Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 20 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da yakeson shiga.

Tun daga shirinsa zuwa zaman cin abincinsa da shirin kwanciya baccin da sukayi ta lura kamar kuzarinsa ya ragu,da tayi complain sai yace

"Yau nayi overwork baby,jikina duka ciwo yakemin" tsam ta miqe,ta shiga kitchen ta hada masa ruwa me dumi,daga gefansa ta zauna ta miqa masa mug din

"Ga wannan kasha,yana sauke gajiya" kurba daya yayi ya miqa mata,saita langabe kai tana kallon fuskarsa

"Ai baka sha ba dear" kansa ya girgixa yana dan qaramin murmushi

"Cikina ya cika fa,ko kin manta abinci na gama ci yanzu?,ba space,hakanma is okay,thank you".

A sanyaye ta sauka daga saman gadon,yadan bita da kallo sannan ya gyara zamansa sosai saman gadon yana dubanta

"Yauwa kafin ki fita kiban wancan briefcase din,ki dawo a kitchen din kizo ki gani" miqa masan tayi taje ta ajjiye mug din a kitchen din sannan ta dawo,ta zauna daga gefansa tana kallon takardun daya fito dasu.

Biyu daga ciki ya zaro ya miqa mata,ta karba amma tana masa duban neman qarin bayani

"Wadan nan filayen ne da mukayi zamu siya ni dake,an gama cinikinsu kamar sauran,ga takardun ki saka hannu" a nutse ta karanta rubutun dake jikin takardan,kamar kullum kamar kuma ko wanne lokaci,duk sadda suka siya wata kadara tare dashi,maimakon sunansu su biyun sunanta yake sanyawa,tasha masa qorafin shi da ita duk daya ne,koda sunansa ya saka dinma ai babu laifi.

Motsa bakinta tayi,yasan qorafin data saba zatayi masa,sai ya saki murmushi ya daga mata hannu

"Bazan fasa saka sunanki ba fa,karkiyi ma magana,don na saka sunanki sai meye?,komai dana mallaka naki ne fa,bare ni dake din mun riga mun zama abu daya,saka hannu kawai" ya fada yana miqa mata biro,cikin sanyin jiki tare da jinjina qauna soyayya da kuma fahimtar juna me zurfi dake tsakaninta da adam din ta yi signing da signature dinta,wata irin sign me matuqar kyau da tsari,ta miqa masa takardun tana cewa

"Allah yasa musu albarka.....ina alfahari da irin tunaninka da qoqarinka" ta fada tana jinjina kai,tsarin daya kawo musu naci gaba ita sam bata taba kawowa ranta tayi hakan ba,daga aurensu zuwa yanzu suna da filaye masu suna filaye da suka hada kudi suka siya masu yawan gaske,hakanan zunzurutun kudin dake join account dinsu dake maqare da kudin da suke zubawa duk wata daga cikin albashin kowannensu,wanda dashi suke saka ran amfani da filinsu da yafi kowanne girma su tayar da ginin katafaren kamfani.

Murmushi yayi bayan ya mayar da takardan cikin takardunss,ya sanya hannunsa ya rungumeta tsam cikin jikinsa yana shaqar lallausan qamshinsa

"Ni yafi dacewa nayi wannan godiyar" saita kwantar da kanta saman qirjinsa tana sakin murmushi,zuciyarta fes,cike da zallar farinciki hadi da samun nutsuwa da cikakkiyar gamsuwa da kalar mijin da take da.

***********Tsaye tayi bayan gama wanke mata kan tana goge ruwan kan nata da qaramin towel don dake saman kanta wanda ke dauke da tambarin katafaren gurin gyaran kai da jiki na mata Thairaphy saloon and spa,zare towel din tayi ta ajjiye,afifa dake zaune tana duba wani magazine ta daga kai tana dubanta

"Ya dai"

"Kifi zanje nemowa,nan haka nasan ba za'a rasa ba" ta fada tana maida rolling Vail dinta saman gown din jikinta da hanzari, rufe magazine din afifa tayi tana kallonta

"Amma kinsan ba'a yi gyaran jikin ba ko?,karmu bata lokaci fa"

"Manta kawai,yanzu zan dawo" ta fada tana zaro key din motarta daga jakar,cikin sauri ta nufi qofa

"Bansan qaunar data shiga tsakaninki da kifi ba"

"Nima haka"ta bata amsa a qagauce,sai afifan ta bita da kallo,wani abu ya darsu a ranta, murmushi ya qwace mata tana jinjina kai

"Allah ameen"ta fada tana ci gaba da gyada kai kamar qadangaruwa,kafin muryar daya daga cikin ma'aikatan dake wajen ta katse mata tunani,ta miqe tana zare nata dankwalin,gashinta me cika da tsaho ya bayyana,ma'aikaciyar taja mata kujera ta zauna aka fara gyara mata nata gashin.

Afifa na zaune daga saman kujerar tana karantar yadda saahar kema kifin wani irin ci,zargin dake ranta yana sake tabbatuwa,iya saninta da asaahar bame ciye ciye bace,hasalima ko yunwa zatayi mata meye bata yarda taci abinci a waje, especially idan wajen na jama'a ne kamar haka,tana da wani irin halayya dda dabi'a ta daban data banbanta data koww,batace mata komai ba har sai data gama,ta wanke hannunta da kyau ta sauke ajiyar zuciya hadi da murmushi tana kallon afifa,sai afifan ta tabe baki tana kau da kai

"Wanda yaci shi kadai dai shi kadai zai mutu" murmushi mai sauti ya kufcewa saahar,tasa hannu tana rufe bakinta

"Am sorry bestie,na manta gaba daya,gaskiya ban kyauta ba,but zan fanshi kaina,zan siyo miki wani harfa sai kinci kin ture"

"Banso" ta fada tana jefa mata hararar wasa,cikin zuciyarta cike fal da wani irin farinciki kyakkyawa fata da kuma zato me qarfi akan saahar din.

Awa biyu suka gama abinda sukeyi sukabar wajen suka wuce zoo road gidansu afifa,tun cikin mota ta fara jin jikinta yayi laushi,kasala duka ta rufeta,ga wani yanayi da yake saukar mata kamar zazzabin cikin qashi.

Afifa dake tuqi ta waiwayo ta kalli saahar din

"Anci kifi anyi dam baki ya mutu" ta fada cikin salon tsokana,wannan ya bawa saahar damar muskutawa tana yatsina fuska

"Jikina me a mace kaman fever keson kamani"

"Ya salam......aiko mu qarasa gida nayi miki test na gani,amma me zai hada madam adam da maleria ma?" Fuska ta yatsina tana jin jikinta sosai babu dadi

"Ba wani test fa,kusan last two weeks ina jin hakan,ko aiki ma daurewa kawai nakeyi,nafi zaton maleria din na kwaso,kinsan munje wata ziyara da momee munyi kwana daya" tsaki afifa taja cikin ranta,yadda bata qaunar d'an matar haka uwarma,saidai ba yadda zatayi sun riga sun zama daya a yanzun,tunda suna auren 'yar uwarta kuma aminiyarta tun daga quruciya har zuwa girma,sai bata sake cewa saahar din komai ba,har zuwa sanda suka qaraso gidan.

A harabar gidansu ta tsaida motar,saahar ta rigata fita ta wuce ciki,sai data kashe motar ta kulleta sannan tabi bayanta.

Saman kujerar falo ta sami saahar din a zaune,ummi mahaifiyar afifa tsaye a kanta suna magana,matar data debo dukka kamannin Dr mamman girema,wanda ko ba'a gaya maka ba zaka fuskanci JINI DAYA ne ke yawo a jikinsu,ba zaka kirata da yayarsa ba,saboda shekarun dake kwance a jiki da fuskarta basu kai na dr mamman din ba,don haka zaifi dacewa ka bata matsayi na qanwarsa.

"Ki duba saahar afifa kafin ku shiga shiriritar taku" abinda ummi ta fada kenan tana wucewa kitchen.

Dakin afifan da bashi da maraba dana saahar suka kwasa suka wuce,dukkansu tun kafin auren saahar ba zaka banbance dakin waccar da waccar cikin gidansu ba,kowacce tana iya amfani da dakin 'yar uwarta,ta kuma yi tasarrufi dashi yadda taga dama,har zuwa yanzun da duka dakunan afifa ke amfani dasu,duk da ita dinma ta kusa kaucewa tabar gaban iyayenta,don akwai kudin khalifa idress a kanta,akwai abinda ya kawo tsaikon sanya rana da mahaifin afifa ya roqa a daga masa,yanason kammaluwarsa kafin saka ranar.

Kan yalwataccen gadon afifan saahar ta zube tana fidda iska daga bakinta,tana daga kwancen tana kallon afifa ta gama hada komai da zata buqata sannan ta kalleta

"Taso mu gani" miqewa tayi tana cire dankwalin kanta da takejin ya mata nauyi ta ajjiye a gefe

"Amma da ki fara da yimin allura ta ko?"

"Waime?,allurar planning?" Kai ta gyada mata a kasalance,wani abu mai tauri yazo ya tsayawa afifa a wuya,ta allura ma take ana batun duba lafiyarta?,duk da hakan afifa ta shanye bacin ranta,don tasan zaiyi wuya idan ramin data ginawa adam din baiyi zuruf ya afka ba,don ba zatace ramin data ginawa saahar ba,domin a gareta ba rami bane wannan,abinda tayin dai dai yake da tudun muntsira data ja hannun saahar din ta kaita ba tare da ita kanta ta sani ba

"To madam biyayya vice's qauna,taso na fara duba lafiyarki tukunna,tunda itace gaba da komai" duk da jikinta ba dadi sai data saki qaramin murmushi ta girgiza kai,tabi qaramar robar da afifa ke miqa mata da kallo

"Me zanyi da wannan?"

"Fitsarinki nake buqata" dan kafe afifa tayi da kallo kamar me tunani,sai kuma tasa hannu ta karba ta shige toilet din afifan.


FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥





*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 39


Bata jima ba ta fito da fitsarin,ta miqawa afifan ta koma ta zauna tana lumshe idanunta,tana jin yadda jikinta yake qara zama weak,ita kanta tana mamakin wanann sauyin da bata taba jin irinsa ba.

"Yes!!!!" Afifa ta fada da wani irin madaukakin sauti

"Alhamdulillah Alhamdulillah" ta maye gurbin furucin nata da sauri tana murza tafukan hannayenta waje daya.

Sai a sannan saahar ta bude idanunta a hankali ta zubesu akan afifa dake tsaye tana ta faman buga murmushi,dukka hankalinta da idanunta nakan saahar

"Me wai?" Ta tambayeta a gajarce,sai fuskar afifan ta sake fadada da farinciki,abinda ke nuni da cewa farincikin dake danqare a zuciyarta ba kadan bane a wannan lokacin

"Congratulations mrs adam,congratulations" ido saahar ta fidda tana duban afifa

"Meye a kanki bestie,da ciwon kikemun murna ko kuwa?" Dariya ta saki a nishadance

"Wannan ciwon ai irinsa muka dade muna nema miki,you are pregnant bestie" cak komai ya tsayawa saahar saboda yadda maganar tazo mata a bazata na farko,na biyu kuma yanayin yadda cikin yazo,murna zatayi ko akasin hakan?,duk da tana da tsananin buqatarsa,tana cikin kewa da qishirwar samun yaro a kusa,tana qaunar yara qwarai da gaske har batasan iyaka ba,to amma kuma har yanzu basu cimma plan dinsu da adam ba,hakan na nufin cikin yazo a lokacin da basu shiryama zuwansa ba ko kuwa?.

"Bestie banason wasa,kina magana ne akan rayuwata fa" batace mata komai ba sai dauko strip din datayi mata test din dashi ta ajjiye mata a gabanta,layuka biyu gasunan sun bayyana radau kamar ma sunfi fitowa a jikin nata tsinken fiye da yadda suka saba fitowa,hakan yana nufin cikin ba na satin jiya ko yau bane.

Kanta ta dago jikinta a sanyaye ta kalli afifa

"How comes afifa?"

"Min indillah" ta amsa mata kai tsaye tana goye da hannyenta a qirji,tana qarewa saahar nazari da karantar yadda ta karbi cikin a ranta.

Akwai farinciki shinfide can qasan fuska da zuciyarta,amma ta karanci kamar akwai wani abu mai nauyi dake tasowa yana danne wannan,wanda jikinta yake bata koma meye baya rasa nasaba da adam

"Ciki dama yana iya samuwa ana tsaka da yi maka injection na planning?" Dukka girarta ta daga kafin ta amsa mata

"Yes mana saahar,akwai wanda ya isa halittar Allah wanzuwa aduk sanda yaso?,allura fa just wani qaramin garkuwa ne da bai isa ya hana Allah yin yadda yaga dama da bayinsa a duk sadda yaso ba"

"That's absolutely true" ta furta a hankali tana gyada kai,bata iya sake cewa komai ba saahar din,sai ta samu kanta da cika da farinciki,dukkan wani kwadayinta da son haihuwarta yana dawowa sabo fil cikin ranta,farinciki takeji yana mamayarta irin wanda bata taba tsammanin zata tsinciki kanta a ciki ba,lallai haihuwa ni'ima ce,'ya'ya kuma rahama ce da babu kamarta(Allah ya azurta masu nema da samu,ya bayar dame albarka ya albarkaci diyoyin musulmai gaba daya).


"Ni ya kamata na yiwa mr adam wannan albishir din,ki kwanciyarki,zan prescribing maki wasu magunguna idan yazo zaku wuce sai ya tsaya ya siya miki,don't mind any changes da zakiji a jikinki,you will be alright in sha Allah soon" kai ta gyada tana lumshe idanunta,afifa ta dauki wayar saahar din da zummar kiran adam din yazo ya dauketa,tabar saahar da ido a lumshe,hannunta saman plate tummy dinta tana shafawa a hankali,tunani fal kwanyarta,wai ita din itace zata zama uwa,itace wata halitta yanzun haka ke rayuwa a jikinta,murmushi ya subuce mata,wata qaqqarfar soyayyar abinda duk ke kwance a marar tata ya fara sauka cikin zuciyarta.

Afifa bata sanar da saahar zuwan adam ba,ta sanya an saukeshi a Parlor din baqi na gidan,ta sanya me aikin gidan takai masa ruwa da lemo,sannan ta shiga daki ta zura dogon hijabi ta fito.

Ta iskeshi zaune a falon,cikin shigar qananun kaya,ya cika falon da turarensa,hannunsa riqe da wayarsa yana chart.

Baki afifa ta tabe sannan tayi sallama,ya daga kai yana amsa mata sallamar,fuskarsa kadaran kadaham,haka kawai jininsa bai taba zuwa daya da yarinyar ba ko sau daya,kamar yadda itama nata jinin da nasa bai haduwa sam,kawai dai kowa yana dakewa ne saboda darajar saahar dake a tsakaninsu.

Hannun kujerar dake daura da qofar fita ta zauna tana cewa

"Sannu da zuwa mr adam" zamansa ya gyara,ya maida wayar aljihunsa,ba tare da ya amsa mata ba ya jefa mata tambayar

"Ina baby?"

"Babynka tana ciki,yanzu zata fito....." Sai tadan dakata,ta fidda iska kadan daga bakinta,bayan ta sake canzawa fuskarta yanayi,babu sauran sassaucin data shigo dashi

"Na fara iskeka ne don nayi miki kyakkyawan albishir din cewa ka kusa zama uba,babyn naka na dauke da wani babyn naku......i mean matarka nada juna biyu" ta qarashe maganar tana zube dukka idanunta akan fuskarsa,tana fatan ko yaya ta fusgi wani reaction nasa,wanda shi zai bata kowacce irin dama da takeson samu daga gareshi.

Cak komai ya tsaya a falon tsakaninta da adam din,kafin daga bisani ya sakar mata murmushi yana juya key din motar dake hannunsa

"Ban taba zaton ke mutuniyar kirki bace irin yau,kin iya kawo kyakkyawan albishir,duk da naso na fara jin hakan daga bakin baby...... anyways.....ke da ita duk daya ne,ina taya junanmu murna" ya qarashe maganar yana tsareta shima da nasa kallon.

Murmushi ta saki tana murza hannunta

"Haka ne abinda ya kamata ya fito daga bakin kowanne magidanci na qwarai.....shikenan daga yau allurar planning ta qare,saika maida hankali ga kula da abinda yake cikin nata,yadda kake kula da duk wani kudi da zai shigo ko ya fita ta account dinta,da yadda kake kiyaye lokuttan yin salary dinta da sauran komai nata.....ina fatan yaron da ba'a shirya zuwansa duniya ba..... ubangiji ya qaddari zuwan nasa ta silar innarsa afifa......zai samu kulawa matuqa da qauna hadi da soyayya,kwatankwacin wadda ake iqirarin ana yiwa mamansa......yanzu zan turo maka babyn naka,ku sauka lafiya" daga haka ta miqe tana ficewa daga falon,yayin da adam ya miqe tsaye yana rakata da ido,zuciyarsa na suya sosai.

Ya akayi yarinyar ta rainashi har haka?, waye ya gaya mata sirrin rayuwarsu da yadda suka tsara zasu tafi da ita tsakaninsa da matarsa mallakinsa?,me yarinyar ke nufi akansa?,wanne kallo takeyi masa?,akwai maganganu da yawa da yakeson gaya mata don tasan shi din ba sa'anta bane,to amma kuma ta riga tayi nisa ba ta yadda zai iya amayar mata da dukkan abinda yakeson fada din.

Sosai Zuciyarsa ke quna,ransa yayi matuqar baci da maganganun afifan,a zafafe ya fita a falon,ya bude motarsa ya zauna yana jiran fitowar saahar,ya tabbatar banda saahar na sonshi so na gasken gaske,yayi amannar da tuni afifa ta dade da tarwatsa kyakkyawar mu'amala ta fahimtar juna kyautatawa da girmamawar dake tsakaninsa da ita.

Sallamar saahar din kawai ya iya amsawa,ba tare daya waiwayo ya dubeta ba ya tayar da motar ya figeta suka fice daga gidan,saahar da batasan abinda ke faruwa ba ta bishi da kallo galala cike da mamaki

"Na dauka zaka shiga ka gaida ummi ne ai" ta fadi a sanyaye tana mamakin abinda ya canjashi da matsanancin fushi haka lokaci guda.

Shuru baice mata komai ba,sai mamaki ya sake kamata,ta gaza dannewa saboda bata saba ganin irin wannan yanayin a tare dashi ba

"Dear......lafiya kuwa?,ko wani abu ya faru?" Da wani irin gudu ya gangara gefan titi ya tsaida motar,cikin tsawa da hargagi ya soma magana

"Saboda zallar rainin hankali ma ni kike tambaya lafiya?,bayan kinsan komai?,kinsan abinda ya farun?,ki aiko 'yaruwarki ta cikin mutunci ta wulaqantani,ashe yawo kike dani kina bayar da labarin ina karbar dukiyarki,kina gayawa duniya nidin makwadaici ne?,to ki sani ba abinda zanyi da dukiyarki,ki kuma gayawa wannan banzar 'yar uwarki taki afifa ta fit......."

"Ya isa!!" Ta fada da qarfi zuciyarta na wata irin suya,mamakin adam yana cikata,ta dinga kallonsa sosai waiko zataga wani sign na fara shaye shaye a tare dashi,tunda take dashi ko kallon banza bai taba hadata dashi ba bare tsawa har irin haka ba, zata iya jure komai amma banda zagin afifa,don ita din Wani sashe ce ta jikinta

"Ta yaya zaka zo kana hukuntani akan al'amarin da bansan dashi ba?,har kana qoqarin zagin afifa,afifan da bata nufinmu da komai sai alkhairi?"

"Kedai!,amma banda ni,yadda ta tsaneni nima haka na tsaneta,i hate her with passion,idiot....." Saiya finciki motar da kyau,har saahar nayin gaba zata daki gaban motar ta kare da hannayenta, hankalinta ya tashi sosai,bata saba ganin tashin hankali ba,kamar yadda bata taba ganin bacin rai makamancin haka daga gurin adam ba,duk da tasan yana da fushi amma bai taba kwatanta mata ba.

Kuka ta fashe dashi tana dora kanta saman cinyarta,wanne abu afifa dinta ta yiwa adam da zai dauki irin wannan mugun fushin?. Suna isa gidan yaci burki,ya fita yabarta a motar bayan ya kashe. Da hanzari itama ta fita a motar tabi bayansa,saidai bata cimmasa cikin falo ba,tana niyyar binsa daki da take jiyo motsinsa da qarfi sai gashi ya fito,hannunsa dauke da wani file.





*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 40


Yana daga tsayi ya wurgoshi kusa da ita,abinda ya baiwa dukka takardun ciki damar fitowa suka warwatsu a falon

"Ga komai naki nan,ki duba dukka abinda babu a ciki ki rubuta zan biyaki,sauran abinda mukayi hadaka kuma ki lissafa nawa ne na cire miki naki" ya qarashe maganar cikin fushi. Iya wuya zuciya tazo mata,sai taji ba zata iya jurewa wannan abun nasa ba,bayan batasan me tayi masa ba,ta miqe a fusace karo na farko a tarihin zamansu data taba maida masa magana

"Basai ka fake da abinda afifa tayi maka ba,zaka iya cin mutuncina duk ta yadda kaso adam,na gode" kuka ya qwace mata ta juya da hanzari ta nufi bedroom dinta.

Sautin kukanta bai hanashi wucewa dakinsa ba yana jan mugun tsaki,amma tsakanin awa daya zuwa biyu sai wayarsa tayi qara,ya kalli wayar yaja tsaki,banda me kiran nada muhimmanci a wajensa ba abinda zai sanyashi daga wata waya a yanzu,shi daya yasan iya adadin yadda ransa yake a bace da kuma irin rudanin daya samu kansa a ciki a iya ranar yau,komai yazo masa a bazata,ya miqa hannu ya daga wayar yana maqaleta a kunnensa.

*_BAYAN AWA DAYA_*

Ajjiye wayar yayi,ya shiga toilet dinsa ya fidda kayan jikinsa yayi wanka,ya dawo ya shirya cikin armless riga da boxer dinta,ya feshe kansa da turare sannan ya wuce dakinta.

Yayi mamakin tarar da ita tana kuka har sannan,yayi tsaye a kanta yana kallonta,sai yaji zuciyarsa ta karyo,ya qarasa kusa da ita ya dora hannunsa saman bayanta

"Awa nawa kikayi kina wannan kukan da bashi da amfani?,bayan kinsan bake kadai bace?" Maganar tasa tazo mata a bazata,sai kukan nata ya tsaya cak,yadda yayi maganar juna biyun dake jikinta kadai ya tabbatar mata shima yana maraba dashi,sabanin yadda tayita tunanin da yadda zata fahimtar dashi. Bata gama wannan tunanin ba taji ya sanya hannunsa duka biyun ya dagota ya rungumeta yana fadin

"Am sorry,raina ne a bace" ajiyar zuciya ta saki tana narkewa a qirjinsa,cikin lokaci qalilan komai ya wuce a tsakaninsu kamar komai bai faru ba,kasancewar basu saba samun sabani a tsakaninsu irin haka ba,sai ya bude sabon shafin tattalinta tare da nunawa abinda ke cikinta zallar qauna muraran,wannan ya wanke komai daga zukatansu.

*********Cikin kwanakin da suka biyo baya komai ya koma normal,hankalin saahar ya sake kwanciya sosai da yadda adam ke tattalinta yana nunawa cikin jikinta qauna,har excuse ya nema mata daga wajen aiki saboda laulayin da take fama dashi,laulayi takeyi sosai,yau lafiya gobe babu lafiya,gaba daya hankalin 'yan gidansu yana kanta,tun daga kan abba har ya zaid da take bi,kowa tattalinta da kuma riritata yakeyi,kamar itace zata haifa musu jikan farko. Saidai duk irin riritar da suke nuna mata bata kai rabin wadda adam ke mata ba.


********Zaune take saman couche,ta miqe qafafunta sosai yadda zata sake,chiffon armless short gown ce a jikinta,wanda rashin tsahonta ya bawa sambala sambalan kyawawan qafafunta damar bayyana.

Waya suke da momee,wadda kullum kwanan duniya sai ta kirata tayi mata sannu da jiki,tun abun yana sata jin kunya da nauyi harta fara sabawa,sukayi sallama da ita dai dai sanda adam ke fitowa daga kitchen,hannuwansa duka biyun riqe da mug dake dan fitar da tururi,qamshin kayan qamshi na tashi a ciki.

Tun kafin ya qaraso ta miqe ta zauna sosai,shima ita yake kallo fuskarsa tana fitar da murmushi,ya soma takowa a hankali saita maqale kafada a shagwabe

"Jan rai ko?"

"Yes" ya amsa mata kai tsaye yana dariya qasa qasa. Kunnuwanta ta kama tana dariya kadan kadan

"Na tuba,don Allah a bani nasha" idanu yadan zubata,yadda tayin tayi masifar burgeshi,kyanta kuma ya sake fita muraran,sai yaji jikinsa yadan saki amma kuma ta wani sashen wata zuciyar ta qara masa qaimi tare da karsashi,ya qarasa gabanta yadan russuna ya miqa mata cup din

"Thanks dear" ta furta da sassanyar muryarta bayan ta saka dukka hannuwanta guda biyun ta karbi mug din cikin zallar kwadayin shan tea din,ta sanya bakinta ta kurba,saita lumshe ido tana sakin murmushi saboda dadin da ya ratsa ta sosai

"Na yarda yau kadai.....ka fini iya hada black tea" murmushi ya sakar mata ba tare da yace komai ba,ba kuma tare da ya dauke kallonsa daga kan fuskarta ba,ta sake kai cup din bakinta ta sake sipping,dai dai lokacin da qaramar wayarsa dake kan wani dan teburin gilashi tare da babbar wayarsa dake charge ta dauki qara,ya qarasa a hankali,ya zareta daga charging ya karata a kunnensa idanunsa har yanzu akan fuskar saahar

"Yanzu?....kamar dai gobe...... alright on my way" ya fada a hankali,saiya cire wayar daga kunnensa ya tako inda saahar take.

Rusunawa yayi yayi kissing goshinta

"Ayimin afwa baby,fita ce ta kamani yanzu,just one hour zanyi zuwan da dawowar...... I hope ba damuwa?" Kai ta jinjina masa tana lumshe kyawawan fararen idanunta

"Babu dear" ciki ya wuce,ba jimawa ya fito,ya canza kaya zuwa qananun kaya,sai zabga qamshi yakeyi,ya mata kyau sosai,ya sunkuya ya sake kissing dinta,har ya wuce ta kira sunansa

"Kayi kyau da yawa,Allah yasa ba zance zaka je ba" ta fada tana langabar da kai. Dariya sosai ya

Please Login or Register in order to submit comment