Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 68 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tanadi mkaman gare dangi ba? bayan na san wacece ke?,ai duk makahon da kaii vace ayi wasan jifa to ya taka dutse ne.….na rasa mijina kin rasa dan uwanki!"

"Kin tafka babbar asara mansura butulu" dariva ta kece da ita

"Ashe? da kunya a idanunki har kina da bakin kiran wani butulu? ,kawai butulu sama dake? wadda taci amanar dan uwanta? taci amanar 'ya'yan dan uwanta? tunda kikaci amanar maji to tabbas ba wanda ba zaki iya butulcewa ba gwara ni.....kishiya ce kome nayi a kanta hada miji mukayi"

"Ke da gamawa da duniya lafiya har abada!" Hajiya garama ta furta a birkice tana jin kamar qwaqwalwarta zata hautsine

"Ke kuma idan aka leqa wuta ba'a ganki ba garwashin wuta ne ya rufeki fauziyya!"

"Dalla malamai ku gara gaba,yanzun ba wata sauran alaqa tsakaninmu daku" haseena da duka wadan nan maganganun basa gabanta ta fadi, don abu daya ke damunta a yanzu,ta yaya zata samu toufeeq?.

"'Me kike ci na baka na zuba meenal ya'aqoub aji?, awanni kadanne kuma suka rage muku a gidan nan yadda kuma ban samu toufeeq ba kema ke dashi saidai a hoto" labiba ta fadi tana jin sassaucin tashin hankalin data shiga a dazun, saboda tayi imanin ita da meenal dukkansu sun rasashi kenan.

"Zo mu tafi mommy bakin alqalaminsu suma ya riga ya bushe musu" labiba ta fadi tana damgar hannun hajiya mansura suna ficewa daga falon. Dukkansu ita da labiban zucivar kowannensu cike take da tashin hankali, komai sunayi ne kawai saboda idanun haseena da hajiya garama,amma sunyi amanna watan fara sanin wahala a rayuwarsu ta kama.

Kuka meenal takeyi sosai tana biye da hajiya garam cikin fushi da fusata da kuma tashin hankali, bata damu ko kadan da zubar hawayen idanun hajiya qarama din ba

"'Ni duka bance kije ki aikata wannan abun ba,kinyi ne kawai saboda son ranki da biyan buqatarki,ni ba damuwa ta bane koma meye zai faru, kawai ni ki cikamin algawarin da kika daukarmin,ni toufeeq nakeso,na riga na tsarawa kaina da shi zanyi rayuwa" kalaman 'yar tata yayi mata tsauri da yawa, tana juyowa ta kwashe haseena din da mari

"Ban taba sanin baki da imani ba sai yanzu, kome da ake tuhumata akai fiye da rabi na aikata shine saboda jin dadin rayuwarki da kuma inganta rayuwar taki amma baki ganib..." Kafin ta rufe bakinta siraran yatsun haseena masu azabar zafi sun samu lafiyayyen muhalli akan fuskar hajiya garaman. Wani mugun shock ne ya shigeta har fitsari yana ballewa a wandonta,da gyar ta tattaro yawun bakinta ta hada kalaman

"Ni kika mara haseena ni uwarki da na dauki cikinki wata tara na haifeki?"

"To sai meye? don kece kika haifeni ai ba kece kika halicceni ba,ga mari ga tsinka jaka? ga duka ga rashin biyan bugata?, to tunda ke sauna ce kin kasa aiwatar da komai ni zan samawa kaina farincikin da kika gaza bani din" saita kewayeta kamar zafa bangaji kafadarta ta wuce dakinta da gudu gudu.

Sulalewa tayi ta zauna saman kujerar da tafi kusa da ita tana dafe da dukkam kuncinta guda biyu tana jinta kamar ba cikin duniya take ba. Tunda take a rayuwarta duk tashen gin jin maganarta taurin kai da* shaharar da tayi wajen iya garya da shirya makirci ko yayanta bata taba mari ba bare akai ga mahaifiya, sai gashi yau itace yarinyar data haifa,ta gwadawa gata fiye da kowa cikin duniya,taketa fadi tashin tara mata dukiyar da ko bayan ranta ba zata wulaganta ba,take ta yunqurin samar mata nagartaccen miji, yau itace ya shimfidawa fuskarta mari?.

Qarar jan luggage dinta ya sanya hajiya qarama din daga kai. Ta shirya abinta kamar yadda tazo cikin gananun kaya. Da sauri ta janye qafafunta wanda banda hakan tsaf zata murjesu tabi ta kansu ta miqe tana kiran sunanta

"Haseena baki da hankali ne? ina zaki haseena? wa kika sani?" Ta fada tana tarar gabanta cikin jin tsoron kada halayyarta ta tsananin fushi ta sanyata ta aikata abinda ba dai dai ba

"Dalla matsa ki bani guri,ni yanzu baki da amfani a gurina, toufeeq shine rayuwata, kuma na rasashi, tunda kuma na rasa shi a shirye nake na rasa komai nawa" ta fada tana jifanta da wani wulaqantaccen kallo sannan ta gogi kafadarta tana wucewa.

Tayi taga taga kamar zata fadi ta samu ta tsaya
kan gafarta, ta bude baki zata sake gwada yunqurin
tsaidata din sai sautin data sanyawa dukkan alert
massages na bankunanta ya fara tashi a jejjere. Da sauri ta miga hannu saman dan table din data ajjiye wayar dazu kafin ta fita tana dubawa, mamaki yana cikata na shigowar massages din a jejjere babu qaqqautawa.

"Na shiga uku......na lalace….meye haka?......kai jama'a
wayyo Allah na ku kawomin agaji….Zasu yasheni.......zasu talautani…..wayyo Allah wai ba kowa
ne a gidan" ta fada cikin budaddiyar murya tana kwasar hanya da mugun gudu tana fita daga sashenta.


Zafafabiyar
"HUGUMA*


_TABARMAR KASHI_

Book 02 Page 68

Dai dai lokacin da alert na qarshe ya shigo wayarta,wanda aka cire ragowar millin uku last amount da ya rage a bankinta, kuma qarshen abinda ta mallaka kenan duk duniya,don ta saida komai nata ta hade kudin cass cikin account dinta zata sake sabuwar order na dukkan shagunanta,har a ciki take sanya ran gyara da same bungasa plazas dinta da wuta tayi musu mugun ragargaza. Tsaiwa tayi cak a wajen,sai ta dafe kanta ta daga qafa da mugun gudu tana fitowa harabar gidan a birkice kamar wadda take da tabbacin barayin da sukayi mata aika aikar suna
tsaye a qofar gidan. Saidar tana gara daga qafarta wata muguwar hajijiya ta debeta ta watsar da ita,sai gata tayi d'ai d'ai warwas a qasa. Amma hakan dai bai hanata miga hannu tana son yin kururuwa ba, kururuwar da babu damar fitarta daga bakinta saboda karkacewar da bakin nata yayi,sai wan! kakkauran yawu data fara zubarwa ta gefen bakin nata.

Caaaa ma'aikatan gidan sukayo a kanta, sai suka rasa yadda zasuyi da ita,saboda sunga fitar masu gidan yanzu. Daga qarshe dai bayan kusan awa daya daya daga cikin masu aikinta tayi gundunbala ta shiga bedroom dinta ta dauko key din motarta. Acanne taci karo da kit na sarqoqin gold dinta rankacakaf data fitar dasu a dazun bayan dawowarsu da zummar zata saidasu saboda taji yadda kudinsu yayi daraja ta aikawa gawarta kudin dake dubai ta siya mata sabon design.
Key din motar kawai ta miga musu ta wuce sashen masu aikin gidan ta hada kayanta zakara ya bata sa'a ta falle, cikin zuciyarta tana fadin


"Allah ne yayi da rabona, muguwa kina samu amma ke kadai kike amfana,saidai mu mu qare ayi miki bauta" ( shawara a gareku masu ma'aikatan a gurin
Sana'a ko kasuwanci ki cikin gidajenku de sauransu,sanda mutum yake zaune qarqashinka yake maka hidima,a duk sanda Allah ya buda maka,kaima kayi goqarin buda masa ku taru duka kuyiwa Allah godiya,wannan shine abinda zai dawwamar da soyayyarka a zuciyar ma'aikatan ka,da wata iriyar mana ta gaske da zaiyi wuya a hada baki dasu a cutar da kai, ko suna ji suna gani su bari a cuceka, Allah ya bamu ikon kyautatawa dukkan wanda muke tare dashi ameen summa ameen).

Private hospital aka kaita kamar yadda sukasan duka iyalin gidan suna zuwa,babban asibiti ne da suke cazar kudi bana wasa ba,sanda aka isa asibitin da ita
likitan da ya fara dubata ya tabbatar zaiyi wuya bata
samu matsala ba,saboda jininta ya hau sosai, hakanan
barin jikinta ya daina aiki, daya barin ma ya tabu sosai
amfanin da zaiyi mata kadanne, duk wani abu dake daya
sashenma totally ya daina amfani, kama daga idonta
kunnenta hannu qafa da sauransu
Sun tsaya anyi mata komai da komai ba don
halinta da dabi' arta ba. Bayan komai ya kammala akayi total na kudin asibitin kwanciyar da zatayi da sauran bill na abubuwan da zata ci. Elyas na daya daga cikin wadanda suka tallafa aka kawota,don toufeeg din bai fita da kowa ba,daga shi sai maji din sai Dr suka wuce dashi asibitin.

Bayan ya gama duba bili din wayarsa ya ciro yayi
kiran toufeeq,cikin rusunawa yayi masa bayani

"'Kana jina elyas?"

"Eh sir"

"Sisina daga abinda na mallaka da kuma abinda
mahaifina ya mallaka ban amince ka cire ka biya komai
ba,ku batta da su tana da gwarin qwiwar yiwa kanta

komai,ka jini?"

Kai ya gyada cike da biyayya

"'Yes sir" sauke wayar yayi daga kunnensa yana furzar da huci daga bakinsa,shi kansa baisan wanne kalar hukunci ne va dace da ita ba.

Zuwa magariba Dr jarma din ya koma normal, saidai sunce lallai dole sai ya kwana,saboda sunason jininsa da yahau ya dai daita kafin su sallameshi, basason ya tafi kuma ya dawo.

"Bari na yiwa jibril magana maji ya maidaku gida ke da nadeeya,zan kwana a gurinsa in sha Allah" toufeea ya fada yana danna wayarsa.

Murmushi maji din ta saki tana kallonsa

"Kaji dan nema,waini zaka yiwa kaara? to ban yarda ba, kada kana tsaka da yimin jinya ka gudu ka barmin miji sai asuba ka dawo" nauyin maji ne ya kamashi sal ya fara shafar sumar kansa yana murmushi, ko ta fahimci tun dazun yaketa kiran number sãahar din dama bata daga ba? duka hankalinsa yana kanta tunda suka zo

"Itama tana bugatar kulawarka Muhammad, ku tafi gida kai da nadeeya din,ka kula da matarka ni zan kula da milina" ta fadi tana maida dubanta kan dr jarma da idanunsa ke rufe kamar alamun yana bacci ne.

Dan rusunawa toufeeg yayi cikin ban girma

"Allah ya qara girma, Allah ya bashi lafiya" yayi musu sallama bayan ya tabbatar babu wani abu da zasu bugata har wayewar gari.

Suna fita tana qoqarin dauko wayarta daga jaka taji an rigo hannunta, ta daga kanta a hankali sai taga Dr ) jarma ne yana daga kwancen, idanunsa da suka nuna jigatarsa da kuma gazawarsa tare da tarin nadama

"'Na dauka bacci kakeyi ai ashe ka farka" ta fadi tana yunqurin migewa. Maidata yayi ya zaunar da hannunsa daya ya buda bakinsa da muryarsa ke fita da gyar yace


"Ido na biyu shifa inajin kunyar hada nawa idanun ne da naki bansan me zance miki ba,bansan ta vadda zan nemi gafararki ba,bansan da wadanne kalamai zanyi amfani wajen neman afuwarki da yafiyarki ba" kanta tadan sadda gasa tana wasa sa hannun jakarta sannan tace

"Tuntuni na yafe maka Dr tun a wancan shekarun don nasan muddin na gullaceka ko na yi maka mummunar addu'a rayuwar 'ya'yana na lalata, saidai kuma daga yau, kada ka sake sakaci da addu'a a rayuwarka,domin ita din garkuwa ce"

"Bazan sake ba shifa,naga illar hakan iyakar ganina,wai 'yaruwata shifa.....uwa daya uba daya..." Sai ya kasa garasa fada. Da sauri ta matso gabansa

"Ka daina tunawa don Allah abban Muhammad taka kalar qaddarar kenan, kuma ai yanzun komai ya wuce ) ko?" Ta fada cikin kalar tausasawar da bai taba gani
daga idanun mansura ba.

Da kalamai masu dadi ta kwantar masa da hankali har sai data tabbatar ya nutsu sannan ta mige

"'Ina zaki?"

"Zan hada maka wani abune ka saka a cikinka" kai ya girgiza

"Ba yanzu ba, banajin cin komai,ki rufe qofar kawai kizo ki zauna kusa dani naji duminki shifa,inason na fanshe bashin shekara da shekarun da na dauka"

murmushi ne ya qwace mata,cikin salon tsokana tace

"Da wannan tsufar naka?,ai ka makaro" ido yadan fidda

"Inii wa? idan kika cikamin baki da yawa ma tazarar haihuwarku keda surukarki zata kasnace ba yawa, nadeeya itama ta samu 'yan uwa" baki maji ta rufe da sauri tana dariya

"Rufamin asiri"

"Na rufa miki" ya amsa matan shima yana dariyar.

A nutse yake takawa zuwa cikin gidan, har cikin ransa yana gara jin gidan ya qarasa fita gaba daya daga kansa. A cikin gidan al amura masu yawan gaske sun afku,wadanda sukayi silar rugujewar farincikinsa, komai na matsalolinsa a gidanne,a yanzun vanajin bashi da wani sauran bugatar ci gaba da zama a gidan,ya fita fitt daga ransa.

A hankali ya ratsa falukan nasa ya fada hallway dinsu sannan kai tsave ya isa ga bedroom dinta. Murza handle din yayi ya bude sannan ya tura gofar ya shige.
Sam dakin babu wadatar haske a ciki,amma
kuma hakan bai hanashi gain komai dake dakin ba.

Daga can saman abun sallah ya hangeta, sanye da wani baby pink hijab, fadeela na saman gadon a nannade, da alama tayi nisa a baccinta.
Duka hannayensa ya zuba a aljihun wandonsa, ya jingina bayansa da bangon dakin yana kallonta,wani irin kallo da yakejin tamkar zuciyarsa tana narkewa saboda ita, A HEROIN…ta kawowa rayuwarsa haske me tarinyawa da bai zaci samunsa a nan kusa kaf cikin rayuwarsa ba.

Jin bai garaso ba ya sanyata daga kanta a nutse ta bude bakinta a hankali ta langabar da kanta

"Me kake kalla?‚ka qaraso" hannayensa ya sauke yana murmushi

"Jarumar matata nake kalla, kinyi missing dina ne? ko na qaraso akwai labari?" Wani narkakken kallo ta watsa masa,tadan juya kanta kadan tana murmushi

"Baka gajiya...

"Shshshsh" ya fada sanda ya iso gabanta,ya tsugunna saman qafafunsa idanunsa cikin fararen qwayoyin idanunta

" will never get enough of you moonbeam,you are the only home i want to stay for ever, kinsan wani abu?"
Yayi mata tambayar kai tsaye. Fararen idanunta ta daga ta kalleshi,saita girgiza kanta tana jin zuciyarta da ruhinta dukka suna narkewa a kansa, tana jin wata iriyar soyayya me zafi da garfi tana fusgarta a kansa. A hankali ya zame va zauna sosai a gabanta kamar me zaman cin abinci,ya kama vatsantsa na tsakiya yana kallon tsakiyar qwayar idanunta,yanason ya aike mata sagon da gaske yadda kowacce gaba ta jikinta zata karba "Duk sanda nakejin kaina ya cika da tunanika kala daban daban my body is weak and my soul is aching....i find everything in your arms,you are my home....you are my peace SAHR" Idanunta ta lumshe qwarai

"Ya salam! wannan wanne irin so ne haka me barazanar fasa zuciva?" Ta furta a hankali da salon magana cikin rad'a. Ji vayi kamar ya hadiyeta su zama abu guda shi da ita ko zasu fi samun saugi a cikin zukatansu. Sai kawai ya jawota a tausashe ya sanyata cikin jikinsa.

Dan janyeta yayi da sauri yana duban fuskarta

"Fever? me yasa zaki damu da yawa hakan akan lamarin matar data riga ta shude cikin rayuwarmu?, muddin wani ,abu ya faru dake tabbas sai ta d'and'ana kudarta bayan wadda zata dandana din, ta gama cutatar mana da ahalinmu har abada in sha Allah " hannunsa ta riqe sosai tana kallonsa

"Cool down hottie, am safe fa,nayi bacci ne da yawa sai ya sanya jikina yayi dumi sosai, but am fine fa" ta fada a shagwabe,iska ya furzar daga bakinsa

"Alright,ta tsira" ya furta a hankali.


Zafafabiyar
"HUGUMA*


•TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 69

Washegari ta zame jikinta daga nashi ta fita a duvet din ta barshi vana bacci ta shiga kitchen.

Breakfast me kyau ta shirya musu gaba daya,harda wanda za'a kaiwa dr asibiti. Ta gama tsaf tana goge waien taji takunsa a hankali da qamshinsa me sanyin nan,ta waiwaya a nutse tana dubansa. Shima ita yake kalla da tattausan kallo ya garaso a hankali yana duban warmer's din data shirya.

Da idanu ya tambayeta, saita saki murmushi tana dora yatsantsa saman lips dinta alamun yayi shuru. Hannu yasa ya fincikota jikinsa,ya riqe qugunta da kyau suna yiwa juna kallon kallo

"Kin karya doka,kika kwantar dani ina bacci kika taso kina aiki, waye kika tambaya?" A nutse ta miga hannunta zuwa sumar dake kwance baqiqqirin qasan habarsa tana dan wasa da ita idanunta cikin nashi tana sakar masa wani kallo

"A yimin afuwa hottie......but hidimar iyaye ba'a sanya wajen yinta" garamin murmushi ya saka yana jin qaunarta cikin ransa, darajarta da kimarta suna sake qaruwa, sai ya sake matso da ita jikinsa sosai yayi kissing nata a tausashe

"Zanyi wanka sai mu fita dasu jibril na miga masa" langabe masa kai tayi a shagwabe

"'Nifa?, zanje fa" hannu yasa ya lakace mata hanci

"Duk sanda kike min magana kamar haka,sai na dinga ji kamar na tsayar da lokaci ya daina tafiya nayita kallonki kamar haka" hannunta ta sanya ta zagaye shi duk da bata iya ratsashi ba,rungumeshi tayi tana dora kanta saman girjinsa

"Am all yours thank you for loving me you have
Brightened up my life with your beautiful spirit and caring heart" kansa ya kwantar tsakiyar lallausan gashinta dake hargitse yana lumshe idanu, har cikin zuciyarsa yana tasirin saukar kalamanta,a hankali yace

"I only regret one thing in our marriage...
.. Zuciyarta tadan buga kadan,sai ta zame kanta a hankali ta dagashi tana kallonsa da fararen idanunta da suka bayyana fargaba

Wata lallausar dariya ya saki, ya sunkuceta gaba daya ya azata saman kitchen cabinet, hannayensa ya zura ta gasan rigar baccinta,ya soma tafiya dasu a hankali cikin wani salo na tafiyat tsutsa, bai tsaya dasu ko ina ba sai da yakai tsakiyar bayan nata, ya sake matsowa da fuskarsa sosai, hucin numfashinsa yana sauka saman fuskarta tata

"One thing i regret in our marriage... that i haven't met
¿ you sooner" murmushi ne ya qwace mata, sai ta karyar da kanta gefe,tsoro da fargabar da ya dasa mata a lafazinsa na farko ya zagwanye. Binta yayi da kallo yana jin gaba daya tana tayar da tsigar jikinsa,wani mahaukacin kyau murmushi yakeyi mata,inda da hali tabbas da ya hana mata yin murmushi a ko ina

"Kinsan me?" Ya fada a hankali yana matso da bakinsa saitin kunnuwanta,abinda ya sanya tsigat jikinta zubawa sosai, taji yarrrr har tsakiyar kanta, kafin tayi controlling

kan nata ya fara sauke mata kalaman da suka fara rikitata

"I've tasted your lips in my dreams,and when i woke up, knew for sure what i wanted for breakfast" numfashinta taja da kyau jin kamar zai subuce mata, idanunta a lumshe, tana kunyar budesu yaga abinda ya cikasu

"I need a big, hot steaming cup of you this morning....kin bani d....." Bai qarasa ba ya tsinci bakinsa dumu dumu cikin nata tana aika masa da salon kiss din da yafiso,bai wani tsaya bata lokaci ko daga qafa ba yayi mata kyakkyawar tarba suka soma rikita juna. Basu fahimci me suka aikata ba saida komai ya kammala,suka kalli juna cikin matsananciyar kunya murya qasa qasa tace dashi

"A kitchen?" Girarsa duka biyun ya daga mata yana fidda murmushin da yake tabashi har can qasan zuciyarsa,saboda wani irin farinciki data bashi

"And whe enjoyed it" sai suka saki siririyar dariya a tare.

Hannu ya miga mata ya kuma sauketa a hankali daga saman cabinet din sannan ya rigeta,a nutse suke takawa zuwa bedroom din shi da ita, ya hada musu ruwan wanka bai tsaya shawara da ita ba ya sunkuceta sai bandakin.

Suna gaban madubi yana busar mata da gashinta,wata sassanyar hira suke a madubin ta cikin qwayar idanuwansu ba tare da baki ya furta komai ba.
Dan garamin tsaki yaja gain yadda aketa neman izinin shigowa hallway din nasu ta garamar na'uarar dake magale a bedrooms dinsu. Cumb din hannunsa ya anivya zaro abayarsa ya zura yana fadin

"'Ina zuwa" ya juya a nutse ya fita.

Murmushi ta saki tana satar kallonsa har ya fice din,ta maida idanunta ta kulle tana jin yadda soyayyarsa keyin yadda taga dama a zuciyarta yadda take kassara kowacce gaba ta jikinta. Wani irin sassanyan mutum ne da ya iya cusa zazzafar qaunarsa a zuciyar iyalinsa.

Adadin yadda mu'amalar aure ta hadasu,adadin yadda yake sake ratsa zuciyarta da wata irin zazzafar soyayya,yasan yadda ake tafiyar da mace over and over, batasan yadda bakinta zai iya fasaltawa ba.
Nadeeya ya gani a tsaye sai ya jefa mata harara cikin salon tuhuma da kuma tsare gida

"Am sorry yaaya‚police ne suke nemanka"

"Shine zakizo kiyita disturbing mutane?" Ya fada hankali kwance

"Yi haquri" ta sake fada. Sai a lokacin yaga kamar akwai alamun tashin hankali kan fuskarta

"Are you okay?" Kai ta gyada tana hadiye yawu da ayar,sai ya kewayeta kawai yana ficewa ta bio bayansa

"Kibi ta daya qofan ki koma cikin gida" yace mata ganin akwai maza da vawa a wajen harda ma'aikatan gidan.

Cikin nutsuwa da kamewarsa ya garasa gurin.
Dukkansu sukayi saluting nasa saboda fuskar da basu zata ba suka gani. Babbansun ya matso ya miga masa hannnu sukayi musaba

"'Sir......na shiga tantama da kokwanto, da gaske a nan din meenal ya'agoub aji take?"

"Meenal?" Ya maimaita sunan cikin tantama

"Oh,right eh nan ne" ya fadi bayan kuma ya tuna wace me sunan. Juyawa yayi kadan ya kalli yaransa sai ya karba wata takarda daga hannunsu ya migawa toufeeq yana cewa

"Am sorru to inform you tayi commiting suicide,ta kashe kanta"

"Subhanallah, subhanallah" toufeeq din ya furta yana maimaitawa tare da karbar takardar yana duba tabbacin gwaji ne na mutuwarta da kuma shaidar kashe kanta tayi din.

"Zamuje tare ku sanya hannu sai mu baku gawarta"

"To babu damuwa, bari na sanarwa da family na"

"Zamuyi gaba sir,sai ka samemu a Murtala Muhammad specialist hospital"

"Ba damuwa" waiwayawa yayi ya kira libril yace ya fiddo mota,ya juya cikin gidan da sassarfa

Sassansu nadeeya ya wuce yana sallama ya samu fadeela zaune tana cin indomie, gefe ga cup data cika da madara, cartoon take kalla a mbc 3. Da mamaki yadan bita da kallo,wasa wasa ta kama abinci sosai tunda akayi aikin fiye da wanda takeci lokacin säahar.
Murmushi ya wadata kan fuskarta,ta ture plate din tana migewa hadi da fadin

"Good morning daddy"

"'Bazan amsa ba, gaisuwarki tazo late" kai ta langabe

"But daddy, banason zuwa na tada ku a bacci fa,nasan anty N a gajiye take sosai,tun kafin ayimin aiki bata bacci, kullum addu'a take kwana tana yimin, inason tayi bacci sosai yanzu don ta haifa min ganne masu garfi da zasu dinga taremin fada" a bisa dole murmushi ya kubce masa,yasan wanna sharrin surutun nadeeya ne, har ya fesa mata kenan, ita kuma bilhaqqi qanne takeso shi yasa take kiyayewa

"Good girl" ya fada yana saluting nata da hannunsa.
Sake gaidashi tayi ya amsa, ya tambayi nadeeya da baaba ramatu tace

"Suna kitchen,abby ka duba abincin da suke bani don
sunga anty N bata kusa" ta fada tana nuna masa abincin da baki. Murmushi ya sake subuce masa,gaba daya yarinyar kamar an sake bude bakinta ne da komai nata

"'Ayyah,zamu kai gara wajen AUNTY N"

"Eh dama na fada,nayi missing abincinta sosai, please
daddy yau tayi mana dinner mana?" Kanta ya shafa

"Nima navi missing abincinta angel, amma sai ta warke sosai zata dafa mana muci ko?"

"Ni ko bata dafa min bama, indai zata kawomin qanne na 1 mu dinga wasa shikenan" dariya ta bashi duk da yanayin zucivarsa babu dadi amma sai da ya sake murmusawa

"'In sha Allah, kiyita mata addu'a yadda tayi miki kema"

"Zanyi daddy,i promise"

"That's good my angel,yanzu jeki kiramin su" da gudu ta cilla tayi kitchen din cike da farinciki, tana wassafa yadda zata kula da nata gannen itama, zata yita bawa 'yan class dinsu labarin qannenta itama yadda kowa yake bata labarin nasa,dama ita kadaice bata da.
Rudewa dukkansu sukayi, nadeeva na hawaye baaba ramatu tana salati

"Relax please, banason SAHR taji yanzu saboda yanayin da take ciki, please take care with her" ya qarashe maganar yana kallon nadeeyan, saboda yasan itace sarkin raki. Kai ta jinjina ya juya yana fita daga sashen.

Batasan me yake faruwa ba,taga dai ya shirya a gaggauce,yayi kissing hannunta yana cewa

"Zanje na dawo,ki kwanta ki sake hutawa kafin anima na sake tara miki wata gajiyar,yanzun bana bugatar kiyi komai saidai ki bani kulawa, idan da hali ma bacci nakeso kiyi" kafada ta maqale a shagwabe

"Kada ki damu,i will handle it with care and softness,it would not be harmful".

Haka ya fita ya barta da tarin tunaninsa a kanta,murmushi kuma fal fuskarta. Ta gaji da zaman,don haka sai ta shirya ta gyara sashen tsaf sannan ta sake gyara jikinta ta fito,don tana sin ganin fadde dinta, tana kewarta.

Hankalin maji yayi masifar tashi da jin labarin mutuwar haseena, ba kuma wai mutuwar ce abun tashin hankalin ba,hanyar da tabi wajen salwantar da rayuwarta.

"Ka shaidawa mamanta ne?" Maji ta tambayi toufeeq

"I think tana asibiti, nidai na gama nawa gawar tana asibiti maji". waiwayawa maji tayi ta dubi Dr jarma da aka gama rubutawa sallama

"Abba,haqqij yi mata sutura yana wuyanku,saidai bansan ta yadda za'a gayawa fauziyya rasuwar ba tunda bata da lafiya itama"

"Dole ta sani ai,ko don ta roqawa 'yarta gafara ko?" Ya fada yana sauka daga saman gadon hadi da duakan wayarsa.

Toufeeq sajjad dr har da maji suka isa asibitin da hajiya qarama ke jinyar.

"Dama muna shirin neman 'van uwanta mu sallameta ne,saboda babu me jinyarta, abinda ya hana mu bata sallama ma ba'a biyamu bill dinmu dake kanta ba" wata nurse ta fada cikin girmamawa sanda taga dr mahmud hadi da toufeeq,wanda kusan ba boyayyu bane kusan kowa yasan fuskarsu.

"Sannan sir,kamar akwai abinda yake shirin taba qwaqwalwarta,akwai magana da yawa da takeson fada ma amma kuma ba'a iya jin abinda take fada sosai,a shawarce a fara ganin likitan qwaqwalwa kafin abin yayi nisa". Shikam toufeeq zame jikinsa yay yabar wajen,don baya jin sisinsa zai iya sanyawa wajen neman lafiyarta.


Zafafabiyar

"HUGUMA*


•_TABARMAR KASHI_*

Book 02 Page 70

A haka aka kinkimeta sukayo gida da ita,

Please Login or Register in order to submit comment