Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 63 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mata komai ba,saboda shi kadai yasan yanayin da yake ciki. Yayi tsammanin so guda daya ne tak!, ya dauka so na gaskiya shine so,wanda babu wani abu da yake iya canzashi, bai taba dauka akwai randa ameesha zata iya neman saki daga hannunsa ba saboda kawai raguwar abun duniya daga hannunsa, bayan bai gaza mata ta fannin ci sha suttura ko lafiyarta ba har a lokacin kuma. Duniya ta yiwa
•/ hajiya garama dadi, dama wani mugun tsana ta yiwa ameeshan,ko kusa ko alama bata gaunarta,don ko sau daya babu jituwa a tsakaninsu.

Sosai hankalin mamarta ya tashi, tayi kuka tayi fadan amma ameesha tayi kunnen uwae shegu,a sannan tayi wani irin kyau ta sake zama mace me aji ta kuma sake sanin cewa ita din matar manya ce duk ta silar auren toufeeq,ta samu sutturu masu aji, ta kuma sake smaun wayewar da take hangen doguwar shimfidaddiyar rayuwa data dara ta gidan toufeeq.yanzu abu daya ne zai zame mata cikas cikin da take dauke dashi,a galla akwai wasu watanni masu yawa a gabanta kafin ta haife ta kuma yaye,ita a yanzun koda haihuwarsa ta samu tayi, komai da zai biyo baya me sauqi ne.
Warning din da toufeeg ya karta mata shine abu guda daya da zai hanata juye cikin. Ta sani su din ba qananun mutane bane don dai kawai toufeeq din yana daukan kansa ba'a kowa ba, danginta kuma basa da garfin karawa dashi,so haquri ya zame mata dole kenan.

A zahiri tana son toufeeg sosai amma rayuwar data tsarawa kanta ta fuskanci ta sha banban datasa rayuwar da ya tsara,dole to ta ajiye nasa tsarin don cikar nata tsari da burin.

Allah me musanyawa bawan da ya dogara dashi daga mummuna zuwa abu mafi kyau cikin rayuwarsa.
Wata guda kacal da rabuwarsa da ameesha wani Erin
1 gofofin alkhairi suka dinga bude masa ta kowacce fuska.wasu alkhairan shi kansa bai taba tsammanin samunsu ba a irin wannan lokacin. Lokaci qalilan ya maida ninkin abinda ya rasa harda ma ninkin abinda ya rasa din a baya.

Cikin wata hudu kacal duk wanda ya kalleshi yasan ya samu sauyi na rayuwa fiye da rayuwarsa ta baya,ya warware sosai yaci gaba da harkokinsa,sabbin hanyoyin neman kudi suka bude masa fiye da zato.

Har a lokacin yana lissafe da watannin cikinsa dake jikin ameesha,kowanne wata yana aika mata da komai da yasan zata bugata, dai dai da ruwan sha na roba haka yake ajiye mata, komai na watanni biyu yake ajewa ninkin abinda zata bugata kenan, hakan baya hanashi sake aika mata da wani bayan kowanne wata.
Mamanta naso gwarai ta ganshi amma bata samu wannan damar ba, saboda bata da wayar hannu,sannan kuma shi kansa toufeeq din bai sake taka gidan ba tun daga ranar, amma kuma hakan bai hanashi yiwa mama din aike ba kamar yadda yakeyi mata a baya.

Tafiyar da yayi china wadda dawowarsa yayi dai dai da shigar cikin ameesha watan haihuwa, ya iso da siyayyar kayan baby me azabar yawa, har hajiya garama ta kasa jurewa

"Kai kam kamar wanda za'a haifawa taron arfa?, yariyar da basusan mutunci da darajarka ba toufeeq kae yiwa* wadan nan hidindimun?, kamar wanda ya rasa mafadi?"

Dan qaramin murmushi kawai ya saki,a sannan kome hajiya qaraman ta fadi baya bata ransa ko yaga cewa hakan ba dai dai bane, saidai idan abinda tace din yaji baiyi masa ba ko bai gamsu ba ya canza da abinda zuciyarsa ta kwanta da shi

"Mahaifiyar ta nagartacciyar macace,wadda nake da imanin da halinta tayo tare zamu tsufa ni da ita din, saidai mutuwa ta raba, haihuwa kuma ta fari ce hajiya, ko china din gaba daya ake da bugatar na siya masa indai arzigina ya kai zan siya din"

"To mara kunya,tashi ka bani waje" ta waske da fadin hakan ta bishi da kallo sanda yake barin wajen ranta a mugun quntace.

Lokacin da siyayyar kayan fitar suna nata da kayan baby ta iski ameesha ta gama saddaqarwa toufeeq din ya fara komawa CLASSY TOUFEEQ JARMA din da takeson gani, ta kasa zaune ta kasa tsaye a ranar sai data samu dukkan information da take nema akan TOUFEEQ din

"Turgashi, seema kina gain ban tafka wauta ba muddin na yarda na haihu a gida?bayan har yanzu da sonsa nake kwana da sonshi nake tashi?" Tace da gawarta da sukeJ zaune cikin dakinta dake eikin gidansu,wanda ta qawata fiye da kowanne guri na gidan. Tayi furucin ne a sanda take tsaye saman kan qawar tata da tirtsetsen cikinta da take lissafe da randa zata saukeshi ta huta


"Ba garamar wauta ba,wannan arzigin dake yafi dacewa,ke yafi cancantar ki cishi"

"Yanzu meye mafita?, ta yaya zan jawo hanakalinsa?"

"Ke kike da hanya kuwa" seema ta fada tana mata nuni da cikinta. Murmushi ta saki tana shafa cikin nata hadi da gyada kai,sai ta koma ta zauna ta jawo wayarta ta fara kiran number wayar toufeeq din.

Har ta garashi ringing dinta ta katse bai daga ba,a qalla ta kirashi ya kusa sau goma amma abiyi picking ba,wannan ya soma daga mata hankali,seema tace

"Yasan ke kike kiransa karanto min numbers din na kira miki shi a wayata ko za'a dace ya daga"

Harara ta watsawa seemar tana jin kamar ta mareta,ita zata bawa kura ajiyar nama?.

"An gaya miki yana daga baqin numbers ne? ai saidai ki dige kina kiransa amma bazai dauka ba,bari ki gani" ameesha ta fada tana gyara zama tare da tura masa gajeran text.

Ba dadewa saiga kiransa, murmushi ameesha tayi
ta migawa seema wayar

"Ki daga kice masa yazo yanzun kamar labour nakeyi yazo mu wuce asibiti" lokacin yana tare da wasu baqi,jin zancan yasa ya barsu ya tsallako ya taho.
Yayi mamaki da ya ganta tana fitowa lafiya sumul, Ransa kuma va baci da jin abinda vasa ta kirashi da wannan sigar data daga hankalinsa. Har ta gama bayaninta da koke koke baice mata ta tafas ba,sai data gama sannan ya juya ya bude motarsa zai shige kafin ya waiwayo

"Karki sake maimaita yimin irin wannan shashancin, don ni din ba mara aikin yi bane ba zaman banza nake ba da zaman jiran kiran wayarki" sai ya tashi motarsa yabar gurin.

Hankalinta yayi gololuwar tashi qwarai, saboda yadda take ganin so kulawa da qauna daga idanun
TOUFEEO din bata taba tsammanin zai juyawa buqatarta baya ba,musamman da ya zamanto a yanzun tana dauke da abu mafi soyuwa a wajensa a jikinta ba. A ranar da gyar ta iya bacci.

Kwana biyu kacal da faruwar hakan Allah ya yiwa mahaifiyarta rasuwa,wanda shine ya zama silar sassautowar zuciyarsa,ya kuma sauka daga dokin nagin da ya hau,ranar sadakar bakwai ya dauketa ya maidata gidansa da kansa. Ashe wasa farin girki!!


Zafafabiyar
🔥🔥🔥🔥🔥🔥🔥

"HUGUMA*


•_TABARMAR KASHI_*


Book 02 Page 57

Zuciyarsa ta sake jin amanna data koma
din, saboda gananun maganganu da yaji sun fara yawo akan shi dinma kada Allah yasa ba irin halin mahaifinsa na auri saki yake dashi ba.

Sanda ta koma din duniya ta samu,don haka ta kwantar da kai sosai, duk wani biyayya kulawa da tattali tana bakin qoqarinta, duk da cikinta yayi nauyi amma bata fasa duk wani abu da tasan yana so din ba. Wani lokaci tausayinta kan lullubeshi qwarai,ya sanya hannu suyi duk wasu ayyuka tare, tayi wani mugun laushi, ta sauya kwata kwata daga ameesha din da ya sani. Tun yana mamaki yana d'ari d'ari har ya saki jikinsa, ya kuma barwa ransa rasuwar mahaifiyarta ne ya kawo hakan, tunda ya san ciwon mahaifiya,shi da ba rasuwa ma tayi ba.

Biyayyarta da canzawarta ya sanya shima yake tuquru wajen kyautata mata, ya sakar mata komai da take da bugata. Wannan ya sanya ta sake ninka biyayyarta,kyautatawa da kulawa da nuna zallar soyayya me zurfi data sake sanyashi sakankacewa da ita,ya kuma sakar mata zuciyarsa,ita kuma hakan ya bude mata gofofi da dama na abubuwa masu yawa.

Cikin wata na goma ta sauka ta haifi fadeela, yarinyar da tazo da wani irin farinjini da tarin alkhairai masu yawa ga mahaifinta harma da mahaifiyar tata.
Suna na kece raini ameesha tayi kanta ya fashe sosai, toufeea ya fasa mata kai ya sanya taji ta kere sa'a cikin mata.

Hankali kwance ta fara rainon fadeela saboda masu aiki biyu da toufeeq ya dauko mata saboda yarinyar. Wani irin raino takeyi mata kamar ba diyarta ba,a lokacin ya siya mata mota irin wadda takeso saboda dadin zama,a sannan ko watanni biyu fadeela batayi ba ameesha tana iya fita ta barta hannun masu aiki ba zata dawo ba sai yamma awa daya ko biyu kafin toufeeq ya dawo,zata shirya ta shiga sabgoginta cikin gidan sannan ta dauki yarinyar, tun bata gama mallakar hankalin kanta ba ta saba da rashin uwa a kusa. Kusan baba ramatu ce ta zame mata kamar kaka kuma uwa,ta jima tana wanann dabi'ar kafin toufeeq ya ankara. Ya nuna mata bacin ransa qwarai, amma saita kwantar da kai ta bashi haguri tare d algawari ba zata sake ba,don a sanann ko zaginta zaiyi bata tada kai bare ta nuna masa ta damu, bata gaunar duk wani abu da zai hadasu, saboda kudade
sosai take karba daga hannunsa, bai kuma taba cewa
a'ah ko don me ba?,shi a ganinsa muddin zaka samu
kulawa daga wajen mace da biyayya meye ba zaka iya
kashe mata ba?,meye ba zaka iyayi mata ba?. Abu daya ne har a sannan ya gaza canzata akai shine bugatar aure, baisan abinda ke faruwa ba da ita sam,amma ya aza hakan akan yanayin halittar ne wanda yasha banban da rasa neeesa ba kusa ba. Damuwar kawai shi tun asali ba meson auren mata biyu bane, hakan ya samo asali da yadda yaga mahaifinsa na yawan aurar mata yana kuma
saki tun bayan rabuwarsa da mahaifiyarsu.


Kyautatawar bogi da biyayyarsa ya sanya yakejin
haquri da mace idan tana da wani nagasu ba aibu
bane, dama duk dan adam tara yake bai cika goma
ba,duk kuwa da yana shan dan karen wahala amma yana goqari tare da neman sani akan hanyoyin da zai
magance matsalar a tsakaninsu a samu daidaito.



•_SHEKARA UKU_*


Shekara uku da haihuwar fadeelan,a wata rana
cikin ranakun sa'a a wajen toufeeq ya samu fiye da
yadda yake samu daga gurin ameesha. Sunyi sallama
dashi sallama me kyau,cike da aminci da qauna, zaiyi
tafiya zuwa Canada.

Har bakin mota ta rakoshi tana koke koken zatayi
kewarsa, vana dauke da fadeela akafadarsa,yayi
murmushi yayi kissing goshin yarinyar yana jin qaunar
yarinyar har gasan zuciyarsa sannan ya miga mata ita
hadi da kamo hannunta va rige cikin nasa a tausashe

"nayi alqawarin ina gama abinda naje yi zan dawo gida immediately, zan iso tare da dream car dinki" wani dan garamin ihu tare da tsalle ta saki ta kuma
rungumeshi, yayi mata suprise, bata taba zaton zai siya mata motar ba,ta dai fada ne kawai

"Thank you, thank you so much"

"You deserved it" ya fada a tausashe yana kissing
goshinta itama. Ita ta bude masa motar ya shiga sannan ta rufe masa sukayi gaba tana gurin a tsaye.

Sanda ya isa airport sai ya samu anyi cancelling
tashin wannan jirgin, sunata bawa mutane irinsa haquri wadanda basu duba sagon da suka tura musu ta email
ba akan hakan tun yau din da sassafe, ransa ya baci da wannan al'amarin da sai a qasata Nigeria kawai yake faruwa.haka suka juyo suka bar airport din. Har zai koma gida sai kawai ya fasa ya wuce sabgoginsa,a can din magriba ta kusa cimmasa,sai ga kiran hajiya qarama

"Ya akayi number dinka na Nigeria ya shiga? kai da yanzu warhaka ya kamata ace kana canada?" Dan garamin tsaki ya ja yana mata bayani

"To Allah yasa hakane yafi alkhairi, yauwa idan zai yuwu don Allah ka dawo yanzun, ina bugatar takardun nan da na baka ajiya,nan da awa daya alhaji kutama zaizo ya karba, ana bugatarsu urgently" ta fada da alamun gaggawa a muryarta


"Alright, na gama abinda nakeyi nima,gani nan"

"Yauwa,sai ka garaso, koda zaka rigani isa ka jirani please,don ina asibiti yanzu duba hajiya barratu"

•"Ba damuwa" yace da ita sannan ya aje wayar.

A hanya ya tsaya ya ya duba musu kayayyaki a wani shopping mall na ciye ciye da yasan ameesha da fadeela sunfi so, kowa ya siya masa nasa. Yana tafe yana imagining murnar da zasuyi da bai samu flight ba,yanason yaga kulawa qwarai da soyayyya daga fuskar matarsa,shi yasa ma yaso mata suprise bai gaya mata bai samu flight din ba.

Suna gab da karya kwanar shiga gidan haka kawai gabansa yaji ya fara faduwa. Ya lumshe ido yana kiran sunan Allah, me yake faruwa haka dashi?, Ya tambayi kana. A haka suka garasa cikin gidan shi da jibril ne ya dauki ledojin ya buda motar ya wuce kai tsaye sashensa. Harabar gidan ba kowa kasancewar magariba ta kawo kai.

Qofar a rufe take, sai ya sanya key dinsa ya bude ya tura ya shiga ya fara takawa a hankali zuwa ciki. Parlor din babu kowa shuru kakeji,ya danji mamaki ya kamashi,sai yaci gaba da kutsawa zuwa hanyar da zata sadashi da stairs yana kyautata zaton sun haura sama ne ita da fadeela din.

Wani mahaukacin bugawa zuciyarsa tayi yaji qwaqwalwarsa na neman tsayawa cak daga aiki. Fadeela ce kwance saman saman sassanyan marbles din dake shinfide a gurin, qafafunta na saman stairs na garshe, kanga kuma daya langabe na a qasa,sassalkar sumarsa ta baje sosai a gasa,yayin da kakkauran jini ya soma bata gurin.

Wani irin mummunar rawa jikinsa ya fara yi yanajin kamar numfashinsa zai bar iikinsa sanda va dagata yaga jikinta ya saki gaba daya kamar babu ruhi a tattare da ita. Bakinsa rawa yakeyi yanason kiran sunanta amma ya kasa yanason ya kira ameesha nan ma komai yaqi fitowa daga bakinsa,sai kawai ya saketa ya haura saman da mugun gudu da zummar nemo ameeshan yaji me ya samu diyarsa, saboda komai ya kwance daga kansa tunanin fara zuwa asibiti ma ya fita a kansa,so yake yaji meye ya sameta.

A hankali va janye hannunsa daga marigin gofar dakin sakamakon sautin darivar ameesha da yaji cakude da sautin muryar wani namijin

"Ya isa haka please mana, kai wai baka gajiya ne?"

"Ta yaya zan gaji? bayan har yanzu kawai dandanamin zuma kike a baki, kinqi barina na shiga ainihin inda abin yake?, kina rudani kawai da jikinki, kina barina akan hanya navita fama"

"Au, hakanma baiyi maka ba?,an gaya maka taba jikina din ma abune mai saugi? to ko mijin aurena sai randa nayi ra'ayi naji jima ina cikin yanayi matuqa nake sallama masa, kaima ka godewa Allah daka samu wannan damar,gaka yau har cikin dakin mijina,zaka kwana kana murzata" Dariya ya saki

"In sha Allahu vau sai na cimma gaci" dan tsaki taja

"To watagila idan naii abun yayimin yadda nakeso"

"Kina son muyita wahala ne na baki shawara ki kashe auren nan kawai kizo muyi aure ki huta da debar masa dukiya da kadan da kadan, kizo inda zan bude miki bakin lalitata kivita diba har sai kin gaji" dan shuru tayi sannan tace

"Ba zaka gane ba, kayi suna a rayuwa ma wani abune,yau ace ni matar dan MT JARMA ne ma wani babban alfarma ne, tabbas kana da kudi irin kudin da nakeso, amma matsalar sunanka baiyi fice kamar nasu ba,sannan kuma inason guy din sosai,yana da kyau ya iya soyayya garshe ne"

"Bansan baki da wayo ba sai yau, don ya fini kyau ni mummuna ne a kansa ai ba wani abu bane, kuma da kike maganar so soyayya, da soyayyarsa da dukiya wanne kika fi so?" Ya tambaya seriously

"KUDI malam sune fa gare magana" gyalgyalewa yayi da dariya

"Yauwa,aini na sani, shi kansa da bashi da komai ba zakiii sonsa ba na san halinki fa....ki bani kanki a yau kawai na miki algawarin million goma yanzun nan zakiji alert idan kin yarda"

"Amazing!" Ta fada da matuqar farinciki da zumudi fal muryarta
"Na yard…" Kamar an hankadashi da baya haka
yaji, bai iya tsaiwa yaji ragowar kalmar daga bakinta ba yaji kamar na daka tsawar sunan

"FADEELA!" tsakiyar kwanyarsa. Da wani mugun gudu da sassarfa ya dinga hada matakala bibbiyu uku uku yana sauka,yana isa yasa hannu ya kwashi fadeelan ya fita da gudu. Jibril na hangoshi ya tabbatar babu lafiya, bai bari ya iso ba ya wangle masa gofa,suna shiga ya figi motar da mugun gudu tare da searching na asibitin da zasuje a kansa ba tare da ya tambayi ogan L nasa ba,hankalinsa a mugun tashe sakamakon ganin hawaye saman fuskar mai gidan nasa,mutumin da ya sani sama da shekaru, bai taba ganin karaya ko girgiza saman fuskarsa ba komai girman tashin hankali, lallai abinda ya sameshi ba qarami bane, duk da kowa yasan tsananin qaunar da yakewa fadeela din wanda bata boyuwa.

Har sukaje asibitin aka karbeta tare da qogarin dawo da ita cikin hayyacinta ameeshan batasan abinda akeyi ba. Sai da likitoci suka gama komai suka masa bayanin idan ta farka za'a yi mata X-ray saboda tabbatar da lafiyar qwaqwalwarta akan buguwar da tayi,yana dakin gaban gadon fadeela din a zaune sannan uwar ta iso a birkice tana kuka.

"Me ya sameta?" Ta jefa masa tambayar da sai da yaji kamar ya Sanya wuga ya yanka maqogaronta banda zuciyar musulunci dake qirjinsa, da sunayen Allah daya dinga kira wadanda suka taimaka waien daidaita shi, banda haka ya tabbatar a yadda qirjinsa yayi nauyi shima iwar haka ba shakka yana kwance saman gado ana jinyarsa

"Fita!!" Ya fada a tsawace muryarsa na wani irin sargewa da matsanancin bacin rai,fitar saurin muryarta ba abinda yake tuna masa sai gazantacciyar hirarsu da kwartonta

"Kayi haquri don Allah, ba laifi ko sakacina bane,na gama mata wanka na shiryata kenan,na hau sama nayi wanka nima kafin na shirya na fito na sauko naga babu ita,sai jini wajen stairs, masu aiki suke gayamin ka fita da ita" ta fada cikin gunjin kuka,gabanta kuma yana faduwa da matsanancin toro da firgicin zaiyiwu yaga ANAS ko Kuma wani abu da yayi kama da haka Zaki fita daga nan ko sai na wulaqantaki?, maci amana me tozarta sunnar ma'aiki banason na sake ganin fuskarki daga yau a gaban ido na, muddin kika sake kika qara nunan fuskarki sai nasa bindiga na harbeki,ki tafi na sakeki saki daya" ya furta cikin matugar danne zuciyarsa ya furta saki dayan, amma zuciyarsa tafi amanna da ya qarasa guntule igiyar guda dayan da a yanzu tayi saura a tsakaninsu.

Sosai ta gigice da jin sakin da ya rattabo matan,ta bude baki cikin rawar murya ta fara roqarsa yace

"Ki yiwa kanki suttura ki fita tun ban tattaka ki a nan wajen ba,kije ki auri me kudin da ya fini,ki tara dukiyar da duk kikeson tarawar wannan damuwarki ne, abu daya zan gaya miki,daga yau ki cire a ranki a duniya kin taba haihuwar wata diya fadeela har abada" zata ci gaba da rogonsa yace

"Duk kalma daya idan kika qafa furtamin a bakin aurenki take, get out from here idiot!!!" Dole taja qafafunta ta fice, yasa hannu ya lullube fuskarsa zuciyarsa na bashi yanxun haka akwai janaba a jikinta na wancan kwarton nata.

Bincike akan fadeela ya kammala,ya kuma tabbatar data samu ciwo cikin qwaqwalwarta wanda shine sila na haduwarta da lalurar EPILEPSY. randa ciwon ya fara motsa mata yayi mugun birkicewar da bai taba yi ba,saboda shi dai bai tana ganin ciwon a gaban idanunsa ba daga wajen wani sai yau akan diyarsa mafi soyuwa a wajensa.


Zafafa biyar
"HUGUMA*


•_TABARMAR KASHI_*


Book 02 Page 58


Tun daga ranar bai sake bari ameesha taga
fadeela ba, kamar yadda ameeshan bata sake ganin
fuskarsa ba sai a hoto ko a media. Duk wanda zai tilasta masa yabar ta ta dinga ganin diyarta ya musu rantsuwar da suka tabbatar babu janyewa,duk da bai fito ya furta ainihin abinda ya rabasu ba,dr jarma kawai ya shaidawa saboda gudun kada yace ya maidata dakinta, ko ya bata diyarta,shi kurna ya gayawa hajiya qarama. Hajiya qaraman murmushi ta saki

"Ehe, ka gani ko? ni dama na jima ina ganinta tana
shigowa da maza gidan, to amma idan kayi magana
yanzu za'a ce ka takurawa surukarka shi yasa na
bari, amma kullum ina addu'ar Ubangi ya nuna maka".

"Ince ga yadda na rayu a wadan nan shekarun cikin ciwuka masu zafi guda biyu bata baki ne,ciwon fadeela da kuma mummunan ciwon da ameesha ta dasawa zuciyata,da gyar nima na qwaci kaina daga bugawar zuciya saboda mummunan hawan jini daya kamani wanda da gyar na qwaci kaina daga gareshi Allah ya kawomin waraka don ya dubi zuciyata akan ban zalunci kowa ba.tun daga sannan ta cire kowanne aminci a zuciyata daga kan diya mace, nayi mata uzuri duk da yadda bayyanar halinta na aureta mun zauna nayi haquri da ita mun rabu na tausaya mata na dawo da ita,na sanya qafa na ture duk wani aibunta saboda ganin kamar ta canza,ashe lumbu lumbu tayimin take cin dunduniyata,A DUNIYA AKWAI ABINDA YAFI CIN AMANAR WANDA KA AMINCEWA CIWO DA ZAFI!" ya furta wani irin dumi yana fita daga numfashinsa, alamu suna nuna cikin gololuwar bacin rai yake

"Babu" yaji sãahar ta fada cikin rawar muryar daya tabbatar kuka takeyi.

Hannunsa yakai ya shafi fuskarta,sai ya samu fuskartata jige sharkaf da hawaye,zuciyarsa ra motsa sosai. shi da itan dukkansu an bar musu wani tabo da har su mutu ba zasu daina tunashi ba,ba kuma lallai su fasa jin ciwo idan an taba musu gurin ba,sai ya zameta daga jikinsa cikin nutsuwa,ya sauka daga saman gadon ya kunna fitilar dakin, haske ya gauraye ko ina.

Stool ya jawo gaban gadon,ya zauna sosai yana kallonta da idanunsa da suka canza launi zuwa kalar ruwan goro kamar an disa jini a cikinsu.

"Tashi" ya furta a tausashe yana miga mata hannunsa. A hankali ta yaye duvet din sannan ta sanya tattausan hannunta saman nasa ya migar da ita ta zauna sosai,sai ya koma shima ya zauna sosai din, yayi folding hannayensa a qirjinsa yana dubanta kai tsaye

"Kiyi haquri, na karanta miki diary ba tare da izininki ba" kai ta daga ta kalleshi sai suka hada do,wasu sabbin hawaye suka zarto mata tana jin tausayinsa yana sauka a girjinta,wasu similarities dake cikin labaran su suna dawo mata

"Yayi fama da yawa,shi din bayan yaudara da cin amana harda nakasa ta barwa 'yar cikinta 'yar cikinsa?"

"I hope you forgiven" kai ta gyada masa a hankali.

"Thank you" ya furta yayi shuru na wasu 'yan daqiqu vanason hada abinda zaice da ita, saboda yanzun lokaci ne da zai nema dukkan wata yarda tata du gina kammalalliyar rayuwar da yake buri,iska ya furzar daga bakinsa,sannan ya sake mayar da dubansa a kanta

"Duk da Allah yana iya jarabtar bawansa ta duk sigar da
yaga dama, amma ina kyautata zaton an zaluncemu ne ni
dake, shi vasa Allah ya hada tarenmu da qaddararmu
waje daya,ya kuma hukunta ni dake mu zama miji da
mata me yiwuwa dama can cikin littafin gaddararmu dani dake din mili da matar ne amma may be idan tun a karon
farko ya gaddara mana zama miji da matar, akwai
possibility din ba zamu san darajar juna da kimar juna
ba, shi yasa ya fara jarabtarmu ta yadda idan zaman
namu yazo zamu riqe juna rigo dan gaske ba tare da
wasa ba" vakai garshen maganar yana sauke
numfashi, idonsa akan kyakkyawar fuskarta

"Hajiya qarama" ya furta sunan da shima ya sanyata
dagowa

"Sai yanzu na fahimci dalilinki nagin aminta da kowa ciki harda NI kina da experience ta wannan fannin wanda ni bani dashi ban taba experiencing haka a rayuwata ba.

Mace ta biyu da tayimin cin amanar da har na koma ga
mahaliccina ba zan taba mantawa da ita ba" ya fadi
fuskarsa tana sake canza launi, alamun baqincikinsa ya sake ninkuwa fiye dana dazu

"Da idona,da kaina na kamata tana canzawa fadeela
magani,wanda daga qarshe bincike ya nuna magani ne
dake da illa ga lafiya da qwaqwalwa, nan asibitin na bayar aka gwadamin ingancinsa" ta girgiza saidai abun ba wani shahararren mamaki ya bata ba,ta riga ta gama duka wadan nan tunanin akan hajiya qaraman, ashe ta lissafa daidai, girgizarta daya yadda mutum mafi kusanci da kai zai ci amanarka har haka? inaga wani bare can wanda baku hada alagar komai dashi ba?.

""'dlan kin shirya cewa na sakeki bayan fadeela ta warke na roqeki kada ki furta min hakan, saboda wallahi wallahi ko sama da qasa zasu hade I can't divorce you" ya fada a raunane. Qasa tayi da idanunta tana jin nauyinsa kadan,kamar ya karanto abinda ta tsara a ranta kenan kafin isowarta qasar.

"'SAHR" ya kirayeta da suna da kuma lafazin dake ratsa kowacce jijiya ta jikinta. Fararen idanunta dake cike taf da hawaye ta daga ta kalli tsakiyar nasa idanun

"I Am done with people who suck on my life and energy and just leave me in the end like i was stupid to trust and give my all to them,SAHR...i just need one human to love me hard and never leave me alone....zaki iya yimin wannan alfarmar? coz naga

Please Login or Register in order to submit comment