Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 55 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Allah, Allah bazan yarda ba, Allah kuwa,bazan yarda ba, tunda ka karya yarjejeniya" murmushi ya sakar yasa tsinin hancinsa saman nata ya gogasu guri guda idanunsa a lumshe

"Keep quiet babe,i also break my rules for you" ya fada softly,sai kawai ji tayi ya tsundumata cikin bathtub.

Ko daya bai saurareta ba,sai data dinga masa magiya tana hawaye sannan yabar mata toilet din. Sanda ta fito kamar surukarsa haka ta koma, kaya ta diba ta koma toilet ta saka sannan ta dawo,har yanzu hawaye takeyi.

Sofa bed ta koma ta cure guri daya,yana zaune daga gefan gadon yana addu'o'in bacci ta gasan idanunsa yake qare mata kallo. Tun yana jin motsinta a hankali har yaji shiru,hakan ne ya bashi alamar cewa bacci ya dauketa. A nutse ya miqe ya isa gareta, tsaye yayi a kanta,hannuwansa zube a qirjinsa yana qare mata kallo,wani sassanyan murmushi ne yake fita daga kan fuskarsa,yana jin zuciyarsa kamqr wanda aka cirota daga qirjinsa aka wanketa. Abu guda daya tal a yanzun zaice yana damunsa,shima kuma tunda ya tsananta addu'a yaketa samun nutsuwa karsashi da kuma kyakkyawan tunani akan hanyoyin da zai magance komai.

A hankali ya durqusa saman kanta,ya sanya hannuwansa duka biyun ya tattarota ya dagata cak zuwa girjinsa. Sosai ta firgita, saidai suna hada ido tayi laqwas, idanunta suna hada wasu sabbin hawayen, saita maidasu ta rufe tana jin,tana jin tsananin kunyar hada idanu dashi a yau din. Hawayen suka biyo gasan rufaffun idanunta,tana jin ya gama da ita,har ya sata ta sauka a layi,da wanne idon zata iya ci gaba da kallon shi?.

Lumshe nasa idon yayi ya bude yana duban fuskarta dake qirjinsa,har cikin zuciyarsa yakejin ba dadi akan fitar hawayenta

"Kina bugatar second round ne?" Ya fada qasa qasa.
Rasa me zatace tayi,wato yama gama rainata gaba daya? sai kawai ta fashe da kukan sosal tana cewa

"Allah sai na rama,Allah"


"That's wonderful.
. I like it, kice nayi kwanciyata za'a
shayar dani da...

.." Bai garasa fadi ba kalaman suka
katse saboda cizon data sakar masa a qirjinsa. Tana jin shi kadai ne abinda zata iyayi ta rama abinda yayi matan.

"Wash Allah...... maji zata jimin ciwo" ya furta yana sakinmurmushi sosai,karon farko da yayi murmushi ne cakude da dariya,yana jin wani shauqi yana dibansa. Sauri yayi ya kaita saman gadon yabi bayanta ya sanyata ta garfin tsiya a jikinsa ya kuma nannadesu da duvet, ya hanata dukkan wani motso,tun tana kici kici har ta sallama masa.


*_Washegari*


Tun da safen taji cikinta yayi wayam kamar bata taba sanya masa abinci ba,sai data leqo taji bataji motsinsa ba,don tun sallar asuba da ya fita ta maida key ta rufe,ta bude ta lallaba ta shige kitchen din.

A gurguje ta dafa tea,ta soya qwai tayi toasting bread guda uku. Daga gaban kitchen cabinet din ta tsaya tana ci a gurguje,so take ta gama ta koma daki kafin ya risketa.

Tana tsaka da ci tattausan gamshinsa yayi mata sallama,bata waiwaya ba don ta saddaqar shine, ta cusa bread din a bakinta tayi tsaye kawai tana jin takunsa. A nutse ya kamo qugunta ya manna da jikinsa,ya dora kansa a kafadarta ya sanya hannunsa ya jiyo da fuskarta ya zamana suna facing juna.
Miskilin murmushin nan nasa dake da wuyar gani ya
saki

"Halan marowaciya ce ke ko?" Ya furta yana lullumshe mata ido, kamar wanda ke jin bacci. Bai jira tace komai ba ya kai bakinsa a nutse saman nata bakin. Bread din ya gutsira a tausashe, numfashinsa ya gauraye da nata,ya janye idanun a nutse yana tauna bread din, sai ya kama hannunta dake riqe da cup na tea din yakai bakinsa ya kurba a hankali. Kai ya jinjina,komai ta dafa yana da wani irin taste na daban da baya jinsa a ko ina. Ko daya hadiye dake gutsire sauran na bakinta yayi,sannu sannu sai gashi ya cinye mata bread din tas da tea din,ya saketa a nutse yana murmushi

"Thanks for this beautiful breakfast,i love you" yayi maganar yana tafiya da baya da baya idanunsa a kanta kamar bazai janye ba. Har yakai qofa sannan ya juya da hanzari ya qarasa ficewa yana jin shauqi na ratsashi.

A gurguje ta juya itama tana wucewa daki, ko ina cikin kanta na maimaita amsa kuwwar muryarsa cikin taushin nan nata da kalmarsa ta qarshe ta

"| LOVE YOU"

"He loves me?" Ta tambayi kanta tana tsaiwa gaban madubi tana duban fuskarta. Ta yaya zai fada sonta indai har da gaske ne? bayan dab take da kammala aikinta ta koma inda tafi wayo?, qwaqwalwarta ta daure tsam, daidai lokacin da kira ya shigo wayarta. Da sauri ta dauka tana komawa gefen gado, maji ce,kamar tasan kuwa a yau take shawarar kiranta,ta tabbatar itace hanya mafi sauqi da zata bi tayi tafiyarta a sirrance cikin kwanciyar hankali. Cikin kunya da nauyi ta daga kiran.

Kamilar muryar maji din ta ziyarci kunnenta da kyakkyawar sallama

"Ibnaty.....kaif einty"

"Barka da warhaka maji" sãahar din ta fada tana murmushi cikin kunya matuqa,kunyar da sai a yanzu takejinta ta gasken,irin kunyar dake wanzuwa tsakanin suruka da surukarta

"Barka kadai d'iyata,munyi waya da nadeeya tace kina sashenki,ina fatan komai lafiya,kuma komai yana tafiya cikin kiyayewar ubangiji ba tare da matsala ba?"

"Komai lafiya alhamdulillah"

"Nima ina gab da dawowa,wata matsala ce takeson faruwa fil usbu'il maadi(cikin satin da ya wuce) wala kin in sha Allah sa'arji'u ilaikum fi hazash shahr(saidai in sha

Allah zan dawo gareku cikin wannan watan)"

"Allah ya amince maji munyi kewarki, nahnu mushtaquna ilaiki(munyi kewarki)" murmushi ta saki cike da jin dadi

"Wa'ana aidan yabnaty (nima haka d'iyata)"

"Maji" ta kirata a sanyaye

"Na'am diyata,me yake faruwa?" Ta fada kai tsaye saboda yanayin kiran da taji tayi mata

"Akwai maganar da nakeso mui,nayi wani danyan hukunci ba tare da neman shawararki ba"

"Karkiji komai diyata,nayi imanin ba zaki taba cutar da kowa nawa ba,saboda addu'ata a kanki take,kuma Allah ya zabar mana ke,na tabbatar in sha Allah ke da duk abinda zakizo mana dashi alkhairi ne,gayamin kanki tsaye, menene?"
*HUGUMA*

* TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 40

"Na shirya tafiya da fadeela don yi mata aiki ta rabu da lalurar da take fama da ita a sirrance ba tare da ko mahaifinta va sani ba bare mutanen da muke rayuwa
tare dasu ba"

"Allahu akhbar " maji ta maimaita har sau uku
"Kamar tare dake muke wanann tunanin? wannan shine abinda na shirya aiwatarwa na farko bayan na dawo Nigeria,na baki goyon baya alf bil alf(dari bisa dari)"

"Amma maji, banason kowa ya sani saboda ina tsoron kada a sanya abun yaqi yiwuwa" kamilin murmushi maji ta saki

"Fauziyya hajiya qarama,ko ba ita kike tsoron kada ta sanya moha ya hana ba?,ina da labarin yadda tayi ruwa tayi tsaki ta hana duk wata maganar da za'a tayar akan a yiwa fadeela aiki,na bar zancen ne akan cewa ni daya zan iya aiwatar da aikin, koda ita din bataso,saboda nasan duk inda takai ga girman kaidinta,bata isa ta sanya moha ya hanani ba.….....har yanzu bakisan me fauziyya ta yiwa rayuwata ba,zauna da kyau diyata yau na gaya miki labarin da masu shekaru irin naki dake rayuwa tare dani basu sani ba" a sanyaye sãahar ta gyara zamanta saman gadon sosai, tun kafin taji komai daga bakin maji jikinta ya sanyaya,ba abinda take haskowa sai fuskar hajiya qarama a sannan.


* TUNA BAYA 1988 *

Mummunar faduwa gabanta yayi,wani irin hargitsatsen kallo daya watsa mata shi ya sanyata cikin rudani, batasan me tayi masa banda kulle qofa da tafiya da key din,kallon daya watsa mata yafi qarfin wannan laifin, kallo ne na zallar qasqanci da kuma tsana,tasan dai ranar yau lafiya galau suka rabu,ya fita cike da murna zai karbo upper dinsa aiki ya samu,suna ta murna dukkansu tare da saka ran fita daga tsanani zuwa sauqi, sai dukka gwiwarta tayi sanyi da irin nau'in kallon da yake jefa mata.

Kafin ta qaraso ainihin tsakar gidan sai wulgawar fauziyya ta gani, wadda kanta ke daure da bandeji da yayi tsatstsafar jini gaba daya daga samansa,ta nufeshi a gigice ta cukuikuyeshi tana neman mafaka a bayansa,bakinta na wani irin rawa na zallar toro da firgici take cewa

"Na shiga uku akh, gata nan ta dawo,don Allah ka boyeni,kada ka bari ta qaraso,wallahi zata qarasa illatani kamar yadda taci alwashi" tayi maganar tana wani irin haki da tawar jiki, kamar wadda tayi gudun kwana da wuni.

Baki kawai ta saki galala tana kallon fauziyya,qwaqwalwarta gaba daya ta rikice,me take nufi ne? saita maida dubanta ga bandejin kanta tana mamakin me ya sameta daga fitarta

"Bata isa tayi miki komai ba,a yau qarshen al 'amarinta yazo, muguntarta a kanki kuma ta qare!" Muryarsa mai zurfi dake fita da amon fushi ta fusgi hankalinta, saita maida dubanta kansu gaba daya, kwanyarta na sake rikicewa da salon maganganunsu da ba ganewa takeyi ba.

Ci gaba tayi da kallonsa, saidai ya zaro biron dake.
gaban aljihunsa ya kuma dauko takarda a daya aljihun nasa,ya bude kan biron cikin fusata. Cikin mamaki me yawa taga fauziyya ta kama biron ta riqe gam

"Me zakayi yaaya, ka rufamin asiri don Allah, kada kace zaka saketa saboda ni" ta fada hawaye na wanke mata fuska. "Ki saki fauziyya,duk mutumin da bayason jininka kaima baya qaunarka,ban ga amfanin zama da ita ba, baya ga tarin dimbin gori da maganganun data fada a kanmu" kuka sosai fauziyya keyi,ta kuma riqe abun rubutun taqi sakar masa tana bashi haquri, abinda yayi masifar daure tunanin SHIFA, me yasa fauziyyan dake burin afkuwar haka ita ke bada haqurin kada a saketa?.

"Kinci darajarta,ki dubi abun kunya wanda kike quntatawa shine yayi silar kubutar dake daga afkuwar wani mummunan abu a kanki" mamaki ya sake kasheta,kanta ya daure tamau, tama kasa cewa komai baki sake take kallonsa har ya miqe ya nufi hanyar soron gidan,har yanzu zallar bacin ran dake saman fuskarsa bata gushe ba. Har yakai bakin qofar sai kuma ya dawo,ya tsaya gaban fauziyya dake zube tana kuka

"Tashi ki wuce ciki". Bai barta ba har sai daya rakata cikin dakinta,ya dan jima ma a ciki kafin ya fito,zuwa sannan shifa ta ja jikinta da qyar ta wuce zuwa nata dakin clkin mawuyacin hali,tare da hasashen me yake ta faruwa da ita ne a rayuwarta haka? tun ranar da fauziyya ta sanya qafarta a gidan da nufin zama dasu,na wata shidda kawai ta samu kwanciyar hanakali bayan zuwan nata,daga bayan wannan watanni shidan bata sake samun sauqi ko salama ba.

Duk wani farinciki nata ta warwareshi tasss ba tare da tasan meye dalilin da yasa taketa aikata hakan ba. A iya saninta,mahaifiyarsu mahmud macace mai kirkin gaske da kowa ke yabonta bayan rasuwarta, zamanta da fauziyya na watanni shidan nan,zama ne na kyautata mata da kula da ita,saboda
tana mata kallon mahmud, mahmud kuwa ba zata manta da soyayyarsa a gareta ba, duk da cewa ba kowa cikin danginta ke son aurensu da shi ba, kasancewarsa shi din dan Nigeria ne, ita kuma 'yar Algeria ce, duk da shi dimma
fari ne tas kalar yarensu da idan ba fada kayi ba za'a
dauka Algerian ne shi dinma, kasancewar ya fita daga
tsatson SHUWA-ARAB wanda asalinsu dama larabawan ne.

Wani irin zama tayi cikin dakin cikin qunci da
kukan zuci,da Muhammad da nadeeya kowa kuka
yake, amma kusan hanakalinta yayi nisa a tunani,taji
alamun kuke sukeyi,amma saboda tsanar tunani da
damuwa bata farga da kukan da sukeyi ba,har sai da
taga fadowar fauziyya dakin kamar wadda aka jeho.
Kafin tayi kowanne irin tunani ta dauke nadeeya dake
tsaye daga bayanta tana kiran sunanta ta hau jijjigata.
Sallamar mahmud da shigowarsa cikin dakin shi ya ankarar da maji dalilin wannan shigowar ta fauziyya ta ba zata,iya saninta ko daya bata iya tayata wahalar yaran,zafi ko sanyi koda azumi akeyi ita zata yi korai dinta fauziyyan na daga kwance, saidai ta fito ta debi abincinta ta koma daki, idan ta gama sabgoginta kuma ta wanke jikinta tayi ficewarta unguwa,ba zata dawo ba sal ta daidaicin lokacin dawowar dan uwanta.
Hannu yasa ya karbi nadeeyan, fauziyyan da ta sake tara wani qwallan ta dubi yaran

"Ku tayani bawa maji dinku haquri, kada tayi fushi da ni,ni din marainiya ce,bani da kowa sai yayana sai ita da nake saka ran ta zamemin makwafin uwa" ta qarasa fada tana share qwallar munafurci. Gaba daya jinin jikin maji so yayi ya tsaya da harbawa,tabi fauziyya dake ci gaba da sharar qwalla da kallo

"Ni kadai na isa na tsaya miki, jeki abinki" mahmud ya fada yana miqa mata leda daya da ya shigo da ita ta takeaway. Har qasa ta durqusa ta saka hannu biyu ta karba tayi masa godiya tana fita.

Wani kallo ya juyo ya watsawa maji, ba komai idanunsa face zallar bacin rai da har yanzu bai gushe ba "Yau na gani da ido na,ansha gayamin yadda yake wulaqantar da yaran nan,hatta a wajen aiki ba wata
Kulawar kirki suke samu ba,saboda baqin hali tun daga waje nake jiyo kukansu amma kin gaza rarrashinsu,to daga rana irin ta yau na soke batun aikinki, ki zauna a gida ki kulamin da yarana da 'yar uwata" yayi maganar yana kamo toufeeq,ya zaunar dashi gefansa nadeeya na saman cinyarsa,ya bude musu daya takeaway din ya fara
basu.

Har yanzu jin komai take kamar a mafarki,sai a lokacin ta samu qwarin gwiwar waiwayawa gareshi

"Allah S W T cewa yayi,yaku wadanda kukayi imani,idan fasiqi yazo muku da labari kuyi bincike a kansa kada ku afkawa wasu mutane cikin rashin sani da jahilci saiku wayi gari kuna masu nadama akan abinda kuka aikata.

Wannan kenan kayi tunani akai,sannan meye hadin matsalar nan da maganar fitata aiki mahmud?" A harzuqe yake kallonta

"Waye jahilin kenan? ‚ni ko 'yaruwata?,ki gayamin?. Ta tabbata kin rainanin d gaske, rainin da ake cewa kinyimin ban sake tabbatarwa ba sai a yanzun,illar mace ta dinga taimaka kenan,koda bakai ka buqata ba wataran sai irin wannan ta gifta a tsakaninku,Allah yasa ba ahaka kika aureni ba da na shiga uku wallahi wallahi, aiki kin daina yinsa,sannan duk wani abu da kikasan kin tallafamin da shi ki zauna ki rubuta daga yau zuwa gobe,tsinke kada ki dagamin qafa,zan maida miki abinki" qas tayi da kanta,hawayen da tun dazu basu zuba ba yanzu suke zuba,maganar da ya gaya mata yanzu tafi zancan barinta aiki ciwo,duk wani fadi tashin rufa musu asiri da takeyi bayan karayar arziqinsa,dai dai da rana daya bata taba jin ta qosa ko ya dameta ba, amma yau da wadan nan kalaman zai saka mata?,komai da tayi musu tayi masa ne saboda tana ganin ya cancanci fiye da haka,namiji ne shi me bala'in kulawa da gida da matarsa,sanda yake dashi babu abinda baiyi mata ba,a lokacin duniya tana kwance, fauziyya bata shigo rayuwarsu ba,sai lokacin ta tuna da kalaman haiia mahaifiyarsu,a duk sanda sukaje borno ba zata dawo ba ba tare da hajjan tayi gorafin fauziyya ba

"Fauziyya, fauziyya,Allah ya shiryamin dai kawai" ba yawan zama take dasu ba,shi yasa a lokacin ba zatace
• ga wani hali nata ba,hakanan ba zatace ga abinda ta taba yi mata maras dadi ba,ashe ita din kara da kiyashi ce daukan mara sani.

Ranar har ta kwanta bata sanyawa cikinta komai ba sai bacin rai da taketa kurba da dogon tunanin ta inda zata kamo bakin zaren. Bayan sallar isha'i tana jinsa shida yara a dakin fauziyyan sunata hirarsu abinsu,kamar ma bata a cikin gidan. Sanda yaran sukayi bacci ya kawo mata su ya shimfide mata su ya juya abinsa ya fice. Kasa haquri tayi,bayan awa daya ta shirya ta miqe ta bishi dakinsa. Tunda ya amsa sallamarta bai sake daga kai ya dubeta ba,gabansa ta tsugunna cikin sanyi da mutuwar jiki

"Ya kamata mu warware sabanin da yake tsakaninmu ta hanyar tattaunawa,bai kamata mu fara yin abinda bamu saba dashi ba" har ta gama maganarta baice ci kanki ba,hasalima shirin bacci ya tashi ya fara yi daya kammala ya haye gadonsa ya kwanta yana fadin

"Idan kin gama ki rufemin qofata" yaja bargo ya lullube har saman kansa. A ranar shifa tayi kuka tayi kuka har taji babu dadi, meye da meye wai fauziyya ta gaya masa haka me zafi? wannan iri fushin koda mahaifiyarsa ta tsinewa albarka ai iyaka kenan.

Washegari saboda bata samu bacci da wuri ba ta makara bata tashi da wuri ba,tana tsaka da baccinta ta dinga jiyo qamshi cikin hancinta,sai ta farka tana salati ganin ta makara,ta shiga toilet tayi brush ta fito tana qoqarin kama ayyukanta na gida,don ko ciwo takeyi babu mataimaki,haka zata rarrafa tayi ayyukan nata, Muhammad na taimaka mata da dauko wannan ajjiye,duk da shekarunsa ba wani kaiwa sukayi ba.

Mamaki ne ya kusa kasheta,don fauziyya ta gyare gidan fes an kintsashi,hatta da yaran tayi musu wanka,hakanan ta kammala breakfast tana ta shiryawa a cooler da take zubawa mahmud abinci, yara nata tsalle hannunsu daya chips daya soyayyan qwai,shi kansa qwai din da chips din batasan ina aka samoshi ba,saboda tasan duk kayan abincin data siya musu wancan watan sun qare. Jiki a sanyaye ta qarasa shiga kitchen din,suka hada ido da fauziyyan tana rufe cooler din,sai ta sakar mata murmushi

"Barka da tashi matar yaaya,nasan tun jiya akwai tambayoyi fal kanki ko?,to yanzun kina da minti talatin zuwa arba'in da zakiyi kowacce tambaya taki zan baki amsarta,saboda yaayan ya fita yomin cefane, zan iya saurarenki kafin ya dawo" kaman majin zata ce wani abun sai ta dauke kanta daga dubanta, dariya ta saki tana cewa

"Bari to na taimakeki na rage miki wasu amsoshin tambayoyin…..nasan kin shiga kogin tunanin meye dalili na na hana yaaya ya sakeki ko? ‚nayi hakanne saboda banason tafiyarki yanzu,nafison saikin gasu yadda ya kamata, idanunki kuma sun gane miki girman matsayina a wajensa da kuma qarfin izzata,ta yadda zaki rayu kina bada labari a duk inda kika zauna"
*HUGUMA*


*_TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 41


Sosai zuciyar maji tayi wani irin nauyi,girman kaidai da dabi'ar fauziyya maras kyau tana ratsata,saidai kuma
ta tuna da wata magana guda daya na cewa
MURMUSHINKA GUDA DAYA TAK NA IYA SANYA
FADUWAR GABA GA MAQIYINKA don haka fa waiwayo tana dubanta da murmushi saman fuskarta

"Kin riga da kin makara,saboda bana tunanin lokacin da za'a rubuta littafin qaddarata kina gurin,na tabbatar da cewa kedin baki da matsayi a wajen Allah da kike da qarfin ikon canza qaddarata,na rigaki tsayawa a gaban Allah,na kuma rigaki ambatonsa" dariya fauziyya ta saki

"To sannu sufiya". Kasa ci gaba da tsaiwa maji tayi a kitchen din,ta juya ta fice a hankali, zuciyarta cike da mamakin wanne abu ta aikatawa fauziyya haka data cancanci irin wannan sakamakon?.

Ranar hatta da yaran basu wuni gurinta ba,sun wuni gurin fauziyya ne tana nan nan da su, sakamakon a ranar mahmud yana gida,saidai yadan fita ya dawo. Fauziyya ita tayi girkin rana da dare, kamar yadda tayi girkin dare,a lokacin idan ka shigo gidan zakayi tsammanin itace matar gidan idan ba kasan cewa matar gidan shifa bace.

Tana daga daki tana sauraren dabdalarsu, yadda suka wuni suka kai kawo haka ta wuni kwance a daki. Sai bayan magariba lokacin da mahmud din yake zaune a parlor suna kallo da yara fauziyya ta shirya komai saman tray ta shigo dashi falon

"Yaaya,don Allah kayi magana da maji,tayi haquri ta tashi taci abinci, yau duka bataci komai ba" dubanta yayi yana jin tausayin fauziyyan yana kama zuciyarsa tare da kallon kyawun halayenta

"Ke kamar baki da zuciya?,kamar baki damu da abinda ta aikata miki ba?,har yanxu fa bandage ne a kanki fa na abinda ta aikata miki" cike da kissa da kisisina tayi gas da kanta

"Bazan manta kyatatawarta a kaina ba,shi yasa bazan iya fushi da ita ba" Numfashi yaja sannan yace

"Ni dai bazanje ba,idan kuma ke zaki iya bismillah".
Hawayen da suka wanke mata fuska ta share,duk abinda suke tattaunawa a tsakaninsu tana jinsu. Zuciyarta ta gama amanna da cewa abinda fauziyya ta shirya aiwatarwa a kanta me girma ne, abu guda ne zai zame mata garkuwa tsakaninta da ita shine addu'a. Bata ko marmarin gain fuskarta,don haka salin alin kafin ma ta kai ga shigo mata daki ta miqe ta murza key ta koma ta kwanta. Tana jinta sanda take knocking da magyar ta bude, zallar kukan dake cin zuciyarta ya hanata koda qwaqwaran motsi. Fauziyyan da koda wasa bata tana kama mata aiki ba koda ciwo zai kayar da ita, fauziyyan da sautin INA KWANA da sunan sun kwana gida daya bai taba hadata da ita ba,fauziyya da bawai ta girka ba,wanda ita ta girka dinma qoqari take ta juye ta cinye, amma wai yau saboda zallar kissa ita ke biyota daki da abinci?.

"Ki gyaleta,ta hadiyi baqar zuciyarta ta mutu ita kadai" shine abinda mahmud ya fada yana sake qufula, tare da garin yarda da dukkan maganganun da fauziyya ta gaya masa.

Har dare ya raba tana kwance tana kuka,sanda agogo ya nuna mata qarfe uku na dare ta yiwa kanta fada,ta sauka daga saman gadon ta bude gofarta a hankali ta fito bandakin dake tsakanin dakunanta guda biyu dake manne da parlor. Ta kammala alwalar tana shirin fitowa mahmud ya shigo. Cikin sanyin jiki da karyewar zuciya take kallonsa, amma sai ya dauke kansa gefe ya rabata ya shige bandakin yana turo mata qofa.

Da qyar ta qarasa dakinta, ta zube saman abun sallar tana bude sabon shafin kuka,abin ya fara wuce tunaninta,ko a lokacin da Mahmud din ke ganiyar karayar arziqinsa wani abu makamancin wannan bai taba hadasu ba,ko da yaushe cikin gogarin kwantar masa da hankali take tare kuma da yin amfani da dukkan abinda take dashi saboda aci gaba da tafiyar da hidimar gidan yadda aka saba.

Sallar data kwana tana yi ita ta sanya sassauci cikin zuciyarta,a washegarin kuma ta tashi da wata irin dakiya tawakkali tare da qarfin zuciya,ta sameshi a tsakar gida yana bawa fauziyyan kudin cefane a madadinta. Ko a fuska bata nuna masa komai ba,ta tsugunna cikin girmamawa ta gaidashi yadda ta saba,yana fiffisgewa ya amsa mata,sai itama fauziyya ta rusuna tana gaidata.

Kallo daya tak tayi mata ta dauke kai, don abun na fauziyya yanzu ya daina bata mamaki, abu daya fa sani, tabbas akwai mummunan qudurin data sanya a ranta.

Mai hali inji hausawa sukace baya fasawa,yana fita ta baje kolin rashin mutuncinta,ta cika gidan da waqe waqe tana kuma bin kowacce waqa sau da qafa cikin daga sauti. Yaran kuwa gaba daya ta tattarowa maji din su ita tabi lafiyar katifa abinta. Bata waiwayesu sai data ga la'asar tayi,lokacin ta fito ya dora girkin dare,ta kuma fara kiran sunan yaran tana hilatarsu, har suka kai ga fitowa,ta tattarasu tana jansu da wasa tana kuma aikin abincin dare.

Cikin kwanakin gaba daya gidanta ya koma kamar ba nata ba,bata dats cewa sai abinda fauziyya ta fada,baya aiwatar da komai sai abinda tace masa. Fadin irin tsananin damuwar da maji ta shiga a lokacin batà baki ne,a sannan tana ji har cikin ranta, inama ace fauziyya ba ganwar miji bace kishiya ce,ba shakka inda kishiya ce koda abun zaiyi mata ciwo bai kai kamar haka ba.

Tun asali rayuwarta da Mahmud rayuwa ce ta soyayya da qaunar juna da kowa ya shaida da hakan,ko yaya ka zauna dasu zaka fahimci hakan,wannan ya
Sanya suke bawa mutane da yawa sha'awa, haihuwar
Muhammad da ta nadeeya ba abinda ta sauya game da yadda suke bawa junansu kulawa,koda kuwa bayan karayar arziqin Mahmud jarma din wanna kyakkyawar dangantakar bata canza ba. Asalin maji ta fito daga babban family a qasar Algeria,family ne na masu da shi,a sannan tana da kadarori, haka ta dinga dagasu daya bayan daya tana saidawa tana kula da Mahmud gidansa da yaranta,ko sau daya bata bari ya shiga damuwa ba game da abinda zasuci ko su sha,ko kuma karatun Muhammad ba. Har zuwa sanda riqon fauziyya ya dawo hannunsu.

Batasan me ake ciki ba,tashin farko kawai ta yiwa rayuwarsu katsalandan,ganin kusan duk wani decision shifa ke yankewa,a hannunta taga yayanta yana karbar kudin duk wata hidima tasa,ba shi ba,hatta ita idan tana da bugatar abu a hannunsa zaice ta yiwa shifa magana ta karba a waienta.wannan vasa sannu a hankali ta dauki dukkan karantsana na duniya ta dorawa shifa,tana ganin ta mallake yayanta ne kawai sai abinda tace, tare da tunanin duk wata hidima da akeyi cikin gidan da kudin yayanta ne, kawai don bashi da katabus ne babu yadda zaiyi shi yasa ake juyashi haka.
Duk wata wahala tare da fadi tashin aikin mahmud tare da shifa akayi, ta qarar da kudi masu dimbin yawa kafin tabbatuwar samun aikinsa a wani babban company. Gabanin ya samu aikin kullum maganarsa itace

"Allah ya bani abinda zan kyautata miki nima, Allah ya bani damar mayar miki da halaccin da kika yimin a yanzun da bani da mahaifiya kece makwafinta a gurina,in sha Allah sai kinfi kowa jin dadi na shifa,bazan manta wannan halaccin naki ba" sau tari

Please Login or Register in order to submit comment