Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sai da ido ya dawo kan ta, cikin qasa da murya ta ce, "Wai me ya sa My Jubeir ka qi gane me nake fada maka, i am just 16, gidannan ba a barin mu fita zance, ko su Yesmeen ba su zance ballantana ni,dan Allah ka koma in ba so ka ke wani ya gan ka ba a raba mu," Nan da nan ta tuna hoton da ya tura mata tabbas a unguwar su ya ke da gaske. "Ba mai gani na Aarce in dai ba ke ce za ki sanar ba, na tabbata ba mai gani na, a yanda kk fada gidan ku ya na a cike, kuma ina hamgo gate a bude za ki iya fita na ga fuskar ki kawai ki koma" "Jubeir..." "Ya isa Aarce, ba sai kin fito ba, tunda ba ki son gani na" "Ba haka bane, kawai, ina tsoron kar Yah Noor ya kama ni a waje ne" "Sai anjima Aarce na koma gida, zan qirga daya zuwa biyar in baki fito ba ba zaki sake gani na ba har abada, na maki wannan alqawarin" Cikin tashin hankali da jin tsoron rasa masoyin ta ta miqe da sauri, ta ja dan siririn mayafin ta ta rufe qirjin ta, cikin sanda ta bar gidan, ta na waige waige tare da sake gwada layin Jubeir dan sanar da shi gata ta fito, sai da ta qaraci ringing bai daga ba, wani irin kuka ne mai cin rai da maqaqi a wuya ya tokare ta,ba ta son yin shi amma, shin da gaske Jubeir zai iya rabuwa da ita har abada saboda bata fita ya gan ta ba? Inaaa ba za ta iya rayuwa ba shi ba. Tafiya take cikin unguwar da haske bai gama wadatar ta ba, Jubeir na zaune saman motar shi ya na kallon ta, cike da shauqi ya ke kallon ta, a bangaren ta kuwa saurin duba hoton da ya tura mata ta yi a wayar ta, nan ta gano inda ya ke,wajen ta nufa a sukwane, ta yi daf da isa wajen da Jubeir yake ta na maida kwallar dake barazanar saukar mata, motar Noor ta shiga layin, tare da haske ta da fitilun motar shi, ba tare da ta san waye a cikin motar ba ta ke qoqarin kaucewa ta qarasa wajen Jubeir, Jubeir kuwa da ya yi ma Noor farin sani, tuni ya janye motar shi ya bar wajen. Noor gani ya yi ta na kuka ta na waige waige, ba ma ta kula da shi ba, dan haka fita ya yi ya sha gaban ta, tare da kama hannayen ta dika biyun, ba zato ba tsammani, Noor ya ji ta kwanta a jikin shi, cikin fashewa da matsanancin kuka ta furta, "Jubeir, da ban gan ka ba yau mutuwa zan yi" Wani irin abu ne mai quna da zafi ya daki zuciyar Noor, cikin wani irin yanayi mai tsananin tashin hankali, tare da jin zafin yanda dikkan jikin ta ke jijjiga sabod kuka akan wani,ya dago ta da qarfi. Su na had'a ido, cikin dan hasken farin watan da bai cika haske ba, sai hasken fitulun gidajen da ke wajen, wanda ba wani haske ne sosai da zai sa ka ga mutum sosai ba, sai dai za ka iya gane shi indai ka san shi sosai, suka qura ma juna ido. Ji ta yi qafafun ta ba za su iya daukan ta ba tsabar shiga damuwa, cikin in ina da damuwa tare da tsoro ta ke magana, ta na qoqarin ja baya, ta ce. "Yyyahh Nnooor" Shiru ya yi bai amsa ba,hannun ta ya ja ya bude motar shi ya wurga ta ciki, ya ja tare da yin baya ya bar unguwar gaba daya, sai kuka take ta na bashi hakuri, tare da fadin ta tuba ba zata sake ba, ya yafe mata za ta dinga jin maganar shi daga yau, ko alamar ma ya na jin ta Noor bai nuna ba balle ta sanya ran zai kula ta. Bai tsayaa ko ina ba sai a jikin wani kango da ba bu kowa motoci ma daga nesa mutum ke iya hango su, cikin zafin nama da zaquwa Noor ya kalli saitin inda Aaseeyah take ta rizgar kukan tsoro, hannun ta ya ja da qarfi ta fada qirjin shi, cikin muryar shi mai amo da rawa ya ce, "Shiiiiiii, ba na son kukan nan ki min shiru, ko kin ji na ce zan maki wani abu?" Cikin sauri ta ke kada kai alamar ah ah, "To ki min shiru," Shiru ta yi, amma hawaye na zuba a idon ta, ita kan ta ba zata ce ga dalilin su ba, shin disappointment ne na rashin ganin Jubeir? Ko kuwa tsoron Yah Noor ya ji ta ambaci sunan masoyin ta da take boyewa ne? Ko kuma kukan tsoron irin hukuncin da za a mata ne? Ta na tsaka da wannan tunanin ta ji saukar hannun shi a kuncin ta,ya na share mata hawayen ta, cikin wani irin salon sa ya sanya tsigar jikin ta miqewa, a hankali ta dora kuncin ta akan tafin hannun shi, tare da lumshe idanun ta, ganin haka Noor ya fara kusanta fuskr shi da ta ta, kafin ta bude ido ya hada fuskokin su waje daya, cikin zaro ido d yunqurin kwacewa Aaseeyah ta kai hannun ta saman qirjin shi ta na tura shi, daga baya ta daina qoqarin tura shi baya ta miqa wuya ga saqon da Yah Noor din ke aikawa jikin ta. Bai bar su sun numfasa ba sai da ya ji numfashi ya ma huhun shi kadan, sannan ya sake ta, da sauri suke shaqar iska, tare da lumshe idanun su, dukkan nin su ba wanda ya yi magana, a hankali Aaseeyah ta bude ido ta sauke a kan agogon da ke cikin motar, 11:04pm shi ne abinda ta gani, cikin wata iriyar murya mai rauni ta ce, "Yah Noorrrr,sha dayahh yanzuu" Sake rintse ido ya yi, dan jin yanda amon muryar ta ke tashi, in bai bar wajen da ita ba, wataqila zai aikata abinda zai zo ya na dana sani, dan haka da bai ce komai ba ya tada motar suka nufi wani dan wajen mai saida naman tsire, wajen qarami ne, ba wani babba bane, amma dake ya saba siyan namn wajen ya san dad'in shi, sai ya tsaya ya sai musu da yawa, yanda wasu ma za su iya ci, sannan ya koma motar ya miqa mata ledar suka fara tafiya zuwa gida. Kanta ya toshe kwarai da abinda ya faru a tsakanin su, domin a iya sanin ta, shi din ustaz ne, bai taba taba jikin ta da wata manufa ba , to me ye ya faru a tsakanin su kenan dazu? Shi fa ya ke hana ta tarayya da wasu mazan me zai sa shi aikata abinda ya yi dazun?(Yaro yaro ne, har wanka yi yake sabo da ke Aaseeyah, amma wala hakilo, baki gane ba). "Aaseeyah tunanin abinda ya faru dazu ki ke?" Kamar ba za ta yi magana ba, can qasan maqoshin ta ta amsa da, "Ehhhh" Wani numfashi ya sauke tare da dan lunshe ido, "Aaseeyah na maki abinda kk fito yi da wani dan iska ne, saboda ba na son ki sake wa kowa jikin ki ya lalata ki, qarshe ya gudu ya barki" "Yah ni fa ba abinda zan yi da Jubeir ba kenan, kawai ya na son ya ganni ne, kuma ya ce in ya qirga biyar ban fita ba ba zan sake ganin shi ba, kuma ga shi yanzu ya tafiiii" Wani irin kuka ta sake mai cin rai, wanda take ji kamar da gaske ba zata sake ganin masoyin nata ba,cikin tsawa tare da take birki Noor ya ce, "Keep shut stupid,ki na da hankali kuwa? Nawa ki ke Aaseeyah da ki ke kuka akan namiji kamar haka? Wai shin yaushe ma kka fara son wani d'an iska haka ban sani ba,wa ya baki damar fara son wani, ke wa ma ya baki damar kula wani?" Shiru ta yi ba tare da ta amsa shi ba; kuka kawai take, "Ba magana nake miki ba?" "Yah ka yi hakuri ba zan sake ba" Jin yanda take matsanancin kuka ne ya sa shi sassauta muryar shi tare da ci gaba da tuqin da yake, ya ce, "Ki daina min kukan nan ba na so, and magana ta ta qarshe da ke akan yaron nan, kar na sake ji ko na ga kin kula shi, zan saka maku ido fiye da da, na ji labari ko kallo kun yi ma juna da sunan kallon so zaki ga yanda zan babballaki, kuma na sanar ma da su Abee irin soyayyar da ku ke ke da shi,ba dai kin fita dan ya je ya lala ta ki ba, to zan sanar da su mammee komai" Habaa ta na jin sunan iyayen ta fa ta rikice, hakuri kan hakuri ta dinga bashi ya na kaucewa,daf sun kusan isa gida ya ce, "Na ji na hakura, ki share hawayen ki, sannan ki daina kukan nan, and act normal," "Yah na gode, inshaa Allahu na hakura da Jubeir har abada" "Thats my baby sis," Hannu ya sa guda daya ya riqe nata, tare da murzawa, sai da ta saki ajiyar zuciya saboda yanda wani abu ya ratsa jikin ta, horn ya yi aka bude masa gate ya shige, da damar wanda suke zaune a tsakar gidan sun ragu, wasu sun shiga bacci, wasu na nan ana hira, ana tabe taben juna, wasu kuma hira suke tsakani da Allah ba wani algus. Motocin mahaifan su maza suka gani alamar sun dawo, kusan a tare suka fita, hannun ta dauke da ledar nama, Noor kashe motar ya yi ya bi bayan ta zuwa saman tavarma inda su Umaimah suke, Umaimah na ganin su tare zuciyar ta ta quntata wanda har ta kasa boyewa cikin fushi ta tashi ta............. Pls Read Understand Comment. 💅🏻 TAUBASHI (COUSINS) 💅🏻 BY HAERMEEBRAERH Page 7: ......Ta shige cikin gida, Noor na ganin yana yin ta ya yi qoqarin bin ta,amma bai cimmata ba ta fada d'aki. Aaseeyah kuwa ba ma ta san me ke faruwa ba, ajiye ledar hannun ta tayi ta musu sai da safe ta shiga gida, ta so a ce dakin ta ita daya ce a yau, ta na buqatar kadaicewa dan tai tunani akan abinda ya faru dazun, amma inaa dakin sun kai su hudu 'yan mata, da dama sun girme ta sosai ma, dan haka bathroom ta shiga ta jingina da sink tare da daddafe kowanne gefe da hannayen ta, lumshe idanun ta tayi tare da daga fuskar ta ta na kallon sama, duk abinda ya faru ne ke sake gilmawa ta cikin idanun ta, me hakan ke nufi? Yah Noor da ma dan iska ne? Ashe zai iya mantawa da cewa ita d'in qanwar shi ce ya aikata abinda ya mata dazun? Shi fa masanin qur'ani ne, masanin addini ne sosai, anya ba laifin ta bane? Tabbas laifin ta ne ita ta jawo, ai ya fada mata, ya mata abinda ta fita yi ne da Jubeir, ashe dai in mace ta fita da saurayi abinda ake yi kenan? Ji ta yi kanta na mata ciwo sosai sabo da tunanin da ta zurfafa a ciki, juyawa ta yi ta kunna tap din da ke sink din, ta watsa ruwa a fuskar ta, a hankali ta bude idon ta ta kalli kan ta tare da kai hannun ta lips din ta, wani qayataccen murmushi ta saki, tare da rufe fuskar ta dan jin kunyar ganin annuri akan fuskarta sakamakon tunawa da Yah Noor. Da sauri ta fita ta samu waje ta kwanta bayan ta saka wayar ta a caji, a hankali suke hira har daga baya bacci ya dauke su. An samu tabbaci daga sarkin Musulmi an ga watan qaramar sallah, dan haka safiyar ranar ta kama ranar sallah kenan, kowa ka gani a gidan cike ya ke da farin ciki, mutanen gidan kowa ya kasu kashi kashi, wasu na ta aniyar wanka dan shirin masallaci, wasu na can na aikin abinci, musamman suyar masa, yin miyar masa, da dai sauran abincin na gargajiya da na zamani, wasu kuwa na qoqarin gyara gidan, sai 'yan zaman banza masu hira, ana aiki ba su sanya hannu, sai surutu. Umaimah da Aaseeyah na daga cikin 'yan zaman banza a daki, bangaren Aaseeyah hankalin ta kwance ta ke chatting da Yah Mahboob, inda ta ke damun shi akan yanzu fa ta girma ba yarinya bace ita da zai ta mata wayo, ya kamata ya cika mata alqawarin da ya dauka na duk sanda ta ce ya dawo zai dawo, shi kuma ya na tabbatar mata da duk abinda ta ce a yi haka za ai, amma ta bashi wani dan lokaci, ya na nan tafe. Umaimah kuwa har yanzu fushi take, kishin Aaseeyah ne kawai ke nuqurqusar zuciyar ta, ta san in da za a bawa Yah Noor zab'i ya dau daya a tsakanin su Aaseehah zai dauka, domin kowannen su na da kyau sai dai Aaseeyah ta kere masu a komai, kyaun ta daban ne da nasu,ba ta mantawa tun su na yara watarana ana ruwan sama, su na ta wanka a cikin ruwa, Aaseeyah ta jiqe sharkaf da ruwa, gashin ta ya kwanta a jikin ta ya na digar da ruwa, Noor ya fito ya tsaya ya na kallon ta ko qiftawa ba ya yi, Umaimah ta tambaye shi da cewar, 'Yah Noor me ya sa ka ke kallon ta haka?' Budar bakin shi sai ya ce mata, 'Murmushin ta kadai zai iya sanya rufaffiyar flower budewa domin daidai yake da hasken rana,ya na sanyaya zuciya kamar danshin da ke a bakin teku,duk sanda idanun ta suka sauka a cikin idanun mai kallon ta, sai sukuni ya samu a zuciya kamar mutumin da ya samu abinda ya dad'e ya na nema, Aaseeyah ta daban ce a cikin mata, ina jiran na ga girman ta domin ina son ganin mai sa'ar da zai mallake ta,ina jiran na ga lokacin da zuciyar ta za ta aminta da masoyin gaskiya' Da sauri Umaimah ta tashi zaune, Yah Noor me ya ke nufi da wadannan kalaman nashi? Ashe ya maida ita sokuwa ne ba ta sani ba? Ya na amfana da jikin ta amma zuciyar shi na wajen Aaseeyah, ba zai yu ba, hakan ba zata taba sabuwa ba wai bindiga a ruwa,to in ma ta bar shi ya zurfafa a son Aaseeyah a barta da wa? Yah Noor na ta ne ita kad'ai, ba zata raba shi da kowa ba, ko za a mutu na ta ne,ba na kowa ba. Cikin sauri ta miqe, ta na ganin Yesmeen ta fito daga wanka ta fad'a, Ummu suleim na ta masifa ta na fad'in sai ta mata rashin M. Ko da ta shiga bathroom din sai da ta yi kukan nauyin da qirjin ta ya mata saboda kishi, ta jima ta na kokawa kafin ta yi wanka ta leqa akan su bata towel, da kyar Ummu suleim da ta rage a dakin ta bata , ko da ta je miqa mata ta ga idanun ta alamar ta yi kuka, sai jikin ta ya dan saki, cikin kulawa ta ce, "Qanwa ta me ke damun ki? Me ye matsalar ne? Tun safe na ke ganin ki wani iri, me ya saki kuka?" Cikin maida kwallar da ta ke barazanar saukar mata a ido ne ta amsa ta koma bayin tare da daura towel din ta, ta tsaya ta sake yin kukan da take ganin daga shi ba zata sake zubar da hawaye ba, sannan ta wanke fuskar ta ta fita, duk yanda Ummu suleim ta so ta lallashe ta sai ta nuna she is Ok,tausayin ta Ummu suleim ke ji sosai, anya ba kewa take ba? Tabbas tunanin baya take kewa ce ta ke damun ta, lallai za ta taimaka ta kawar mata da dukkan wani quncin dake damun zuciyar qanwar ta ta. Ko da ta fito daga wanka ba ta ga kowa ba, alama ce na Umaimah ta shirya ta fita kenan, ita ma shiryawa ta yi cikin shadda kalar pink da suka yi anko su hudun, kuma sun tsayar akan yau za su sanya ta, ta na gamawa ta feshe jikin ta da turaruka ta dauki hoto kala kala ta turawa Yah Hussein,shi ma tura mata na shi wankan ya yi, nan suka dinga yabawa junan su, kafin ta fita wajen sauran 'yan uwa, wasu sun bi samarin gidan zuwa masallaci, su kuwa dama ba su taba zuwa sallahr idi ba, dan haka suka nufi babban parlourn da ya fi kama da a kira shi da hall, ya sha gyara, na musamman aka kawo masu decoration su ka yi decorating wajen, ga tables nan an saka da kujeru wanda za su wadatar da kowa, already wajen da mutane sai dai ba yawa, saboda masallacin da suka tafi. Har yanzu Aaseeyah sarkin gayu bata gama gayen ta ba, in ka ga lokacin da ta dauka sai ka rantse wani make up ta tsaya tsantsarawa, wanda ita tun da can yawan cika fuska da kwalliya ba nata bane, wannan aikin Yesmeen ne, ita ce gwanar kwalliya,ta fi bada qarfi wajen gyara idanun ta, ta hanyar sanya masu kwalli na daukan hankali, tare da taje girar ta ta qayata ta kamar wadda aka yi ma aski,a ka daidaita ta, lips din ta kuwa ta na da kala kalan man lebe masu haske da in ta saka suke qara kyawun shi, sai powder da take amfani da ita dan kyautata kwalliyar ta. Qamshi Aaseeyah ta fi bawa mahimmanci, dan ma Mammee na hana ta, ta na fada mata bata kai wadda za ta na saka turare masu qarfi ba, roll on da body spray sun ishe ta, ta sha ce ma Mammeen ta, 'Mammee ke ma fa ki na sakawa' Sai ta ba ta amsa da cewa, 'Ni ai matar aure ce, ki jira lokacin ki, ni ma miji na nake sakawa' Kunya ke hana Aaseeyah jan maganar amma ba dan ta gamsu da hana ta sanya turare da ake ba. Daurin da ta kafe kan ta da shi mai sauqi ne, amma kyaun da ya mata mai daukan hankalin mai kallo ne,gashin ta nannade a qasan daurin ta, wayar ta ta dauka, da dan siririn mayafin ta mai suna da babu gwanda ba dad'i, ta dora a kafadar ta, dakin Mammee ta shiga, ita ma ta caba ado sosai, ga sarqa nan ta zinare hannun ta sanye da awarwaro na zinare, kamannin su da Aaseeyah ya fito sosai, ba mai cewa ita ta haifi 'yan biyu, saboda kyaun jiki. Kallon Aaseeyah ta yi ta ga kunnen ta ba dan kunne balle sarqa, sai wani juyi take a gaban ta ta na tambayar ta ta yi kyau? "Ke din kyakkyawa ce ko ba kwalliya Aaseeyah na, amma cikar adon mace kwalli,qayatuwar adon ta dan kunne ko da ba sarqa" "Mammeeee ni fa ba na son dan kunne kin sani damu na suke" "Daurewa za ki, ko so ki ke su Yesmeen su fiki kyau?" "In ma sun fi ni kyau ba komai, kowa da yanda Allah ya halicce shi" Wannan halin na yaran nasu ne ya lafar da duk wata tarzoma da aka sha fama da ita a baya, dan basu yarda da hada su da juna ba sam. Dan kunne da sarqar ta Mammee ta dakko mata a amajiyar da suke aje kayan su masu tsada, sanya mata ta yi ta na tasbihi ga Allah da ya bata kyakkyawar yarinya kamar Aaseeyah, murmushi ta ke ta zubawa domin jin yabon da mahaifiyar ta take mata, su na nan tsaye ta ji motoci na dawowa, cikin zaquwa ta ce, "Mammee sarqar nan ta min nauyi ko za ki ciren ki barni da dan kunnen?" "Ba zan cire ba, kuma kar ki kuskura na gan ki ba bu ita" Mammee na son ta burge dangi a ga cewar ba ya ita da yaran ta a gidan, ta bangaren Ummee ma haka ne, wannan dalilin ne ya sa itama ta bama yaran ta duk wata kulawa dan dai su fito fess. Ko da Aaseeyah ta fita, sanye da takalmin ta mai tsini, irin siririn nan, duk inda ta taka sai qarar ta dau hankali, babu mai cewa shekarar ta sha shida zuwa sha bakwai,dauka za ka yi wata hadaddiyar budurewa ce da ta gama mallakar hankalin kan ta. Kallo ne ya mata yawa tun kan ta fita daga parlourn su, kawai sai ta samu waje ta zauna, ta qi daga kai, balle ta hada ido da kowa, hakan ya bawa kowa mamaki,a iya sanin su Aaseeyah ba mai kunya bace balle taqi shiga mutane, wasu sun zo ma cikin taka tsan-tsan ne saboda shaqiyancin ta da ta saba, kusan duk zuwa sai an tafi da ita a baki wajen rashin ji da tsokana, hada ma mutane franks da sauran su,daya daga cikin wanda Aaseeyah ta taba yi wa shaqiyanci da qullin funkaso tun ta na da shekara shida ce ta kalle ta ta ce, "Ohhh Aaseeyah n Mammee jiya ba yau ba, ashe a duniya za ki zama mai kunya? A zato na ba ranar barin shaqiyanci a tattare da ke" Dariya ake cike da nishadi, Aaseeyah ta rufe fuskar ta ta miqe ta fita da d'an gudu-gudu sauri-sauri, wayar ta ce ta fara ringing, sunan, 'Zubaida' shi ne ya bayyana a screen din wayar ta, cike da shauqin so ta daga wayar, ta fara magana da Jubeir, roqon ta ya dinya yi akan ta tura masa wankan sallan ta ya gani ta na masa yanga ita kuma, har ta isa babban parlourn da mutane a yanzu sun cika danqam ana ta cin abinci ana hira da raha, ba tare sa ta san ta isa wajen ba, fuskar ta na ta fidda annuri, murmushin ta na haskawa kamar hasken wata, hannu ta sanya ta kare bakin ta ta na dariyar hirar da Jubeir yake mata, Noor kuwa wani irin kishi ne ya tokare zuciyar shi, yanda ya kula matasan wajen kaff hankalin su na kan ta, cikin bata rai ya miqe ya isa gaban ta,ta na daga kai suka had'a ido, zuciyar ta ta buga da qarfi dan tsoro, 'Wayyooo Allah na shiga uku, Yah Noor ya hana ni kula Jubeir,Allah ka sa kar ya gane' Cikin qasa da murya ya fara mata magana, ran shi a bace, "Wanan wanne irin d'an iskan dinki ki ka yi?kuma kin zo gand'an-gand'an za ki shigo ba mayafi, ki na hauka ne?" Da sauri ta fara qoqarin yafa dan siririn mayafin da ta san ta sanya kan ta fito, wayam ta ga ba bu shi ba alamar shi, dube dube ta fara, can ta hango shi daga waje a qasa, da gudu ta fita ta dau mayafin ta yafa, kowa idon shi akan su, ganin haka ne ya sa bai koma ciki ba ya fita ya bar wajen shi ma, bai zame ko ina ba sai unguwar Nasarawa, inda budurwar shi da ba wanda ya san ya na da ita a dangi sai shi sai Allah take, a nan ya ke duk wani babban iskancin shi, yarinyar na mutuwar son shi duba da qoqarin shi da kuma sanin gidan su akwai maiqo, ajin su daya a jami'a, sun jima suna tare, tsananin iya taku ne ya sa ba wanda ya taba sanin ya na tare da ita, domin Noor ba abinda ya fi kwarewa akai sama da boye halayen shi. Aaseeyah kuwa can bayan gidan ta nufa ta zauna ta na maida numfashi, kallon dinkin da aka kira dan iskan dinki ta shiga yi, dinki ne na doguwar riga, wanda ya dan kama ta daga sama, sannan ya bude har qasa, ya sha aiki mai matuqar kyau, kuma su Umaimah da Yesmeen shi suka sanya, mayafin su dik iri saya ne, me ne iskancin anan? Su mai ya sa bai musu magana ba? 'Wataqila ya musu magana kan na je, shi ya sa ban gan su a wajen ba' Tunani ta dinga yi na dalilin da ya sa yanzu yake neman takurawa rayuwar ta da tsanani da matsi, wanda a baya ba haka bane, shi din mai tsananin kulawa ne a gare ta da lamuran ta ne, sannan ita din ta saba matuqa da shi, me ne ne ya shiga tsakanin su da ya tsane ta yanzu? Hawaye ta ji su na saukar mata, da sauri ta share su, tare da qudirta in ta sake haduwa da shi za ta bashi hakuri, wataqila laifi ta yi,ita yanzu wanne laifi ma take a gidan? Rabon da a kawo qarar ta ko da a makaranta ne ta manta, to

Chapter 5 of 41