Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 35 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tsinci hannunsa riqe da empty cup,ya maida a hankali ya ajjiye yana tunanin rabonsa da shan madara a tea,sai gashi yanzu ya shanye ta tsaf,har yana jin buqatar qarin wani tea din,to amma bayason ya aika din,zaidai binciki yadda ake sarrafashi.

*********A tsaye suke suna fuskantar juna,duk da cewa ita din bashi take kalla ba hakanan akwai 'yar tazara a tsakaninsu. Irin kallon da yake mata kadai zai gaya maka zallar yadda zuciyarsa ta narke da soyayyarta

"Zan tafi.don Allah ina roon kici gaba da bani dama"

"Allah ya kiyaye ka gaida gida" ta fada tana
Juyawa,zuciyarta a quntace saboda abubuwa biyu,na farko tasa yasa an tilastata ta bashi damar zuwa zance gidan mutane,taso ta furje amma Dr girema ya kirata da kansa,yayi masa irin fadan da bai taba mata irinsa ba,sannan kuma ya tabbatar mata wa'adin sati biyu kacal ke gareta,ruwanta ta bashi dama ta bude masa zuciyarta ta fadada tunaninta su fahimci juna,ruwanta ne kuma taqi. Maganganun dr sun daga mata hankali sosai,don bai taba mata magana da salon fada da bacin rai irin haka ba.

•Ci gaba da kallonta mahmud yayi har zuwa sanda ta bacewa ganinsa,ya sauke hannunsa yana furzar da iska daga bakinsa,sannan ya juya yana nufar inda gurd dinsa da ya masa rakiya yake. Hakan yayi dai dai da shigowarsa ta qaramar qofar gidan,yana sanye da wani lallausan yadi da aka yiwa dinkin african kaftan na maza,fuskarsa ta cika da wani irin kwarjini,elyas da jibril na biye dashi.

Dawowarsu kenan daga masallacin layinsu wansa aka gudanar sa taro da akanv duk sanda aka samu dama,kusan duk wan ke muqami ko babba a unguwar yana halartar taron. Lokaci guda idanunsu suka sarge ana juna,murmushi mahmud ya saki cikin hanzar ya maida akalarsa zuwa gabansa

"Sir" ya furta yana saluting nashi cikin murmushi,fuskar toufeeg ta motsa kadan alamun murmushin shina yayi, ya migawa mahmud din hannu
"Barka da yamma sir"

"Barka,kana lafiya?"

"Lafiya alhamdulillah,kwana da yawa sir,tun a
Singapore,ban zaci zamu sake haduwa nan kusa ba"

"Gashi Allah ya nufi hakan" ya fadi yana maida hannunsa ga aljihunsa fuskarsa a dan sake ba kamar yadda take ba

"'Gaskiya ne,ina fatan zamu sake haduwa anan kurkusa"

"In sha Allah" ya fada yana gyada kanshi

"Nazo ne wajen qanwata da kuka riqemin a gidanku"

"A nan din?" Ya fadi cikin mamaki

"Yes sir" ya fada yana waiwaya hadi da
duban inda sãahar ta tsaya a dazun. A ran
toufeeq din ya danji mamaki,me kuma zaya
kawo qanwar mahmud gana gidan?,ko cikin
qawayen nadeeya ne?,shine tunanin da yafi
kwanta masa

"She's my soulmate,inata qoqarin ganin mun
dai daita ne,she's my wife to be in sha Allah"
sake daurewa kansa yayi,har ya kalla ainihin
sashen cikin gidan ba tare da ya shirya ba,sai
ya gyada kai yana sake bashi hannu

"Allah ya taimaka" ya fadi ya zame hannunsa
bayan sunyi musabaha yayi ciki.
Dab da zai shiga sashensa nadeeya ta
fito tana laluben sãahar sabida shurun da taji
tun bayan fitarta,tayi masa sannu da zuwa
ya amsa yana tambayar fadeela,sai tace
masa tayi bacci yanzun nan bayan ta gana
jiran dawowarsa,yana wucewa ciki yana gaya mata ta kawo masa cottee nan da kamar awa daya, murmushi ta saki gain yadda ta zama addicted da coffee din nanny,shi da baya cin komai a hannun kowa. Har ya zarta ya dawo da baya yana tambayarta waye yayi bago a gidan?

"Nanny N ce,ko ba mahmud ba?" Kai ya jinjina,sai kuma yayi gaba ba tare da ya sake cewa komai ba,amma can qasan ransa cike yake da mamaki,mahmud ke son nanny din gidansa?,abun sai yaji baiyi making sense ba,so amma shi din ba mai damuwa da shiga rayuwar wasu bane,don haka tun bai isa sashensa ba ya tattara lamarin ya watsar.

Sai daya gama komai ya sauya kayan jikinsa zuwa wata shirt,v neck ne daya fidda sirrin ginannen girjinsa me yawan gargasa,sai dogon wandon joggers pants,qafarsa saye da socks da baya rabo da ita yawancin lokuta.

Farfajiya ce ta musamman da akayi mata gofa daga cikin falonsa, wanda aka qawatata da wasu irin sofas masu retractable canopy a samansu,wanda zasu baka daman zama comfortable kamar kana kan gado,samansu ya zauna yayi relaxing sosai sannan ya kunna system dinsa bayan ya duba lokaci ya tabbatar lokacin da suka sanva don yin meeting dinsu through video call da directors na companies dinsa dake gasashe daban daban lokacin ya cika,ya bude system din ya saita komai sannan yayi group call in general.

Ba jimawa kusan kowa ya daga din,mutanene da sukasan muhimmancin lokaci da kuma na aikinsu,don haka komai suna yinsa ne akan lokacin da aka tsara zaa yi din. Cikin salo da qwarewa da sanin makamar aiki suke tattaunawa,da zallar qwarewa a harshensa na furta kalmomin yaren turanci,a haka suka cinye awa guda cif,wanda basu qara ba kuma basu rage ba aka tsaida taron,suka sanya wani lokacin da zasu sake haduwa su tattauna.

Sake zama yayi saman sosai saman sofa din,yana gyara rumfar dake saman sofa din. A yanzun yana jin aminci da nutsuwa sosai akan kasuwancinsa,dukka directors dinsa amintattu ne,ya tabbatar koda babu shi zasu iya gudanar da kamfanin fiye ma da yadda zaiyi.

Wayarsa ya ciro ya lalubi number nadeeya,bugu daya ta daga

"Yaa gani nan,kana ta baya ne?"

"Yeah be hurry"

"Okay tom" ta amsa masa,tana maida dubanta kan säahar dake hada coffe din zata dora masa

"Don Allah yafi na ko yaushe,zan tambayi wani abune, inaso a bani da wuri,kinsan yaa moha shi da girki two and one ne" murmushi tayi tana girgiza kai,tuni ta fahimci hakan al,yanason laflyayyen abincihakanan baya shiri da yunwa.

Tun kafin ya kashe kiran da ya yiwa nadeeyan yaga kira nata shigowa wayar tasa baisan number din ba bashi da niyyar picking,saidai yana gogarin katse kiran nadeeva din kiran ya shigo ya daga lokaci guda ba tare da ya shirya ba,dai dai lokacin kuma true caller dinsa ya nuna masa sunan me kiran AMEESHA!.

lya sunan kawai ya haifar da wani irin bala'i cikin zuciyarsa,lokacin da sautin muryarta kuma ya baqunci kunnensa sai ya ja fikinsa ya sauko daga saman sofa din yayi tsaye,kowacce jijiya ta jikinsa tana miqewa

"Ina fatan kana lafiya,babu wata doguwar gaisuwa,don na tabbatar ba amsamin zakayi ba.....inason naga 'yata,inason a bani lokaci nazo na dauketa tayimin hutu,tunda nasan zuwa sati me zuwa zasu fara exam,upper kuma sun gama..

"'Stop!" Ya tsaidata a tsawace, yanajin wani abu na masa tururi tun daga zuciyarsa zuwa saman fuskarsa

"Lokaci na farko kuma na qarshe da zanyi warning dinki,ki cire a ranki cewa kin taba haihuwa da toufeeq jarma,ki cire a ranki cewa kina da 'ya a duniya tare dani,wannan shine gargadina gareki" yayi maganar yana nuna gabansa cikin wani irin fushi da deepness a cikin muryarsa

"Ta yaya? ka taba ganin an raba uwa da
'yarta?,laifin dana aikata tsakanina da ubangiji na ne,so bai shafi alaqata da dangantakata da

'yata ba,inata kawaici,inata dannewa,ina tsoro da fargabar kiranka,for what! fadeela yata ce, kuma har abada ba'a taba canzawa tuwo suna"

"Idan kin isa ki kusanceta da taqi daya tak!,kiga yadda sunanki zai sauya" ya fada cikin tsawa da matsanancin fada

"Bazan kusanceta a zahiri ba,amma zan kusanceta ta hanyar da duniya zata sake shaidawa diyata ce halak malak'

"Go ahead. karki fasa,zan nuna miki other side dina da baki taba gani ba,stupid idiot" ya fadi yana wurgar da wayaryasa hannunsa ya shafi sumar kansa da qarfi hadi da yarfar da hannunsa.

"Ka dinga yawan ambaton Allah duk sanda zuciyarka ta zafafa" daya daga cikin maganganun maji suka fado masa a ransa,sai ya koma da baya da baya ya zauna gefan sofa din,qafafunsa a qasa,ya lumshe idanunsa yana kiran

"Hasbunallahu wani'imal wakil,wala'udwana illa alazzalimin,ya hayyu ya qayyumu birahmatika astagis, aslih li sha'any kullah,fala takilni ila nafsy darfata ainin" a hankali sai numfashinsa dava fara canzawa sakamakon tuna wace ameesha da tabon da ta barwa rayuwarsa ya fara daidaita.

Duban sãahar data shirya tea din nadeeya tayi

"Don Allah anty N,taimakeni,magana mukeyi me muhimmanci da maji banason ta katse,ki migawa yaa moha din,yana ta baya idan kuma ta falonsa zaki shiga ki tambaya guards zasu saita miki" duban nadeeyan tayi,sai taji ta kasa musanta mata. Ba sau daya ba ba sau biyu ba,a kwanaki goman da yayi da dawowa tana nemanta alfarma taje su gaisa,har ta gaji ta daina,batason taji wani abu a ranta kota dauka wani abune na daban,don haka ta gyada kanta tana gyara yafen dan mayafin pakistani dress din dake kanta,wanda ya lullube asirin sumarta me tsaho cika santsi da kuma laushi,ta juya a hankali tana fita a kitchen din

"Maji tace tanaso yau ku gaisa, wana biyu bataga fuskar diyarta ba,kamar ma tace akwai maganar da zakuyi,zan rige wayar harki dawo"

"Alright" ta fada tana murmushi,haka nan itama Allah ya sanya mata gaunar matar kamar yadda take gaunarta,tana burgeta,tana da wata irin kamala da dattako sosal.

Haka nan takejin gafafunta babu nauyi sanda ta nufi gofar bayan da zata sadata da farfajiyar da yake din, taci gaba da takawa a nutsen,sassanyar iskar dake gurin tana kada turaren iikinta zuwa kowanne sashe na wajen.

Kafin ta garaso ta hangi mutum zaune saman bagar sofa din da aka yiwa farar shimfida,saidai bata iya ganinsa fuskarsa saboda yayi qasa da kansa. Tana sake kusanto gurin tana kasa sarrafa idanunta daga dauke dubanta daqa kansa,cikin jikinta takejin kamar tana dosar wani mutum ne data taba saninsa ko ganinsa,a haka har ya rage saura taqi kadan ta cimmasa,ta bude bakinta da taji ya soma rawa da nufin yin sallama,dai dai lokacin da ya daga fararen manyan idanunsa da suka rune zuwa kalar jaaa.

*HUGUMA*

* TABARMAR KASHI_*

Page 71

Guri guda idanunsu suka hade,wani abu me matugar garfi ya fusgeta,ya kuma ratsata tun daga tsakiyar kanta har zuwa tafin qafafunta,a hankali tray din dake hannunta ya sulale yayi d'ai d'ai a gasa,bata bawa kanta wani option ba da ya wuce juyawa cikin hanzari da sassarfa tana barin gurin.

Ko motsawa baiyi ba daga inda yake zaunen,tamkar an dasa shi a wajen ya bita da kallo harta qule ta bacewa ganinsa. Kaf tunaninsa ya katse ya kuma tsinke,babu abinda ke kai kawo a fuska da kuma zuciyarsa sai fuskarta,his ex president......me takeyi a gidan? wayo ya kawota cikin gidan?. A hankali ya sauke dubansa kan farantin da yayi d'ai d'ai a gurin,komai ya kama gabansa,tunanin da ya darsu a ransa ya sanyashi zaro wayarsa ya sake kiran number nadeeya,bugu daya ta dauka

"Waye kika aiko ya kawomin coffee?"

"Am sorry yaaya,muna magana ne da maii nannyn fadeela ne"

"Nanny?" Ya tambayeta da wani irin murya

"Eh yaa,am sorry ya mohai didn't intend to offend you" bai tsaya ce mata komai ba ya kashe wayar kawai

"What if itama ta shigo rayuwar su ne ta cutar masa da fadeela?" Shine kawai abinda ya samu zuciyarsa na jaddada masa,dukkan alamu sun nuna she's not in need bare yace hakan va sanyata aikatau,bata fito daga gidan da suke da qaramin qarfi ba bare yace a buqace take,ko kuma ta cancanci tayi aiki a wani guri, qaramin aiki ma irin wannan, she's well educated,tana da qualifications din da zata iya samun aiki ako ina Nigeria da waienta,amma sai ta zauna yin aikin nanny?no...ko daya zuciyarsa bata kwanta masa da hakan ba,kai tsaye ya tashi a wajen,ya bulla ta falonsa ya shiga ya dauki wayarsa ya fara neman layin mommy qarama.

Da gyar ta isa dakinta saboda wani irin bugawa da zuciyarta keyi,kamar zata balle qirjinta ta fito ko kuma ta amayota ta baki.

Gefan gado ta samu ta zauna tana maida numfashi,idanunta dukka a rufe,tana ganin shacin inuwarsa ta cikin duhun rufaffun idanunta

"Yaa moha,shine toufeeq? daddyn fadeela? ‚yayan nadeeya?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar,wanda motsin fadeela da sunan kiranta da takeyi tun kafin ta shigo dakin ya sanyata bude idanuwan nata,sai ta mige da hanzari ta fada toilet ta maida gofar ta rufe.

Tsaye tayi a jikin gofar tana jin sautin siriryar muryar yarinyar tana kiranta,sai zuciyarta ta gaza jurewa da shurun da tayi mata

"Anty N idan kin fito maji na jiranki" saita sake mata gyaran muryar alamar ta amsa

'i love you anty" ta fada tana dariya ta fice.
Hawaye masu zafi ne taji sun taru mata a ido,yarinyar ta saba gaya mata wanann kalmar duk sanda ta danyi wasu awanni bata ganta ba,a yanzun data gaya matan sai takeiin kamar furucin da zai shiga tsakaninta da ita kenan na qarshe ita fadeelan ......koda wasa batajin zata iya lamuntar zama gida daya da MT jarma,mutumin da ya wulaqantata,ya tozartata,yaci mutuncinta,mutumin da baisan darajar dan adam ba,sai taji tana jajantawa fadeela,yarinyar batayi sa'ar uba ba sam,ta fito daga tsatson da bai dace da halayyar yarinyar ba.

Wani kuzari ne yazo mata da ya sanyata bude gofar dakin ta fito,ta nufi qofar dakin ta murza mata key sannan ta dawo da sauri ta jawo luggage dinta ta fara zuba kayanta a ciki.

Cikin mintuna galilan ta gama hada dukka kayanta waje guda,dama ba wasu kaya masu yawa take bari cikin gidan ba,tunda kowanne sati tana zuwa gida ta maida wasu ta dauko wasu,ta zari Vail dinta dake saman couch ta nannade kanta zuwa wuyanta,ta jawo luggage din ta bude qofar dakin fa fito.

Tana sako gofarta a hallway din suka bangaji juna ita da nadeeya wadda ga biyota da iPad din ta bata maji din kamar yadda maji ta bugata. Da sauri nadeeya taja baya tana kallonta mamaki kadan na nunawa saman fuskarta

"Ina zuwa haka da akwati da yammar nan?"
Sosai tayi gogarin dadaita muryarta

"Gida zan koma nadeeya" razani ne ya nuna
sosai a fuskarta,sai lokacin ta samu damar
qarewa birkitaccen yanayin sãahar din kallo

"'Gida kamar vaaya anty N,me ya faru?"
Hannun nadeeya ta laluba ta sanya mata key din dakin a hannunta

"Kuyi haquri,bazan iya ci gaba da zama tare daku ba"

"Me kike cewa säahar? don Allah me

mukayi miki? …baaba ramatu!" Nadeeya ta
gwalawa baaba kira a rude ganin sãahar ta
ja luggage dinta tana barin hallway din zuwa
falonsu,wanda daga shi sai babban falonsu sai
fita daga sashen gaba daya.

Kiran baaba ramatu din da tayi yaja
hankalin fadeela ta fito daga dakin nadeeya
din

"Baaba,wai anty nanny ce kawai ta hada
kayanta wai gida zata koma"
"Subhanallahi,me ya faru?,me akayi mata?"

"Wallahi ban sani ba baaba" nadeeya ta bata
amsa ita da fadeelan suna rige rigen cimmata.
A falon garshe suka tareta har baaba
ramatun

"Haba Khadija,me ya faru haka rana tsaka zaki
ce gida zaki koma"

"'Ba komai baaba,na ajiye aikin ne" teddy din hannunta fadeela ta yar,ta kama hannun sãahar ta rige tsam

"Don Allah anty karki taft,idan kuma zaki tafin bari na dauko kayana mu tafi tare" zuciyarta ta sosu da yadda taga yarinyar ta rude lokaci daya,sai ta tsugunna a gabanta tana riqe da hannayenta

"Tafiya ta zama dole faddee na,kiyi haquri kinji,babu komai, sister nadeeya tana tare da ke,zata kula da ke,hakama baaba ramatu" saita zame hannun zata miqe,amma fadeelan taqi sakinta,ta fara hawaye tana cewa

"Allah ni bazan zauna bake zanbi"

"Am sorry my faddee" ta fada tana shafa sumarta da ta gama gyara mata ita dazu da azahar,tayi mata ado da wasu pink din ribbons.

Zame hannunta tayi ta soma nufar waje,tana qwararawa kanta gwiwa daga raunin da zuciyarta ke shirin yi,batason ta karaya har taji ba zata iya tafiya ta barsu ba,tanason ta tsira da mutuncinta,wanda ta tabbatar idan tana gidan a qarqashinsa babu inda mutuncinta zaije,tunda har ya nemi take mata kima da martabar ta a muhallin da ba nashi ba....yaya kenan zai faru a yanzun da zata zamanto qarqashin ci da sha da inuwar gidansa?.

Iska me zafi ya furzar daga bakinsa sanda ya gama jin komai daga bakin hajiya garama,zuciyarsa bata nutsu ba,yafi gasgata akwai manufa cikin shigowarta rayuwarsu,don haka zuciyarsa tafi aminta da sallamarta daga gidan,koda ko wanne irin kulawa take bawa fadeelan.

A hankali kunnuwansa suka fara jiyo masa sautin kukan fadeelan,ya mige a nutse yana riqe da wayarsa a aljihunsa,ya kuma tunkari barandarsa ta inda yake iya ganin komai dake faruwa a farfajiyar gidan.

Itace a gaba janye da luggage dinta,fadeela na biye da ita,nadeeya da baaba ramatu kuma suna biye da su cikin hanzari da alama suna nufin dakatar da ita ne,sauran maaikatan gidan kuma sunyi carko carko cikin damuwa,kowa ya kasa aikata komai,saboda basusan maqasudin abinda ke faruwa ba.

Ransa ya sosu da ganin yadda fadeelan ke binta gudu gudu sauri sauri,amma ko sau daya bata tsaya ba bare ta waiwayo ta dubi kukan da takeyi ba
"Fadeela!" Ya kirata a tsawace,abinda bai taba yi ba tsahon rayuwarsu shi da ita.

Dukkansu suka tsaya cak,har saahar din da kiran nasa yayi wata irin tsawa a tsakiyar kanta,ta kuma runtse ido tana fatan Allah ya sanya ba dukan fadeelan zaiyi ba.

A zafafe yake takowa har ya iso gurin

"Tashi ki wuce ciki!" Ya fadi da muguwar tsawar da ta sanya nadeeya ja baya da sauri ta koma bayan baaba ramatu ta boye,saboda a yau din gaba daya a birkice take ganin yaa moha din.

"Abby tafiya zatayi ta barmu,me mukayi mata,don Allah ka bata haquri"

"Ba abinda kukayi mata,ko bata tafi ba daman zan sallameta,saboda bata dace ta rayu daku ba" maganganun nasa sai suka zame mata tamkar zubar dafi tsakiyar naman zuciyarta,tana da muradin ko sau daya ta waiwaya ta sake kallon fadeelan dake kuka iya qarfinta saboda ita kadai,amma kalmarsa ta sanya ta lanqwasa zuciyarta taci gaba da takawa ba tare data waiwayo ba. Tsawar data sake ji ya yiwa fadeela karo na biyu ya sanya qwallar dake magale a idanunta qarasa gangarowa,zuciyarta na kwarara da wata matsananciyar tsanarsa,sai ta qara sauri tana ficewa a gidan,lokacin da ya sanya hannu daya ya dauketa cak ya nufi cikin gidan,ta qwalla garar kiran sunanta full, abinda bata taba yi ba

"Anty saahaaarrrr" kamar zata shide,sai ya dageta ya rungumeta tsam a jikinsa zuciyarsa na wani irin bugawa a mugun jargiy,yana jin kamar ana yankar naman zuciyarsa.

Duk yadda taso riqe qwallarta cikin mota amma abun ya faskara,sai tasa tafukan hannayenta kawai ta lullube fuskarta tana sauke hawaye masu dumi qwarai,ba abinda ke dawo mata cikin kwanyarta sai sautin kukan fadeela da yadda ta qwalla kiran sunanta har zuwa sanda sautin ya dusashe daga kunnuwanta. Sanda suka isa qofar gidansu ta cire kudin ta miqawa me napep,yana fadin

"Hajiya ga canjinki fa" ko waiwayowa bata iyayi ba ta daga masa hannu,ya fuskanci me take nufi sai hau zabga godiya yaja macnine dinsa yayi gaba

Baaba habu ne ya karba mata kayan,yadda yake mata sannu da zuwa yaji batace komai ba sai ilkinsa ya bashi akwai matsala,don haka bai sake cewa komai ba ya migawa jamilu luggage din yace ya garasa mata ciki da ita.

Can gasan magoshinta tayi sallama,falon nasu ba kowa kaman yaushe,yana nan a tsaftace da qamshinsa,da kuma ac dake bada iska me sanyin dadi,sai gamshin sanwar dare dake sirarowa kai tsaye daga kitchen dinsu.

Baaba rabi ce ta fito daga kitchen din sai taci burki tana cewa

"Ah ah,maraba da farar diya,kece yanzun nan akan hanya?" Kai ta gyada muryarta can qasa

"'Nice baaba rabi,barkanmu da yamma"

"Yauwa barka kadai" daga haka tayi hanyar bedroom dinta tana tambayar maama

"Basu jima da fita ba ita da afifa"

"To yayi" abinda ta fadi kenan ta wuce shige dakin nata.

Saman gadonta ta zube kamar wata kayan wanki tana qoqarin samarwa kanta saugin abinda takeji a zuciyarta,tayi lamo idanunta a rufe tana jin yadda zuciyarta ke gonewa. Inda ace ta san wannan gidan nasa ne,inda tasan ace wannan ahalin nasa ne inda ace tasan wannan diyar tasa ce.....to babu shakka,duk yadda zuciyarta zata kai ga tausayinta ba zata taba rabarsu ba.

Duk iya yadda yake tunanin zai iya lallashinta ko kuma ya bata baki amma abun ya faskara,har ya gaji da lallashin,ya koma bakin window din dakinsa yayi tsaye yana duban farfajiyar gidan, zuciyarsa na masa mugun zafi. Me yasa suna zamansu lafiya suna lallaba rayuwarsu zata shigo ta hargitsasu?,bayajin fadeela ta taba kuka irin wannan,koda kuwa ranar data rabu da mahaifiyar da tayi silar kawota duniya ne. Wai me yasa ne su mata basu da tausayi?,basu da imani?,a duk sanda zuciyoyinsu masu cike da ra'ayoyin qeta da son kai ta mosa musu,tabbas sai sun shiga rayuwar dukkan wanda suka hara sun aiwatar da koma meye sukayi niyya. Bayajin zai saurari kuka ko rigingimun fadeela,zata gaji ta haqura ta bari, dole ta koyi rayuwa babu mutanen da zasu zame mata baraza ko matsala,kamar yadda suka tashi shi da NADEEYA,suka rayu kuma a hakan,babu kuma wani abu da ya canza kalar qaddararsu,gasunan cikin qoshin lafiya da wadatar Allah.
Bismillahir rahmanir rahim

*HUGUMA*


*_TABARMAR KASHI_*


Book 02 Page 01

A ranar cikin su hudun säahar nadeeya taoufeeq da mai gayya me aiki fadeela babu wanda yayi wani cikakken baccin dadi, nadeeva ranta a jagule zuciyarta fal tambayoyi tare da neman dalilin tafiyar sãahar din lokaci guda,sai kuma yadda yaga zallae bacin rai daga fuskar ya moha,idan har kunnuwanta sunji mata dai dai da bakinsa yake gayawa fadeela

"Let her go,zaki ci gaba da rayuwa ko babu ita.." Sake juyawa nadeeya tavi tavi rub da ciki tana sake nazarin matsalar,a yadda idanunta suka karanci yaa moha din,kamar wata alaqar sanayya a tsakaninsu,to amma a ina ya santa ko kuma a ina sukasan juna? ,shine dai bata sani ba. Iska ta furzar daga bakinta,fatanta dai Allah yasa ba wani abu me muni bane va hadasu kwatankwacin na Ameesha. Sai ta girgiza kai da sauri tana gayawa kanta A'AH.

********Duk da kumburin idanuwan da basu samu bacci ba,da kuma ciwon kai da yakeson taso mata kadan kadan,amma hakan bai hanata shiga kitchen taya maama hadawa dr breakfast dinshi ba. Tana aikin amma yau so silent take,ba kamar baya da takanyi hira da masu aikin nasu ba. Afifa tun sassafe ta fice asibiti,saboda samun marasa lafiya da akayi daren jiya wadanda sukayi hadarin mota.

A daki ta iske maaman,ta gaya mata ta gama

"Ki shiryawa abbanku a dining na sashensa,fita zaiyi yau din yana da baqi,yanzu zan iso sashen" amsawa tayi da to ta juya tana fita, maaman ta bita da kallo. Tun jiyan datayi mata sannu da zuwa bayan dawowarsu da afifa ta karanci akwai wani abu dake damunta,to amma tasan halin kayarta da shegen zurfin ciki. Sannan tana zaune ma afifa zata gano musu komai. Sau da dama tana iya gayawa afifa damuwar da ita bata iya gaya mata ita,wannan din kuma wani haduwar iini ne da zumunci me qarfi a tsakaninsu fiye dasu iyayensu.

Ta gama shiryawa tsaf ta juya zata fita muryar dr girema ta sauka kunnenta,cikin kamilalliyar muryarsa yake sallama a falon.
Sai da gabanta ya fadi,amma ta tattara dukka nutsuwarta waje guda ta amsa masa sannan ta rusuna tana gaidashi


"Zauna muyi magana" ya fada maya shima yana laluben wajen zama,sai ta zame ta zauna daura dashi kanta a qasa.

"Jiya akacemin kinzo,ina fata ki dawo kenan,saboda ba zaki sake komawa ko ina ba,ladan da aka samu Allah ya amfanashi" a ladabce tace

"'Eh,na dawo kenan abba,ina godiya kuma da dukka damar da aka bani"

"Bata haka nake buqatar godiyarki ba ummi na" sai ya gyara zamansa sosai yana dora hannunsa saman hannun kujerar

"Zuciyata ta gama nutsuwa da aminta da yaron nan,don haka ina me shaida miki,muddin kin bani dama kamar yadda musulunci ya tsara mu nemi izinin bazawara,to zan bashi damar turo magabatansa,yazo ayi a gama komai a wuce gurin,kema ki tattara hankalinki waje guda"

"Na baka izini abba" ta fada kanta tsaye, zuciyarta na qeqashewa,tana jin yanzun bata da sauran mafaka kuma,guje gujenta ya qare,babu wani abu da ya rage mata,
MAHMUD GANA yayi winning.
shuru dr girema yayi yana son karantar fuskarta,yadda tayi saurin amsawa yadan daure masa kai,saboda ya riga ya ajema ransa ko yaya zai ta dan ja,amma karon farko babu jaa babu komai ta sallama?. Kai ya gyada

"Shikenan kije,Allah yayi miki albarka,ko meye ake ciki zan sanya mahaifiyarki ta sanar miki"

"Ameen abba" ta amsa tana migewa, kowanne sashe na jikinta na qarasa sakewa yana mutuwa dukkan wani qwarin gwiwarta yana zagwanyewa,qarshen tika tiki tik,mai afkuwa zata afku a kanta.

Da gyar ta tattara nutsuwarta tayi wanka,batason duka wannan bacin rai qunci da damuwar da take yawaita samun kanta a ciki,ga tunanin fadeela cunkushe cikin zuicyarta,duk wani motsi da zatayi sai taji kamar sautin muryar fadeela ne keci gaba da kiranta. Wannan ya sanya ta shirya ta nema izini wajen maama,ta wuce gidan yaa muhyi ta dauko khaleefa,daga nan suka zarce gidan ya Saifullahi ta dauko fadeel,ta sauka gidan yaa zaid ta dauko zaahid. Tana Sanya ran kasancewarta tare da yaran zaiyi matuqar debe mata kewa,duk da cewa yara maza ne ba mata ba,amma tana da yaginin zai dauke mata damuwa me yawa,ya kuma rage mata zaman kadaici.

********Dukka manyan idanunsa ya ware a kanta,yana ci gaba da sanya spoon din abincin a bakinta cikin tsare gida tare da sake tsuke dinkakkiyar fuskarsa. Hakan ya qara ta'azzara rashin fara'arsa tare da garawa fuskarsa kwarjini.

Duk sanda zata karba abincin saita kalli idanunsa sannan,ya sake kawo spoon din bakinta,sai taqi bude bakin bare ta

Please Login or Register in order to submit comment