Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
qawa, abokiyar hira da shawara, ina son na haifi mace dan kula da tarbiyyar ta, budar bakin Zainab sai ta ce, "Hummm ai da ganin ki juya ce, dan ba lallai ki haihu ba,ki yi sanadin da iyayen ki za su mace sannan ki sa rai kema Allah zai baki? Hummm ai ko za ki samu sai sun rama abinda ki ka wa na ki tsoffafin, ai abun da kai sai an maka" Haka suka tafi tare da dasa min baqin ciki a zuciya, tare da tsananin tsoro, ko dai da gaske Zainab take, sai na haifi dan da zai ramawa iyaye na abinda na musu? Na shiga damuwa da tashin hankali, ba na bacci, saboda tashin hankali,roqo na Allah ya sa kar maganar Zainab ta tabbta. Sanda suka dawo, sun dawo da tsaraba kala kala, jakunkunan da suka dawo da su za su nuna maki an kashe nera, amma carbi da zamzam, sai kwalin dabino qarami, da wata rigar bacci irin wanda takari ke sakawa, su ne tsaraba ta daga dikkan su, da gani hadin baki ne. Na musu godiya na zauna naci dabinon kamar zan shide saboda yanda yake min dad'i a baki na? Daya qare sai na ji raina ya baci, in taqaita maki dai a ranar sai da Abeen ku ya je ya samon irin dabinon, tun daga nan ya zama ban da wani abu na ci sai shi, ba ni da qiba a da yanda kk gan ki haka nake, shape dina mai kyau ne kamar naki, a hankali hips dina ya qara cika da qirji na, wataranar asabar bana.mantawa. Na je na kai wa Goggo Ayshaa abinci, sai muka hadu da su Zainab a wajen ta, na ajiye na zauna nima a taba hira da ni, duk da ba wata mai mutunci ake sawa da ni ba, sai na ga zainab da Fateema na qus qus, nan da nan na ji raina ya baci, na kasa jurewa, sai na ce, 'Ku dai Allah ya nuna min sanda xa ku daina gulma, ana xaune ana hira ku hau rad'a,' 'Inyee, ehhh lallai ne,shi da ma ciki ya na zuwa ma kowa da yanayi kala kala, naki cikin masifa ya sa ki ko' 'Ciki,me ki ke fada hk' Kallon juna sukai da mamaki, 'Baki san ma ki na dauke da juna biyu ba?' Miqewa na yi tsaye na kalle su, 'Ku na kira na mayya,ashe ku ne mayu masu gani har hanji, in ba mayu ba ta ya akai ku ka san ina dauke da ciki?' Goggo Ayshaa ce ta fito ta kalle ni ta ga yanda raina yake a bace abinda bata taba gani ba, nan da nan ta qaraso, tare da tambayar me ya faru, sanar da ita na yi abinda ya faru, ita kuwa da kallo ta bini daga sama har qasa, sai na ga ta na murmushi, "Subai'a jeki bangaren ki, idan Ibraheem ya zo sai a je asibi a duba ki, ai ba abin damuwa bane, dan an ce ki na da ciki ai abun murna ne, tunda abinda mu da ke muke fata kenan ko ba haka ba?" Cikin jin kunya na sunkuyar da kai na, sannan na daga mata kai, tare da saurin barin sashen nata, Zainab da Fateema kuwa da alama samun ciki na bai musu dadi ba, duk da cewa kowa da mijin ta, ba miji daya muke da shi ba, amma su na baqin ciki matuqa su ga ina da abu basu da shi, ko su na da abu ni ma.na yi shi, su na jin takaici matuqa su ga sabon abu a waje na, ba su iya boyewa, ko dai su aiko yara su bata, ko kuma su bata da kan su in sun samu dama, ko kuma su qi min murna, wanda ni ina musu murna, ku ma ina zuwa har wajen su na musu addu'a akan abinda suke da shi na farin ciki. Ranar litinin muka je asibiti aka auna ni aka tabbatar da ina dauke da cikin wata uku da sati biyu, murna kamar me, sai da muka yi sallar nafila a ranar da dare dan godewa Allah, amma ina ta mamaki tunda duk wata ina ganin jini, sai dai d'an kadan, kuma a yini d'aya, tun da na fara zuwa asibiti likita ba duba ni ya bn magunguna na dai na zubar da jinin nan, sannan aka hana ni aiki mai yawa. Wata biyar ciki ya yi girma kamar na wata bakwai, ko da muka je aka duba sai aka gane cikin na yan biyu ne, mun yi murna sosai, su Zainab kuwa sun sha baqin ciki, gashi xan fi su yara, su ba su gane dukiyar gidan ta waye ba takamaimai. Wata tara na haifi yara na kyawawa guda biyu.maza, aka bar masu sunan su Hassan da Hussein, nan na daina shiga sabgar su, na dinga kula da yara na, da miji na, dan ko Goggo sai na yi kwana biyu bamu hadu ba, sai dai ita ta zo, ko da na haihu a dangi na ba wanda ya zo, na sha habaici da gori wajen su Zainab, ni ma na zage na dinga masu rashin kunya,saboda sin yarda girman su na raina su a lokacin. Bayan wasu shekaru lamura suka fara tabarbarewa tsakanin Zainab da Mahmood saboda ta bata Mahboob da kashe kudi,abokan shi har da yaran arna, sun san shi yaron masu kudi ne, har sata suke saka shi, su yi shaye shaye da kudin, shi kuma ya na bin su,duk da ba ya shan komai, amma ba mai son yaron shi ya na hulda da masu shaye shaye, Zainb ba kunya ba tsoron Allah ta rufe ido ta dinga yi wa mijin ta rashin kunya,dole ya sa mata ido, saboda gudun fitina. Yan biyu na da shekara biyu Fateema ta samu ciki ita ma, kuma an tabatar mata da 'yan biyu n itama, habici kala kala na sha shi, akan ba ni kadai Allah ke so ba, su ma ya na son su. Na ta ya ta murna ban biye mata ba, domin har raina na yi farin ciki da jin haka. Bayan ta haifi Ummu Sulem da Yesmeen,Zainab ta samu cikin Umaimah, bana jin habicin su haka zan shiga na dau yaran in masu hidima, ina son mata,ina son na samu mace, kullum ina addu'a ban cire rai ba,sanda Zainab ta haihu ta haifi Umaimah, nn ma sai da suka min dariya, abinda na ke so Allah ya basu, ni ko oho. Sanda kuwa na tabbatar ina dauke da cikin ki, daina bari nai mu hadu da su, sai da ciki ya girma, shi ma ta sanadin Mahboob da ya zo da abokan shi, suka saci kudi ya na waje ya na jire masu qofa, zasu gudu Zainab ta fito ta gan su, suka gudu, shi ya yo waje na, sai ta ce ai ni ke sa shi sata dama ta san jinin ta ba zai sata ba. Mu na cikin rikicin ta kula da ciki na da ya girma, ya kai watanni biyar, mamaki ne a ran ta matuqa, ko magana ba ta yi ba ta nufi wajen Fatee, tare suka dawo, ba kunya suke tambaya ta ciki garen? Nace masu ciki garen? Fatee tace, 'Shi ya sa ashe kk nacewa hijabi, ashe kin qunso mugun abu,' 'Sai dai in ke ce mai mugun abu, ni dai ban qunshi mugun abu ba sai alkhairi,' Nan muka hau kace nace, ban aune ba na ji Zainab ta tsinkan mari, tare da cewa, 'Wannan cikin da ki ka dakko ke ya dama, duk abin ki yaran mu ne manya, magana ta akan d'ana ne da kika yi asiri da maitar ki ya koma barawo, ki karya asirin nan in ba haka ba, naki yaran har fashi da makami sai sun yi' 'Ta Allah ba taki ba, ba zan ga d'an fashi a yara na ba sai dai ke ki gani, wai ni me na tsare maku ne? Me ye matsala ta da ku ne a rayuwa? Ba abinda nake da shi wanda ba ku da shi, musamman ke Zainab, ki na da kyau, ilimi na boko da islama, ki na da azziki, Allah ya wadata ki da kyaun sura, me ye damuwar ku ne dani?' 'Yabon da ki ke samu wajen mazan mu shi ne matsalar mu da ke, kin hada har mazan mu kin mallake,ki tsaya a kan mijin ki, shi ne naki, shi kike da iko akai, mayya kawai dangin mayu' Nan Zainab ta ja hannun Fateema suka wuce, na zauna ina kuka, Mahboob ya fito daga maboyar shi ya durqusa gaba na, ya na son ya yi magana ya fasa ya fice. Tun daga nan bamu sake haduwa da su ba, dan ko na hango su wajen Goggo fasa zuwa nake, har na samu Allah ya sauken lafiya, na haife ki murna a wajen mu ni da Abeen ku ba a magana, ki na da wata sha tara muka je hajji muma. Na kawo masu tsaraba sosai da ta basu mamaki, amma suka amshe ba ko godiya, nima ba na buqata na yi ne dan Allah da zumunci. Kullum rikici akan yara, in dan kunne na sai maki, sai sun nemo sak irin shi sun sawa yaran su, gaki ki na son wasa, Mahboob na son daukan ki matuqa, amma mahaifiyar shi in ta gani tai ta fada. Ya na ajin shi na qarshe a sakandire mummunan lamarin ya afku. Aaseeyah na gama baki labari na, za so ace ki bari Mahboob ya qarasa baki wannan labari domin shi tashafa" "Har abada kuwa ba zan ji qarshen labarin ba indai shi zai ban" Cikin goge idon ta da ya yi ja dan kukan tausayin Mammeen ta ta juya baya ta kwanta, shafa kan ta Mammee tayi sannan ta ce, "Umarni na ke baki ba shawara ba, ki manta da komai, ki yi tunani, zunubi nawa ki ka aikata a duniya, kuma ki ke neman gafarar Allah akai, in Allah ya qi yafe maki fa saboda baki yafema bawan shi ba fa? Ki tunani akai, kuma ni aka ma laifi bake ba, ni kuma na yafe, ke a wa da ba zaki yafe ba? Ina mai sanar da ke komai ya wuce, ni ban riqe kowa ba, musamman zainab data riga mu gidan gaskiya" Shiru kawai Aaseeyah ta yi, qarshe ma bacci ne ya dauke ta, Mammeen ta ta rufe ta,ta ja mata qofa, ta wuce dakin ta, lokacin uku na dare ya wuce. Da asuba....... Akai meeeeeeeee Mu bari zuwa gobe muji me ya faru. Habaaa na ji dadin comments din ku gaskiya comment ai shi ne takin marubuci, a zuba ruwan comments a ga yadon shukar rubutu😂 na janye magana ta makaranta n ba marowata bane much love to u guys😍😍😍 TAUBASHI P 20 Da asuba Aseeyah ta tashi cikin farin ciki da annashuwa, har zuwa gari ya waye. Mammee da dikka mutanen gidan, banda ummee da ba su hadu ba zaci sun zaci za su ga Aaseeyah cikin baqin ciki da bata rai da kowa, sai ta basu mamaki, hankalin ta kwance kamar kullum, fara'a da walwalar ta na gado na manne a fuskar ta,kamar ma ba a taba bata labarin da ya quntata zuciyar ta irin na jiya ba. A bangaren ta kuwa ta san tunda take bata taba jin bacin rai da tsanar kowa irin na jiya ba, amma Mammee ta mata qarfa qarfa na dole ta yi hakuri ta yafewa kowa, ba yanda za ta yi illa ta aro farin cikin ta da annashuwar ta na da ta sanya ma fuskar ta kafin ta ga abinda hali zai yi. A tare su ka yi abincin safe da Mammee, su na girki ta ce, "Mammee, tun da na san ina da wani yare bayan larabci da fullanci, ki koya min Nufanci shima, ina qaunar yaren daga jiya zuwa yau,soyayyar shi ta kama ni kinga ga hausa da turanci sai ya zama ina jin yare shida cif" Dariya suka yi saboda yanda take maganar cikin nuna shauqin son yaren, Mammee ta ji dad'i kuwa, nan da nan fuskar ta ta haska, saboda shi kadai ne kadarar ta a garin su, shi kadai ne shaidar cewa itan ba bahaushiya ko bafulatana ko balarabiya, ko dai wata qabila ba ce ta daban, yaren ta da shi ta tsira, tunda mutanen ta sun yada ta, dan haka cikin zumudi, ta kalli Aaseeyah ta ce "To za mu fara da gaisuwa, kin shirya?" "Dan Allah a dan yi sauri a kawon abincin nan, zan makara, duk da dai na ga sauri kuke yi, amma a dan qara akan na da," in ji Abee da ya leqa cikin shirin fita aiki. "To inshaa Allahu, ka bamu minti biyu kacal" "Ina jiran ki mar'atussaliha" Murmushi ta yi mai kyau, Aaseeyah ta kalle ta ta ce "Ehhhhh Mammee you ar blushiiiinnggg? Kinga yanda fuskar ki ta sauya kuwa, wai dama har a wannan shekarun ana jin kunyar miji Mammee?" "Aaseeyah ba ki jin magana, ga tambayar tsiya akan aure,ko dai aure ki ke so ne a maki auren nan a huta?" "Mammee dole nai tambaya, tunda ban san komai ba, kwanaki ba dan Allah ya taimake ni na yi bincike akan wasu abubuwan ba a Internet ba da shi kenan an dinga min wayo kenan" "Me ki ke nufi da hakan" Mammee ta fada cikin nuna halin ko in kula, ta na magana ta na qoqarin hada abincin mijin ta za ta kai mishi, ba ta jira me Aaseeyah za ta ce ba ta fita, tare da fada mata, "Za mu ci gaba da koyon Nupanci anjima, bari na sallami Abeen ku, ki hada abincin Mahboob ki kai mishi" "To Mammee," (Da a ce ta maida hankali da ta ji meye matsalar diyar ta, wadanne kuraye ne ke farautar ta a tsakanin idanun su) Hada abincin ta yi tsaf ta dauka ta nufi bangaren Mahboob wanda ya ke a bude, kasancewar har yanzu 'yan biyu wajen shi suke kwana. Da alama tunda suka dawo masallaci ba su rufe wajen ba, da sallama dauke a bakin ta ta shiga, Mahboob na zaune a saman sallaya da qur'ani a hannun shi ya na karantawa can qasa, in ba ka saurara ba ba zaka ji muryar shi ba ma, hakan sai ya sa ja hankali Aaseeyah gare shi, wani takaicin shi da ta ke ji a qasan ran ta,ya ragu da kaso 30%, sai da ya kai qarshen aya ya kalle ta, murmushi ya ke son yi mata bai san da wacce ta zo ba, ya na son bata hakuri bai sani ba ko ta na ma da shirin saurarar shi,gani ya yi ta zauna a kusa da shi ta ce, "Yah Mahboob Sabahul khair" "Sabahul khair ya bintu al-3am, kin tashi lafiya?" "Na tashi lau qalau, ba haka ka zata ba ko, ka zaci zan tashi da ciwon zuciya ko da hawan jini, tunda kun saka uwa ta a gaba kai da iyayen ka ko?" Dariya ta dan yi wadda take qoqarin danne bacin ran ta, ta ce, "Kar ka damu, na aje komai a rayuwata ta jiya da ta gabata, ba ni da sauran dalilin riqe daya daga cikin ku, wadda ka sheme ka fasawa qeya ma ta yafe maka balle ni, wadda suka azabtar gangar jiki da ruhi ta ce ta yafe masu ballanta ni karan kada miya,me ye nawa a ciki, kawai dai jiyan labarin ya zo min a ba zata, tunda ko da wasa ba wanda ya taba daga maganar, shi yasa, hope kai ma za ka manta da komai, sannan anjima ka ci gaba da bamu labarin" "Kayyaa, a yanzu ma na tarwatsa zuqatan ku ballantana na baku sauran mummunan labarin da ba zan taba yafewa kaina ba, labarin da ya sa na tsangwami kaina, na nesanta kaina da qasa ta, da kowa nawa, dan tsira da rayuwa ta,inna cika gaba da bada labarin nan Umaimah za ta tsane ni, dikkan nin ku ma, na san ba wanda zai sake kallo na da mutunci" "Kar ka damu, d'an uwa, ka ba su labarin, ba abinda zai dawwama a boye, tunda ka dawo Nigeria watarana sai sun sani,ka sanar da su komai kawai, bawa ba ya wuce qaddarar shi" Jijiyoyin kan shi ne suka fito rudu rudu, da halin da ya shiga a yanzu gwanda ya yi kuka da hawayen shi da muryar shi, wataqila zai samu sauqin zuciyar shi. Aaseeyah na ganin haka sai ta yi shiru ta fara qoqarin hada masa tea, Noor da ya fito tun shigar Aaseeyah yake tsaye a wajen dan saka ido ya ga me zai gudana ya ce mata, "Barshi kawai ki je ciki,zan hada mana dika,sannun ki da aiki" "Toh Yah Noor" Ta na miqewa ya ga wandon da ke jikin ta, da rigar da ta kama ta, ya saki wata qaramar qara, da zabura kamar zai dake ta, "Keeee! Ashe ba ki da hankali? Ina ga sai na maki shegen duka a gidannan, jikin ki ya yi mugun tsami kamar ruwan yin awara zaki fi fahintar yaren da na ke, dan tsabar iskanci da wannan kayan dama ki ka zo, ina nan saqale kamar igiya ke kuma ki na yawo tsirara, Aaseeyah me ya sa ba ki jin magana ta ne? Ashe da ban ji muryar ki na fito ba haka za ki zo da wadanan yan iskan kayan a gama gane ki ki koma" Fad'an da ya ke ta zabgawa ya sa tashin hankalin da Mahboob ya shiga raguwa, dan kuwa duk wani mai rai ya gan shi a wannan halin sai ya yi dariya, 'Yan biyu da suka fito tun qarar da ya sake suna tsaye suna ta sheqa dariya, sai watsa siririn hannun shi yake a iska kamar zai sauke su akan Aaseeyah, da ido Hussien ya mata nuni da ta gudu, ai kuwa juyawa tai ta saiti hanya, ta sheqa da gudu, Noor kuwa kare ganin Mahboob ya yi kar ya ga gudun ta zuwa gida,girgiza kai Mahboob ya yi ya furta, "Noor da yarintar shi," "Waye yaron?" "Ni dai ban kula ka ba, ka yi alqawarin hada mana Tea hada mana na sha yunwa na ke ji" "Anqi a hada din, ashe ma ba yunwa ka ke ji ba in sai ka jira ni," Tsaki ya yi ya fada daki, 'yan biyu na ganin zai wuce suka manne da juna suka bashi hanya, ya na shiga suka kece da dariya, sun gano komai yanzu game da Noor, son Aaseeyah yake,wai shi Ustaz ba ya son a ga mishi budurwa da qananan kaya. Nan sukai ta gulmar shi qasa qasa su na karyawa, Umaimah ta kawo abinci itama daga wajen Ummee. Cikin shirin boko suka fito, lokacin bakwai da kusan minti arba'in, Aaseeyah na tsaye gaban mota ta na duba wani English book din ta Mahboob ya fita tsakar gidan ya na hango ta, lumshe ido ya yi, sannan ya furta, "Masha Allah, innaha Jamila" Kamar an ce ta daga kai, sukai ido hudu da shi,ba ta san sanda murmushi ya kwace mata ba, cikin jin kunya ta zagaya ta shige gaban mota, driver na zaune tin dazu dama a ciki, su Yesmeen ne suka fito cikin hayaniyar su, daga masu hannu Mahboob ya yi,suma suka daga mishi, tare da yi mishi sallama. Su na shiga suka ga Aaseeyah ciki, nan ta juya ta gaishe su, abin ma mamaki ya basu, meye haka? "Ke lafiya ki ke kuwa? Yau baki biya mana ba, sannan meye haka, wai gaisuwa, yaushe ki ka fara gaida mu?" "Yesmeen kenan, rayuwa kullum ilimi ka ke qarawa cikin ta, sannan girma in ka na yin shi ba hankali ba ka da maraba da jakin gida" Shiru suka yi kamar yanda ita ma bata sake magana ba, fatan ta Allah raba su da Malam salisu Tumbi, dan ba ta cikin yanayi na guje guje yau, a kame take. Ranar har aka tashi ba wanda ya kai qarar Aaseeyah, salin alim, har yan ajin su na tambayar ta ko bata da lafiya ne, nan fa ta huce takaicin da ke can cikin qasan ran ta a kan su, ta dinga surfa masu masifa har da zagin duk wanda ya sake tambayar lafiya take. Daga baya kuwa bayan ta fidda wannan boyayyan baqin cikin da ke cin ta, ba sai hira ba, da ta balle sai da suka tabbatar da wannan ita ce Aaseeyahn da muka sani. An tashi daga makaranta suka jira a gate, aka je aka dauke su sai gida. A daki ta ga Mammeen ta, abinda ba ta saba gani ba, kwance take ta juya baya, da dikkan alamu ba bacci take ba, zama ta yi a gefen ta,ta dafa ta, sannan ta ce, "Mammee na dawo, lafiya kike kuwa?" Juyawa ta yi tare da sauke ajiyar zuciya,sannan ta ce, "Sannun ku da dawowa, and lfy ta qalou, kawai dai jiki da jini, ban dan jin dadi ne na shigo na kwanta, ki je ki wanka ki ci abinci,na gama" "Ok Allah ya baki lafiya Mammee na" "Ameen my dear" Dakin ta taje ta cire kaya ta fada wanka,Mammee kuwa damuwa take akan labarin da suka dakkowa kan su suna son ji,ta tabbata Mahboob zai shiga mummunan hali ta wajen tunawa da baya, sannan wataqila zai samu mummunar tsangwama daga 'yan uwan nashi, amma tunda sun matsa ba yanda zatai, sai dai ta yi fatan Allah ya sa su fahimce shi. *************************** Tun da suka je masallaci bai dawo gida ba, Noor da 'yan biyu na hanya suna hirar rashin ganin shi da basu yi ba, "Ku ba yaro bane,wataqila ya na gida, in ba ya gidan ai zai dawo da kan shi,tin kan a haife ku ya ke zagaye wannan wajen, ba inda bai sani ba," in ji Noor. "Amma da da yanzu akwai banbanci ai,da ba gine-ginen da muke da shi a yanzu," Kamar an wurgo shi suka gan shi ya wuce su ya na haki, rufa masa baya suka yi suma a guje. Sai da suka shiga gida suka ga ya na bama mai gadi umarnin ya sa ido sosai in b mutanen gidan nan ba kar ya bude wa kowa, bangaren Mammee ya nufa, ya na kwala mata kira, da sauri ta fita kan ta ba ko dankwali, "Lafiya Mahboob ka ke kwala kira haka?" "Mammee na gan su, yanzu na gan su, da alama sun san na dawo, kuma su na kula da gidannan, suna kula da shige da fice na, an tashi daga masjid zan dawo gida na gan su,na ga Gazaa da ido na Mammee" "Innalillahi wa inna ilaihirraji'un, Ohh ni Subai'a na ga abinda ya qi qarewa a rayuwa ta, shin wai ba an ce an kama su ba? Me suke a waje ba a daure a gidan maza ba" "Ni fa ina zaton qarya ne Mammee,ko kuma an sake su ne ban san me ke faruwa ba,ba mai bamu wannan amsa in ba su ba" "Mahboob ka yi taka tsantsan, ka na sallah a gida, dan fitar ka bata da wani amfani, bari na sanar da Abeen ku ya ma 'yan sanda magana, dan a san matakin dauka" "Ah ah Mammee,ni shawarata ina so na hadu da su, na san da wadda suke tafe, mutanen nan a ganin da na masu sun fi da hatsari, ba dan na musu farin sani ba ma ba zan gane su ba," "Ka na da hankali kuwa? Su wa din za ka gani?" "Su Gazaa din," "Ehh lallai yaron nan baka da hankali, kan ka ya motsu, mutanen da ba su dauki rai a bakin komai ba tun da can su zaka je ka gani? Ka ce musu me? Ka san inda za ka gan su nema?....kaga ka nutsu, ka koma ka kwanta, ba na son ka sake fita, na ji Abeen ku ma na cewa za a sama maka aiki, ba inda zaka sai an tabbatar da komai lafiya," "Mammee zauna ki ji," Zama ta yi shi ma ya zauna, cikin nutsuwa ya mata bayanin mahimmancin haduwa da su, ya ce mata in ma suka ji shi shiru a sanar da hukuma, amma ya na da mahimmanci ya ji da me suka zo, dan indai za a ga wadannan yara a waje da irin sufar da ya gan su, to suna da daurin gi... a qasar nan. Ta fahimce shi dan haka dafa kan shi ta yi ta masa addu'a da neman tsari, sannan ta ce ya je ya sanar da Ummee. Ko da ya je ya sanar da ita ihu ta dinga zundumawa ta na ashar tare da zagin Mammee, ta na ce wa za ta tura d'an 'yar uwar ta wajen makasa, da kyar Mahboob ya fahintar da ita plan din su, ba addu'a ba komai ta dinga gyada kai alamar ta

Chapter 14 of 41