Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 13 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Lokaci kadan tama manta da daddyn nata dake tsaye,hira suke abinsu,kamar ba daga wata qasa maji din ke kira ba,bata jin katinta sam da take yawan qonawa akan fadeela.

Sun jima kafin daga bisani suyi sallama,ta kawo masa wayar,fuskarta qunshe da murmushi

"Daddy,wai a ina maji take?" Ta jefa masa tambayar da baiyi zaton jinta daga bakinta ba

"Bata a nan qasar angel"

"Tana ina?" Ta sake tambayarsa,da alamar da gaske tanason jin a inda take din

"Algeria"

"Yaushe zamuje daddy?,tanason ta ganni nima inason na ganta" ta tambayeshi a shagwabe. Ido ya zuba mata sosai,shi kansa a yanzu bazai iya kai kasa kai tsaye inda maji take ba,tun haihuwarsa har girmansa bai taba zuwa,a baya yana da kwadayin zuwan,amma a yanzun kwata kwata babu wannan cikin ransa,baisan kuma yaushe hakan ta faru ba,kawai dai ya tashi ne dare daya yaji yayi loosing interest akan dukkan abinda ya shafeta,kafin daga bisani kuma ya yakan yawaita samun mantuwa akan komai daga danganceta.

"Zamuje angel"

"Daddy yaushe?" Ta sake tambayarsa tana kafeshi da idanu,idanunsa ya janye daga kanta,murmushi kadan yana subuce masa,ya fuskanci rigima takeji

"Wata rana" ya bata amsa yana sanya hannuwansa ya dauketa cak hadi da cewa

"Muje muci dinner" zata sake magana ya dora yatsansa akan lips dinsa gami da cewa

"Shshshsh,ya isa" duk da qanqantarta amma tana gudun abinda zai bata masa rai,tana matuqar jin maganarsa fiye da tunani,saita kwantar da kanta a kafadarsa,a haka suka qarasa dining room din.

Sallamar cook din nasa dake jiran ya iso yayi serving nashi yayi,da kansa ya zuba musu iya abinda zasu iya ci shi da fadeelan yabar sauran.

*********Karfe daya na rana ne,lokacin da kowanne ma'aikaci dake qarqashin company din yake morewa lokuttansa na break. Dai dai lokacin da sãahar a cikin nata office din ta duqufa wajen ganin ta gama hada dukka bayanan data samu daga financial team na company,tana duba yiwuwar yin magana akan document dinta dake office na CEO,batason tayi aikin banza,tanaso ta aiwatar da dukka tsare tsaren da tayi,don ta tabbatar zai kawo gagarumin ci gaba da kuma sauyi cikin company din.

Buda qofar da akayi ya sakata daga fararen idanunta tana kallon bakin qofar,mr sameera ce,ta bata izinin qarasowa bayan ta janye hannuwanta daga kan system din

"Ranki ya dade,sir hamza ne ya sake dawowa" idanunta da suka dan daure saboda kallon allon system din tadan juya kadan,qaramin tsaki taja,hamzan yanason shiga rayuwarta,kaf fadin company din a yanzu bata da wata matsala saishi,yaqi fahimtar inda tasa gaba,gaba daya sake shige mata yakeyi a kowanne lokaci,don kawai office dinta yana da alaqa da department dinsa,don ko yanzu report din da take dubawa daga office dinsa ya fito,banda haka da tuni ta yanke dukkan wata alaqa da zaya bashi damar ganinta

"Ki gaya masa ba yanzu ba,aiki nakeyi,ya tura kowanne saqo ta email din office,zan duba sanda na zama available" jinjina kai sameera tayi,ta juya ta fice.

Cak ta tsaya da aikin da takeyi tana sake jan wani dogon tsakin da yafi na farko,saita tura kujerarta baya tana dan fidda iska daga bakinta,da alama wani tunani ne ya darsu a ranta lokaci daya. Yatsunta tasa tana murza goshinta dasu,tana tuna shigowarta company a safiyar dazu,yadda ta tadda employee a dan hautsine,sakamakon korar wasu ma'aikatan guda uku da ceo yayi a safiyar

"wanne irin mutum ne shi?,me izza da dagawa?,he doesn't give excuse to anyone?,abu kadan kora?,kowa ma yana iya kora ko yayi masa fada?" Tayi maganar can qasan zuciyarta,haushinsa da kuma tsanarsa suna huda zuciyar tata,abinda ta lura dashi ma,gaba daya yafi zafafa al'amuransa akan mata. Sake jan wani dogon tsakin tayi karo na uku,gaba daya tuna abin da ya farun yasa tayo loosing interest akan aikin,ta duba baqin agogon dake daure a tsintsaye hannunta qirar kamfanin Casio,akwai ragowar mintuna talatin kafin lokacin komawa bakin aiki yayi,coffe take da buqata,amma batason takura mr sameera,don haka ta tsugunna a hankali ta daura igiyoyin baqon takalaminta daya mugun haska farar qafarta me dauke da dogayen yatsu,ta miqe a nutse ta dauki iya wayarta ta fita a office din.

A nutse take takawa a farfajiyar gurin,cikin girmamawa ma'aikatan ke gaidata,saboda Suna respecting nata sosai,duk wanda yayi mu'alama da ita kuma kusan sai ya fadi halinta ya kuma yi mata shaida me kyau.

Ko kusa ko alama bata ga koda inuwarsa ba,saijin maganarsa tayi a bayanta

"Ranki ya dade,barka sa fitowa" mr hamza kenan,wanda ke biye da takunta yana son ya cimmata cikin zumudin da katarin ganin fitowarta da yayi. Kadan ta waiwaya ta aje masa kallo daya

"Ya kake?" Ta fada a daqile,hamza na daya daga cikin mutanen dakeson zame mata barazana cikin company din,tare da yi mata kutse cikin walwalarta da al'amuranta,duk wani hanya da zatayi avoiding nasa tayi,amma ta karanci kamar baya fahimta,da alama yana sahun mazan dake da shegen naci da kafiya ne

"Lafiya amma ba qalau ba,please ki taimaka ki gayawa secretary dinki,ta daina min shamaki da ganinki,wallahi it really hurts me" sunzo bakin qofar kitchen din,kuma bata da buqatar yaci gaba da binta,don haka ta dakata,ta juyo gaba daya tana dubansa

"Excuse me mr hamza.....ko zaka taimaka ka juya,saboda banason ka shigarmin lokacin nawa hutun,na gaya maka idan maganar office ce ka tura ta email zan duba,idan kuma bata office bane, please i beg you,banason wani abu da bashi ya taramu a nan ba ya hadani da kai,bama kai ba,koma waye bana buqatar wata hulda ko alaqa" da hanzari ya buda baki zai maida mata da martani,amma sai taji yayi dif,batasan dalilin daukewar wutarsa haka lokaci guda ba,amma koma meye sanadi ita ba damuwarta bane,don dama tafi buqatar shirunsa akan amsarsa,don haka ta juya ta shige kitchen din kanta tsaye.

Wayam din data gani a kitchen din babu kowa da kuma qarancin haskensa bai sanya ta zaci akwai wani abu ba,saboda wannan shine karon farko data taba shigowa kitchen din. Coffe dama kadai tazo nema,don haka ta nufi mini coffee maker din data gani a jone,data duba sai taga akwai saura a ciki,don haka ta ciri mug guda daya,ta cikashi dashi,yawunta yana tsinkewa,saboda wani qamshi da taji yanayi na musamman,uwa uba kuma kana kallonsa zakasan ya hadu iya kwadayinka da shan coffee.

Dan qaramin murmushi ta sauke,saita gyata tsaiwarta tana kai mug din bakinta,dai dai sanda ta juyo. Babu zato ta saki mug din,cikin razana taja baya,fararen idanunta suna sake girma hadi da fitowa waje. Tsoratar da tayi yasa bata iya tsaiwa ta tantance waye ba tayi qofar waje da sassarfa,saidai kuma tana dab da isa ya rigata isa gurin,ya saka hannu ya tura qofar ya rufeta bam,taja birki a mugun hautsine tana sauke dubanta a kansa,sai a lokacinne ta gane waye.

MT jarma ne da kansa,cikin shigar suit dinsa ta ko yaushe,saidai kuma a yau din babu suit jacket din a jikinsa,alamu suna nuna ya barota a office,hannun rigar ciki da ya kasance dogo ya tattareshi ya barshi iya gwiwar hannunsa,wannan ya bawa murdadden hannunsa dake cike da gargasa da wasu irin jijiyoyin da yawan shiga gym ya haifar dasu. Kwantacciyar sumarsa me santsi a dan hargitse take kadan,lips dinsa sundan sake yin jaa saboda zazzafan coffee din da yake sipping a hankali.

Ko a yanzun ma da yake tsaye ci gaba yayi da sipping abinsa cikin nutsuwarsa da kamewarsa,kamar bashi ya tsorata ta ba,sanann yasa hannu ya garqame musu qofa haka kawai ana zaune qalau. Ranta ne taji yayi mummunan baci,tadan motsa fuskarta kadan saboda yadda zafin coffee din data saki ya dan taba qafarta yake mata zafi kadan kadan,wannan wacce irin dabi'a ce zai samu guri ya zauna a kitchen,a corner din da ba lallai kai ka iya ganinsa ba?,saita janye idanunta ta taka zuwa qofar don ta bude ta fice,don bata qaunar hada rufi daya dashi bare taci gaba da zuqar qamshin turarenta da yake neman sanyaya dukkan wani zafi data dauka akan abinda yayin.

Table din dake daura dashi ya matsa kadan ya dora cup din,cikin zuzzurfar muryarsa dake cakude da wani irin amo me ya soma magana

"You must learn saying salam a duk wajen da zaki shiga,saboda nan din mudai musulmai sunfi yawa......sannan bari na taimakeki na tuna miki wani abu daya,nan masana'anta ce,kayi aiki a biyaka da gwargwadon wahalarka na wata daya,ba waje bane da aka bude saboda soyayya ba,saboda haka ki kiyayi bawa wani damar ganinki a office da kebantacciyar buqatarku wadda bata da alaqa da company,idan ba haka ba,you will loose your job" ya qarasa maganar yana dora hannunsa a mariqin qofar,ya budeta sannan yace

"Dont try to do this again......inda kin fita a yadda kikaso fita,wani ya ganki me kike tunani zai zata" bai jira amsarta ba ya taka zai fita, zuciyarta tazo mata iya wuya sosai. Yama gama raina mata hankali,yaso qona mata qafafuwa,sannan kuma ya bita da wasu sharuddansa marasa amfani a gurinta,tunda dai ai ita ba yarinya bace,tasan meye ya dace da ita. Ji tayi idan ya fita ba tare datace masa komai ba tabbas yaci bulus,duk da zuicyarta na qoqarin tuna mata maganganun yaa Saifullahi da yaa zaid na ta girmamashi,gaba yake da ita

"Shi kuma wannan kullemu da kayi fa?,idan wanin ya gani yace me?" Ta fada tana jin takaicin yadda tayi dogon zama a guri daya dashi,harta shaqi turarensa da kyau,ya shiga kowacce kafa ta hanci da kwanyarta.

Waiwayowa yayi ya zube mata manyan kewayayyun idanun nasa dake da wani irin magnet da kwarjini,har sai dataji kamar zata zube,yayo taku biyu ya dawo baya kadan

"Kina iya gayawa duk wanda ya tambayeki..... nayi raping naki ne,don wanann din kadanne daga aikinku".

"Ya salam" ta fada can qasan zuciyarta hade da wani mugun bugawa da zuciyar tata tayi,ba kuma tare data shirya ba ta koma da baya ta zauna saman kujerar dake kusa da ita,wanda tayi yaqinin banda taimakon Allah kujerar tana kusa da ita lallai zata iya faduwa qasa. Kamar baice komai ba ya juya a nutsensa ya fita a kitchen din.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥
[8/17, 6:49 PM] +234 806 578 4295: *H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 25

Wasu hawaye masu zafi taji sun cika mata idanu,qarshen cin zarafi yayi mata shi,FYADE ai ba qanqanuwar kalma bace da furtata zai zama abu me sauqi har haka ba,kadan daga aikinsu me yake nufi kenan da ita?,kawai saita kasa riqe hawayenta,ta barsu suka silalo ko zata samu ganin gabanta da kyau,tun bayan abinda adam yayi mata.....ba wani mahaluqin daya taba mata kalma me tsananin daci zafi da qasqantarwa irin haka ba,sai ta miqe kawai a gaggauce tana fita a kitchen din,har ranta tana jin tsanar shi kansa kitchen din,da kuma dalilin daya kawota.

Tana fitowa a hanya suka hadu da sameera,ta tareta da yanayi ya dan rudani kadan

"Ance kitchen kika tafi,inata qoqarin tsaidaki saboda time ne na shigan sir kitchen din yayi lunch,karkije a samu matsala"

"Ba'a samu ba,gashi na dawo" ta bawa sameera amsa a taqaice tana wuceta.

Toilet dinta ta fada tana sake rage qwallar takaicinsa data sake taruwar mata,sai data kusan minti goma kafin tayi controlling kanta,ta daura alwala ta fito ta tayar da sallah,tana sake jin tsanarsa qwarai a ranta,tana kuma sake tabbatarwa da kanta shi din wani irin mutum ne mara iya mu'amala da gautsin harshe.

Ko bayan ta idar zamanta taci gaba dayi saman abun sallar,duk da akwai sauran ayyukan da takeson gamasu a yau din,a haka miss sameera ta nemi izinin shigowa.

"Boss ne yake neman izinin ganinki" tunda tace boss ta gama fahimtar waye,abun sai ya girmame mata,dr Ahmed da kansa yafi qarfin neman izini wai don zai shigo office dinta,da sauri ta tashi saman abun sallar tana dubanta

"Yafi qarfin neman izini miss sameera,maza bude masa qofa" saita juya a gaggauce tana murmushi,tabbas sãhaar din batasan waye boss ba,da batayi mamaki ba don ya nemi izinin shigowa ba.

Cike da tarin haiba kwarjini da kuma kamalarsa yayi sallama,saita miqe tsaye tana masa sannu da zuwa tare da nuna masa gurin zama,da kanta ta bude qawataccen fridge din dake office din ta ciro masa ruwa da lemo masu matsakaitan sanyi,kasancewar ita dinma ba mai yawan shan abu me sanyi bace

"Na gode sosai diyata" ya fada yana yaba dattakonta,da yadda take da girmama manya tare da sanin kimarsu. Ita kunyar godiyar ne ya kamata,tana neman gurin zama yace da ita

"Ya ayyukan?,ina fatan kina jin dadin aiki da yayan naki?" Qaramin murmushi ta kuma saki,kanta a qasa tace

"Alhamdulillah abba"

"Ma sha Allah,na sanshi sarai,wasu lokutan bashi da kirki,yana da zafin zuciya,amma kuma yana da tausayi" kai ta jinjina tana kokwanton tausayin da Dr yace toufeeq yana dashi.

Ruwa kadan yasha,sanann suka fara tattaunawa kan sabbin ci gaban da aka samu cikin company din,daga bisani yace

"Sajjad ya gayamin,akwai kundin da kika bayar,ya gamsu da ayyukan ciki,ya kuma yimin bayani,amma har yanzu banga an aiwatar da komai ba"

"Tuni na miqa su ga office din ceo muna jiran sign dinsa"

"Kina da copy dinsa a gurinki?" Miqewa tayi a nutse,ta buda computer ta kawo masa gabansa. A nutse ya dinga karanta komai,

"Ma sha Allah,ma sha Allah" kawai bakinsa yake furtawa,baiko kai ga qarasawa ba ya dago kai

"Akwai ideas masu kyau da muhimmanci a nan,zaifi kyau a saka hannun da wuri,inaji a jikina za'a samu cimma gaci yadda akeso" sosai taji dadin yadda ya yaba mata din,har ta rakashi yana mata addu'a gami da sanya mata albarka.

Lokacin tashi yana cika ta baro office dinta,kai tsaye ta sauka zuwa qasa,tana daga cikin sahun farko na ma'aikatan da suka baro office dinsu,don haka gurin ba cikowar masu daukan ababen hawansu. Hakan dama takeso,tayi ta fice kafin wancan mayataccen ya isketa,sam baya yin fushi ko kuma zuciya game da dukkan abinda zata gaya masa.

Sau uku tana qoqarin kunna motar amma taqi kawo wuta gaba daya,abun ya bata mamaki ya kuma daure mata kai,tunda dai tasan lafiya lafiya ta tafi ta barta. Ta gwada dukkan wata dabara amma taqi,dole ta fito ta rufe motar,ta fidda wayarta tana gwada kiran mechanic dinsu,tana masa bayanin abinda ya faru,tare da kwatanta masa kamfanin,kamfanin ba wani boyayye bane,don haka yace yana zuwa nan da minti arba'in zuwa awa daya.

Sauya akalar kiran nata tayi zuwa ga number afifa,bugu biyu ta daga

"Bestie,kin tashi daga aiki ne?"

"A'ah,sai sixs,wani abu ne?" Lumshe idanunta tayi cikin damuwa

"Motana yaqi tashi,baisan meye damuwarta ba,kuma banason fita neman abun hawa na haya"

"Subhanallahi,to ba damuwa,bari zan iso kamar nan da awa daya saina daukeki,kinga na rage time din tashin kada ya zamana na fito da wuri"

"Okay,thanks" ta fada tana tsinke kiran. Da isowar mechanic din dana afifa tana sanya ran yayi lokaci daya,ta dubi agogon hannunta sannan ta sauke tana duban building din,ma'aikata sunata fitowa kowa yana kama gabansa,batason komawa can saman nan,don haka ta yanke ta wuce executive garden dake kamfanin ta zauna ta jirasu a can,da wannan shawarar ta karkata akalarta zuwa can din.

A nutse ta durfafi gurin,yanayin wajen yana sake burgeta,da alama yana samun kyakkyawar kulawa. Sanya qafafunta kenan sautin muryarsa shine abu na farko daya fara ziyartar kunnenta,kafin daga bisani idanunta su sauka a kansa,dai dai lokacin da shima dan motsin da yaji ya sakashi daga kai,idanunsu suka sarqe waje daya,yana daga tsaye hannunsa guda daya cikin aljihunsa yana magana da wasu mutum biyu da bata gane ko su waye ba,saboda suna dan gaba kadan dashi.

Qaramin tsakin da batasan meye dalilin yinsa ba ta saki,kawai dai tasan taji haushin ganinsa a wajen,ya kuma bata mata budget din da tayi na sakewa ta zauna a wajen ta jirayi afifa,saita juya a nutse tana fita a wajen.

Dif maganar da yakeyi ta dauke,ya lumshe idanunsa a nutse yana jin wani irin bacin rai na taso masa,idan har dai dai kunnuwansa suka jiye masa,sautin tsaki ya jiyo,wanda yaga alamun fitarsa daga dan qaramin bakinta data turoshi gaba lokacin da take hada sautukan tsakin.

Ransa ne yaji yayi wani mugun baci,tunda yake zai iya cewa ba wata diya mace data taba masa tsaki,tsakinma mara dalili,haka siddan saboda ganin araharsa?,nan take yaji bazai iya tolerating ba,don ya gama fahimtar kamar tana daukan kanta wani abu,tana da ji da kanta over.

Sam basu lura da barin wajen yakeyi ba har sai da yakai qofar fita,cikin daga murya sajjad yace

"Hi man......ya kamata mu gama kafin mu wuce fa"

"One minute" kawai ya iya ce masa,idanunsa na biye da ita,duk da cewa ta danyi masa nisa kadan. Sai ya qara yawan takunsa,mutum ne ingarma me yawan kuzari,ga kuma tsaho da yake dashi,wannan ya taimaka masa nan da nan ya rage tazarar dake tsakaninsu,wanda sam bata sani ba,ta yanke shawarar ta buda office dinta kawai ta zauna ta jirayesu acan,ko hawa na nawa ne ta gwammace ta koma ta jirasu,akan dai ta sake ganin fuskarsa.

Hankali kwance elevator ta bude mata ta shige,tana shirin komawa ta rufe shima ya shigo,ta koma ruf ta rufe sannan ta fara aikin haurawa dasu zuwa saman.

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k

*Al'ummar NIJER ku kira wannan number don yin naku pyment din*

+22799643131

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥






*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔

Page 26


Haka kawai taji gabanta yayi mummunar faduwa,kowanne sashe na jikinta yayi sanyi saboda yadda ya zuba mata mayatattun idanunsa,yana jifanta da kallon tsana. Tayi tunanin zata iya jurewa kallonsa kamar yadda ya ritsata da nasa idanun,amma tun ba'a yi nisan zango ba taji ta gaza dauke nauyin zagayyun idanunsan nan masu tsananin haske,kamar ba idanun namiji ba. Gaba daya sai ta jita kamar wadda aka nannade aka jefa cikin wani keji,kamar an sanya igiya an daureta,ta dinga fatan na'urar ta sauketa da inda ta umarceta tayi ta fice ta bashi guri.

Saidai kuma suna isa floor din ya matsa gurin madannan ya sake bata direction na dawowa dasu floor din qasa,a sannan ta waiwayo ta sake dubansa da fararen idanunta karo na biyu,still har yanzu ita yake kalla,kallon dake sake bayyana fushin dake kwance a zuciyarsa. Sake janye idanun nata tayi ta maida dubanta wani wajen,gaba daya kallon da yake mata ya wuce qa'idar da jarumtarta zata iya dauka,uwa uba kuma shirin rikicewa takeyi gaba daya,saboda yadda qamshinsa yake sake cika elevator din. Tattara hankalinta tayi tana jiran jin sun isa,ta riga ta gama ayyanawa a ranta suna isa zatayi hanzarin ficewa,don ta fuskanci kamar ya shirya tayita yawo dasu daga sama zuwa qasa,can can qasan ranta tana tuna tsakin data sakar masa.

Da wani irin hanzari ta nufi qofar da zummar fita,amma kuma kafin ta isa har ya maida qofar ya rufe,ya kuma sake sakata ta lula sama dasu. Wannan karon tsaiwa tayi daga bakin qofar yana lumshe idonta,ranta itama ya soma baci da rainin hankalinsa,ta yaya zayazo ya sameta a waje ya kuma dinga mata wasa hankali?,na meye?,zata tsaya gab da qofa,zataga gudun ruwansa,idan ta fita yasa qarin tuwo ya dawo da ita.

Duk yadda taci buri kuwa suna isa sai gashi tsaye bakin qofar,abun yayi matuqar bata mamaki,batasan wanne irin zafin nama gareshi ba

"Excuse me mana,fita zanyi" ta fada da siririyar lallausar muryarta

"Wa kika yiwa tsaki?" Ya jefe mata tambayar kansa tsaye cikin izza da qasaitarsa kamar wani basarake,duk da yadda yayi mata matuqar kwarjini,amma motsawar tata izzar ta bata qwarin gwiwar amsashi

"Da wanda ya tsargu" ta amsa masa tana qoqarin kaucewa qwayar idanunsa,don har yanzu tana cike da takaicin abinda yayi mata dazu a kitchen.

"Ko?" Ya fadi wani miskilin murmushin gefen baki na subuce masa,duk da cewa ba murmushi bane na kyautatawa ko jin dadi,amma wani irin sirrin taccen kyau ya bayyana muraran kan fuskarsa,fuskarta yake duba,yanason gano daga inda ta samo wannan qwarin gwiwar tsaiwa ta gwada masa rashin kunya,yayi imanin batasan wane shi ba,amma a yadda ya lura akwai quruciya sosai tattare da ita,qaramin abu kawai zaiyi da zai bata zazzafan warning,ta yadda ba zata sake marmarin maida masa martanin magana ba.

Bata taba kawowa ba ko kusa ko alama,kamar a mafarki taji an take dogayen yatsunta da qarfi,sosai zafi ya ziyarceta,ya kuma ratsata tun daga saman qafarta zuwa qwaqwalwarta

"Wayyo Allah na" ta fada a jigace

"Wa kika yiwa tsaki nace?" Ya sake maimaita mata tambayar wannan karon da wani irin zafin rai,har hakan na bayyana kan fuskarsa

"Sa'anki ne ni?" Ya kuma jefa mata tambayar,duk da bata samu damar amsa masa tambayar farko ba

"Ko don kinga Dr ya baki damarmaki da yawa kike tunanin kanmu daya dake?" Ya kuma fadi a mugun tsawace,sautin tsawar tasa tana ratsa mata kunne

"Bakizan tsaki zagi bane a gurin wanda ya girmeka?" Still dai ya tambayeta yana kallon fuskarta,wadda zufa ta fara wanke goshinta dake lullube da wasu irin gashi masu matuqar santsi

"Lemme warn you......daga yau,duk randa kika kuskura kika qara yimin tsaki ko......." Sai ya murza yatsunsa akan fuskarta

"Bazan koreki ba,bare kisa Dr yaga baqina,amma sai na ɓarka bakin tsakin,ki zama me d'a'a ga wanda yake sama dake" yana qarasa fada ya dage mata qafar,ya kuma kauce ya bata hanya yana jira ta fita.

A wahalce ta tashi daga tsugunnawar da tayi,hawaye sun jiqa mata fuska,wannan shine qarshen cin zarafi da tozarcin da zaiyi mata,ba tare data kalleshi ba ta juya ta fita daga elevator din tana jan qafarta da tayi mata nauyi.

Floor din qasa ya sanyata ta maidashi,yana tsaye yana kallon yadda take sauka qasa dashi,sai furzar da iska yake daga bakinsa,yana son ya fifita zuciyarsa daga zafin data dauka. A wajensa wannan din zallar raini ne,ba abinda ya tsana a duniya sama da tsaki,tsakinma a rasa daga gurin wanda zai fito sai mace?,macenma yarinya qarama wadda ya girmewa da shekaru masu dan dama,kuma ma ma'aikaciyarsu dake qarqashinsu,wanda kaf rayuwarsa ba yarinyar data taba masa irin hakan,kawai don ta samu dama daga gurin Dr,ko don tana ganin tana da kyau?, abinda ya gani dazu tsakaninta da hamza ya fado masa a rai,ya dunqule hannu ya kaiwa iska naushi,yana jin tsanar mata na nikuwa a ransa. Ya tsani mata totally, especially masu kyau irin haka,tabbas koda yaushe basu rabuwa da shaidan,babu wani alkhairi sam a tattare dasu sai tarin sharri,bazai bar mr hamza yaci gaba da barar musu da mutunci ba. Har ya saka

Please Login or Register in order to submit comment