Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 67 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tsananin kunya ta sanyata juyowa da sauri ta bawa madubin baya tana boye kanta a qirjinsa.

Wani galabaitaccen murmushi ya saki yana ci gaba da kallonta ta cikin madubin, yana jin yadda zuciyarsa ke sake laushi tana narkewa cikin soyayyarta. A nutse ya sanya lausasan tafukan hannunsa ya dago fuskarta yana kallon tsakiyar qwayar idanunta. Irin wanann kallon yana da bala'in tasiri cikin zukatan da jikkunansu su duka,musamman da suke kan irin wannan yanayin

"'Biyan bashi zanyi yau din,i hope you're ready?" Wani lallausan murmushi da tasan vana tarwatsa duk wata
nutsuwa tashi ta sakar masa,sanann tayi farrr da fararen idanunta da suka qara haske sosai,da zazzaqar muryarta tace dashi

"Babies sun shirya sada zumunci da abbynsu...
sassauta muryarta sosai

"Nima ummien babies din a shire nake,i crave for you since

"Shshshsh" ya furta yana murmushi hadi da dora yatsansa saman labbansa yana sakin murmushi

"I know,i can read it ta can gasan wadan nan fitinannun idanuwan" tabe baki tayi kamar me shirin sanya masa kuka

"You mean.....na zama fitinanniya fa?" Qaramar dariya ya saki

"Ba ke bace ai nasan laifin babies ne"

"Allah Allah nasan ni kake nufi" ta furta tana narke masa tare da dunqule hannunta ta daki qirjinsa. Hannu daya yasa ya dafe saitin zuciyarsa hadi da lumshe ido

"Ya salam ya Allah, maji zata illatani, bayan ban fara komai akan sonta ba,zo muje ki gani,na tabbatar hallway din nan yayi mana kadan" sai ya dauketa ya wuce nutsatsen bedroom din nan nasa dake da wani irin tattausan yanayi dake garawa zukata da feelings na masoya armashi.

Yadda a yau din ya susuce a kanta sai da abun ya bata mamaki ya kuma tsaye mata sosai a rai, don daga ita har shi din sun aminta da juna maqura,sai ya dinga jin kamar säahar din an sake sabunta masa ita ne,da ayar ta samu ta lallabashi ya shiga wanka itama ta wuce nata dakin don ta shiva,ranta da zuciyarta cike fal da mamakin sauyawarta,bata gajiya ko kadan da bugatuwa zuwa ga toufeeq din

"Allah yasa kici gaba da tabbata a haka koda bayan kin bani ajiyata ne" furucin da ya fada mata kenan a dazun yana gangame da ita.

Tsaf ta shirva cikin wani material me sulbi sosai
cream color da adon brown flowers da wani avalli a jiki.
Ta kusa mintuna ukun tana tsaye gaban madubi tana kallon kanta da kanta, bataga laifin toufeeq ba, dole ya sake haukacewa a kanta ya kuma sake manne mata, fuskarta ta aje wani kyau na musamman tayi mugu mugun yin fresh.Qaramin murmushi ta saki tana daukan wani siririn turarenta dake da wani sirrintaccen gamshi ta feshe jikinta da dashi sannan tasa wasu slippers masu taushi a gafarta da suka dace da kalar material din jikin nata.

Har ta juya ta dakata,ta dawo da bava tana duban cikinta. Har yanzu a shafe yake ga idanun mutane saidai idan ta sanya English wears ko kuma ta dora hannun nata saman mararta shine take iya jin tasawarsa. Ko a yanzun saman mararta ta dora hannun nata, ta shafi cikin a hankali, iva tudun nasa da takeii kadai vana saukar mata da wani irin farinciki me tarin yawa,qauna mara misaltuwa da ita kanta batasan adadinta ba akan cikin.

Yadda soyayyar mahaifinsu ke haukata a ranta, haka kullum rana takejin soyyayar 'yan tayin. Duk wannan abun kuma sai taga kamar toufeeq ya fita gaunarsu da nuna tsantsar kulawa. Kullum Allah shine da kullum sai yayi aqalla mintuna kusan hudu ko biyar kunnensa yana saman mararta wai yana gaisawa da biyunsa, hakanan kullum sai ya sanya tape ya auna tsaho da fadin cikin wai yaga sun qara girma?. Tun abun yana bata dariya harma ta riga data saba.

"I love you and your daddy so much"

"'Daddyn nasu shima yana masiliifar gaunar mamansu" taji an fada daga bayanta. Da hanzari ta juyo don bata tsammaci tsaiwarsa a gurin ba. Yana jingine da gofa hannuwansa goye a qirjinsa yana mata wani narkakken kallo. Sosai kunya ta kamata, batasan me yasa yakejin dadin yi mata labe yaji tace masa i love you ba, kunyar ta sanyata jan gefan mayafin boubou din tana sunne fuskarta a jiki.

Dukka hannuwansa va bude mata yana dariya

"Come-on babe bea, ba kalmar da yafi dadi a bakinki irin inji kince I LOVE YOU MY NUGGET the best name da nafiso bayan duk wani suna da za'a kirani da shi idan ka cire MUHAMMAD dina, taho taho" y fada yana sake ware mata hannuwansa.

Iya takun data iss gareshi kawai sun tafi da imaninsa,sanann ya sanya tana isa gareshi ya bata hotties kisses ssman fuskarta wuyanta da goshinta,ya tsugunna sukayi hirarsu da yaransa kamar yadda yake fada sannan ya riqe hannunta suka nufi main parlor na gidan kamar yadda aka sanar masa.

Kamar ma kowa su yake jira,don duk sun samu kowa cikin parlor din, maji na zaune gefe guda ita da nadeeya suna magana qasa qasa, fadeela na cinyar Dr jarma,hajiya qarama haseena na gefanta itama,hakama hajya mansura labiba na zaune daura da ita.

Kallo daya zaka yiwa kowa dake wajen kasan zukata na cike da abubuwa masu tarin vawa da zukatan kadai aka barwa sani akan su. Sallamarsu ta maida hankula a kansu,zukatan maji dr nadeeya da fadeela cike da farinciki da alfaharin ganinsu. Yayin da mansura labiba da hajiya qarama abubuwan da suke zakatansu sun banbanta da na juna.

Wani irin kallo na qurilla hajiya garama takebin säahar dashi, irin kallon da tunda suka je germany har suka dawo bata yi masa irinsa ba sai yau.

Qirjinta yayi wani mugun bugawa sanda sahar din ke kaiwa gasa tana musu barka da warhaka. Idanunta ta maida ta kulle tana fadin

""Na shiga uku" saboda tudun data hanga daga gasan mararta

"Yaushe tayi wani cikin har ya fito?, bayan a yanzun shine lokacin da zanyi kyakkyawan shirin cireta daga jarma family?, fita kuwa ta har abada? ba irin fitar da ameesha tayi ba tabar musu irin FADEELA?, ko dama qarya yakeyi mata toufeeq?, dama ba miscarriage tayi ba?" Wani mugun sarawa kanta yayi, har sai da takai hannunta da ya fara rawa ta dafe kanta tana sake kulle idanunta

"Relax.....relax mana fauziyya‚u are a strong woman" ta gayawa kanta da kanta, saita bude idanunta cike da qwarin gwiwa tana furzar da iska me zafi daga bakinta.

Kowa ya kama gurin zamansa,kamar yadda toufeed ke zaune kusa da säahar din, nadeeya da hajiya mansura ne suke serving, saidai shi din kuma ya kasa ya tsare. Bayajin zai iya barinta taci komai dake wajen, zuwa yanzu mutum uku ya yarda dasu akan säahar din. Maji cs ta farko sai nadeeya sai kuma baaba ramatu.

"Me zakici ne surukata?" Hajiya qarama dake fidda shu'umin murmushi ta tambayi sahar idanunta yana tsakanin fuska da cikin säahar. Motsawa kadan säahar tayi, bagin matar yana sake mamaye zuciyarta,taso ace wannan tambayar tayi mata ita ne lokacin da babu mutanen da takejin nauyi da ganin qimarsu a wajen, tabbas da ta bata cikakkiyar amsar da zata isar da
L sago, ba iya kanta kadai ba,har izuwa kunnuwan gadangarun 'yammatan dakeson shiga rayuwar toufeeq din nata.

"Karki damu da abinda zataci,ke dai ki lura da abinda zai iya zuwa gabanki" toufeeq ya bata amsar da wani irin qwarin gwiwa hadi da wani tsattsauran kallo cikin idanunsa. A hankali ta janye idanunta daga kansa gabanta yana faduwa,iya kallon da toufeea yakeyi mata a yau ya dasa gaqgarfan zargi a ranta

"Akwai abinda yake faruwa" ta bawa kanta amsa.
"Tabbas akwai ayar tambaya,tsahon shekaru sama da ashirin ban taba gain irin wannan kallon daga idanun Muhammad ba" ta sake jaddadawa kanta tana recalling abubuwan da suke faffaru tsahon satittikan da sukayita wucewa.


Zafafabiyar
"HUGUMA*

_TABARMAR KASHI_*


Book 02 Page 66

Maji kamar bata a wajen,saidai tana ankare da komai, dr jarma da hankalinsa duka yake akan majin da duk wani motsi nata,ya dan waiwaya sashenta

"Shifa matsomin da wannan ruwan na gabanki na wanke hannuna" cokalin hannun hajiya mansura ne ya subuce ya fadi, ta watsa kallonta ga dr jarma. Alamu da dama suna mata nuni da yiwuwar faruwar was al'amura

"Meye hadinka da tsohuwar matarka da zata baka ruwan wanke hannu?,duk da nayi kara da alkunyar ciyar da abincin da na girka da hannuna ba tare da nayi qorafi ba"

"'Matarsa dai a karo na biyu ko?" Muryar hajiya qarama ta ratsa hargagin mansura. A gigice mansura ta waiwayo tana kallon fauziyya. Murmushin nan nata dake dauke da tarin ma'anoni ta jefeta dashi

"Af, nayi hanzarin shaida miki maganar da ba'a bakina ya kamata a jita ba ko?, to tunda dai na riga na fada bari na garasa miki.

"Ya isa fauziyya" Dr jarma ya dakatar da hajiya qarama a tsawace

"Da dai ka barni na qarasa yaaya" ta sake fadi tana sakin garamar dariyar da zaka dauka cikin tarin zallar nishadi take

"Da gaske ne abinda fauziyya take gayamin?" Hajiya mansura da tashi d'aya kamanninta suka juye saboda zallar tashin hankali ta furta

"Samu guri ki zauna muyi magana,wanann zaman bana hayaniya bane" dr jarma ya fada cikin nutsuwa da tsare gida

"Ban bugatar zama mahmud,amsa nake nema eh ko a'ah" ta fadi tana rige qugunta wutar bala'i da masifa tana ruruwa saman fuskarta.

Toufeeq da kansa ke duqe,tunda hayaniyar ta fara tashi kansa yake a qasa yana son hadiye nasa bacin ran sal a sannan ya daga kai yana kallon mansura,cikin kakkausar murya yace

"Malama ki zauna akace!!" Ya fada a dan tsawace da bacin rai, ita da hajiya garama din suna cikin sahun farko da a yanzun baisan me ya tsana kamarsu ba

"Karka sake magana toufeeq, ba huruminka bane" mai tace dashi tana tsare gida. Motsawa yayi alamun zai mige yabar wajen, don bayajin zai iya jurewa kallon mansurar tana yiwa Dr haka

"Koma ka zauna, matsala ce da ta shafi kowa da kowa"

Dr jarma ya fadi, sannan ya mayar da dubansa ga mansura

"Shifa matatace ta lalle uwar 'ya'yana,matar da duk duniya tayimin abinda ko.mahaifiyata iya abinda zata iya yimin kenan,wata gaddara da bansan meye silar faruwarta ba ta datse igiyar aurena da ita,na jima ina addu'a da bansan iya adadinta ba,a yanzun haka shifa na matsayin matata ta sunnah, an maida aurenmu a Algeria qarqashin jagorancin kawunta"

"Tabbas!" Hajiya garama ta rufe da fadin haka duk da bata jin ko mansurar tana jin dacin da takeji a zuciyarta akan dawowar maji gargashin igiyar auren dr jarma din.

Saidai a yanzun mansurar ce first target dinta, tanason ta nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane.

"Mahmud saidai kuwa ka zaba,ko ni ko shifa wallahi tallahi!" Ta furta tana buga table din gabanta

"'Maji kina gani fa!" Toufeeq ya fada yana yunqurin migewa cikin huci

"Koma ka zauna Muhammad!" Ta sake daka masa tsawa.

Da garfi ya koma ya zaune kan kujerar tasa. Säahar da ta tsorata da irin fushin da take gani kan fuskarsa ta laluba hannunsa cikin tafin hannunta. A hankali ya juyo ya zuba mata jajayen idanunsa, sai ta lumshe idanunta hadi da budesu ta kuma matse hannunsun guri guda, abinda ya kawo wani gwaggwaban gudun mawa,ya sauke wata nannauyar ajiyar zuciya can qasa yadda babu me jinsa yace

“can't take it moon"

"For maji's sake" ta maida masa a taqaice.

"Bazan tsaya doguwar magana ko bata bakina wajen gaya miki na san wacace ke, nasan irin zaman da nayi dake dukka shekarun da muka kwashe ba,amma ina me shaida miki na bar miki dukka dukiyata da kika dinga diba da kadan da kadan kina tarawa….amma kuma ina me farincikin shaida miki,NA ZABI SHIFA, NA ZABI SHIFA,NA ZABI SHIFA, don haka na sakeki saki daya,na sakeki saki biyu....”

"Dr!" Maji ta gwala kiran sunansa da garfi saboda ta fahimci me yake shirin qarasawa aikatawa,saidai kiran sunan nasa da tayi sam bai sakashi ya dakata ba sai daya kai inda yakeso yakai din

"Na sakeki saki uku ni Mahmud jarma, ku shaida" tsaf labiba dake zaune saman daya daga cikin kujerun dining din ta sulale tayi zaman dirshan qasan marbles din dake gurin ta saki wani irin kukan tashin hankali. Cikin izza da tagama da madaukakin farinciki haseena dake daura da ita ta waiwaya tana kallonta,sai taja kujerarta gefe tana tabe baki

"Su ungulu sai a shirya komawa gidan tsamiya ko?, abar masu abu da abunsu, banzar da akazo ci bata samu yadda akeso ba,sai a tashi aje gida". Maganganun haseenan sun sake jefa labiba cikin magurar tashin hankali, don me yasa mommyn zata bari har haka ta faru? me yasa zata janyo mata wanna babbar asarar?, gwara ita ta samu ta abinda ta samu,ta kuma tara abinda ta tara, amma ita fa?,ba toufeeq din, kuma bata tara komai ba.

Kai tsaye mansura ta juyo tana aje kallonta ga hajiya qarama, ta san shaidanci da shu'umancinta,lallai ita fa qulla wanna abun, dawowar shifa da kuma sakin da dr jarma yayi mata a yanzun, saidai batasan cewa har kanta da kanta ta ballowa ruwan ba

"Tabbas kin cika shu' uma,sannan na sake yarda ke kike aura masa mata ki kuma saketa a duk sanda kikaso kamar yadda kikayi igirari...... Mahmud" ta fadi tana waiwaya ga dr jarma. Yadda ta kira sunan nasa yaja hankalinsa

"Duk cutar da nayi maka ba zata kama gafar wadda fauziyya tayi maka ba,duk wani ha'inci da na aikata maka baiyi rabin rabin wanda jininka tayi maka ba. Ha'inci cin amana da ha'intar gauna tana kasnacewa me saugi ne akan ace makusancinka ne yayi maka, yau zan fito maka da ainihin wacece fauziyya da fuskarta da baka sani ba" sai ta tsugunna qasan table din.

Wata tsohuwar leda ta dauko da tasha qu|li ta fara kunceta. Kallon ledar kadai hajiya garama tayi hanakalinta yayi mugun tashi. Ashe!,har yanzu bata samu damar badda sahun wannan abun ba? ita kuwa ta yaya zata bari mansura tayi mata irin wannan tonon sililin a yau wanda yake dai dai da mutuwarta murus. A zabure. ta mige tana nuna mansura

"Qaryarki tasha qarya mansura,dama ashe da gaskene shi matsiyaci idan ka daukoshi daga rana zuwa inuwa yana hucewa burinsa na gaba shine yaga ya tunkudaka wannan ranar?, to kin makaro,duk wani sharrinki don ki shiga soyayya da fahimtar juna dake tsakanina da yayana da yaransa baki isa ki shiga tsakanin wannan hadin da ubangiji ba" murmushi me ciwo mansura ta fidda tana dakatawa daga bude ledar

"Ki bari na kammala fito da abinda ke ciki idan na gama nuna tawa shaidar kina iya musawa ko hajiya me gaskiya ) da amana?" . Koda Karen mahaukata ne ya cijeta ta yaya zata bari mansura ta kunce wannana ajiyar,sai ta maida dubanta ga dr mahmud wanda idanunsa yake a kansu yana kallonsu..

Kuka ta saki cikin salon da take amfani da shi a duk sanda takeson cimma wani buri nata akan yayan nata

"Dama na sani akwai mutane da yawa a duniya da basason suga kulawa cikin idanunka a kaina, to matarka da na yiwa halacci ashe tana ciki, kada ka saurareta yaaya,wallahi tallahi kome zata gabatar maka garya ne"

"Fauziyya!" Maji dake zaune tana karantar dukkan wani motsi na fauzivvan ta kirayi sunanta. Fitar sautin muryar maji da yadda ta kira sunan nata da wani irin amon sauti ya sakata waiwayowa ta kalleta

"Ki nutsu kinji fauziyya,ita gaskiya fure take ai bata
'ya'ya, gaskiya bata bugatar rantsuwa ko ay mata ado don a gawatata a idanun mutane a fidda ainihin kamanninta,tafi buqatar a qyaleta da zahirin kalarta...
...banga abun tashin hankali ba akan leda kawai
da ko budeta ba'a kai ga yi ba,ki dakata ta fadi duk abinda takeson ta fada din, ita gaskiya zatayi halinta da kanta" maganganun shifa sunyi dai dai da abinda Dr jarma yakeson fada,wanda tsabar mutuwar jiki ta hanashi furtasu. Haka kawai yaji jikinsa yayi wani mugun sanyi kamar babu laka a tare dashi.

"'Fauziyya kenan" mansura ta fadi tana ware ledar cikin karsashi da qwarin gwiwa.

Qulli biyu ne cikin ledar ta ajjiye qaramin ciki, sannan ta bude babbban. Wasu irin tarkace ne a ciki, wasu gananun tukwane da wasu tarin allurai da layoyi masu yawan gasken, sai ginin mutum mutumi guda biyu kowanne jilkinsa zagaye da allurar da layoyi da wasu gananun abubuwa kamar danyan nama yana wari wari.

Da mugun hanzari har tanayin taga taga kamar zata fadi hajiya qarama ta mige tana duban mansura, ilahirin jikinta da bakinta suna rawa. A ina mansura ta tono wanann tsimammen sirrin da ya dauki shekaru kusan talatin a binne?.

"Mansura!!!" Ta kirata da garfi, kiran da ya maido idanun kowa kanta. A take kuma kaicon yadda take qoqarin tonawa kanta a siri ya kamata,sai ta koma da baya ta zauna kafin irin da ta soma ji yana yawo da ita ya kwasheta ya zubar

Ko kallon inda hajiya garama mansura batayi ba gaban maji da Dr jarma ta turasu tana dubansu

"Wannan duka an shiryasu ne saboda ku,a raba tsakanin zucivarka da ta shifa,a raba tsakanin shifa da nadeeva Muhammad dake da gauna da qulafucin uwa a cire masa shifa daga zuciyarsa, sannan a mantar da shi uwarsa,saboda shi din namiji ne,yana da
power taurarinsa tun a wancan shekarun sun haska,sun nuna kuma shi din rayuwarsa na cike da arzigi me yalwa da ya ninka na mahaifinsa, fauziyya kuma ta shirya ita daya zata mori wannan arziqin, daga nasa har na ubansa sai wanda taga dama"

"Qarva kike mansura,garva ne wallahi " haiiya garama ta fada cikin hargagi tana nuna mansura da yatsa,duk da ciwon da kanta ya fara kamar zai rabe gida biyu.
Murmushi mansura ta sake mata tana jin farincikin yadda fauziyya ta soma birkicewa tana fita daga saitinta,alamu kuma suna nuna dukka dabarunta sun fara qwace mata.

"Saurin me kike fauziyya? idan duka kin musa wadan nan saboda daga ke sai malaminki kuka shirya shi,bakisan ina biye da kowanne taku naki ba,wannan ai baki isa ki garyatashi ba" ta fadi tana takawa dauke da qaramar ledar tana garasa budeta, sannan kanta tsaye ta isa ga tafkekiyar TV plasma din dake dining room din. A nutse ta jona komai, ta cire garamin memory card din ta soka shi a gefan tv din. Cikin qasa da second goma yayi loading ya hau,video clip guda daya ne akai, hajiya mansura ta daukj remote din tayi clicking akan video din.


_TURK'ASHI_*


Zafafabiyar

"HUGUMA*


•_TABARMAR KASHI*


Book 02 Page 67


• TURK'ASHI_*

Tarrrr baby fadeela da a lokacin da kwanan watan dake a rubuce b'aro b'aro ya nuna tana da shekaru uku ne a duniya ta bayyana,sanye da wata pink gown wadda tsahonta yake iya qaurinta, an raba dogon sassalkan gashinta gida biyu an matseshi da pink din bands gananu masu kyau‚ba takalmi gafarta sai pink sock's me ‘yar teddy qananu a samanta.

Tana tsave saman stair na can qarshe, bakin qofar da idan aka budeta zata sadaka da ainihin babban parlor zuwa bedroom din toufeeq. Bubbuga qofar takeyi a hankali tana faman kiran sunan ameesha

"Mommy, Imommy yunwa nakeji, mummy kingi fitowa tun dazu,kizo ki bani abincin bacci zanyi mommy, mommy don Allah" daga yadda yarinyar ke magana tana goge hawayenta zai nuna maka ta jima tana bugun gofar, kuma tabbas har ta fara gajiya da bugawar. Zamewa tayi ta tsugunna bakin gofar dakin dai dai lokacin da video din ya dauko hoton hajiya qarama.

Cikin sand'a da alamu na rashin gaskiya ta zame takalman gafarta ta ajjiye gasan stairs din, ta fara takawa cikin sanda da takatsantsan, ta yadda ko cikakken motsinta baka isa kaji ba. Bata tsaya ba har ta cimma fadeela wadda ta bawa stairs din baya, babu kuma ta yadda za'a yi taga tahowar wani don kamar ma ta fara gyangadi a wajen.

Kamar qiftawar ido da budewarsa ta miga
hannunta ta finciko gashin kan fadeela ta wancakalar da ita , abinda yayi sanadiyyar wata muguwar gangarowa da yarinyar ta farayi ba matakala bayan matakala ba,'ah bibbiyu bibbiyu ta dinga tsallakewa jikinta da kanta yana buguwa ta kowanne sashe, kama daga tiles din dake shimfide a wajen zuwa garfen jikin stairs din

"Ab......mom....abbyyyy...." Sunan data furta kenan na qarshe ta qarsa gangarowa stair din garshe ji kake tassss! kanta ya bugu da marbles din.

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" sãahar ta furta da garfin amo cikin gigicewa tana kama fadeela gami da kauda fuskarta daga gain jinin dake malala saman kanta. Tsam fadeelan ta riqeta da gaske,ga mamakin säahar kuka yarinyar ta saki

"Randa na fadin nan ko anty? tun daga ranar abby yace bani da lafiya,ashe fadowa nayi daga stairs" yarinyar dake lullube cikin jikin säahar ta fadi.

Tuni Dr jarma ya mige tsaye yanajin jikinsa kamar an kwara masa tafasashen ruwan zafi, maji kuwa tafukan hannayenta ta sanya ta lullube fuskarta tana kiran sunayen Allah duk nau'in wanda yazo bakinta cikin gigita da bada amannar tabbas fauziyya ba mutum bace.

Nadeeva gam ta rige maji tana wani irin kuka,tsoron haiiva garama yana mugun shigarta, tana jin kamar zata dauki wuga a yanzun nan ta sossoke cikin kowa a cikinsu.

"Bagar annamimiya ni zaki shiryawa wannan sharrin?.

"Shut up!, Ba sharri bane" toufeeq ya furta yana qogarin zaqulo nasa memory din ya jona musu da abinda suka gama gani yanzu. Doka wayar yayi da gasa saboda rawar da hannunsa yakeyi ya kuma samu ya cire memory din da gyar. Fusge wancan yayi ya watsar don ko ganin Ralarsa bayason yi ya saka na hannunsa.

A hankali video din ya fara da nuna blank kafin fitowarta daga bedroom dinta cikin tsakiyar daren tai zaman irga tablet din. Wani dadi ya ratsa hajiya qarama,qasan ranta ta cika da fatan ya kasance komai yayi formatting ne.

Tsulum kamar wadda aka jeho sai gata ta fito,wani annamimin gumi ya soma tsatstsafo mata ta kowacce kafa ta jikinta. Komai ya fara bayyana tiryan tiryan, tun daga nan har zuwa isarta dakin fadeela,musanyan magungunan da kalaman bakinta da sai da taji kamar ta hadiye kanta da kanta a lokacin

_bagar matsiyaciya,kin kusa fita daga rayuwata,kin kusa barin gidan nan, gidan nan gidan meenal ne, toufeeq da abinda ya mallaka dama wanda ubansa ya mallaka duka na meenal ne da abinda zata haifa_

*Qarya ta gare bori ya kar boka*

"Innalillahi wa inna laihi raji' un, allahumma la sahla illa ma ja'altuhu sahla,wa'anta taj' alal hazna iza shi'ita sahla" shine abinda Dr kawai yake fadi jikinsa na wani kakkarwa da mazari,ko ina na jikinsa yana rawa kai kace ciwon fargadiya yana shirin kamashi.

Duka hankula sai sukayo kansa,hankalin maji
'yayi mummunan tashi, ta dafashi da hanzari, toufeea ya garaso da gaggawa yana yunqurin zaunar da shi.

"Yaaya....don Allah yaaya!" Hajiya qarama dake gunjin kuka ta taso tana son isowa inda yake

"Kina garasowa nan zan manta dake wacace karki kuskura ki garaso nan, kiyi gaggawar fita a wajen nan,idan ba haka ba na sakar miki karnuka su yagalgalamin namanki da ranki!munafuka azzaluma annamimiya" Toufeeq din ya furta wasu hawaye masu tsananin zafi da radadi suna zartowa a idanunsa.
Idanuwan da sukayi wani mugun jaaa har baya iya ganin abinda ke gabansa sosai

"Yaaya..... toufeeq......

"Kibar gurin nan fauziyya,bana qaunar na sake ganin fuskarki har abada" Dr jarma da yake fusgar numfashinsa da qyar ya fada yana dafe qirjinsa,ji yake kamar zuciyarsa tana shirin bugawa.

Tunda uwarta ta haifeta bata taba ganin tashin hankali tozarta da abun kunya irin na yau ba,sanda take tafiya zuwa dakinta jiri ne yake angizata daga gaba zuwa baya. Meenal tana biye da ita itama cikin kukan,kukan nata da yake da nasaba da hango rasa toufeeq rashi na har abada. Yadda gaba daya parlor din ya rude ya birkice ya sanya dole maji ta gayyato juriya da dakiya irin ta uwa ta azawa zuciyarta da ruhinta, don dukkansu a yanzu suna bugatar wanda zai jagoranci tunaninsu ya kwantar musu da hankali

"Dauko mota Muhammad mu kaishi asibiti, nadeeya kira baaba rabi tazo takai sãahar daki ta huta, ki cire damuwa daga ranki, jarrabawa ce mun ganta kuma mun cinyeta a yanzun in sha Allah alhamdulillah, Allah dai yayi nufin sai mun gani ne kawai ki cire damuwa saboda abinda yake jikinki" dai dai toufeea ya dawo a gaggauce, ya kama Dr jarma wanda yaketa ambaton sunan Allah sanoda vadda numfashinsa da girjinsa suka rige va fita dashi zuwa harabar gidan. Sai da maji taga baaba ramatu ta kama hannun sãahar sun wuce daki da ita,tace fadeela ma ta zauna gudun shiga tunani sannan suka wuce asibitin.

Falon ya zamana babu kowa,hajiya qarama aneesa hajiya mansura da labiba sune suka rage.

Wata shu'umar dariya mansura ta saki, ta hada hannuwanta dukka biyun ta tafasu da kyau, tayi taku biyu ta tsaya gaban hajiya garama

"Tabbas abinda malam ya fada haka yake, faduwa guda biyun tawace da taki, nasara kuwa ta maji ce,a yau na tsinciki kaina banji takaici ko baqincikin yin nasarar wani ba..... Fauziyya kin dauka kai kadai ce kika iya shu'umanci? kin dauka ke daya aka yankewa tuggu cibiya a gabanki? kina tunanin zan zauna ne haka. sasakai kara zube ba tare da na

Please Login or Register in order to submit comment