Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
fahimta. Bakin gate din gidan ya je ya tsaya, ya san indai su na wajen to za su gan shi. Bai fi minti goma da tsaiwa ba wani ya lallaba ta gefen shi ya toshe masa hanci da wani tsimma, ba bata lokaci kuwa ya fadi a wajen,mota ta zo a guje ta ci birki a gaban su, suka dauke shi suka sanya a mota, suka bar wajen da gudu. Qarar motar da mutan gidan suka ji ne ya sa su fita a guje, Ummee kuka Mammee addu'a, wayar ta ta ce Aaseeyah ta dakko mata, ta na son sanar da Abeen su, "Mammee duk da kun qi sanar da mu me ke faruwa amma plan din da kuka hada zai rushe in kk sanar da su Abee me ya faru, mu bashi ko da zuwa dare sosai ne ko zuwa gobe, in ba a ji shi ba sai a kai ma 'yan sanda rahoto,tunda ai ba za su tsaya qofar gidannan su ce za su yi magana ba ko?" "Shegiya mai mugun hali, ki na nufin an sacen d'an 'yar uwa ta kawai sai mu zauna mu jira har sai an dawo da shi, in suka kashe shi fa?" Wani mugun kallo Aaseeyah ta wurga ma Ummee, za ta yi magana Mammee ta riga ta, "Inshaa Allahu ba abinda zai same shi, da izinin Allah, sanin kan ki ke ne ya kamata a ce su na daure ga hukuma, tunda kk gan su a sake suna yawo sun san me suka taka, akwai wata a qasa, Mahboob ne kawai amsar mu, hakuri kuma shi ne zai sa mu jira har mu ga me zai faru" "Kaiii jama'a, ashe mu na nan baki sakatoooo zaune ashe zama bata qare mana ba," "Allah dai ya kyauta ya jiyar da mu alkhairi" "Ameeen" Yesmeen sai tambayar Ummee take wai meke faruwa ne, wata uwar tsawa ta daka mata tace ta rabu da ita ta ji da me ke damun ta,dole suka ja suka zuba mata ido ta na ta kuka, ta na surutai. Mammee kuwa alwala ta yi ta hau sallah, tare da roqon Allah ya kare Mahboob a duk inda yake,domin ta san yaran farin sani, indai za su iya kisa da qananun shekaru yanzu ba ta san me zasu aikata ba kuma. Ta na addu'a ta na samun nutsuwar zuciya, har Abee da Abbu suka dawo, kowa ya shiga bangaren shi, a nutse Abee ya same ta, ta na sallah, daki ya je ya yi wanka, ya shirya ya je ya fara cin abinci, ya na mamakin doguwar addu'ar da take, ya kai loma ta uku ya ji buga qofar bangaren shi, ya san yayan shi ne ke irin bugawar nan, dan haka jallabiyya ya koma ya saka akan wando da vest da ke jikin shi, ya fita. Cikin tashin hankali ya gan shi, kafin ya ma dan uwan nashi bayani, ya ji qarar gate, su na dubawa sai suka ga an wurgo wata takarda anannade, budewa Abbu ya yi hannu na rawa, Abee na ta tambayar shi me ya sa shi cikin tashin hankali haka? _Zuwa ga Alhaji Muhammad, da Alhaji ibraheem,kar ku sake ku je wajen hukuma akan batan d'an ku Mahboob, ya na wajen mu, za mu gaisa ne irin gaisuwa ta tsoffin abokai,ku kiyaye, in magana ta je wajen hukuma zamu aikata masa abinda muka aikata a baya,wannan gargadi ne daga Gazaa wanda in aka qi bin magana ta za ku yi jana'izar d'an ku washegari_ "Innalillahi wa inna ilaihirraji'un, Yaya wai kana nufin yaran nan ne suka dauke Mahboob?" "Abinda Fateema ke fadan kenan, na zo sanar da kai wannan takarda ta same mu, yanzu ne ka ke gani za ai?" "Mu jira Yaya kar mu sa rayuwar shi a hatsari, zuwa gobe in basu dawo da shi ba sai mu kai maganar wajen hukuma, ashe shi ya sa na ga Subai'a na ta sallah da addu'a ina mamakin jimawar ta,har na shiga bata zo waje na ba, ta riga ta saba kafin mu dawo ta yi sallar ta" "Ita waccan shashashar kuka kawai take, bata san tai addu'a bama balle sallar, kaiii Allah ya kyauta" "Ameen Yaya, mu yi ta addu'a zuwa gobe, inshaa Allahu ba komai, mu kwantar da hankalin mu, da izinin Allah ba komai, ba abinda zai faru, ba abinda za su mishi" **************************** Mahboob ne kwance a qasa a daure, kan shi na qasa ta gefe, hannayen shi na daure ta baya, a wani rantsattsen parlour, hayaqi kawai ke tashi a wajen, tsabar shan shisha,ga wani kida mai fasa dodon kunne da ke tashi a wajen, 'yan mata kusan tsirara suke yawo daga su sai dan kamfai da rigar mama,wasu na busa sigari, wasu na shan wani abu a glass cup, sai rawa suke ta rashin mutunci, zaune yake a kujera da shisha a hannu ya na daga kai ya na fesar da hayaqin, idanun nan ja jawur, da alama fari ne a baya, ya rine zuwa baqin hayaqi. A hankali idon Mahboob ke budewa, ya na son daga kai ya kalli inda yake ba dama, ya na daga kwancen dishi dishi ya ke ganin gilmawar matan da carpet din da yake kai. "Gazaa man ya tashi fa," "Kunce shi ku bashi ruwa" "Ruwan mu ko ruwan su" Dariya suka kece da ita, "Shege Sam,ba shi duk wanda ka ga dama" Wata kwalba ya bude ya zuba ruwan cikin ta a glass cup ya zaunar da Mahboob, ya kai masa bakin shi, kauda kai ya yi saboda gane warin abun da ke ciki da ya yi. Aje cup din ya yi ya na juya kai cikin takaicin qin karba da Mahboob ya yi, "Well da alama har yanzu qaramin kwaro ne shi Gazaa man" "Kunce shi na ce Sam" Kunce shi ya yi, Mahboob ya hau kama hannun shi da ya yi jawur, ya na zafin daurin, zama ya yi sosai ya na bin su da kallo, Gazaa ne ya zamo daga kujera ya kai fuskar shi daidai jikin ta Mahboob ya ce, "Wellcome back home old friend" Hummmm in ana sallah ba a magana......... Su waye kuma wadannan muka samu? Ku biyo ni a next page dan jin ko waye Gaza, more comment more typing less comment a ga dan gundun uban lalaci😂 ko dake yanzu abun na ga ba rowaaaa😂much love to u all. TAUBASHI PAGE 21 A hankali idanun Mahboob ke rarrabewa a tsakanin su, zuciyar shi na matsewa waje guda saboda qunci, da danasanin ranar da ya qulla abota da su, haqoran shi ya hade waje daya, tare da taune su, kamar wani abu ya ke son ganin baya a cikin bakin na shi. "Well, Mahboob a zato na ka bar qasar kenan har abada, kwatsam masu min gadin gidan ku su ka ce sun gan ka, ban gasgata su ba sai da na gan ka da ido na,....ahhhff sorry fa ban baka labarin bayan rabuwa ba, a taqaice dai bayan kammala makaranta ta ta jami'a fannin kasuwanci na karanta,sai kawai na amshi Business din babana, i am now officially a druk dealer,booom bite me baby." Waro idanu waje Mahboob yayi,kamar za su fado qasa, mamaki, tsoro da tashin hankali ne a cikin idanun shi,ta ya ya za ai ya gaji mummunar sana'ar mahaifin shi, sune fashi da makami, su ne kisa ba gaira ba dalili, in aka basu contrant din kashe mutum a guje suke zuwa,su ne siyar da miyagun kwayoyi,su ne raping yara mata da maza,wadannan mutanen na da matuqar hatsari ba kadan ba,ga shi ya gaji duk wadannan a wajen mahaifin shi, ya tabbata sai ya fi mahaifin shi shaqiyanci. Kallon Mahboob Gazaa ya yi ya saki wata mahaukaciyar dariya tare da d'aga kan shi sama, ya zuqi hayaqi ya fesar a sama, sannan ya kafe Mahboob da ya had'iyi yawun tsoro da idon shi jajaye, "What? Are you scared old friend? ( meye? Ka na tsoro ne tsohon aboki?) Ka ga, ba abin tsoro a nan,kamar yanda wasu 'ya'yan ke gadon, walda,likitanci,bokanci,malanta,dinki,kafinta,to ni kasuwanci na gada, meye a ciki? Ku naku iyayen ba sana'ar qarfe suka gada ba? Kowa da gadon da iyayen shi ke bar masa" Cikin shaqewar Murya Mahboob ya ce, "Kana nufin Dad din ka ya mutu?" "Meye wani ya mutu kamar wani anne dan uwan su Sam? Mahaifi na bai rasu ba, ya na nan da rai,amma ya na jinya, sakamakon artabu da police da su ka yi a wani gagarumin aiki da suka fita, matashin dan sandan ya yi nasarar harbin dad a qafar dama, ido na idon shi,har yau na kasa samun nasarar daukan fansa" Cikin d'acin zuciya ya qarasa maganar, Mahboob ne ya kalle shi ya yi murmushi,zuciyar shi ba tsoro sam ya ce wa Gazaa, "Dan Allah ya ka ke ji a zuciyar ka a yanzu da ka tuna mahaifin ka na kwance ya na jinya saboda an harbe shi a qafa?" Wani kallo Gazaa ya ma Mahboob mai cike da ma'anoni da yawa,amma Mahboob sai ya yi kamar bai gani ba, ya ci gaba d magana, "Zafin da na ke ji da da yanzu,da kuma wanda ka ke ji nawa ya fi naka Gazaa,a kullum ina danasanin sanin ku gaba daya a rayuwa ta,na tsinewa ranar da na fara ganin ka har na shaqu da kai, ban taba son kowanne aboki ba yanda na so ka, amma ka kashe min iyaye na, sannan a ka kasa daukan mataki akan ku, qarshe kuka so juya magana akai na, ba dan na gudu ba da shikenan ni zan yi zaman gidan maza a madadin ku, ku masu laifin, to ka sani, ni ban dawo qasar nan dan daukan fansa ba, ban kuma dawo dan ina tunanin sake ganin ka ba ma a rayuwa ta kwata kwata, da ba ku bayyanan kan ku ba da ban san a wace duniyar kuke ba, dan ban ma yi tinanin ka na raye ba, ko ka na mace, ko ka na gidan maza ko ka na yawo a gari ba, ganin ka a yanzu ba zai sauya komai ba, in ni ma kashe ni za ku yi bismillah, amma ina roqon ku, kar ku had'a da kowa a ahali na, ba su maku komai ba, soyayya ce a tsakani n da kai irin ta abota a baya, amma a yanzu ba wanda na tsana sama da kai,na barka da Allah akan abinda ka wa iyaye na, ban da hukuncin da zan maka in huce, domin wani abun ya fi qarfin daukan fansa" Idanun Gaza sun kada sun yi jawur, bai iya cewa komai ba, sai kallon Sam da ke fushi da fushin wani da ya yi, ya lumshe ido, tare da sauke jiyar zuciya, ya wani kada kai cikin kwarewa ta duniyanci. Cikin fushi Sam ya kalle shi, ya fara magana, "Gazaa man ya za ka ce haka, barin shi babban hatsari ne fa," "Are u the boss?" "No" "To umarni na ne, ku maida shi inda kuka dakko shi.....amma ka sani, idan na ji kyasss ka kai rahoto wajen 'yan sanda za ka sha mamakin yanda zan qarar da zuri'ar ku, har ta can Jordan din, da ta Yola, d dik inda dangin ku suke, saboda ni yanzu a Nigeria na yi kafuwar da ko kotu aka je sai an sallamen,ya rage ya naka,ka kame kan ka da bakin ka, kai da qannen ka ku tsira,ko kuma ka yi giggiwar kai magana gaban hukuma, da na fito na kashe mutanen gidan ku, na kwashe kyawawan 'yan matan ina hutawa da su" Kallon shi kawai Mahboob ke yi, cikin takaici da qunar rai,ya tabbata har yanzu Gazaa na son shi kamar da, ba dan haka ba da zai iya kashe shi,ko dan rufuwar asirin su, amma shi kam a duniya ba wanda ya tsana sama da su, ba shi da yanda zai yi ne. Ya na ci gaba da kallon Gazaa ya ji ya shaqi wani abu, nan da nan ganin shi ya fara lumshewa,hankalin shi ya fara gushewa, kafin qanqanin lokaci ganin shi ya dauke dika, ya fad'a wata duniyar ta daban. Ciccibar shi su sam suka yi suka kai mota, a cikin daren qarfe wajen biyu na dare suka maida shi gida, suka yi parking mota daga nesa da gidan, suka kwantar da shi a gate, suka juya, Sam ya so su harbe shi kawai, amma umarnin Ogan nasu ba abun tsallakewa bane,da qafa ya hauri cikin Mahboob da qarfi, sannan ya sakar mishi naushi a kunci, suka yi gaba, ya na yarfa hannu, da sabulallen wandon shi a saman mazaunan shi,motar su suka fada suka bar wajen. Mahboob na nan kwance ba tare da sanin kowa ba, Mammee na saman sallaya ta na roqon Allah dawowar Mahboob cikin qoshin lafiya. Ummee na ta sharar bacci har da gwarti, sai Abbu ya buga tsaki ya taba ta dan ta gyara kwanciya ta daina ja masa gwarti sai ta farka cikin magagi ta na tambayar "ya dawo?" Banza Abbu ke mata,kowa na gidan idon shi biyu, hankalin shi a tashe banda ita,baccin ta ma take. Da asuba Abee ya riga kowa shirin masallaci, Aaseeyah ta riqe shi ta na kuka, ta na roqon kar ya fita, lallashin ta ya yi, sannan ya nuna mata ba abinda bawa ya isa ya yi ma bawa, sai a binda Allah ya hukunta,zuwa masallaci ba fashi. Ta na kuka ta shige dakin ta, sallah ta tada cikin duk sujjada ta na roqon Allah ya kare su daga sharrin wadan nan mutanen, Allah ya dawo da Yah Mahboob gida lafiya,har alqawari ta yi da Allah, ta fasa yi mishi abinda ta qudirta zata masa saboda wahal mata da mahaifiya da suka yi a baya, domin ta qullace shi, Aaseeyah kuwa ta qullaci mutum sai ya gane kuren shi. Da Mahboob Abee ya yi tuntub'e, nan da nan kuwa ya leqa ya kira mai gadi, da driver, suka ciccibe shi suka nufi bangaren shi da shi,sai da suka aje shi a dakin Aaseeyah da ke ta sallah sannan suka fita, Abbu kawai ya sanar ma da dawowar Mahboob din, amma fa kamar sun bugar da shi ne, sai ya farka sun ji me ke faruwa, Aaseeyah na idar da sallah ta nufi gadon ta da aka shimfide Mahboob din, nan ta ga kuncin shi ya dan kunbura, ta sama ya yi jawur, da alama dukan shi akai, d gudu ta je wajen Mamme ta sanar da ita, ta na tsaka da azkar din sallar Subh da ta idar, 'yan biyu da sai a lokacin suka bude dakin su dan tafiya masallaci, ne suka ji me Mammee da Aaseeyah ke fada, suma rufa masu baya sukai, a tare suka sauke a jiyar zuciyar ganin Mahboob din, tattabashi Mammee ta yi ta tabbatar ya na numfashi,bacci yake, kitchen taje ta dora ruwan dumi, ta juyo a bowl ta shiga bathroom din Aaseeyah ta jefa hand towel, Hussein ta bawa ta ce ya gasa mishi kuncin shi,sai da ya gama gasa mashi sannan sika koma dakin su dan yin sallah, dan kuwa an idar a masjid. Mahboob bai farka ba sai da misalin takwas na safiya, idanun shi sun masa nauyi sosai, a hankali ya ke tuna duk abinda ya faru a gidan Gazaa, kada kan shi da ke sara mishi ya fara, ya na zubar da wasu irin hawaye masu zafi masu qona zuciya,qirjin shi na dagawa saboda gudun da jini ke yi da dauri da sauri a zuciyar shi, wanda gudun ya kusan wuce qa'ida. "Hadha kulluhu khad'a'i" (Duk laifi na ne) Shi ne abinda ya ke ta maimaitawa, tun hawaye na zuba a hankali sautin kukan shi ke fita, har ya jawo hankalin Mammee da Aaseeyah dake parlour a zaune, da sauri Aaseeyah ta bi Mammee suka shiga dakin, ganin shi a wannan halin ya sanya zuciyar ta karyewa sosai,wanda ya sanya ta zubar da hawaye ba tare da ta shiryawa hakan ba,Mammee ke lallashin shi, ta na nuna masa qaddara ce, kar ya damu, bari ta kawo masa tea ya sha, kafin su Abeen su su dawo. "Zan yi sallah Mammee," "To bismillah" Har ya yi hanyar bayin ,Aaseeyah ta shige gaban shi da gudu,ta fad'a bayin, panties din ta da bra da ta shanya ta kwashe, garin gudu ta kwashe ta yarda bra din ta guda daya, fev. Color din ta wato pink,a bayan ta ta boye su, ta wuce shi ta na yaqe, tare da nuna masa da hannu daya, alamar ya shige, ta na tsaye ta na yaqe ta na rawa da qafar ta, ya na shiga ta dafe qirjin ta, ta nufi wardrobe da gudu ta wurga su, ta kulle,hannun rigar bra ya fito ta gefe bata kula ba. Mammee ke mata dariya, ita kuma ta na tura baki, "Ni ban ma san me ya sa Abee kai qaton saurayi kamar Yah Mahboob daki na ba ma in the first place," "Ahhh to ina zai kai shi, ki na dai gani yaran can ko tashi ba su yi ba a lokacin , ke kuwa dakin ki bude fitila a kunne, sannan ba a gado kike ba,kema sallah kike, to dakin mu kike ganin ya fi dacewa akai shi?" Shiru Aaseeyah ta yi, ita dai har yanzu ta na haushin kai mata garjejen qato daki da akai, ba ruwan ta da duk wani uzirin kowa, kawai a fitar mata da qato daga daki. Ganin bra din ta a qasa ne ya bashi tabbacin kwashe su tai, murmushi ya yi ya wuce, ya fara gyara jikin shi, tare da d'aga rigar shi inda ya ke jin zafi, ya ga shatin ja a wajen, da alama sun dake shi ne a lokacin da baya cikin hayyacin shi, sakin rigar ya yi ya yi alwala, ya fita, Aaseeyah na sake gyara masa sallaya ya fita, riqe da bra din ta a hannu, kallon wardrobe din ta ya yi, ya ga hannun bra a waje, ta na duqe ta na shimfida sallaya ya nufi wajen, a son shi ba sai ta gan shi riqe da bra din ta a hannu ba, kawai ya aje mata ya bar wajen, ya na budewa sauran na watsowa qasa, Aaseyah na kallon wajen, qara ta sake, sannan ta nufi wajen da gudu,ta na kwashe su ta na mayarwa,cike da jin kunya, fuskar ta ta dau dumi saboda tsabar kunyar da ta kama ta, shi kuwa in ba dariya ba ba abinda yake mata kwace ta hannun shi ta yi ta mayar ta bar dakin da gudu. Dariya ya yi sosai, sannan ya tada sallah, ko meye abun jin kunyar dan an ga bra din ta oho? Aaseeyah bata taba jin haushin kanta ba irin na yau, dama Mammee na mata fadan wurga kaya ba ninki, ba cikin tsari ba, tun ta na qarama ake fama, yau ga abinda rashin ji ya ja mata, "Yanzu shi kenan ya san size dina fa ko" 'Yar qara ta saki, sannan ta fada kitchen ta na tura baki,Mammee bata tambaye ta komai ba, dan a zaton ta fushin kai mata Mahboob daki take har yanzu. Abee da Abbu na tattaunawa akan abinda ya faru a babban parlourn gidan, kiran Noor sukai a waya, suka ce ya sanar ma da kowa a nan za su karya, sannan a kira Mahboob shi ma anan za a karya dika. Haka kuwa akai, Ummee da Mammee can suka aika abinci,kowa ya maida hankali ya cika tumbin shi, sun ci sun sha, sannan Abbu ya kalli Mahboob da kuncin shi ya yi ja, kumburin ya sabe, ya ce, "Uhumm ka bamu labarin me ya faru, sannan me ake ciki," Nan Mahboob ya zayyana masu komai, daga lokacin da aka sanqame shi aka tafi,zuwa sanda suka fesa masa abu ya shaqa da farkawar shi a dakin Aaseeyah. Kowa ya sha mamakin ta'azzara da Gazaa ya yi, tare da daurin gindin da ya ke da shi a qasar,lallai dole su hakura da lamarin hada shi da hukuma,domin kuwa suma tsoron su suke. Nan Abbu ya umarci kowa na gidan da ya manta da komai, da duk abinda ya faru, kar wanda ya je ga hukuma, wani kallo Aaseeyah ta yi ma iyayen nata kamar sun fadi sabo. "Abbu, ka na nufin sun kashe Uncle Mahmood a banza kenan? Shin ko dai Uncle din ba shi da gaskiya ne shima kamar su?" Cikin bacin rai Mahboob ya kalle ta,ya ce, "Abana ba shi da wani laifi, ba shi da laifin komai, shi dan kasuwa ne, mai saida qarafa, ba d'an fashi da makami bane, shi mutumin kirki ne, wanda ban taba ji ko ganin mai halaye masu kyau irin shi ba, ni ne silar mutuwar iyaye na, da hannu na na shigo da makasan su,kar ki sake zargin mahaifi na da fashi da makami," "To in ba su da hannu a fashi da makami,kai ke da hannu a ciki? Meye wahala a sanar da mu me ya faru a baya? Ka na ta mana yawo da hankali," "Sabo da ba na so ku tsane ni, musamman Umaimah da na raba ta da iyayen ta ta na da qananan shekaru, ba ta san dadin iyaye ba,ni ne silar raba ta da su" "Kashe su kai ko me? Ka sanar da mu mana" "Aaseeyah, ki mana shiru" In ji cewar Mammee. Cikin fushi ta miqe za ta bar parlourn, sautin Muryar Mahboob ne ya tsaida ta, "Abinda ya sa na ce maki ni ne silar kashe iyaye na shi ne.......... Tadaaaaaa......mu had'u a next page inshaa Allah, za ku ji yanda labarin zai kasance, Assalamu alaikum warahmatullahi wa barakatuhu ya ikhwanee fil islam, ana uhibbukum katheeran fillah. TAUBASHI PAGE 22 "Shekaru da dama da suka gabata,lokacin ina secondary school, na kasance ina da abokai da na ke matuqae ji da su, su ma suna ji da ni sosai, dikkanin mu a lokacin yaran masu arziqi ne, sai dai iyaye na ne kadai masu neman arziqin su ta hanyar halal, Garzali shi ne wanda ya ke a matsayin group leader din mu, duk abinda ya ce haka za a yi ko mutum ba ya so,mahaifin shi babban dan daba ne a lokacin wanda ya zama shahararre wajen aikata duk wasu laifuka da kk san in mutum ya yi hukuma za ta daure shi, ko a kashe shi ma. Garzali ya sha sanya abokai na aikata manyan abubuwan da zai zauna ya na kallo ya na jin dad'i,misali fyade, shan giya, da sata, da ke Garzali na so na a cikin abokan mu bai taba sanya ni komai ba, sai watarana da muka tashi ba mu da kudi, kusan mu biyu ne a cikin mu bakwai din muka je da kudi, dake su suna shaye-shayen kayan maye,ni kuma a lokacin ina dan shan sigari amma ba ko yaushe ba, sai sun matsa min na sha wani abun shi ne nake shan sigari. Mu na zaune dika da Garzali a saman katangar bayan gidan su da muke zuwa mu zauna, mu na hango mahaifin shi da abokan shi su na abubuwa dai haka marasa kyau da 'yan mata, (cikin dan jin kunyar idanun su Abbu ya fad'i hakan) Garzali ya ce min, 'Aboki na gari ya yi zafi fa, ba nera, jiya Popcy ya ban kudi masu yawa mun kashe su mun sai sweet (kwaya) na tambayi kudi ya fara min tambayoyi,ba na son ya gane na fara shan sweet tun yanzu, ko akwai wani abu wajen ka?' Duba aljihu na na yi na zaro dari biyar na miqa masa, dariya suka sa, shi da sauran abokan mu, ya karba ya na juya kudin a hannun shi, 'Fito da sauran mana ya za ka ban wannan, ko ruwa ba zai ishe mu sha ba ai wannan (giya) balle sweet (kwaya)' 'Shi kadai nake da shi Garzali, amma ka tambayi su Abu da Sam ko akwai wani abu wajen su sai ka hada' Cewa suka yi duk ba su da kud'i, maida idanun su suka yi kaina, har sai da na tsargu, Sam ne da ke kishin yanda Garzali ke ban kulawa ya ce, 'Ya kamata mu je gidan ku ko za mu samu wani abu, kai ma fa Baban ka Don ne, akwai Nera,' 'Ba mai zuwa gidan mu gaskiya, a yi amfani da wannan ko a bar shi' Kallo na Garzali ya ke ta yi, sai da jiki na ya yi sanyi, daga qarshe na ce, 'Mu je yau kawai, daga yau ba za mu sake zuwa gidan mu tare ba, in Abana ya gan ku fad'a zai min' Nan muka tafi gidan mu, mun shiga ba wanda ya gan mu,muka saci kudi masu yawa muka fita, ni dai ba ni na dauka ba, na nuna masu suka diba, muka fita ba wanda ya gan mu. Tun daga nan,in

Chapter 15 of 41