Reading TABARMAR KASHI 1&2 complete by SAFIYYA HUGUMA Chapter 22 | TKNovels


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yakai munzalin magidanci kamar adam,saidai wannan ko daya bai kashe wutar dake ruruwa cikin zuciyarta ba.

"Na roqeki kiyimin alfarma ki yafemin,kiyi haquri kiyimin dukka kalar hukuncin da kikaga dama,amma karki nesanceni,kada ki gujemin,ina mai hadaki da girman Allah......ki yafemin,na miki alqawari ba zaki sake samuna da wani laifi kwatankwacin wannan ba,sharrin zuciya da na shaidan ne,duk sanda kika sake kamani da laifi mai shigen wanan bama wannan din ba,na amince na kuma lamunce miki kiyimin dukka irin hukuncin da kikaga dama" duk yadda taso ya sakar mata hannu ya barta da abinda takeji a zuciyarta amma yaqi bata wannan damar,yaci gaba da amfani da baiwar iya sarrafa kalamai da yake da ita,ya dinga zaftare tsananin fushi da bacin ran da suka kafa sansani mai girma da qarfi a zuciyarta,har sai da yayi nasarar ture kaso mai girma daga cikinsa

"Ka sakarmin hannu.......har yanzu bansan makomar zamana ni dakai ba...."

"Har sai yaushe saahar?,me kikeso nayi miki wanda zai wanke wannan mummunan laifin da na aikata?"

"Sai nayi tunani" ta fada kanta tsaye. Da gaske tana buqatar nutsuwa,tana buqatar tayi tunani me kyau,tana buqatar su zauna ita dashi su tattauna,tana kuma da buqatar lalubar daga inda matsalar take. Lamarin babban abun tashin hankali ne daga gurin diya mace,ba kowa ke iya jurewa ta fuskanci irin wannan babban qalubalen ba.

Ya qyaletan kamar yadda taso,ba kuma wai ya qyaleta bane dukka yadda ta buqata,yayi kane kane tsakanin dakinta da nasa,wunin ranar gaba daya bai zauna guri daya ba,dukka hidimar gidan ya dauka ya aza a wuyansa,dukka wani abu da saahar din keda buqata shi ya dinga yi mata,duk da bata buqaci komai daga wajensa ba,daga bisani da taga bashi da niyyar bata space kamar yadda ta buqata,sai ta murza key ta rufe dakin.

Tayi kuka tayi kuka har taji babu dadi,tayi addu'a da dukkan iyawarta da nau'ikan addu'o'in data sani,ta nema ubangiji ya shiga lamarinta ya kuma bata juriya,taji ta muzanta da yawa ta kuma qasqanta,ta kalli kanta a madubi har sau babu adadi,tanason zaqulo abinda ta rasa,tanason zaqulo inda ta gaza,tana kuma son gano wanne GURBI ne da bata cikewa adam ba har ya tsinciki kansa cikin irin wannan qazamin sahun?. Saidai a dukka hasashe da dogon nazarin da tayi,bata tsinkayi abu daya da ta kasa cikawa adam ba.

Babu wanda yasan halin da take ciki,babu kuma wanda tayi niyyar gayawa koda afifa kuwa,tanaji har cikin zuciyarta ba zata iya tonawa adam asiri ba,sun fara hawa matakin fara samun zuri'a,ko taqi ko taso,a yau ko kuma gobe ana iya kiransa da uban 'ya'yanta,shike da matsala ita ke zaune dashi,su tattauna a tsakaninsu su kamo bakin zaren tare tana ganin shine hanyar da zasu samu mafita.

Tun washegarin ranar data dawo momee ta bata aron rahina a cewarta har sai jikinta ya warware tunda ita din bata da ra'ayin me aiki,yarinyar itake komai na gidan tamkar saahar ba a kwance take ba,ita din bata iya hassala komai,daga kwanciya sai kwanciya,damuwa ta farmaketa ta cimmata a lokacin da bata taba hasashen wata matsala ko damuwa cikin rayuwarta ba,tana ganin komai nata ya cika cif cif,gibi guda daya daya ragema rayuwarta na rashin haihuwa shima ya cikashe!,ashe qalubalen yana gaba!.

Sati guda bata ko yarda sun sake hada hanya da adam ba,har sai zuwa ranar data gamsu a karan kanta lokaci yayi daya kamata ta fuskanceshi da dukka tarin tambayoyi da tuhume tuhumenta. Ranar tun da safe bayan ya fita itama ta fito ta qwarara jikinta,rahina nata murnar ganin fitowar saahar din,kusan wunin ranar tare sukayi komai da ita,har zuwa magrib inda saahar ta wuce dakinta.

Qarfe takwas da wani abu na dare tana gaban madubi tana daure dogon gashinta mai santsi da baya rabo da gyara adam ya turo qofar dakin ya shigo,idanu suka hada saita janye nata idanun ta maida kan mudubin,yayin da shi kuma ya kafeta da kallonsa cike da kewarta,jikinsa fes da alama tun daxun ya shigo,yayi wanka ya canza kayansa cikin wasu qananun kaya da suka amsheshi qwarai.

Hannunsa ya cire daga aljihunsa,yaji bazai iya ci gaba da jurewa shariyarta ba,ya tako zuwa inda take,ya tsaya dab da bayanta yana kallon kyakkyawar fuskarta ta madubin,ta sake haske,fuskarta tayi fayau.

Jikinta ta zame daga wajen,ya bita da kallo,ya motsa bakinsa zaiyi magana,ta rigashi ta hanyar masa nuni da wajen zama,sannan itama ta koma daga gefan gadonta ta zauna.

Dukka idanunta ta zuba masa,wani bacin rai yana motsawa daga qasan zuciyarta zuwa saman fuskarta,idan tace ta taba jin tashin hankali mai gauraye da bacin rai irin wannan tayi qarya,tayi namijin qoqari qwarai,ta tattare dukkan abinda ke taso matan,ta jefa masa tambayar data dade tana son amayar da ita,ko zata samu sauqin radadin dake yankar naman zuciyarta kowanne dare zuwa rana

"Yaushe ka fara neman mata adam?" A hargitse ya kalleta,don tambayar ta dakeshi qwarai,yanayin fuskarsa ta sauya yayi wani mugun laushi

"Idan kikace neman mata.....kina nufin zina fa kenan?" Kai ta jinjina kai masa

"Qwarai kuwa,domin abinda idanuwa suka karanto kenan,qwaqwalwata kuma ta fahimta"

"Subhanallah,wa'iyazubillah" ya fada fuskarsa na nuna girman yadda furucin yayi masa radadi a zuciya,tsahon wasu sakanni sannan ya iya daga kai ya dubeta

"Ba neman mata nakeyi ba,duk da tarayyar da mukeyi akwai sabon Allah a ciki,tunda zataga tsiraici na zanga nata..... Ta rudeni watanni uku baya da suka shude,banda ita na rantse da Allah ban taba neman kowa ba,ban taba tarayya da kowacce mace ba,kuma tun daga ranar ban sake kulata ba,ban sake bi ta kanta ba"

"Ta ina na gaza maka adam?,ko akwai wani waje da na gaza maka daka rufeni ka kasa gayamin?" Kai ya girgiza da sauri

"Ke din ta kowacce fuska kin kerewa kowacce mace,idan nace kowacce mace.....ina nufin nau'in kowacce mace daga kowanne jinsi da yare na duniya ni a wajena" wayarsa dake aljihunsa ya ciro,ya kuma fidda layukansa gaba daya ya lanqwashesu suka karye,sannan ya qarasa gabanta ya ajjiye mata wayar

"Idan kinso daga yau ni adam na ajjiye wayatama gaba daya sai sanda kika lamunce min,kiyi haquri ki yafemin,kici gaba da zama dani,sannan ki lullube sirrina,na miki alqawari saahar,muddin na sauya ko naci amana,na yarda amanar Allah ta cini nima" kalmarsa ta qarshe tayi masifar yi mata nauyin da har sai data tilasta mata rufe idanuwanta,amanar Allah ta cishi?,lallai da gaske yake mata,ba shakka ya canza ya kuma shiryu da gasken gaske.

Ta dauki wannan kalmar ta azata bisa babban ma'auni,ta bata matsayi me girma,irin matsayin daya zarta ta qiyasceshi,a nata dabi'ar da kuma kyakkyawar tarbiyyar data samu,girman ubangiji ya wuce wani dan adam yayi wasa dashi,ko ya fake a bayansa ya aiwatar da dukka abinda son zuciya da qaawar duniya zai sawwarawa mutum. Ta dauki wannan kalmar a matsayin madogara,ta fifitata ta karbi nadamar adam,cikin sati guda ta fara qoqarin daidaita kanta tare da daidaita dukka lamuranta,ta dinga kokawa da kanta da yaqi da kanta tana son komawa ainihin saahar,tare da qoqarin maida komai a tsakaninsu ya koma bisa mizanin daidaito.

Cikin lokaci qalilan ya sake canza mata,ya zame mata tamkar bawa dake qarqashin ikon uban gidansa,sai abinda tace shi zai aiwatar,sai abinda ta zaba,ya ninka dukka kyautatawa da kuma soyayyar da yake nuna mata,kulawa da tattali marasa misali,cikin wata guda kacal ya mantar da ita komai,ya kuma sake amintar da ita,ya nisanci dukka abinda zai kawo zargi da kokwanto a tsakaninsu shi da ita. Rayuwa taci gaba da tafiya sannu a hankali,wannan amincin.....wannan yardar.....wannan hadakar da wannan gamayyar dake a tsakaninsu tana ci gaba da wanzuwa.

*_WASA FARIN GIRKI_*😭





*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 43


*_WASA FARIN GIRKI_*


Totally adam ya sauya mata,ya sake zama wani me mugun sanyi tare da takatsantsan da damuwarta da duk wani buqata tata,a tsakiyar wannnan,watanni biyar da rasa wancan cikin wani cikin ya sake samuwa. A wannan karonma itama hankalinta baikai kai ba,tana dai yawan jin jikinta babu dadi sam,adam ne ya fara ganowa,ya kuma kaita asibiti da kansa don tabbatarwa. Irin girman farincikin data gani a idanu da fuskarsa ya ninka nata ya shanye,harda qwallarsa,ya rasa inda zai sakata. Lokacin da take gayawa afifa cikin murnar yadda adam ya karbi cikin,haka kawai jikinta ya sanyaya,amma ta hadiye abunta,cikin farinciki ta taya sãahar din murna. Komai adam ya hanata yi a gidan,shike komai,yayi hidimarta yayi tasa,ya kuma shirya ya fita aiki,bashi ma da wani cikakken lokacin kansa,ya dawo dakinta gaba daya ya tare,yabar nasa bedroom din,sai kuma ya fara bata tausayi,tayi qoqarin komawa dai dai itama,tare da sake saisaita tsarin gidanta,saidai duk da haka bai fasa yi mata hidima ba.

*******K'arfe sha daya na safe ta fito daga wanka,daure da babban towel daya rufe jikinta sosai,tana a tsaye gaban madubi tana ware gashinta daya jiqe don busar dashi da hand drayer,tana ware gashin tana kallon fuskarta,tayi fresh sosai ta kuma fara dan cikowa. Cikinta ya shiga wata na uku har ya fara nisa,wannan ya sanya ta fara samun sauqin laulaye laulayen da take fama dashi,taji jiki iya jin jiki,ta gasu,don kusan yafi cikinta na baya bata wahala.

A nutse aka turo qofar dakin nata,ta maida dubanta ga qofar,adam ne ke shigowa da innocent face din nan nashi,yana sanye da shirt turtle neck me dogon hannu da trouser dinta data zauna masa a jiki sosai tayi masa kyau,idanunsa akan sãahar,yana jifanta da wani iri kallo dake cike da tarin soyayya,kamar zai cinyeta.

Har ya iso ya ajjiye madaidaicin tray din hannunsa idanunsa na a kanta,sai daya daidaita zaman tray din saman madubin sannan ya sanya hannuwansa ya jawota jikinsa yana dora kansa a gefan kafadarta

"Qara kyau kike kullum my heart" dan qaramin murmushi ta saki

"Shine kaketa wani kallo na kamar zaka cinyeni?" Ta fada shagwabe sosai,sai ya saki dariya me qaramin sauti

"Bakisan matsayinki bane a zuciyata,da ba zakiyi mamakin irin kallon da nake miki ba" shuru tayi tana jin saukar numfashinsa a wuyanta,kowacce rana sake jinjina soyayyarta dake ninkuwa a zuciyar adam takeyi,a duk sanda kuma ta tuna da incident dinsu na watannin baya sai taji tana sake gayawa kanta tabbas sharrin shaidanne da kowacce irin zuciya bata iya tsallake masa idan yazo da qaddara.

Dan janye jikinta tayi daga gareshi jin shurun nasa yayi yawa,ta waiwayo tana duban fuskarsa,damuwar da take hanga tun jiya ta sake ganinta muraran kwance saman fuskarsa,duk sai taji babu dadi,don ta tabbatar inda shine da tuni ya sakata a gaba da tambaya,har sai yaji menene?,ya kuma tayata sun magance abun koda da shawara ne

"Damuwa naketa gani fa a fuskarka" murmushi ya sake saki yana girgiza kai,tare da saka hannu ya maida gashinta dake son tsole mata ido baya

"Ba wani damuwa fa,kawai sauyin yanayi ne" fuska tadan bata

"Amma ko da ban cika mace ba,mata na rako duniya,almost three years amma ace na kasa gane damuwa a fuskar mijina?, c'mon,tell me kawai,ba'a boyewa abokin kuka mutuwa" ajiyar zuciya ya saki me nauyi dake alamta lallai akwai damuwar sosai a ransa,ya koma gefan gado ya zauna yana goye da hannayensa,idanunsan nan dake cike da wani irin kallo a kanta,sannan ya fara magana

"Momee ce......" Sai yayi shuru yana duban wani gurin

"Uhmmm,me tayi momee din?" Kansa ya girgixa sannan cikin damuwa yaci gaba da magana

"Wai lallai saina canza mota motar da take hawa,jarinta kuma yayi qasa,saboda ta tana kudinta sosai wanna zuwan da tayi Ghana,tana buqatar wasu kudi ta dora jarinta" qaramin murmushi sãahar ta saki,duk da taji maganar wani iri,saboda motar momee din ba wani dadewa tayi ba,hasalima tata ce adam din yake hawa,momee ta nuna sha'awarta,sãahar din tace yabar mata,gif ne ya Saifullahi ya bata. Bataji komai ba,don iyakar kirki matar tana dashi,hakanan soyayyar da take nuna mata ko adam data haifa baya samun ire irenta ma,bata qaunar bacin ranta ko dis!. Uwa uba kuma ita din tana comparing momee da maama dinta,ta tabbatar yadda adam yake sonta yake kuma girmama iyayenta......ba shakka zai iya yiwa abba da maama komai muddin yana da dama

"To meye abun damuwa a ciki dear?,uwa ce fa?,ko ranka tana ce kana so ba zaka iya cirewa ka bata ba?" Kai ya girgiza da sauri

"No heart.....ba haka bane,kinsan a yanzu babu agenda na taba kudaden dake hannuna....infact ma ni banason taba abinda yake ba mallakina bane ni kadai" ido tadan fidda tana kallonsa,sai kuma ta bata fuska tayi kicin kicin

"Kanason gayamin momee bata haifeni ba,kai kadaine danta" dariya sosai ya saki

"Nidai bance ba,kawai dai banason taba kudin ya kawo delay wajen cikar burinmu,inason kafin babymu ya iso duniya,yazo ya samu mahaifinsa wanda yake tsaye saman qafafunsa,sai raɓi inuwa ko alfarmar kowa ba" ya qarashe maganar bayan ya iso gabanta,ya dora hannunsa plate tummy dinta da har yau yake mamaki da kuma tantamar tabbatuwar samuwarsa.

K'awataccen murmushi ta saki,ta dora nata hannun saman nasa,wannan ya bashi damar dago fuskarta yana kalla

"An soso miki inda yake miki qaiqayi ko?,na lura kafuwar kamfanin ma bata dameki ba kamar yadda kika damu da zuwan babyn nan" kai ta jinjina

"Allah ya jarabceni da son yara,inajin ranar dana haihu bazan iya bacci ba,har ina rayawa a raina,wannan tsananin son yaran kada ya zama tawa jarrabawar kenan,na mutu ban haihu ba"

"Komai lokaci ne,gashi yanzu yana hanya?"

"In sha Allah" ta fada tana jin wani farinciki yana lullubeta,ta jarabtu da son wannan cikin fiye da cikinta na baya.

Zame jikinta tayi daga nasa,ta matsa zuwa side bed drawer dinta,ta budeta,sannan ta jawo safe dinta,ta ciro wani bangul guda biyu me kyan gaske daketa daukar ido,ta qaraso wajen adam dake tsaye daga bayanta, hannayensa cikin aljihun wandonsa yana kallonta. Miqa masa tayi

"Abun hannun nan yana da matuqar muhimmanci a wajena,amma duk muhimmancinsa baikai na miji na gari irinka ba,na amince ka siyar dashi,ka siyawa momee duk abinda takeso,idan da saura a zuba a kudaden da suka rage mana na gininmu,koda foundation a fara sakawa na ginin" baya yaja yana zare idanu

"What?, a'ah,ba za'a yi haka dani ba,Allah ya sawwaqe"ya fada yana yarfar da hannu,fuska ta bata tana kallonsa,sai shima ya tsaya ya zuba mata ido yana kallon yadda rashin jin dadi ya ratsa har cikin zuicyarta

"Ni ba kyauta na baka ba,ka rubuta idan komai na kamfani ya kammala zaka biyani" dariya ya saki sosai

"Matata me wayo,to godiya nake" ya fada yasa hannu biyu ya karba yana juya abun hannun,wanda ya tabbatar idan aka kaishi kasuwa kudade ne masu nauyi za'a karba. Ya sani yayi kuma imani sãahar ta dabance ko cikin mata,tana cikin sahun mutanen da idan suka soka qaramin abu bai sanyawa su gujeka,zasu iya sadaukar maka da dukkan farincikinsu muddin zasu samu soyayya da kulawa daga gareka,hakanan idan suka qika,zaiyi wuya wani abu yasa su soka.

Da hannunsa ya dinga bata breakfast din har taci ta qoshi,ya tattare plates din zai fita dasu yana cewa

"Bari na watsa ruwa,inason zan dan fita,sai naga waya kamata ya siya banguls din" miqewa tayi a nutse tana daure lallausan gashinta da wani qaramin scarf kalar english wears din jikinta

"Yaukam ko ladan hada maka ruwan wanka ka barni na samu please" ta fada a shagwabe,kai ya girgiza

"Indai nine na yafe" tsaiwa tayi tana dubansa,kamar me tuna wani abu

"Amma,yau kusan two weeks kana hanani shiga dakinka,why?" Ta fada tana bata fuska, murmushi ya sakar mata,ya kama kumatunta yaja

"Banason kiyi dukkan wani aiki bare ki wahala,idan kika shiga da zummar hadamin ruwan wanka,zakice zakimin gyaran daki ne,don dakin yayi qazanta da yawa,abinda ni kuma bana so kenan" kanta ta kawar gefe cikin nuna tata rigimar

"Wannan gatan yayi yawa,ba'a kaina aka fara samun ciki ba,gidanmu cike yake da 'yan aikin da idan na buqata za'a kawomin,amma banason,saboda me?,aure nazo bautar Allah,ba zaman jin dadi da baiwa zuciya da rayuka abinda sukeso ba,ina fatan samun dacewa" ta qarasa maganar tana zube idanunta a kansa.

Kai ya jinjina,shi kansa shaida ne,gata kyau ko wani matsayi na rayuwa bai sanyata ta dakaki kanta a gidan aurenta ba

"Shikenan,let's go" ya fadi yana bata hanya,saita miqe tana harararshi

"Da ladan kakemin buqulu?"

"Ban isa ba" ya fada yana daga hannu sama alamun surrender.

Koda suka shiga dakin bataga wani datti me yawa da yake magana a kai ba,ta hada masa ruwan yayi wankan a gurguje ya fito ya shirya,tana zaune daga gefan gadonsa suna hira har ya kammala,sannan suka fito tare,sai taga yana saka key yana kulle dakin,abinda ya maidashi dabi'a kenan a kwanakin,to amma da yake tana da nata bedroom din,kuma ba wani abu take ajjiyewa cikin dakin ba,sai bata taba damuwa ba,yayi kissing nata lightly a forehead dinta sannan ya wuce.

Ba abinda zatayi,yau ko aiki ba zata fita ba,don haka tayi zamanta a Parlor,ta kunna kallo,jita jifa tana taba chart a wayarta.

Sallar azahar ce kadai ta tasheta,tayi sallar ta duba fridge ta dauko fresh samosa da adam din ya mata order ya cika mata fridge dashi wai saboda yunwar dare,ta soyata,ta hado da hollandia me sanyi ta dawo ta zauna.

Tana tsaka daci kiran afifa ya shigo wayarta

"Uwar biyu" ta fada cikin salon tsokana

"Allah yasa,tabbas da kin samu kyautar kujerar umra daga adam" zuciyar afifa daga can ta tsinke,batasan wanne suna zata bawa adam ba,har yanzu zuciyarta bata taba nutsuwa da komai na adam ba,ta rasa me yasa?,duk da cewa ya bada dalilai masu yawa da yaci ace kowa ya gamsu ya kuma aminta dashi,amma ta nata bangaren hakan ya gaza samuwa

"Allah yasa" ta amsawa sãahar din

"Kudaden nan sunzo ko?" Kai ta girgiza tana sipping madarar

"A'ah,anya?,banga alert ba"

"Haba?,amma tun jiya da dare fa,kuma sunyi debiting dina,receipt din na manta banyi generating ba"

"Karki damu,zan duba balance,nasan sunzo ma"

"A'ah,duba dai yanzu ki gayamin,amana ce ya zaid ya bani kuma kafin na gaya masa na saka sai nayi confirming ya shiga Account dinki" qaramin murmushin dake qara mata kyau tayi

"Bestie koni kika siyar kikaci kudin kinci halak"

"Na sani,amma yanzun ki duba tukunna" ta fada tana katse kiran,ta ajiye wayar a gefe tana jiran kiran sãahar,akwai abinda takeson takai sãahar din gashi,addu'a kuma take takai gano.

Tana murmushi ta soma checking balance dinsu ta USSD CODE,tayi na farko yayi cancelling,ta sake gwadawa har sau uku yana cancelling,tayi duk wami qoqari na checking din amma yaqi yiwuwa,abinka dame ciki,haka kawai abun ya zafafeta,sai ta soma trying number wani ma'aikacin banking da suke ajiyar.

Sanda ta gama masa bayanin cewa yayi

"It seems like anyi disconnecting duk wani details naki daga Account din,to amma kuma ina doubting,saboda indai za'a yi hakan saida saninki da yardarki,anyway,gobe zan shiga bankin,zan duba miki komai in sha Allah" godiya tayi masa ta sauke wayar,duk da cewa wani bangare na zuciyarta cike yake da mamaki,amma wani sashen kuma cikin tantama yake,kanta ya kulle dason gane gaskiya da kuma meye dai dai?,ganin zata batawa kanta lokaci saita ajiye komai,don bata da tabbacin gaskiyar ko rashinta akan duk abinda zuciyarta zata raya mata,taci gaba da cin samosa dinta.

Takai plates din kitchen kenan ta fito taji ana knocking,ta fasa zaman da tayi niyya,ta isa qofar falon ta budeta.

Mamaki ne sosai ya kamata ganin raihanatu,don tsahon aurensu da adam batajin yarinyar tazo gidan yakai sau uku,duk da yadda takeson yarinyar saboda hankali da nutsuwarta,da kuma yadda take girmamata.










*H U G U M A*

*_TABARMAR ƘASHI_*💔
https://arewabooks.com/u/huguma

Page 44


Ta taba yiwa momee din complain akan hakan,tabe baki tayi

"Na rabaki da wannan,wannan me baqin halin,sumumu kasau" murmushi ta danyi kadan,can qasan zuciyarta cike da mamaki,bata taba ganin wani abu na rashin kyautawa raihanatu tayi ba,duk tsahon zuwanta gidan kullum cikin hidima takewa momee,bata tana tsallake umarninta,tausayi da nutsuwarta yake qarawa sãahar qaunarta,wannan ya sanya koda kayan bayarwa zata fitar,raihanan take baiwa,ko yanzu kayan jikinta na sãahar dinne,don ba kasafai momee ke mata dinki ba,takance tana yi mata, yarinyar ce kamar ba mace ba,batason kwalliya bata sawa, sãahar dai bata taba ganinta cikin qazanta ba,ko yaushe fess take da tsaftatattun kaya.

"Shigo ciki mana" sãahar ta fada ganin wani abu me kama da tsoro a fuskar raihana dake tsaye daga bakin qofa,hannunta dauke da ledar dake nuna aikenta momee tayi ta biyo nan,sau biyu tana waigawa tana kallon bayanta kafin ta fado falon.

A qasa ta zauna, sãahar ta tasheta tace ta koma saman kujera

"Ya gida yasu momee?" Ta fara tambayarta ganin har yanzu batace komai ba tana nufar qofar kitchen,hannunta taji an riqo,saita juyo,fuskarta ta sauka akan raihanatu. K'walla ta gani cike fal da idanun nata,yanayinta ya sake sauyawa qwarai,kowanne lokaci zata iya sakin kuka

"Ki zauna anty don Allah,magana nakeson zamuyi,gida nakeson komawa da sauri,kada momee ta fahimci na biya wani gurin" kai ta jinjina,saita dawo da baya ta zauna dab da raihanatu ta zuba mata ido,jikinta yayi wani mugun sanyi da kuma mutuwa,wanda batasan dalilin hakan ba,sai taji gabanta yana faduwa kadan kadan lokacin da taga raihana ta sad da kanta qasa,qwalla tana diga.

Tsahon zamanta da yarinyar bata taba zama irin haka da ita ba,zuciyarta ta shiga fargaba da taraddadi,kafin tace wani abu raihanatu cikin rawar murya ta fara magana

"Kafin rasuwar mamana ta gayamin duniya a yanzu cike take da mutane azzalumai,marasa amana,marasa kuma saka alkhairi da alkhairi,na sake tabbatarwa a yanzu akan yayar mahaifiyata,na kuma sake tabbatarwa a yanzu a zamanki da yaya adam da momee. Bazan taba nutsuwa ba,bazan taba samun kwanciyar hankali ba idan har na bari akayo miki wannan zaluncin,bayan kunnuwa na sunji amma na gagara gaya miki" sai tayi shuru hawayen naci gaba da zuba tana hadiyar zuciya

"Na baro yaya adam a gida yanzu suna shirya yadda zasu qarasa murqushe dukiyarki" ta tsaya da zancan tana kallon sãahar. Ido sosai sãahar din ta zuba mata,maganar tana neman matsugunni a kunnuwanta sannan ta isa ga kwanyarta,tsahon wasu sakanni sannan ta danyi murmushi tace

"Ba murqushewa zaiyi ba ba raihanatu,nina dauka da kaina na bashi,ba bangula guda biyu ba?" Kai ta girgiza alamun a'ah

"Duk wata dukiya dake hannunki da wadda take hannunsa,bama wannan ba anty.....kinsan yaa adam yana da wata matar bayan ke?" Wani irin mugun hautsinawa kanta yayi,mararta kuma ta damqe guri guda kamar curarren alkaki,amai ya taso masa me bala'in zafi tare da tashin hankalin daya daki zuciyarta,saita miqe da mugun gudu ta nufi kitchen wanda shine yafi kusa da ita.

Sosai ta dinga kwarara amai,har sai dan samosa da madarar da tasha babu jimawa suka fice gaba daya,a sannan raihanatu tana tsaye a bayanta tanayi mata sannu cikin tashin hankali,a wahalce sãahar ta gama kuskure bakinta tana maida numfashi ta juyo tana duban raihanatu data gama tsurewa gaba daya,zuciyarta kuma ta fara shiga tsoro da nadamar abinda yasa ta gaya mata wannan babban sirrin

"Kiyi haquri anty,ban gaya miki don na daga hankalinki ba,na gaya miki ne saboda kina da kirki,ke din mutuniyar arziqi ce,barin wasu mutane masu mummunar zuciya su cutar daku babban zunubi ne" hannu ta dora a

Please Login or Register in order to submit comment