro office din.

Tsahon zaman da sukayi a dakin shida momee din taqi koda bude idanunta bare su gaisa,har suka gama zamansu sukayi sallama suka wuce gida ita da adam din.

Wata irin jinya saahar takeyi me wahala tare da qoqarin danne abinda ke cikin zuciyarta,jinyar ta zame mata guda biyu,ta zuciya data gangar jikinta,tayi masifar kewa tare da rashin jin dadin rasa abinda ke cikinta,saboda yadda ta qwallafa rai a kansa,ta kuma aza dukka burinta a kansa,sai gashi rana daya sanadin kuskuren adam tazo ta rasashi,abu na biyu mummunan ganin da tayi a wayar adam din,wanda ya zama silar tarwatsa wani sashe mai girma na farinciki da walwalar rayuwarta,banda Allah yasa kota ina tana da matallafa,da family me qarfi dake tattalin farincikinta.

Da farko baccin qarya ya tsira duk sanda adam yazo har kuwa ya tafi koda awa nawa zaiyi,daga bisani ta fahimci abun yayi yawa,kuma har kamar an fara fahimtar ta,wannan yasa ta canza salo,zaizo kuma har ya tafi bata barin kowacce kalma ta hadata dashi,koda kuwa kallon fuskarsa batayi,rabon data dora qwayar idanunta akan fuskarsa tun randa fa kalli fuskar wayarta,duk sanda tayi yunqurin kallon nasa saita hangeshi cikin qazamin hoton da ya dauka shida yarinyar da bata gama tantance kamanninta ba cikin wani qazantaccen yanayi da ko a mafarki bata taba tunanin ganin hakan akan adam ba,dukka wani yarda da aminci daya samu daga zuciyarta sai taji a hankali a hankali yana sulalewa. Yanayin da yaga saahar din ta koma yayi matuqar girgiza adam din hadi da sanyashi cikin matuqar tashin hankali,yanason ko yaya ne ta bashi dama da zasuyi magana amma ta hana hakan faruwa,har zuwa randa aka basu sallama.

Kai tsaye ta wuce motar yaa Saifullahi,yaa saif din ya ranqwafo yana kallonta

"Ki koma matar mijinki mana,ina cewa ke ya budewa motar yana jiranki ki shiga?". Kanta ta langabe,idanunta nason kawo ruwa amma kuma tana hana hakan faruwa,su dukka basu sani ba,sam a yanzun bata da sha'awar komawarta gidan adam,to amma kuma idan tace ma ba zata koma din ba tasan bata isa ba,dole saita bada gamsashshiyar hujjar da zata zame mata garkuwa,ta kuma zama silar da zasu karbi uzurinta suyi mata yadda takeso,su barta a gida ta gama warkewa,ta kuma yi nazari a tsanake kan makomar zamanta da adam,ta gano daga ina kuskuren yake?,sakacinta ne ko nasa?,amma hakan dukka ba zata samu ba,don duk da yadda suke gatantata,suke kuma shagwabata ba shakka basa lamuntar wasa da harkar aure,ba kanta farau ba,ta gani daga kan yayarta wadda ya zaid yake bi Anty ANUUM.

Tana fita a motar yaa Saifullahi adam ya nufo gurin da sassarfa,yamatso da nufin tallafa mata ta isa motar duk da tana takawa sosai amma saita zame,ta matsa gefe kadan dashi tayi gaba ta barshi.

Bai sare ba ya bita,ya kuma cimmata tana kici kicin bude motar,sai ya bude mata front seat,sabanin ita dake qoqarin bude back seat.

Karon farko ta daga manyan fararen idanunta ta zube masa su ba tare da tace komai ba. Wani abu yaji ya dakeshi sosai,kwarjini tayi masa sosai,haryaji yana shirin narkewa a wajen,saiya kauda nasa idanun,bai sake dubanta ba har zuwa sanda tashige ya maida qofar ya rufe ya zagaya ya tashi motar suka fice daga harabar asibitin.

Shuru ne kawai ya baqunci motar,kaiba zaka ce akwai mai rai a cikinta ba,karo nafarko tun aurensu da irin hakan ta faru. Saahar din wata irin macace ta daban da take da matuqar qoqari wajen iya kula da miji,taka tsantsan tare da qoqarin barin dukkan wani abu da adam bayaso,bata daukan fushi dashi koda ya bata mata,tafi gane ta sanar masa su tattauna su yiwa kansu sulhu,a tsahon zamansu na wannan shekarun babu wanda ya taba jin kansu,sun zama wadansu irin ababen koyi da kwatance ga kowa.
[8/29, 2:05 PM] KYAUTA: *H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 42


"Saahar" adam din ya kira sunanta kai tsaye da wata irin murya dake shaking,sarai ta jishi amma saita lumshe idanu kawai batare data amsa ba. Sake kiran sunanta yayi amma kamar dazun,ya fahimci ba zata amsashi ba koda zai kwana yana kiran sunanta,a duk sanda take cikin maquracin bacin rai, dabi'ar miskilanci itace abokiyarta a sannan. Samun tabbacin ba zata amsa masa ba sai ya fada jero mata kalamai na kare kai da kaifin harshe da kuma zaqin iya tsara kalamai da Allah ya bashi. Wata irin baiwa ce dashi kansa yake alfahari da ita,baiwar da yasan cewa ta siyo masa abubuwa masu yawa masu tsada da daraja.....cikinsu kuwa harda ita saahar din.

Dukka wata kalma da yasan zata iya tasiri a zuciyar saahar din a lokacin ya arota yayi amfani da ita,to amma ko gezau,kamar ma bata wajen,abinda yayi matuqar karyashi,don bata taba gwada masa irin wannan dabi'ar ba.

Har suka isa gida,bata tada kai koda sau daya ta kalleshi ba,ta sani muddin ma tace zata kalleshi to ba abinda zata hango tattare da adam din face baqinsa da zuciya da idanuwanta zasu dinga gani,hakanan matuqar tace zata bude baki tayi wata magana.....to lallai kalmar da dukka zata fita a bakinta muninta zaiyi yawan da zata iya haifar da faruwar komai.

Yana tsaida motar ta budeta ta fice a gaggauce,cikin zafin nama shima ya bude bangarensa ya take mata baya,yakuma yi nasarar cimmata a tsakiyar falon gidan,ya sha gabanta yana kallon fusatattun idanuwanta da suka tashi daga ainihin launinsu na fari qal da baqi sidik din qwayar idanuwa,zuwa pink da surkin red. Wani mugun kwarjini tayi masa da ya qarasa karyashi gaba daya,sai yayi qasa da qwayar idanuwansa yana cewa

"Dukkan laifin da kike tuhumata dashi saahar na yarda na aikata.....amma ban aikata babban laifin da zuciyarki ke miki hasashen na aikata din ba,ban taba yi ba na rantse miki da girman Allah"
"Ka bani guri na wuce adam!" Furucin ya fita daga bakinta da wani irin madaukakin sauti daya canza tone na muryarta,karo nafarko data taba tanka masa tun daga waccar ranar da abun ya faru
"Bazan matsa ba saahar,kiyimin dukka kalar hukuncin da kikeso muddin zaki tsaya muyi magana koda ba zaki fahimceni ba". Juyawa tayi kawai ta doshi hanyar fita ba tare data sake koda motsa bakinta da nufin tankawa maganarsa ba. Yayi wata muguwar zabura yabi bayanta,don ya tabbatar tana nufin ficewa daga gidansa,wanda faruwar hakan yana nufin faruwar komai da komai,yana nufin tonuwar asirinsa,yana kuma nufin subucewarsa daga kafatanin rayuwarsa,abinda a yanzun bai shirya masa ba.

Hannu yasa ya maida qofar parlor din ya rufe,ya kuma murza key ya zare key din ya jefa a aljihun rigarsa,sai yasa dukka hannuwansa ya hade a nasa,ya kuma sulale a wajen ya tsugunna bisa gwiwoyinsa,sannan ya buda tafukan hannayen nata ya saka fuskarsa a ciki ya rufe ruf tare da kubcewar kuka.

Duk da a yanzun batajin adam din bisa kowanne matsayi a zuciyarta,bata jinsa kwata kwata daga guraben da a baya yakai,amma kukansa yazo mata a bazata,ya kuma bata mamaki,kuka koda ga qaramin yaro abune me cin rai da zuciya gaba daya,bare ga babban mutum da

Please Login or Register in order to submit comment