Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 32 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sosai akan sabuwar nanny din fadeelan.

Tunda ta fahimci ta janye camera din sai ta koma gefe ta zauna tana maida numfashi, wani abune da bata taba zata ba shi yasa ta razana,wayarta ta jawo ta buda don rage zaman da bugawar da zuciyarta keyi akan abun,tana danne danne tana kiran sunan
Allah,har batasan fadeela ta kammala wayar ba,saijin mutum tayi tsugunne gabanta

"Aunty,am sorry,abby yace na baki haquri,na juya miki camera without your permission" ido ta zuba mata,sai ta murmusa ta sanya hannunta ta dagota ta dorata kan cinyarta

"Abby yace babu kyau kada na sake" kai ta jinjina

"Abby dinki is a good person,gaskiya ya fada,na haqura nasan kema ba kina sane bane ko?"

Kai ra gyada mata tana murmushin jin dadin yabon da ta yiwa mahaifinta,riqe hannunta tayi suka miqe
"Oya,muje a kwanta,gobe da school,next week kuma zaku fara revision,sai C.A then exams ko?

"Yes" ta fada tana murmushi

"Abby yamin alqawura da yawa,yace ya gaji da ganin third position,da second yakeson ganina,if possible ma first,idan na kawo first din kuwa,sai ya gyada kai,nasan abby naidan ya gyada kai baice komai ba.....hmmmmm,zai baka mamaki ne,anty ki tayani addu'a na samu first position" ta garasa maganar tana
marairaicewa dai dai sanda sãahar ke lullubeta
da duvet.
Murmushi ta saki,ta kama hannunta ta rige
cikin nata
"Kiyi karatu sosai kiyi addu'a da yawa,you will pass in sha Allah, kuma duka zan tayaki fadee"

qanqameta tayi tana dariya cikin jin dadi
"Na gode aunty nanny"

Shuru yayi idanunsa akan system dinsa
bayan sallama da fadeelan,hannunsa rige da
dan qaramin spoon yana ta juya tea din da
already ya riga ya gama juyuwa,ya rasa me
yake tunani,hirarsu da fadeela....abubuwan
da yaji.
.ko abinda ta nuna masa bai shirya
gani ba?, Sai kawai ya zame hannunsa daga
tea din,ya mige yana zuba hannuwansa dukka
biyu a aliihun wandonsa yana furta "La haula wala quwwata illa billah" tattaki yayi kadan ya matsa gaban balcony dinsa,ya zube idanunsa a gurin yana kallon jerarrun tsirran dake gurin suna rayuwarsu hankali kwance,duhun dare da hasken fitilu suna sake qawata ganin mutum. Qarar wayarsa ta sanyashi waiwayowa,ya zubawa wayar ido yana karanta sunan NADEEYA cikin ransa,sai data kusa katsewa sannan ya daga ya sanyata a kunnensa yayi shuru ba tare da yace komai ba.


*HUGUMA*

64

* TABARMAR KASHI_*

Page 64

"barka da warhaka yaa toufeeg" daga can daya sashen aka fada cikin d'ari d'ari,kamar me tsoron yin magana

"Barka" ya fada a dake kuma a taqaice

"Ya aiki yaa?"

"'Alhamdulillah" ya sake amsa mata a taqaice,duk sai taji ba dadi,saboda ba haka suka saba yin waya ba,ba kuma da irin wannan yanayin yake magana da ita ba,duk da ta saba da miskilancin sa,amma yanayinsa na yanzu ba dashi suka saba magana ba

"Yaaya upper week zan dawo gida,finally na gama exam dina,zaman canada ya qare"

"Good.....ina miki murna" ya sake amsa mata a taqaice. Marairaicewa tayi zuciyarta na karyewa,tamkar tana a gabansa

"Am sorry yaaya"

"Sorry for what?" Yayi tambayar hankali kwance kamar dai da gaske baisan abinda yake faruwa din ba

"Yaaya,nasan kasan nayi maka laifi,amma wallahi it was not my fault,tanata sakamin pressure akan tanason ganin FADEELA..

"Ki gaya mata,ta sanya a ranta bata haifi wata 'ya ba a duniya kwata kwata,fadeela a yanzun ba jininta bace" yayi maganar cikin zafi tamkar itace a gabansa. Laqwas NADEEYA tayi cikin toro da firgicin jin sautin muryarsa mara hayaniya lokaci guda ta cika da kauri.
Iska yadan furzar yadda nadeeya din tayi shuru ya tabbatar masa ta tsorata da yadda yay maganar ne,sai ya lumshe idonsa yana gogarin yiwa kansa saiti,bayan ratsawar shuru na wasu sakanni sal yace
"Ticket din wacce rana kikayi booking?"

"Sunday" ta fada a sanyaye

"Alright,zan dawo miki da abinda kika kashe,don nayi fushi bashi zai baki lasisin yiwa kanki wata hidima ba,don't tray to buy anything da kudinki,as long as iam alive"

"In sha Allah" ta amsa masa a sanyaye, zuciyarta cike fal da qauna da kuma soyayyarsa,irin zallar soyayyar yan uwantaka,wadda babu algus a ciki. Labarai kadan ta bashi suka katse kiran,don ta fuskanci yanayinsa kamar he's not in mood.
Ya jima da wayarsa a hannu yana jujjuyata ba tare da iya yin komai ba,haka kawai wasu abubuwa na rayuwa suke dauko kansu suna kawo kansu da kansu gabansa,rayuwarsu yadda ta gudana shi da
'yaruwarsa,shekara kusan ashirin da biyar baya.

Ajiyar zuciya hade zazzafar iska ya fesar,ya sake juya wayar a hannunsa sannan ya lalubi number hajiya qarama.

Tashi tayi ta zauna sasai tana cire hankalinta daga lissafin ribar kayan data kawo daga china da suka samu qarewa,ta

bada dukka hankalinta akan wayar ganin me sunan,tayi gyaran murya sannan ta saka wayar a kunnenta.

"Barka da dare"

"Barka kadai,yanzu yanzu na shigo daga gurin mutuniyar,suna can ita da nannynta suna shirin bacci"

"Ummm,yayi,batun nanny dinne dama na kira,nawa ta buqaci albashinta?" Wuyan rigar lace din jikinta ta gyara

"Har yanzu taqi fadin nawa,ni bansan kalar nanny din da muka samo ba wannan karon,nayi mata zancan kudin amma sai tacemin ba komai,aikin yafi kudin muhimmanci" gyara zamansa yayi,shima maganar ta dan bashi mamaki

"'Noo,ta fadi ko nawan ne,sai a yiwa elyas magana,a dinga cire mata on time " yayi maganar ne har qasan zuciyarsa, yana lua hangen canji qarara daga fadeela,a yadda zuciya da ransa sukayi masa dadi,yana ganin ko nawa ne ta bugaci a biyata baiyi tsada ba

"Okay,i will talk to her'

"Yayi' ya amsa a kasalance,tanaso su tattauna wasu abubuwa amma ya bata uzurinta,sai tayi masa addu'a sosai sannan ya katse wayar,ya jefara gefe yana jin dukka gabban jikinsa suna sake zama weak,don haka sai ya kwashe wayoyinsa yabar dukka sauran tarkacen a gurin, saboda akwai wadanda xasu gyara gurin,komai kuma su sanyashi a muhallinsa.
Wanka yasoyi daya dawo amma saboda ya kira fadeelan baiyi ba,don haka yana shiga ya zare kayan jikinsa,ya lullube murdadden jikinsa da babban lallausan towel. Minti talatin kacal ya fito yana qamshin shower gel,da hair shampoo dinsa me tsada da yake amfani dashi waien wanke sassalkan gashinsa da ko yaushe yake cikin daukar idanu da hankulan tarin matan da shi kansa baisan adadinsu ba,saboda mafi yawansu bashi da masaniya akan fadawar da sukayi cikin matsananciyar soyayyarsa. Mintuna sha biyar ya gama shirinsa,a hakan yayi sauri akan yadda ya saba,don shirinsa yana daukar lokaci,sosai yake bawa jikinsa da fatarsa kulawa da mayuka da turaruka masu shegen tsada,ko nawa yana iya kashewa ya siya turare zuwa mayuka,ko a yanzun kudin wasu turarukan nasa sun isa jari a waien mutane da dama. A gurguje ya feshe gashinsa da turaren ka,hakanan beard dinsa da nasa turaren na musamman tamkar wani mace haka yake a wannan bangaren.

Guri na musamman da yake gabatar da ibadunsa ya shimfida lallausar dadduma,cikin daidaituwa da miga dukka tunanin damuwar duniya izuwa bayanka ya fuskanci alqibla,cikin cikakkiyar tsaiwa da daidaito ya kabbara sallarsa.

Dukka raka'o'in daya saba yi babu wadda ya rage a ciki,ya dade saman abun sallah yana addu'o'in sa,bayan ya kammala yana nade abun sallar akayi masa knocking,sai ya waiwaya yana duban wata maqalalliyar na'ura dake nuna masa fuskar wanda ke knocking din. Jibril ne,matsawa yayi gaban bedside drawer ya ciro wasu files,sannan ya zura wasu lallausasan takalma da aka yi da wani gashi me laushi ya buda gofar da zata sadashi da setting room na gidan.
Cikin girmamawa ya rusuna yana gaidashi

"Sir... bakaci dinner dinka ba,ina fatan lafiya" kai ya girgiza yana miga masa files din

"Am too tired,ina bugatar hutu,gobe inaso mu fita da wuri,zan kwanta yanzun,ko meye please kada wanda ya tasheni,zan nemeka idan ina da buqatar hakan" hannu biyu yasa ya karba cikin girmamawa

"Yes Sir,have a goodnight"

"Allah ya tashemu lafiya" sai ya juya a nutse yana komawa dakin.

Saman lallausan carfet din dakin ya yada pillow,ba kasafai yake iya kwana samam shimfida me laushi ko katifa ba,yayi rigingine idanuwansa na kallon roofing din dakin cikin dim light din daya saki,ya kammala addi' o'insa ya shafe jikinsa,ya koma riginginen ya kwanta yana sauraren zuwan bacci.

A hankali jinsa da ganinsa ya fara nisa da wannan duniyar da muke ciki,ya haurawa zuwa duniyar bacci,irin baccin da kake tsakanin wannan duniyartamu da duniyar baccin,zuciya da ruhinsa suka fara haska masa wani abu da ya faru zahiran dazu dazu cikin rayuwarsa ta ainihi. Tana tsaye ta basu baya kamar yadda ya gani a mafarkinsa, dogon gashinta me tsananin duhu da sheqi daya raba tsakiyar bayanta,hips dinta da mazaunanta da suka fita ainun ta shape din doguwar rigar.
A mugun firgice ya bude
idanunsa,sannan yayi wani irin tsalle ya miqe ya zauna sosai saman carfet din,hannunsa ya sanya ya tallafi goshinsa da ya dan fara hada zufa,a hankali labbansa suka motsa da fadin

"Hasbunallahu la'ilaha illa huwa,alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem" ya maimaita ta kusa sau goma,sannan a hankali zufar ta fara ragywa tana bushewa da kanta,sai ya daga kansa yana bude idanunsa a hankali

"Meye hadin sa da nanny fadeela da har zata biyoshi cikin mafarkinsa?,me yasa duk yadda yakai ga kame kansa da idanunsa daga kan kowacce diya mace,amma hakan bai rabashi da tarin mafarkan kasancewa da wata diya mace dako fuskarta bai taba samun nasarar
gani ba? mafarkinsa na yanxun ya kusa yin
dai dai da yarinyar dake yawan zuwa debe
masa kewa,duk da baisan saurin murya ko ta
fuskarta ba,ya tsani wannan mafarkin da ko
yaushe idan ya yishi take sake haukatashi ya
maidashi mabuqacinsa,lalurar da ya dauka
yayi adabo da ita,ya tasa ta gofar da zai yaqi
hakan,yawan nauye nauyen da yake dorawa
kansa da ayyuka babu ji babu gani,ya dauka
sun isa su cire wannan buqatuwar daga
jikinsa. Yasan yayi nasara da idanunsa da
kuma zuciyarsa,ta yadda duk tarin matan dake
kai kawo a gabansa dama bayan idanunsa,bai
taba daga kai ya kalli wata yaji shaawar
kasantuwa da ita ko kuma ta burgeshi
ba.amma ta bayan fage, wata mace guda daya
tal da baisan wace ba na neman matsanta
masa,cikin watannin da duka duka basu gaza
biyar na.

Siririn tsaki yaja shi daya cikin dakin,ya
miqe cikin matuqar mutuwar jiki ya nufi toilet.
Alwala ya daura,ya dawo ya tsaya gaban
wardrobe ya cire qaramin towel ya goge lemar
jikinsa,ya saki towel din ya koma makwancinsa na dazu. Duk da bayason kwanciyar rub da ciki ko kadan,amma yau din ta zame masa dole haka ya kwanta a rub da cikin yana qangame dukka pillows din dake kewaye dashi.

****Tsam fadeela dake sanye da uniform dinsu,cikin tsafta kulawa da kuma tsaarin sãahar ta rige hannun sãahar din tana langabar da kai

"Ni ba itace zata kaini ba Allah kece zaki kaini" ta gadi a mugun shagwabe tana daf da sakin kuka. Waiwayowa hajiya qarama tay,tadan hade fuska

"Me yasa bakiji uktie,ta yaya nanny zata kaiki school,shin tama iya mota da kike zancan ta kaiki makaranta? idan kuma kinaso ki makara ne shikenan" labiba dake tsaye riqe da key din tata motar da zata miga fadeelan makaranta,saboda driver dinta da hajiya garama ta aika ta jefawa fadeelan harara,sannan tace

"Ta ina zata iya mota? bayan ba itace dasu ba a gida?‚an saba hawa motor din kasuwa?" A nutse säahar ta dag kai,kallo daya tayi mata ta bawa banza ajiyarta,don tun zuwan labiba gidan ta gama karantarta,ta kuma yi aji guda ta sanyata a ciki.

"Allah mommy ta iya,Allan kuwa"

"Ke ko ta iya bazan bayar da motata ba,saidai ku ira a wanke wata cikin motocin gidan nan sannan a kaiki" ta fada cikin fushi ta juva da zummar komawa cikin gidan

"Zo nan labiba" hajiya garaman ta kirayeta,ta dawo a fusace ta tsaya tana huci

"Bata key din ta tuqaku,saiku tafi tare ki dinga monitoring dinta kada ayi miki barna" fuska ta hade cikin fada take magana

"Allah kune kuke sangarta yarinyar nan,sai abinda takeso sannan za'a yi mata?"

"Waishin ba daga jikin kakanta da mahaifinta kudin motar suka samu ba?" Haiiya garama ta jefawa labiba tambayar. Sak labiba tayi tana duban tsakiyar idanun hajiyan,itama kafeta tayi da kallo. Sometimes kamar yarinyar tana manta waye ita,har suso wuce gona da iri a wasu lokuttan,shi yasa takanyi hakan,saboda makaho yasan cewa fa ana ganinsa.

Jiki a sanyaye ba tare kuma data sake cewa komai ba ta migawa saahar key din.
Kamar ba zata karba sannan tasa Hanna ta karba,tana ji a ranta wasu lokutan wasu mutanen suna da bugatar a koya musu hankali,a kuma basu darasin rayuwa.

Jikinta ta kalla babu buqatar sai ta koma ta canza kaya,doguwar riga ce da hijab dinta madaidaici duka golden yellow,sai wani adon wani abu me kama da lace da akayi daga qasan hijab da rigar sai slippers dake qafafunta.

Juya muqullin tayi tana duban
motar,qirar motar ba baquwarta bace duk da tana da tsada,ta saki boyayyen murmushi,tana rige da hannun fadeela daketa tsallen murna sukayi gaba,labiba dake cika tana batsewa ta biyo bayansu.

Kafin labiban ta iso tuni ta bude front seat ta sanya fadeela,ta zagaya sashen driver ta bude ta shige,dole da tazo back seat ta bude ta shigan tana qwafar raina mata wayon da sãahar din tayi

"Ko ba komai yau mun samu new driver" ta fadi don ta baiwa sãahar din haushi

Sarai ta jita,amma saitagi nuna hakan,murmushin da ya subuce mata ma kauda kanta tavi gefe don kada ta gani

"Zakiga new driver gain idonki" ta furta gasan zuciyarta.

Hira sukeyi da fadeela irin wadda suka saba,daga yadda suke hiran kadai zai gaya maka zallar shaquwar dake tsakaninsu da kuma gaunar juna,labiba na zaune a baya kamar zata fashe,ita taso samun wannan damar, amma kuma bata sameta ba koda quater dinta,yanzun ga wata banzan nanny daga sama tazo ta mamaye rayuwar yarinyar.

Sai data tabbatar fadeela ta shiga class,ta kuma sanya hannu akan kawota sannan ta fito. Zata tada motar mrs sadeega ta sanvo kan tata,dole ta tsaya suka gaisa "Kina aiki me kyau miss säahar, kowa ya kalli fadeela yasan tana samun canji garara,hatta da performance dinta a class ya qaru,tiny baby ta fara komawa chubby ma sha Allah"

"Alhamdulillah" sãahar ta fada,ita kanta tana jin dadi ko yaushe yadda yarinyar ke wayar gari da goshin lafiyarta da kuxarinta suna garuwa,basu jima ba sukayi sallama,mrs sadeega ta wuce su kuma suka fice.

Ta cikin mirror ta dubi labiba dake zaune a bayan ta toshe kunnuwanta da earpiece tana bin waqoqin turawa tana gyada kai,murmushin mugunta ta saki, saita take motar ta qara mata gudu. Da sauri labiban ta daga kai,ta zare earpiece din daga kunnenta

"Ke meye haka? ki rage gudu da Allah" tana kaiwa nan ta maida earpiece din. Da kadan kadan ta sake garawa motar gudu fiye da dazun,tuni labiba ta cire earpiece din harma da wayar duka ta ajjiye,cikin fada da tashin hankali take magana

"'Wai bakya gani ne,wanne irin gudu ne
wannan?,kashemu zakiyi ne,dake fa nake
magana!" Kunnen uwar shegu tayi da ita,salma
sake qara gudun da tayi,ta shiga kurdawa
tsakanin motoci tana overtaking,ta tuna
da tsohuwar dabi'arta na mugun gudu a
hanya,don a baya saida yaa Saifullahi yasa aka hanata mota na wasu watanni sannan ta bari.
Tun labiba na hayaniya har ta fuskanci
hayaniyar ba zata kaita ba,ta koma lallashi
da kwantar da murya,amma sãahar kam ko
a jikinta,ta dinga shimfida gudu da ita,sai ga
labiban tana sakin hawaye,kowanne sashe a
jikinta rawa yakeyi,don babu abinda ta tsana a
mota irin gudu.

Daga bakin gate din gidan ta tsaida motarta bude ta fice abinta tare da bar mata
key din a jikin motar,tayi knocking gofar gate
din,daya daga cikin security din ya taso ya duba wacece sannan ya bude mata. Baya yaja cikin rusunawa,saboda sosai Allah ya sanya ma ma'aikatan gidan gaba daya gain wani irin girmanta. Yadda suke mu'alama da masu aikin gidansu haka ta dauki kowa cikin gidan,tana girmamasu qwarai, irin girman da duka cikin gidan ba wanda ke basu irinsa,bugu da qari me hannun kyauta ce ita,a hakanma afifa tace mata saita rage,don kada su lura da ita din wace,su sanya ayar tambaya a kanta.

"Madam ya na ganki a qasa?" Ya fada da 'yaf gaurayayyiyar hausarsa da bata fita tarr
"Daga waje na sauka"

"Welcome" ya sake fadi yana dage gate din don yasan yana jinkirin budewa labiban yau shine mutum na farko da zata fara saukewa kwandon rashin mutuncinta na safe.

65
*HUGUMA*


* TABARMAR KASHI_*8


DON MARTABAR MANZAN ALLAH ME
FITARWA KIYI HAKURI KIYI HAKURI.

Hankalinta kwance tama manta da wani abu da ta yiwa labiban,ta gama shirinta tsaf ta canza kava,tana duba saqon afifa a waya da take gaya mata mahmud nason a bashi dama yazo ganinta,sai taji sallamar hajiya qarama cikin matsakaicin parlor din da daga shi sai hallway na dakunansu,don ba kasafai take fita babban falonsu ba indai ba kitchen zata ta shiryama fadeela abinci ba.

A nutse ta daga kai tana amsa
sallamar,kamar kullum hajiya qaraman cikin shigar alfarma dake nuna zallar alfaharinta take,labiba ce da tayi firgai firgai ke take mata baya,ta zamu daya daga cikin kujerun ta zauna idanunta akan sãahar tana karantar yadda yarinyar sam wani abu baya mata kwarjini ko va tsoratata

"Barka da safiya" ta gaidata cikin salon data saba gaisuwa,sai data gyara zamanta sannan tace

"'Barkanki,ya kwanan uktie?"

"Alhamdulillah ta amsa mata tana qogarin katse kiran dake shigo mata waya.

"Ya akayi kikayi gudun wuce sa'a haka da labiba.har kina shirin hallakata?" A nutse ta sake kallon labiba sannan ta maida kan hajiya garama

"Ni din?"

"Kefa" ta amsa kai tsaye tana kallonta,tare da mamakin yadda take bada amsa lokuta da dama kanta tsaye,kamar ba wadda ke aiki a qarqashinsu ba,ita din kuma sai ta gaza daukan kowanne hukunci koda da zazzafar magana ne,abinda bai taba faruwa ba tsakaninta da duk wani me hidima dake qarqashin ikonta.
Ajiye wayarta sãahar din tayi sannan tace

"To bansan sanda akavi haka ba,don normal driving nayi yadda na saba,saidai ko a idonta ne ya zamana gudun daya wuce qaida,asalima a waie na sauka nabar mata motarta ta qarasa shigowa da ita,kina iya tambayarsu idrith dake bakin gate" yadda tayi maganar a miqe kai tsaye yasa hajiya qarama duban labiba

"Wallahi qarya takeyi,jini na saura kadan ya hau" labiban ta furta kamar zata saki kuka

"Bansan waye me gaskiya a tsakaninku ba,sai kiyi haquri, tunda bakison hudu next time karku sake hada mota" baqinciki kamar zai kashe labiban haka ta juya ta fita, sãahar kuwa ko daga kai ta kalleta bata sake yi ba.

"Ina fatan magungunan nan sun qare kamar yadda na irgasu?" Hajiya garama ta fada bavan ficewar labiba,wayar ta kuma ajiyewa,ta dora idanunta duka cikin na hajiyan. Wani abu me qarfi hajiyan taji tattare dasu,sai ta zame ganinta tana cewa

"Kin zubamin ido baki amsamin tambayata ba"

"Sun qare‚na yau kawai ya rage"

"Kin tabbatar?" Saita jinina kanta kawai ba tare data ce komai ba. Tsam hajiyan ta miqe tana mata wani kallo

"Yayi kyau,cikin satin nan ganwar mahaifin fadeela zata dawo rayuwa damu cikin gidan nan,banason komai ya canza daga cikin sharudan dana gindaya miki,and then....magungunanta duka zasu dawo hannuna,duk lokacin da zata sha ki kaimin ita tasha sannan ta taho,wasu lokutan tafiye tafiye na kasuwanci na suna kamani,idan hakan ta taso zan damqa su a hannunki ta yanayin daya dace" daga haka ta juva tana fita daga falon.
Kasa dauke kallonta sãahar tayi daga kanta,haka kawai a yau din wani qaqqarfan zargi ya taba zuciyarta,sai taji gaba daya zuciyarta tayi mugun matsewa da takurar son jin wanne matsayi hajiya qaraman ke dashi a gurin fadeelan.

Kusan zaman banza tayi a gurin,ta kasa tabuka komai,zuciyarta da kwanyarta nata jujjuya mata al'amura masu dama game da rayuwa,hango kanta ta dinga yi shekarun baya,lokacin da adam ya maidata mahaukaciya tuburan,ya dinga shayar da ita gubar allurai da magungunan da suka kusa sanyata amsa sunan mahaukaciyar me license ma,tsoro ya shigeta bayan wata zuciyar ta ayyana mata.
.. hajiya garama na
daya daga cikin masu wanna hali da dabiar.
Wani gumi ne ya karyo mata,ta yaya zata bari hakan ya faru da zuciya da ruhin da suke da rauni,salihar zuciya da kyakkyawan ruhin da basusan sabo ko cuta ba,sam sam....ba zata taba bada wannan damar ba,zata yi dukkan me yiwuwa ta katange fadeela daga dukkan wata cuta muddin ranta matugar ta samu kuma tabbaci da yaqinin abinda take zato din,sai inda qarfinta ya qare.

Sau uku baaba ramatu na wuceta,tun batayi magana ba harta tambaya

"Antyn fadeela lafiya kike yau kuwa?" Dan garamin murmushi ta saki tana gyara kwanciyarta cikin sofa

"Lafiya lau nake baaba, kasala kawai nakeji"

"Jiki da jini dama,to Allah ya garemu da lafiya"

"Ameen ya hayyu ya gayyumu" ta amsa mata tana maida idanunta ta lumshesu

Dawowar fadeela daga makaranta ne ya tasheta a wajen,yau gaba daya zancanta na dawowar sister nadeeya ne(haka take kiranta kamar yadda taji abby dinta wani lokaci yana kiranta da shi),ta hana sãahar yau sakat,alamu sun nuna akwai qaqqarfar shaquwa a tsakaninsu,bata samu hutu ba sai da suka kammala komai,ta hau google meet ta kira mata abby dinta,ta ja mata qofar dakin ta barta a ciki. Tun wancan ranar bata sake bari nasu take barin parlor din ko gurin,har sai ta
kammala sannan ta biyota tana bata labarin hirar da sukayi da abby dinta.

Tana kitchen tana hada mata abinci ta
shigo da gudu da tab din a hannun ta

"'aunty,don Allah sister nadeeya zaki kiramin" ta
fada a marairaice,murmushi ta saka ta ajjiye
wuqar hannunta,ta goge ruwan hannun nata
jikin towel,ta koma ta watsapp din da aka
budeshi saboda ita kadai ta kira matan,cikin
sa' a tana online sai ta miga mata ta koma aikin
nata,ita kuma ta juya da gudu ta fice.

Tun daga kitchen din take jiyo hirarsu da
dariyarsu,allai nadeeyan uwa ce da fadeela keyi da ita sosai. Har ta gama abincin ta
baro zuwaira hirar bata qare ba,sai ta wuce
dakinta ta daura alwalar sallar la'asar. Tana
idarwa fadeelan na shigowa rungume da tab
din,murya qasa qasa tace

"Sister nadeeya tace na kawomiki ku gaisa,nace abby ya hana sai an fara tambayar mutum tukunna,don Allah aunty nanny zaki gaisa da ita?" Murmushi ya subuce mata, fadeelan badai jin magana ba,saita miqa hannu ta kamota jikinta,ta karba tab din ta ajjiye a gabansu,fuskar nadeeya ta fito sosai a screen din.
Murmushi ya wadaci fuskar nadeeya, okaci daya da idanunsu suka gauraya waje daya kowa yaji wani abu game da dan uwansa

"Barkaaa" nadeeva ta fada tana waving hannayenta wa sãahar

"Barka kadai" sãahar ta maida mata itama cikin murmushi

"Yamma ne nan ko? to kin yini lafiya auntynmu?" Murmushi ya sake subucewa

sãahar tare da jin nauyin kiranta anty da nadeeya tayi tunda ko a ido kana ganinta zaka san sun kusa sa'anni da ita idan ma zata girme mata to da kadan ne
"Lafiya alhmdlh sister nadeeya,ya karatu?"

Cikin jin dadin sunan data ambaceta dashi da qaramar dariyar farinciki tace

"Karatu ya qare, in sha Allah nan da kwanaki uku ina tare da ku,nazo naga the world talented nanny dinmu" murmushin sãahar ta sakeyi

"Ma sha Allah,to Allah ya amince sisternmu" matsowa fadeela tayi tana sake zayyano mata dame dame zata taho mata da shi. Saahar din zata matsa don ta basu guri nadeeya tace

"Don Allah karki tafi,yanzu kin fini iya ji da rigimammiyar 'yar nan,ki zauna kya tayani lissafa wadan nan kavan wasan da taketa fadi,ta dauka ni abbynta ce da zan mata tawagar kaya?" Ta fada tana dariya. Murmushi saahar ta saki,sai ta koma ta zauna,wayarta na hannunta ta hau watsapp tana duba kwantan sagonni;,lokaci lokaci takan daga kai ta kallesu cikin ban sha'awa da burgewa idan sukayi wani abun,duk sanda zata daga kan sai sun hada idanu da nadeeya,saidai su sakarwa juna murmushi.


******Washegari aka bude daya dakin da tun zuwan säahar din yana rufe,saboda me dakin wato nadeeya din bata nan. Dukka furniture din din ciki aka fidda,aka shirya sababbi,sannan aka maida mata kayanta ciki aka sake gyara dakin da kyau. Fadeela da suke tare da sãahar din ta kasa sukuni saboda murna,dole karatun ranar da ba'a yi ba kenan,sai ta barta.

*******Karfe hudu da rabi na ranar lahadin motar da take mallakin nadeeya ta shigo da ita katafaren farfajiyar gidan mahaifin nata.
Seatbelt dinta ta cire tana duban ilahirin harabar gidan,ita sam banda Dr jarma din yace lallai ta sauka a nan din,da sai ta gama kwanakinta a gida sannan zata zo gaidasu,sam zama a gidan koda na minti daya ne bai taba mata dadi ko kuma ya burgeta ba,bawai don bata samun kulawa ko wani abu na jin dadin rayuwa ba.

Oofar motar ta bude da kanta ba tare data jira tarin ma'aikatan dake yungurin mata hakan ba,fuskarta a sake,kasancewarta mutum itama me fara'a da haba haba da al'umma cikin kuma kulawa take amsa barka da dawowar da kowa keyi mata,bayan tafiyarta karatun data shekara hudu tana yinsa,wanda a shekara hudun sau biyu kacal tazo gida bisa tsarin yaa toufeeq da yace baison yawo,idan karatun zatayi tayi basai tazo musu gida ba

A haka ta gama gaisawa kaf dasu,sannan ta tuqe ga hajiya mansura dake tsaye tana faman doka mata murmushi

"Lale maraba da dawowar diyata cikin aminci"
ta furta tana yunqurin kamo nadeeya zuwa
jikinta. Kadan tadan zame tana murmushin
itama

"'Na sameku lafiya?"

"Wannan gaisuwar sai a ciki za'a yita,abbanku
yana toilet yana qarasawa shiryawa,muje cikin
tukunna" waiwayawa tayi tana bawa masu
aikin umarnin shigowa da jakankunanta

"A'ah,ai basai sun shigo dasu ba,zan wuce
gidan yaa toufeeq ne" fuska tadan bata

"Me zakiyi a can nadeeya?‚ga gidanku?"

"Fadeela nacan na jirana,zanfi jin dadin can
din" ta bata amsar tana takawa zuwa cikin
gidan rungume da wata jaka

Please Login or Register in order to submit comment