Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 6 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Riqe da glass coffee mug din a hannunsa da yake kurba time to time,yana zaune daya daga cikin kujeru hudu dake gurin,sauran biyun baqinsa ne a kai,idanunsa akan takardun dasu Mr Paul suka gabatar masa yana irga adadinsu da idanunsa ba tare da yakai ga tabasu ba. A nutse ya ajjiye mug din yasa hannu ya rufe file din

"We will contact you after two weeks" kai suka jinjina cikin fara'a suka miqa masa hannu,saidai kafin yakai nasa hannun muryarta ta ratsa dodon kunnensa

"Hi......" Ta furta, cikin qasa da second biyar kuma ta bayyana a gabansu.

Dukka su ukun suke kallonta,saidai kowannensu da irin kallon da yake mata,mr isaac da Mr Paul kallo suke mata na zallar burgesu da tayi,kyawunta kuma ya ratsa har cikin jininsu,yayin da nasa idanun suka cika da tsananin bacin rai da haushi mara misali. Idanunsa ya janye daga kanta ya miqa musu hannu sukayi musabahar da basuyi din ba,sannan ya miqe yasa hannu daya ya dauki mug dinsa,daya hannun kuma ya fara danna wayarsa yana son kiran jibril yaso ya shiga masa da file din. Cikin second kadan ya iso,ya masa nuni da takardun,yasa hannu biyu ya dauka ya wuce dasu.

Tana tsaye a gurin,ta zuba masa dukka idanuwanta,tana jin wata mahaukaciyar qaunarsa tana tasiri a jikinta da zuciyarta,tana jin kamar ta taka da gudu ta rungumeshi cikin jikinta,ta kwantar da kanta saman ingarman qirjin nan nasa,ta kuma shafi gefan fuskarsa dake dauke da lallausan gashin da tana iya hango gyaran da yasha ya kuma kwanta luf. Saidai inaaaa,tasan hakan shine babban kuskuren da zata tafka a rayuwarta,tasan wayeshi qwarai da gaske,ko a yanzun ma tana cin albarkacin wani abu ne,tabbas!,da bata isa ta bibiyeshi har haka ba.

Ganin ya fara barin inda take din ba tare daya nuna wata alama na sanin wanzuwarta a wajen ba yasa itama ta cira qafarta dake sanye da high heels ta fara binsa

"Hello" ta gada da muryarta mai yauqi,shuru ba amsa,wannan ya sanya tadan qara daga qafa

"Muhammad" tayi kiransa da ainihin zallar sunansa. Shi kansa a karan kansa yasan girma qima da martabar me asalin sunan,mahaifinsa ya dauka ya bashi shi,zaiyi wuya ka kirashi da sunan zalla ya iya tafiya ya barka a guri saboda girmamawa ga sunan kansa,batasan hakan yana masa tasiri ba,tana kiransa ne kawai duk sanda taji nishadin kiran nasa da sunan nasa. Ya tsaya cak,har zuwa sanda yaji qarasowarta bayansa dab dashi,cikin deep voice dinsa yace mata

"Ki juya ki koma inda kika fito"

"Saboda me?,don kai fa nazo"

"Ba matsala bace......i said ki juya ki koma inda kika fito,if not....." Maqale hannayenta tayi a qirji,alamun gargadinsa ko a jikinta

"Idan nace a nan zan kwana fa,kuma a kusa dakai?"

"You are mad,ki gwada ki gani" ya fada yana jin zallar tsanarta tana shigarsa,cikin second kadan tasa kansa ya fara ciwo,duk duniya ita daya ta isa ta tsaya haka a gabansa a matsayinta na MACE ya fada sau daya ta maida masa,ita dimma tana cin wata daraja ne guda daya,sai ya fara yin gaba ba tare daya waiwayo ba.

Baisan daga ina ba,baisan ya akayi ba......saiji yayi an masa wawar runguma ta baya,he was shock beyond the words,bai taba zata ba bai taba kawowa ba,bai taba tunani haukan LABIBA yakai haka ba. Wani irin mahaukacin fushi ya yunquro masa,yana waiwayo ya zube mata yatsunsa guda biyar saman fuskarta.

Hannu bibbiyu ta saka tana dafe dukka kuncinta guda biyun hadi da rintse idanu tamkar ita aka mara bayan ta saki wayar hannunta da take dannawa don rage tsahon lokacin jiran yaa zaid,sai kuma ta bude idanun nata a hankali tana laluben daga inda wannan zazzafan marin ya fito,dai dai lokacin da ya fara magana cikin deep voice dinsa data cika da tsananin fushi

"Shashasha wawiya, I can't tolerate it, next time kika sake gwada irin haka kiyi tsammanin abinda yafi haka" yayi wurgi da mug din hannunsa ya hadu da qarfen dake riqe da fitilun gurin ya tarwatse,baiko bi ta kansa ba ya wuce yana taku da sassarfa duk da hakan kuma majestically.

Mutuwar zaune sãahar tayi,kunnuwanta suna bitar mugayen maganganun da yanzun nan kunnuwanta suka saurara,duk da cewa bataga fuskarsa da kyau ba amma muryarsa ta fita clearly kamar a gabanta yake maganar,a hankali kalaman suka fara mata suya a qirji tamkar ita aka gayawa,me yasa maza suka raina mata?,itace tambayar data dinga yi mata sukuwa cikin tsakiyar kanta,idanunta nakan labiba data sulale a gun tana kuka,kukan nata ya dinga taba sãahar,ta lumshe ido tana jin kamar ita ya zaga. Me tayi masa ne da har zai daga hannu saboda zallar rashin sanin darajar mace ya zabga mata irin wannan marin?,bata iya shiga abinda babu ruwanta ba,da ta qarasa ta daga labiba data zube a gun tana kuka sosai,ta bata haquri tare da bata shawarar ta manta dashi koda ba zata iya rama abinda yayi mata ba.

Kasa jure sautin kukan nata tayi,saboda yana son taso mata da nata tsohon ciwon,don haka ta miqe a gaggauce ta zagayawa zuwa inda yaa zaid ya ajjiye motarsa,tayi amfani da key din daya bata ta bude motar ta shige tana maida numfashi ranta a matuqar jagule.


FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥


*H U G U M A*

_*TABARMAR ƘASHI*_💔

*Arewabooks: huguma*
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 11

A gaggauce yake komawa cikin hotel din cikin sassarfa da wani irin bacin rai kwance saman kyakkyawar fuskarsa da bata da annuri tun asali ko kadan,jibril dake biye dashi yana maida qafarsa duk inda ya ajjiye,tabbas yasan yau an taboshi fiye da ko yaushe,saidai baiga laifin fushin nasa ba,don shi kansa yarinyar ta fara gundurarsa bare kuma shi da ake bibiyar.

Suna shiga lobby ya waiwaya ya dubeshi,zuwa sannan fuskarsa harta fara yin ja,musamman hancinsa,abinka da farar fata

"Ka kiramin dukka wadanda muka shigo wajen nan tare,su sameni a living room now!" Yana fadin haka ya qara sauri ya wuce zuwa elevator.

Da sauri matashin daya bari zaune cikin living room din ya daga kai yana dubansa,yasan yana da matuqar zafi da rashin fara'a,amma yana saurin gane canzawarsa idan wani abun ya sameshi,kamar dai yanzun daya kasa zama,sai iska mai zafi da yake furzawarwa daga bakinsa

"What's going on?" Ya jefa masa tambayar yana binsa da kallo,kai ya girgiza masa ba tare da ya iya ce masa komai ba

"Come on please,take it easy mana man" yayi maganar yana sauke qafafunsa dake harde qasa,tare da yunqurin cooling temper din da hanga cikin idanunsa,dai dai lokacin da aka nema izinin shigowa living room din.

Dukkansu suka dinga shigowa daya bayan daya,kowanne a yanzu wasu kayanne a jikinsa ba baqar suit din dazu ba,da alama kowanne yana dakinsa ne yayi shirin kwanciya. Da wani zazzafan kallo ya bisu,dakin ya dauki shiru na wasu yan daqiqu,sannan ya buda bakinsa da zuzzurfar muryarsa data qara nauyi saboda bacin rai

"i regard one of you was betrayal" yayi furucin da gasken gaske,babu alamun sassauci ko wasa ko kadan saman fuskarsa. Tsit dakin yayi,jikin kowa ya amsa,aka rasa me motsawa bare ya bashi amsa

"Who told her I was there?" Dif dakin ya sakeyi,yayin da yake sake bin fuskarsu da kallo daya bayan daya,yana hucin bacin rai yana fita daga fuskarsa,ya dauke kansa daga dubansu,ya maida hannayensa cikin aljihun wandonsa ya soma takawa a hankali zuwa gaba

"I will not repeat my question....." Ya fada bayan ya basu baya

"Nine" daya daga cikinsu dake rakube acan gefe ya fada,zufa tayi wani irin wankeshi,yasan sakamakonsa,babbar asarar ce zata sameshi wadda ba lallai ya maida gurbinta,sai ta ninka abinda ya samu daga gareta bayan dogon lallashin data masa ta ciyo kansa ya shaida mata sun sauka a bristol din.

A nutse ya waiwayo ya kuma zuba masa idanu,zuciyarsa tana tafasa

"All this while......." Sai kuma ya kasa qarasawa saboda bacin ran dake sake taso masa idan ya tuna yadda ta rungumeshi,yanajin kamar ya zauna ya daye fatar wajen,ko ya maido da lokacin ya goge faruwar hakan

"You're fired!" Ya fada kawai bayan ya duqa ya dauki wayarsa yana nufar qofa

"Anyone who deliberately does what he has done deserves to be fired from his job" statement dinsa na qarshe kenan,yasa kai ya fice daga dakin ba tare daya sake waiwayar kowa a cikinsu ba.

A nutse saurayin SAJJAD ya miqe yabi bayansa,yana shiga dakin shima yana sanya qafarsa

"Me kake aikatawa ne TAUFEEQ?,firing a person from work is not a joke"

"Did I tell you I was kidding? I really mean what I said,i dismissed him,idan kuna tunanin wasa ne na ganshi cikin maaikatana gobe" yayi maganar yana bude fridge,ya cire ruwa me sanyi ya balle murfin gorar yana tuttulawa cikinsa ba tare daya nema koda cup ba.

Da kallo SAJJAD ya bishi,tabbas shan ruwa me sanyi sam ba dabi'ar taufeeq din bane,idan kaga hakan ya faru to alamu ne na tsananin bacin ransa,ko meye zai gaya masa a yanzun bazaiyi tasiri ba,sai yaja qaramin tsaki

"since that's how you choose to be,sai kaci gaba,sai da safe"

"Ka sallamesu ka rufemin qofofina" ya fada masa a taqaice yana cillar da robar ruwan gefe,ko a jikinsa na fushin da sajjad din yayi,bazaita zama bai takawa yarinyar burki ba ita da duk wanda yake bata information na wanzuwarsa a waje ba,tabbas muddin akaci gaba da haka to babu shakka watarana zata zubar masa da mutunci kima da kuma martabarsa,tunda har ta farajin takai hannu jikinsa,the worst part ma a waje na jama'a irin wannan,daya daga cikin dalilan da yasa yake sake tsanar mata a ransa,zasu iya yin komai.......zasu iya aikata komai da gajeran tunani da qwaqwalwarsu.

Qarar wayarsa ce ta dakatar dashi,ya fidda hannayensa daga aljihunsa ya taka a hankali zuwa inda ya ajjiye wayar,kiran dake shigowa ta cikin wayar me muhimmanci ne,ya ajjiyeta ne kawai saboda ire iren kira masu muhimmancin da suka shafi family dinsa.

Wani abun mamaki qaramin murmushin daya ratsa murtukekkiyar fuskarsa har labbansa suka motsa,wani irin sirrintaccen kyau ya bayyana kan fuskarsa,ya dauki wayar yana daga kiran

"Daddy" siririyar muryar qaramar yarinyar ta bayyana cikin wayar,ta kuma ratsa kunnensa,ya lumshe idanunsa ya budesu a hankali,yana jin duk wata damuwa da bacin ransa suna narkewa

"Daddy's angel" ya maida mata a tausashe

"Wai da gaske kazo?"

"Ki fara gaisheni tukunna" ya gyara mata bayan ya bude dukka idanunsa yana kallon gabansa

"Good evening daddy"

"That's my girl......kina lafiya?"

"Lafiya lau daddy,da gaske kazo?" Gyara zamansa yayi ya zauna sosai sannan ya amsa mata kanshi tsaye,don bai saba yi mata qarya ba,bare ma kwata kwata shi din yana cikin jerin mutanen da komai tsanani komai wuya basa barinsa yayi qarya,tun daga yarinya har kawo yau,komai girman situation din da za'a shiga

"Na dawo angel,but wani aiki ya riqe daddynki,i really miss you, I can't wait to see you,but in sha Allah gobe komai dare,you will be next to your daddy,please apologize me" dariya ta qyalqyale dashi cikin nishadi da siririyar muryarta sannan tace

"Apology accepted daddy"

"Thank you princess" ya fada cikin nuna kulawa.

Sosai zakayi mamakin yadda ya saki jiki yana hira da ita cikin kulawa,a hankali kuma bacin ransa yana narkewa,ita din duniyarsa ce,wata qwayar halitta guda daya dake da mazaunin komai na rayuwarsa,baya wasa da dukka abinda ya shafeta,matsayinta da qaunarta a ransa ta zarta komai. Bugu da qari lalurar dake tattare da ita tana sake sanya masa wata qaunar yarinyar tare da mugun tausayinta,tattalinta da kuma bata dukkan kulawar daya kamata,idan ba tayi mugun takewa ba,baya bari ko kadan yayi nisa da ita.



*_F R I D A Y_*


K'arfe d'aya da rabi na rana suka fito daga town hall meeting,wanda ya sake maida kowanne ma'aikaci cikin nutsuwarsa,ya kuma girgiza zukatan duka wasu marasa gaskiya. Iya abinda aka tattauna a gurin kawai tsaiwarsa da yadda ya tsara abubuwa ya tabbatarwa da kowa ba wasa yazo yi ba,daga nan suka wuce sallar juma'a da dukkan Wani ma'aikaci musulmi,sannan ya sallami kowa da zazzafan gargadin haduwarsu da fara aiwatar da komai ranar litinin.

Suit coat dinsa ya cire yana ratayeta,sannan ya jawo kujerarsa ya zauna bayan ya nade hannun rigarsa zuwa sama kadan,yakai hannu ya dauki drink din da jibril ya ajjiye masa yana duban mutum biyun dake zaune,ya tsaya ya saurari dayan ya sallameshi,sannan ya maida dubansa ga sajjad

"Who is my new president?"

"she didn't come" komawa yayi baya yayi relaxing jikin kujerar,idanunsa a lumshe yana jin kansa ya dauki caji da yawa

"Is she a female?"

"Eh" ya amsa masa yana kallonsa,don yasan anzo gurin,idanunsa ya bude tarwai,ya zubesu kan fuskar sajjad

"A female president? why?"

"it's dad's choice" shuru ya danyi,kamar bazai sake magana ba,sajjad ya kafeshi da ido,sai ya janye nasa idanun,ya janyo system dinsa yana budewa

"If she is not ready to work with us, we will replace her with someone else,let her know,dole ta zama serious,ba zamu dinga biyanta tana abinda taga dama ba"

"Za'a gaya mata,but wannan dogon statement din yayi yawa sir" ya fada yana bincika jerin sunaye da address phone number da email address na ma'aikatan dake hannunsa,duk wasu ayyukan ba nasa bane basa a wuyansa,amma sanin hali ya sanya abba ya hadashi dashi,yace kuma ya dinga zama by his side lokaci lokaci,yana monitoring wasu abubuwan,yasan taufeeq din da zafin kai qwarai.

Bazai iya challenging daddy din ba,amma tabbas da ya sauya ta da namiji,matsayine da yake ganin mace sam ba zata iya riqeshi ba,koda zata iya din ma,zuciyarsa bata basu wannan amincin na riqe babban matsayi har haka ba,rashin amanarsu kadai ya sanya baya qaunar wani hulda a tsakaninsu,bare har akai ga zama na aiki da musayen ideas.

Kwata kwata ma basu cancanci dukka wata mu'amala data qunshi aminci ba,yana musu kallon wata halitta ta daban,KUDI shine abinda sukafi bawa daraja kima mutunci da muhimmanci,zaifi kyau su tsaya iya nan.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥


[8/8, 3:54 PM] Maman Aslam: *H U G U M A*

_*TABARMAR ƘASHI*_💔

*Arewabooks: huguma*
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 12

Tunda yaa zaid ya sauketa a jiyan abun yaqi barin ranta,kusan zata iya cewa dashi ta kwana,wanda ya haifar mata da wani irin bacci mara dadi,da mafarkai barkatai wadanda suka shafi wasu al'amura dake da alaqa da rayuwarta. Cikin dare ciwon kai ya saukar mata,wannan ya sabbaba mata makara a sallar asuba,kuma ko bayan tayi sallar wani baccin ya sake daukarta,sam ta mance da batun fara zuwa aikinta a yau,wanda dama zataje ne kawai don ta fara karantar yanayin yadda abubuwan suke.

Kwata kwata bata tashi farkawa ba sai qarfe goma na safe,ta tashi da sauqin ciwon kan,ta miqe daga gadon tana shirin shiga toilet akayi knocking qofarta.

Maama ce ta shigo,cikin kamalar nan tata wadda kusan a nan da wajen abba sãahar din ta gadota

"Kina lafiya kuwa?" Tayi mata tambayar tana kallon qwayar idanunta tare da fatan ba damuwarta ce ta sake motsawa ba

"Ina kwana maama" ta maida mata da gaisuwa

"Lafiya qalau,kin tashi lafiya?"

"Alhamdulillah,na dan tashi da ciwon kaine,bayan asuba kuma saina samu bacci"

"Subhanallah,Allah ya sawwaqe,ko zaki asibiti?,banason zama da ciwo" ta fada cikin damuwa,saboda tasan yanayin ciwon kan sãahar din,baya yi mata da sauqi idan ya tashi,saboda ciwo ne da ya samo asali ta Wani dalili,ba hakanan ta sameshi ba

"Alhamdulillah naji sauqi yanzu,wanka kawai zanyi na sauko"

"To alhmdlh,yayanki ne ya dameni da waya tun dazu,yace yana kiran wayarki bata shiga ba"

"Ya muhyi" ta fada kai tsaye,tasan yanason jin ta fita aikinne ko kuwa

"Zan kirashi idan na fito a wanka"

"To madalla,yayi" saita juya tana shirin fita

"Abbanku ya fita,amma shima ya tambaya kafin ya fita din"

"Zan kirashi shima" ta sake fada tana yunqurin zare rigar baccin jikinta

"Don Allah maama,baba rabi ta kawomin ruwan dumi a cup"

"Shikenan" ta amsa tana qarasa fita a dakin.

Da ruwa me dumi sosai tayi wankan nata,ta fito fatarta na wani irin sulbi da qamshi daya hade da tururin ruwan dumin da tayi wankan,ta fito ta tsaya gaban mudubi tana kallon fuskarta dake subul kamar ta jariri,babu tabo babu komai,sai tsananin taushi da sulbi da take sakeyi,alamun product din da take amfani dashi ya karbeta. Tasa hannu ta dauki mug din ruwan dumin da baaba rabi ta kawo mata ta aje ta soma kurba a hankali,saboda muhimmancinsa a jiki bata skipping shansa kowacce safiya kafin taci komai,koda kuwa ta makara bata tashi da wuri ba.

Da wani irin sauri sautin marin jiya ya gilma a kunnenta,ta runtse idanu kamar a sannan abun ya faru,ta cire cup din da takai bakinta a hankali ta ajjiye saman madubin sannan ta bude idanunta tarwai tana kallon fuskarta. Tsantsar rashin sanin darajar dan adam ta tabbata ga duk mutumin da zai iya shimfida yatsunsa akan muhallin da yafi ko ina daraja a jikin dan adam,wani abu yazo ya tsaye mata a wuya,ta saka hannuwanta biyu saman kuncinta,tana tuna wani lokaci can baya daya wuce,tana tuna marukan da tasha saman fuskarta,wanda batasan iya adadinsu ba.

Sauke hannuwanta tayi taja da baya tana barin gaban madubin ganin bacin ran da bataso tana yawan ji yana qoqarin taso mata,sai ta koma gefan gadonta ta zauna tana hadiyeshi,idanunta suka sauka kan ledar siyayyarta data shigo da ita jiya,ta miqa hannu ta janyota,ta fara buda kayan ciki tana sake dubawa,bawai don batasan me ta siya din ba,a'ah tanason kore bacin ran dake taso mata ne.

Sai data shirya kayan cikin walking closet dinta sannan ta fara gyara jikinta,ta shirya kanta cikin wata sassauqar gown fara,alamu suna nuna ita din ma'abociyar son fararen abubuwa ne,musamman kayan zaman gida da qananun abubuwan amfani irin haka. Cikin qasa da awa daya ta sauko qasan riqe da system dinta tana amsa wayar afifa,ta saka system din a chargy,ta leqa ta gayawa maama ta fito wadda ke saman abun sallah zata tayar da salatud duha(sallar walaha),sannan ta nufa kitchen ta samo abinda zata iya ci.

"Barka da fitowa" baba rabi ta fada cikin girmamawa,tadan murmusa kadan,baba rabin ba zata taba daina gaisheta ba

"Ina kwana?"

"Kin tashi lafiya farar d'iya" suna ne da takan kirata dashi lokaci lokaci

"Lafiya qalau,me zan samu?" Fara bude mata abubuwan da suke dashi da safen a kitchen tayi,kusan duka ba cimarta bane,amma batason bawa kowa aiki da safen nan,ita kuma qyuyar aikin yau takeji,don haka sai ta jawo plate ta tsakuri iya abinda take ganin zata iya a plate daya,ta fice zuwa Parlor din.

Tana cin abincin kamar wasan yara ta kunna laptop din nata,gidan gaba daya ya mata shuru ba dadi,afifa bata dawo ba kwata kwata wannan satin,shi yasa takeson yara,bata rabo da dauko 'ya'yan yayyen nata,to wannan karon su fadil suna umra duka gidan,khalifa na exam,aleena tayi qanqanta don ko yayeta ba'ayi ba,ya zaid kuma ya maidasu na'eem canada,cikin satin nan shima zai bisu,dole ta zauna zaman kadaici,idan taji ta matsu da yawa kuma tabi afifa.

Sai data gama duk uzurinta sannan ta shiga ma'ajiyar saqonnin email dinta da nufin share saqonnin da suke kai ko zata ragewa computer din nauyi,har ta fara marking idanunta suka kai kan sabon saqon daya shigo mata daga MT GLOBAL COMPANY,ta dan tsaya tana tunanin inda tasan sunan,kafin daga baya hankalinta yakai kai,takai arrow din kai tayi clicking ta shiga.

Dogon tsaki taja bayan ta gama karanta abinda saqon ya qunsa,and so what don zasu canzata da wata muddin bata shiga aiki ba on Monday,ko an gaya musu aiki da su damuwarta ne?,ko basusan alfarma zatayi musu ba saboda darajar masu daraja?,cikin jin haushi ta soma rubuta musu reply na basu damar sanya watan,cikin ranta tana jin ta samu hanya mafi sauqi ma da zata sabule wannan alaqaqai din aikin,saidai tana kammala rubutawa kafin ta tura taji muryar yaa muhyi yana magana da masu aikin gidan dake harabar gidan,saita dora hannuwanta saman fuskarta tana jin ba dadi,a sanyaye tayi highlight na duka rubutu tayi cutting dinsa,ta goge email din ta sauka daga ciki,tayi shutting down na system din,dai dai lokacin ya sanyo kansa cikin parlor din.

A nutse ta amsa sallamarsa,tayi masa barka da safiya sannan ta miqe ta yiwa maama magana,ta kuma wuce kitchen ta hado masa dan abin motsa baki,ta kawo ta ajjiye masa

"Ya na ganki gida,nayita kiran wayarki kuma bakiyi picking ba,kada dai ace tun ranarki ta farko kin fada wasa da aikinki?" Yaa muhyi ya fada yana kallonta hadi da dan kada key din hannunsa.

Fuskarta ta tattare tayi alamun tausayi ta zauna daga kujerar dake gefansa

"Da ciwon kai na tashi yaa,kuma ma Allah......" Kasa qarasa masa tayi,tadan lanqwasa yatsun hannunsa

"Eheenn,Allah me?" Ya tambayeta kai tsaye yana dubanta bayan yadan tsuke fuskarsa kadan,don bayason jin wani zance sabanin wanda sukayi da ita

"Yaa ko zaka taimakamin su sauyamin position din da suka bani,bana son president din nan wallahi" ta qarashe fada tana narke murya. Ajiyar zuciya yadan sauke yana furzar da iska daga bakinsa sannan ya sake maida dubansa kanta

"Dr yana da matuqar kirki da sanin ya kamata,haka d'an nasa,yana da kamewa da sanin ya kamata,na tabbatar ba zaki taba fuskantar wata matsala wajen yin aiki dasu ba,inda nasan akwai matsalar kema kin sani,bazan karba miki ba,so please accept it,kiyi aiki tuquru,ko don saboda ni" qas tayi da kanta,tanason tilastawa zuciyarta da har yanzu taqi jin nutsuwa aminci wa aikin kan ta karba buqatar dan uwanta,sake gyara zamansa yayi sannan yace

"Shi da kansa Dr yin ya zaba miki position din,ya fimu shekaru da hangen nesa,yana ganin kin cancanta ne,ko abba dana gaya masa baice wani abu ba,kuma koni din nasan you can do it,so please kada kiyi discouraging kanki,you will made it in sha Allah" Shuru tayi tana sauke ajiyar zuciya qasan ranta,bai fahimceta bane,bawai ba zata iya bane,ita sam harkar da duk zai hadata mu'alama da jama'a ne bataso. Ganin ta shiga tunani sau ya katse tunanin nata ta hanyar miqa mata key din mota

"Gashi,gift na fara zuwa aiki,daga ni da kuma Saifullahi" hannu biyu tasa ta karba tana masa godiya,saidai sanda ta duba sunan motar sai da zuciyarta ta tsinke,motace sabuwar qira me kyau ta mata,tana kuma da dan

Please Login or Register in order to submit comment