Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 23 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kafadar raihanatu

"Karki damu raihanatu,jikina yana bani da dukkan gaskiyarki kikayi maganar nan" saita jawo yarinyar jikinta tana jin zuciyarta tana karyewa,duk da a yanzu tana gayawa kanta ba rauni take buqata ba,tana buqatar qarfin hali da dauriya me tarin yawa don ta gano ainihin gaskiyar maganar,duk da wani sashe na zuciyar yana mata tantama,anya adam?,adam da momee?,zasu aikata?.

"Na gode raihanatu" ta fada sannan ta janyeta daga jikinta,hannuwan sãahar duka biyun raihanatu ta kamo ta riqe,abinda bata taba yi ba,cikin rawar murya tace

"Amma don Allah anty kiyimin alqawarin ba wanda zaisan ni na gaya miki maganar nan"

"Komai rintsi komai tsanani raihanatu,na miki wannan alqawarin" tana nan tsaye kamar statue har raihanatu ta fice a gidan. Gaba daya ji tayi kamar an yashe komai daga cikin kanta,ta rasa dukkan wata idea da matakin daya kamata ta fara dauka,babu abinda yake mata amsa kuwwa a kunne sai YAYA ADAM YANA DA WATA MATAR BAYAN KE,ta yaya hakan zata kasance?,ta yaya hakan zata yiwu?,bayan ko yaushe suna tare da dam?,shiba matafiyi ba ba komai ba bare tace yayi amfani da wannan damar yayi auren a wani garin bata sani ba?,sai ta sulale ta zauna a wajen,tasa hannunta guda biyun ta dafe kanta wanda taji yana sara mata,kanta taji yana cushewa,zai buga da kalar tunanin da take takurawa kanta dashi,saita fara karanto sunayen Allah,da haka ta samu taja jikinta ta koma falon ta zube saman kujera.

Tunda ta kwanta bata tashi ba sai da akayi sallar la'asar,kana kallonta zakace bata da lafiya,dab da kiran magariba adam ya shigo,tana daga kwancen ta daga kanta tana kallonsa,fuskarsa cike da walwala da wani irin nishadi wanda batasan daga ina ya samo asali ba,saita samu kanta da qarewa fuskarka kallo da kyau,zuciyarta tana nazartarsa,nazarin da bata taba yinsa a kan adam ba.

Ganinta a kwance yasa ya sauke hannayensa daya ware mata yana jiran ta shigo ya rungumeta,duka sai walwalarsa ta koma,ya tako da sassarfa cikin nuna damuwa me yawa ya iso gareta

"Heart,what happened?" Yayi maganar yana dagota zuwa jikinsa

'banajin dadi" ta bashi amsa a taqaice

"What?,kada dai ace a kwance kika wuni?"kai ta sake gyada masa

"Ya salam,me yasa baki kirani ba?,amma baki kyautamin ba, please please karki qara yimin haka,idan wani abu ya sameki fa?" Yayi maganar kamar zai fashe da kuka,sai ya kwantar da ita,ya ciro waya,saiji tayi yana kiran wani likitansa. Drip yasa aka daura mata,wai tafijin qwarin jikinta,ya kasa zaune ya kasa tsaye,bayan fitar likitan ya shiga kitchen ya dora abincin dare,yayi yayi ta fada me takeson ci tace masa babu komai.

Wanzuwarsa a kitchen din ya bata damar sake zurfafa cikin tunaninta,ta dinga hango mode dinsa tun daga shigowarsa gidan kawo yanzu,tarin qauna kulawa da kuma riritawa ce zallah,sai zuciyarta ta cika da kokwanto,amma kuma ta rasa meye yake bata qwarin gwiwa da tabbaci.

Karin ruwan babu abinda ya qara mata,saboda wata irin narkakkiyar damuwa ce dake kwance qasan a zuciya,a haka suka kwana. Washegari tunda wuri ya hada mata breakfast ya shirya yace mata zai fita,amma azahar ko la'asar zai dawo. Har ya fita saita miqe ta bishi,a qofar dakinsa sukaci karo,yasa hannu ya jawo qofar yana kullewa da dan sauri,yayin da idanunsa ke a kanta yana kasheta da murmushi.

"Akwai wani abu ne?,ko kinaso na taho miki da wani abun?" Kai ta girgiza

"A'ah,zan dan fita strolling ne idan na gaji da kwanciyar"

"Ba damuwa,amma ko nasa momee ta kawo miki raihanatu?"kiran sunan kawai yasa gabanta ya fadi,saboda tuna gagarumin abun da muddin ta samu tabbacin afkuwarsa,zai zama sila ta guntulewar alaqar auratayya tsakaninta da adam,duk yadda take da kai, muddin kai din maha'inci ko maciyin amana ne.....to tana shata layi me girma a tsakaninka da ita.

"Ka barta,na danji dadin jikin ai" ta amsa masa.

Kasa komawa dakinta tayi bayan fitarsa,taja jiki ta zauna saman kujera,kamar kuma wadda aka mintsina saita miqe da sauri,kai tsaye ta doshi dakin adam. Tambayar kanta takeyi me zataje tayi a dakin?,tunda ta tabbatar ya rufe dakin a gabanta,kuma bata da sauran spare key da zai bata damar shiga?,amma duk da wannan tunanin sai ta gaza tsaida kanta daga dosar dakin da takeyi.

Sau daya ta murda dakin bawai don tana tantama ko tana da masaniyar bai rufe ba,amma cikin iko da qudurar ubangiji taji ya bude,mamaki ya cikata,ta tsaya tana duban qofar bayan ta bude,ta leqa sai ta fahimci yana sauri ne bai murza key din da kyau ba,lock din bai gama shiga ba ya zare ya dauka ya shige. Sakin wannan tunanin tayi ta wuce dakin da gaggawa.

Cak ta tsaya tana qarewa dakin kallo,tana nazarin ta ina zata fara binciken da zai bata shaida ko tabbacin abinda take zargi?,shikam adam ma bashi da safe irin nata,saboda yasha gaya mata ya yarda da ita. Wani tunani ya fado mata,a dazu da suka shiga dakin taga yanata kaffa kaffa da wardrobe dinsa,tun bata ankara ba har hankalinta yakai kai,amma bata kawo komai a ranta ba ko kadan,saboda tasan zuwa yanzu ya wanke dukkan wani zarginsa a ranta.

Cike da fargaba ta buda wardrobe din,cikin ranta tana addu'ar Allah yasa komai ya zama hasashe ne,Allah yasa komai ya zama tunani ne,muddin ta samu adam da cin amanarta,batasan ta yadda zuciyarta zata iya dauka ba.

Tsaf ta bincike wardrobe din,saidai bataga komai ba,tasa hannu tana shirin rufewa idanunta ya sauka daga can qasanta,wani abu me kama da jaka ta gani a jingine daga can gefe,saita tsugunna ta jawo,jakace baqa mai cike da zips kala kala,tunda take da adam bata taba ganin jakar ba,wannan ya qara mata qaimi da karsashi,ta fara bude zips din,take kudade masu tarin yawa daure cikin kyauraye da kuma takardu masu yawa suka fado.










*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 45


Kafafunta ne taji sunyi wani irin sanyi suna kamar zasu lanqwashe da kansu kai kace narkakkiyar roba ce,sai ta zame ta zauna sosai a qasa,ta ajjiye kudaden da suka kasance dollars masu tarin yawa bandir bandir gefe guda,ta zube takardun da kyau,ta soma dauka tana dubawa.

Wani irin gumi ne ya fara yanko mata,tun daga tsakiyar kanta zuwa tafin qafafunta,kowacce takarda da original copy dinta,da kuma wadda aka sauya a manne da 'yar uwarta,indai idanunta dai dai suke gane mata......takardun dukka filayenta da sauran kadarorinta ne dake wajensa aka sauyasu da wasu sunaye na wasu mutane da batasansu ba,affidavit na court dake bada tabbacin sunayen da kuma mallakar dake jikin takardun na asali,takardun withdrawal da akayi daga joint account dinsu,statement of account gaba daya,dama rufe account din da akayi kwata kwata.

Tashin hankali wanda ba'a saka masa rana,komai ya canza,ya tashi daga mallakinta zuwa mallakar ADAM ADAM,FAINUSA ADAM da kuma WARISHA KHADIRI,mutanen da batasan su waye ba banda sunan adam din dake maqale a jikin sunan kowannensu.

Kamar wadda aka tsinkawa jijiyar hannu ta zaro takardar gaba, certificate of birth ne me dauke da sunayen dake a sama,FAINUSA ADAM da ADAM ADAM,kanta ya sake kullewa da kyau,wani irin tashin hankali ya dira a tsakiyar zuciya dama kwanyarta tunanin da ya darsu a ranta ya sanyata ci gaba da birkita takardun gabanta cikin hanzari,caraf hannunta ya sauka akan takardar shaidar zama ma'aurata ADAM/WARISHA.

Sosai hannuwanta suka fara rawa,da gaske ne ashe?, abinda raihanatu ta gaya mata da gaske ne?,adam yana da wata matar bayan ita?,da gaske ne adam ya shirya cin amanarta?,indai waccan matarsa ce su kuma yaran fa na waye?, tambayar data sanyata surar passport din data gani guda hudu a gabanta,wanda budeshi ya zame mata tamkar madubi ko amsa na dukka tambayoyin dake karakaina a tsakiyar kwanyarta zuwa zuciyarta,suna barazanar fasa mata tunani.

Fes kamannin yaran suka bayyana kansu da kansu,adam sak!,kamar yayi kaki ya ajjiye,ko kamar karan da aka samu gwanin iya rabo ya tsagashi gida biyu.

Dif komai ya tsaya mata,ta dinga jujjuya korayen fasfunan da suka kasance baqaqe wuluk a idanunta,fasfunan dake dauke da visa ta qasar england,visa din da zata basu damar zama a qasar na shekaru ɗai ɗai har shekaru biyar cif!. Da qyar ta qwaci kanta ta fusgi harshenta ta kawowa kanta da kanta dauki ta hanyar furta
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, la'ilaha illa anta subhanaka inji kuntu minazzalimin" ta fara maimaitawa wasu hawaye masu zafi suna malala daga idanun nata.

Qoqarin hanawa kanta tashin hankalin kanta takeyi da gasken gaske,saboda yadda taji mararta tana qullewa,bata shirya asarar abinda yake cikinta ba,don haka tayita kokawa da numfashinta tana jansa tare da fitar dashi da sunan Allah,wata 'yar qaramar nutsuwa ta sauko mata,saidai zuciyarta na mata wani irin ciwo da zafi tana jin inda za'a dubata a yanzu qila a tarar ta kumbura.

Miqewa tayi jiri yana dibarta ta wuce toilet dinsa,ta tsaya gaban sink ta kunna famfo ta daura alwala tana fatan tiririn yaji da zafin dake fita a fuskarta ya tsagaita,ta kusa kashe minti goma tana daura alwalar tana kuma maimaitawa,ita kadai tasan dimuwa da razanar da zuciyarta take ciki,daga bisani tilas ta daure famfon ta fito zuwa bedroom din.

Gefe guda ta zauna,ta zubawa takardun da kudaden da fiye da rabinsu haqqinta ne ido,shi yasa ta daina jin alert?,ya zare duk wani kudi data nema da guminta?,ya yiwa matarsa da yaransa wadanda batasan da zamansu ba visa na barin qasar?,ya dauke duk wata dukiya tata ya maidata mallakinsa?,ya hanata haihuwa,ya hanata morar komai nata,ya yaudareta yaudara mafi muni,ya shiga rayuwarta a lokacin da taqi baiwa kowanne namiji fuska,yayi amfani da iya kalamansa, kyakkyawar mu'amala da kulawa mai matuqar nauyi da zurfi,irin kulawar da komai taurin kai da kafiyarki dole ki amshi soyayyar mutum,ya hada da wayo da dabara irin wanda itadin qarancin shekarunta basukai kansu ba,ya cusa mata soyayyarsa ya mallaketa yake kuma neman sanyata cikin musiba mara misali,me ta yiwa adam haka na cutarwa tsahon rayuwarsu da zaiyi mata wannan mummunar sakayyar?.

Ji tayi kamar zuciyarta tana narkewa,kukanta yanason fitowa fili ta yishi sosai,amma zuciyartata tana tunasar da ita

"Lokacine daya kamata ace kinyi abinda ya dace,ba lokacin kuka bane yanzu" maganar data fito daga can qarqashin zuciyarta kenan,ta kuma zaburar da ita,ta barota daga inda take zaunen,ta dawo ta tattara takardun da kudin,passport din da komai da komai yadda suke a tsare a jakar,bayan ta gama ta zuge jakar,ta daukota ta fita daga dakin,bayan taja kowacce qofa ta maidata yadda take,tamkar ma bata shiga dakin ba.

Doguwar riga me sulbi ta zura saman kayan jikinta,ta yane kanta da mayafin rigar,bayan ta shafa fuskarta da hoda ta zizara kwalli daya qarawa idanunta haske,duk da yawan kukan da tasha,sannan ta wuce zuwa farfajiyar gidan,ta bude motarta ta jefa jakar a ciki,ta tashi motar ta fice a gidan da gudun tsiya.

Kai tsaye gidansu ta nufa,tanason ta yiwa jakar ajiya a muhalli me kyau,tanason taga iya gudun ruwan adam,tanason ya kama kanshi da kanshi ta hanya mafi sauqi da dacewa.

Qasa da mintinan data saba isa gida a yau ta isa,don gudu tayi sosai saman titi,tanason ta riga adam komawa gida,batason yasan cewa ma tafita kwata kwata daga gidan.

Biyu cikin ma'aikatan gidansu ne suka taso suna mata sannu da zuwa,a yau din bata cikin dukkan wani yanayi na walwala ko sakewar data saba yi musu,don haka sama sama ta amsa musu,ta bude baya ta dauki jakar,saita barwa marwa key din motar tace ta rufe mata,ta wuce gidan dauke da jakar.

Gidan babu kowa sai masu aikin daketa kaikawo,ko maama ma a sannan tana daki a kwance tana hutawa,da kallo ta bita lokacin data shiga dakin,ta miqe ta zauna tana ci gaba da nazartarta

"Ajiya na kawo miki maama,wasu kaya ne masu muhimmanci,don Allah karki barsu nan kusa,nima ajiya aka ban,ina tsoron tabasu ko kuma nayi sakaci wajen ajiyarsu" abinda tace da maama din kenan,sai tabi jakar da kallo sannan ta sake maida dubanta ga sãahar

"To shikenan,amma dai,kedin lafiya lau kike kuwa?" Wani abu me nauyi ya sauka a qirjinta,tana jin kamar ta budewa maama zuciyarta taga tsantsar damuwa da kuma tashin hankalin da take ciki,to amma idan ta aikata hakan tasan zata jefata ne a damuwar data ninka tata. Dukkaninsu wani irin so suke mata,sam basu ajeta nan kusa ba a zukatansu

"Ba komai,kawai yau inajin weakness ne,gida ma zan wuce nadan kwanta,zan samu relief in sha Allah idan na tashi" kai tadan jinjina tana dan jin tantama,amma dai bata sake hango komai dazai bata hujja ba

"Allah ya qara lafiya,ya raba lafiya,kinqi bari a kawo miki me tayaki hidimar gida,ke kadai a family kin fita zakka sãahar,ba wanda babu me aiki a gidansa sai ke" murmushin da yafi kama da yaqe ta saki

"Maama saina haihu in sha Allah"

"Dolenki ai" ta fada tana miqewa da jakar a hannunta.

Kamar a zuwa haka a komawa ta dinga tsala gudu,cikin mintuna qalilan ta isa gidan,ta qarasa da motarta parking lot ta kasheta ta fito zuwa cikin gidan.

A parlor ta zube,dauriyarta tana nan qarewa,ba abinda ke mata yawo a idanu sai hotunan yaran dake jikin passport din,da sunan ADAM a matsayin ubansu,da kuma matar dake a mazaunin matarsa, kuma mahaifiya ga yaran kamar yadda ta gani a sauran takardun dake dauke da gurbin da ake buqatar sunan mahaifiya. To hakan me yake nufi?,tun asali adam baya sonta kenan?, auren jari yaso yayi da ita?,ko cin amana ne zallah ya sauka zuwa zuciyarsa?,mummunar zuciya suka hadu da iblis sukayi masa muguwar kururuwa?,adam da d'a?,wanda ba ita ta haifa ba?,adam da mata bayan ita da duniya ta gama sani?,ya maye gurbin kowacce kadara tata da dukiyarta da sunan 'ya'yansa?,wanann wacce irin azzalumar duniya ce muke rayuwa a cikinta?.

Duk yadda taso ci gaba da jurewa abun ya faskara,kuka ta zauna tanayi wiwiwi a falon,tafukan hannayenta shinfide saman fuskarta. Karar shigowar motarsa harabar gidan ya sanyata miqewa,kai tsaye ta wuce dakinta,ta kuma zarce bedroom ta fara hada ruwan wanka tana zare kayan jikinta,sam batason adam ya fuskanci komai bare wani abu ya darsu a ransa,don haka ta hada ruwa me dumi sosai,wanda tana gab da fara wankan ya Murda qofar dakin ya shigo, muryarsa cike da wani irin nishadi da a karon farko sãahar ta fassarashi,cikin muryar shauqi da nuna zallar soyayya yake kiranta

"Heart!,heart kina ina?" Lamarin da ya sakata lumshe idanuwa,wasu hawaye masu dumin gaske suka sulalo mata

"Har tsahon yaushe zai dauka yana yaudararta kafin ya gaya mata gaskiya?,ko kuma har sai lokacin da zata bude ido ta laluba sama da qasa babushi?,ya tattara komai nasa da ba nasa ba sun bar qasar shida iyalinsa?.

Gyaran murya tayi masa,saiya murda qofar bandakin

"Budemin nayi joining dinki mana" bata iya furta komai ba saboda ta tabbatar muryarta ta shaqe,saita sakeyi masa gyaran murya,dai dai sanda kira ya shigo wayarsa,saiya maida hankali kan kiran ya juya yana ficewa daga dakin tare da daga wayar duk a lokaci guda.


FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 46


Sake fashewa tayi da kuka cikin bathtub din,tanajin kamar ana matsa zuciyarta,ta jima a hakan sannan ta fito daga bandakin,tana takawa a hankali saboda yadda mararta ta riqe, idanunta suka sauka akan ledar daya shigo da ita ya ajjiye mata,wadda kullum yake kawo mata dukka abinda ta zabi ci kafin fitarsa,a yau sai taji ta tsani ledar da kuma tsani wanda ya kawo ledar,ta matsa gaban madubi tana goge ruwan jikinta,bata da karsashi ko sha'awar komai,kawai zata daure tayi komai ne don batason ya fuskanci wani abu,batason bashi qofar da zai dago akwai wani abu daya faru bayan fitarsa,tanason ta kamashi ne red handed,tana son ya kawo kanshi da kanshi,a dole ta shafa mai,ta zaro wata doguwar rigar ta zura,dai dai sanda taji an budo qofar da qarfi,har sai data hadu da bango ta bada wani bammm!.

Da sauri ta daga kai tana dubansa,shima ita yake kallo,ta tsirashi da idanu,wani lafiyayyen tashin hankali ne a kwance saman fuskarsa,ta hadiye wani abu me daci da tauri,nata bacin ran yana son yin tasirin da taketa danne masa tun awannin dazu,amma kuma sai tayi wani qaqqarfan yunquri ta kauda shi gefe,ta maye gurbinsa da lallausan murmushin da idan kayi masa nazari me kyau zakasan cewa zallar yaqe ne takeyi me masifar ciwo

"Sannu da zuwa,ka dade kuma cemin kayi da wuri zaka dawo" ta fada a shagwabe kamar yadda ta saba. Wani abu me matuqar girma ya hadiye a maqoshinsa,wanda ita kanta dake tsaye tana iya ganin yadda maqwallatonsa maqogaronsa yayi sama sannan yayi qasa,mummunar faduwar gaba da kokwanto suka lullubeshi,yayi namijin qoqarin qaqaro murmushin da yafi kama da kuka,cikin sanyin murya yace

"Eh......na dan tsaya ne,momee na raka wani guri" murmushi ta kuma saki tana gyada kai,amma kuma zuciyarta na wani irin qonewa,ba zata iya ci gaba dayi masa wannan murmushin tana kallon fuskar da take da mugun baqi a idanunta ba,don haka ta waske ta hanyar juyawa zuwa ga ledar tana cewa

"Let me see me aka kawomin" baice komai ba sai cika qofar da yayi ya juya ya fita a dakin,ta daga kanta a hankali tana sakin ledar ta fadi qasa,tabi qofar daya bar mata a bude da kallo,ruwan hawaye suna cika idanunta,dukkan wani tabbaci da yaqini yana sake samuwa a tatttare da ita.

A daren babu wani abu data iya ci,hakanan bata sake ganin adam ba,sai sintiri da motsinsa me qarfi data dinga jiyowa daga dakinsa zuwa parlor,haka ta duqunquna cikin duvet,idanunta a runtse zazzabi yanason kamata.

Sai wajen sha biyu saura sannan ya shigo dakin,har a sannan tana kwance ne kawai idanunta sun soye,babu wani alamun bacci,tana ga monitoring motsin adam din. Yana kunna fitilar dakin ta miqe tana hamma tamkar daga bacci ta tashi,ta kalleshi suka hada idanu tana mutstsuka ido

"Kada kacemin sai yanzu ka shigo?,har nayi baccin farko?" Ta fada tana qare masa kallo,daga shigowarsa gida zuwa yanzu har wata rama taga yayi,fuskarsa ta fada,ya firgice gaba daya

"Eh sai yanzu......ina wani aiki ne"

"Maimakon ka kirani na tayaka saika barni nayi bacci ni kadai?" Ta saje fada a shagwabe,kamar amma gasa zuciyarta,bata iya jin amsar daya bata ba,sai kansa daya shafa.

Saukowa tayi da niyyar zuwa tayi fitsari sannan ta daura alwala ko zataji sauqin zuciyarta,amma mararta ta riqe gam,saita zauna daga bakin gadon tana cije lebe,kanta a qasa tana ambaton sunan Allah

"Yau su waye da waye sukazo gidan nan kam?" A hankali ta daga kai ta kalleshi,yana zaune gefan gadon ko kayan jikinsa baiyi nufin cirewa ba,kai ta girgiza

"Ai yau ni kadai ka bari a gidan na wuni kamar tsohuwar mayya" ta amsa masa tana kafeshi da ido,sai ya danyi jim sannan ya zame ya kwanta kamar wanda zazzabi ke shirin saukar masa.

Koda ta dawo kwanciyar ta tayi,ta kuma saki jiki sosai kamar wadda ke bacci,tana jinsa yanata juyi,ta kwanta ya tashi ya miqe ya fita ya dawo,har zuwa sanda addu'a taci qarfin idanunta baccin da takewa kanta fata yazo.

Washegari bayan ta farka daga baccin daya dauketa bayan sallar asuba baya dakin,data fito falo sai taji motsinsa a bedroom dinsa,koda fa leqa ya yiwa komai na dakin filla filla

"Halan furniture zaka sake mana?" Ta fada tana dariya,ba fara'a ko daya a fuskarsa,sai kai daya girgiza

"Sanitation nakeyi" ya amsa mata a taqaice
"Ya kamata, shikenan yau bari na fansheka na hada mana breakfast" bata jira cewarsa ba ta juya ta fice.

Tana girkin tunani fal zuciyarta da ranta, sauqinta daya tun jiya bata fasa kiran sunan Allah a baki da zuci ba,tana samun raguwar quncin sosai da sukunin zuciya,tanason gayawa afifa,to amma ta tabbatar yadda afifa keda haushin adam komai ma zata dagulashi,ashe akwai abinda 'yaruwarta keji a jikinta shi yasa ta tsani adam har haka?,me yasa ita bata taba jin komai a kansa ba?,sai tarin yarda da aminci?,ko don ita za'a jarraba?,shi yasa komai nasa yayi tasiri a kanta?,bata taba manta yadda haduwarsu da adam ta samo asali,a b u k,yana level 400 gab dasu fara final exam,tana level 200.

Sam adam ba ajinta bane,hasali ma sãahar din tun a sannan da take da shekaru qanana she has a CHARISMA that attract many people to her,ba kowanne namiji ke iya tararta da sunan soyayya ba,amma adam din ya daukarma ransa saiya siya soyayyarta,yana da baiwar BAKI da IYA TSARA MAGANA(abubuwa biyun dake cutar 'yammatan wannan zamanin kenan game da maza),tun daga randa ya bayyana mata soyayyarsa tayi gaba a wajen ta barshi kamar sauran samarin dake yawo a kanta,ya shiga ya fita yasan komai a kanta,ya zaqulo dukkan wani abu dake burge sãahar,abinda tafiso da wanda bataso,ya maida kansa irin wannan mutumin sak,a duk inda yasan zasu hadu,sai yayi wani abu daya tabbatar zai burgeta ko kuma yana cikin likes dinta.

Ya jima yana bibiyarta da rayuwarta kafin ta daina ganinsa tsaf,abinka da zuciya da akace tanason me kyautata mata,tana kuma qin me munana mata,tun bata damu ba har ta fara jin babu dadi,basa makaranta daya da afifa,afifa na northwest a sannan,a b u k din da take kuma ita bamai kule kulen qawaye bace,tana da mugun miskilanci sosai,idan kaga sakewarta to irin iyayen nan masu zuwa da qananun yara,a nan ne zaka ga jerarrun fararen haqoranta,wannan din kuma sai ya sanya mata farinjini sosai gurin matan,gefe guda ga mazan dakeson miqa soyayyarsu a gareta,wadanda sukasan ita din me ajice kuma tafi qarfin ajin ajinsi,suna fatan koda abota ko qawance tayi dasu uwa uba tana da wata irin basira,tana da brain qwarai da gaske,wadan nan su suka sanyata zama sananniya sosai.

Sai bayan wani lokaci sannan ya dawo,ko a sannan bata sake masa yadda yakeso ba,saidai an samu improvement akan yadda suke a baya,da wannan ya samu qofa ya kuma baje duk wata basirarsa,wadda sai data kusa

Please Login or Register in order to submit comment