Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da ni me ne makamin da nake da shi bata da shi? Kuma mene ne dalilin da ya sa za a qara ma Hussein mata" "Sai da safe zan sanar da ke, yanzu dai ki samarwa da yayana abinci sannan ki sa masa ruwa ya yi wanka ya ji dadin jikin shi," "Tabb ruwan ma ni zan sa masa, ai ya iya hadawa da kan shi" "Hummm lallai baki shirya kwatar mijin ki ba, da Ruqayya ce har wanka sai ta masa, a yanda na san ta da iya tarairaya" "Ohhh dama kin san ta? Aaseeyah na jima da sanin banda maqiyi a gidan ku sama da ke," "Wai me ya sa baki da zurfin nazari ne? Na santa man saboda Yah Hussein, ko kin ji na ce ban san ta ba tun da can? Ya rage naki, matan yanzu miji irin naki da akai wasarairai da shi suke nema su aure su su yi masa abinda ba a masa, kinga tafiya ta, in kk gyara halin ki na maki alqawarin sawa a fasa auren nan,amma in ban ga sauyi ba, kin san Allah sai na zuga an aura masa wadda zata kula da shi kin dad'e baki kira ni maqiyyiyar ki ba, Yayana na ke so shima ya dangwali damukuradiyyar aure ehe,sai da safe" "Aaseeyah tsaya dan Allah, zo mu yi magana" "Da wa ni? Inaaa ai ba a magana da maqiyi,ni na tafi wajen miji na ya na buqata ta" Duniyar gaba daya ta yi wa Tasneem zafi, masifa ce fall zuciyar ta, amma in ta kalli wanda zata saukewa din sai ta ji gaban ta ya yi mummunar faduwa,ba zata iya ba, shi kuwa ya zauna a gaban ta ya na ta rantsuwa da karkata kai akan bai san wata me suna Ruqayya ba all his life. Miqewa ta yi cikin jin haushi har zata shige daki ta tuna kalaman Aaseeyah, kitchen ta nufa ta dora tukunya, ta dafa masa indomie da kwai, ta juye masa ta ajiye,sanan ta je bayi ta hada masa ruwan wanka me dumi, bata masa magana ba ta yi shigewar ta dakin yarinyar su ta kwanta da ita. Hussein kuwa ganin abincin nan ya motsa masa da yunwar shi,da sauri yake zuba loma,sai da ya cinye tass sanan ya dauke kwanon ya wanke ya ajiye. Bayi ya shiga ya ga ruwan dumi na wanka a ajiye,dakin da ta shiga ya je ya riqe murfin qofar,cikin sassanyar murya ya ce, "Naga ruwan wanka zaki amfani da shi ne?" "Ban sani ba, na ce ban sani ba,tunda ba a kunnen ka qanwar ka ta ce a saka maka kai wanka ba" Murmushi ya yi na jin dadi, for the first time tun auren su yau ce rana ta farko da ta taba saka masa ruwan wanka, da sai dai ya sa da kan shi, watarana har ya sa mata, ya yi ma babyn su wanka. Wanka ya yi, ya fita, ganin bata da niyyar komawa dakin su ne ya sanya shi rufe gidan ya kwanta a bayan ta,ji ya yi yau ya na shaqar iska mai dadi a jikin ta, duk da bata saka turare ba, ba tsamin nan dake damun hancin shi. Da safe ko da ya tashi bai ga Tasneem ba, a guje ya fita daga dakin ya na kwala mata kira,cike da damuwa,tun daga sanya qafar shi a parlourn ya ga sauyi, duk tarkacen kayan da ta jibge a parlour ta kwashe su,ta yi shara, ta yi goge goge, ga qamshin soyayyan kwai na tashi,hankalin shi be kwanta ba sai da ya isa kitchen din ya gan ta tsaye ta na soya dankalin turawa da kwai, duk ya dahu lugub ya na ragargajewa, amma ba komai, da babu gwanda ba dadi. Sai surutu take ita daya ta na aikin, "Na ga dan bur....uban da zai min kishiya a duk fadin garin nan,me aka fini iyawa? Mutane na baqin cikin su ga miji na maka bauta se a ce ka mallake shi" Rungume ta Hussein ya yi ta baya, tare da dora kan shi a wuyan ta,ya na sumbata. "Haba Sweet, da kan ki ki ke aiki haka? Baki bari na tashi ba" "Kai ni rabu da ni da munafurcin ku na maza, da ba ka je ka na talla dani ba da ba me sa mana ido, baqin cikin dan abinda ka ke min suke,to na hutasshe ka,ai ba wai ban iya bane,a zato na soyayyar mu me dorewa ce, ashe 'yan baqin ciki da sa ido da hassada,ba za su barta tai qarko ba" Shi dai shiru ya yi, bai magana ba, ta na gamawa ta kashe gas ta kai saman dinning table ta ajiye, yarinyar su ta hango hannun Hussein a guje ta isata ta amshe ta ta ajiye ta tare da jan hannun ta zuwa bayi, "Ba na son neman magana Husseini na fada maka ka rabu da ni na yi aiki na da kai na,tam shi kenan" A zafafe ta ke komai, yarinya kuwa ta ji wankan da bata saba ji ba ta dinga tsala kuka, a kan ta ta huce, ta dinga banka mata mari da duka, ta na fadin ta mata shiru, Hussein ba baki sai ido, suna gamawa ta hada masa ruwan wankan,tace ya shiga, ko uhum bai ce ba ya shige, bayan ya fito ya tarar ta fiddo masa da kaya ta ajiye ya saka ya na ta mamakin ta,abincin ta zuba musu ta hada shayi suka ci. Tsabar dankalin ya nadi mai ba su jima su na ci ba yarinyar su ta fara kwara amai,Hussein kuwa cikin shi ne ya juya, da gudu ya shige bayi. A ranar ba wanda ya iya fita a cikin su, sai riqe riqen shiga bayi suke, Allah ya taimake su ba bayi daya gare su ba, kafin azahar sun yi zuru zuru. Suna zaune a kujera a parlour Hussein ya kalli Tasneem ya ce, "Sweet ni dai dan Allah ko zaki aikin komai ki aje maganar girki, in ban yi ba na siyo,mu yi yanda muke yi a baya" "Baka isa ba Hussein, azzalumi,tunda kai in an maka aure holewa zakai da matar ka, ni nice yar iska na qarata ko?a haka din dai zan ta girkawa ai da koyo ake zama gwani" Shiru ya yi be ce komai ba,maganin da suka sha ba laifi ya daure masu ciki,zawon ya tsaya, wanka taje ta yi ta saka wasu qananan kaya tun na lefe ta ajiye taqi sakawa, ta yi kyau masha Allah, amma har yanzu ita ba tasan mahimmancin qamshi ba. Hussein kuwa sake baki ya yi yana kallon ta,daga baya kuma ya hau yabon ta tare da nuna mata jin dadin ganin ta da kayan,sai a sannan ta dan saki ran ta, suka dan yi hirar arziqi. Hassan ne ya yi sallama a bakin qofa,dan jin dalilin da ya hana Hussein zuwa wajen aiki yau, bayan sun gaisa ne Hussein ya masa izini suka shiga, mamakin ganin wajen kal Hassan ya yi, amma sai nan da nan ya ji ran shi ya baci, ya tabbata d'an uwan shi ne ya yi wannan aikin. Hussein ne ya masa qaryar ya tashi ba lafiya shi da Tasneem shi ya sa bai je ba, bai sanar da shi dalilin ciwon ba amma a ido ma Hussein din ya fada. Fatan samun sauqi Hassan ya mishi, sannan ya miqe zai tafi, Tasneem ce ta fito daga ita sai qananan kayan nan kai ba dankwali, mamakin Hassan ya qaru ne sanda ya gan ta riqe da tsintsiya da parker ta fito da su riqe a hannun ta, gaisawa sukai ya tafi. Ko da ya je ya na bawa Yesmeen labari,batai mamaki ba, dan ta san yanda Tasneem ke gudun kishiya, gashi Aaseeyah ba tare da ta san ma Tasneem na tsoron kishiyar ba ta fara maganin matsalar gidan yayan nata. Da la'asar sakaliya,Mahboob ya dawo hannun shi riqe da leda baqa, bayan sun gama soyayyar su ta barka da dawowa ya miqawa Aaseeyah ledar tare da kafe ta da idanu, "Mar'atee, anyaaa kar fa ki sa jinin 'yar mutane ya haye," Dariya sosai Aaseeyah ta bude ledar ta leqa, ta duba komai ta gan shi daidai yanda ta ce ya siyo ya siyo mata, murmushi ta yi ta ce, "Kar ka ji komai Roohee,ina zuwa,ai maganin shege karen maguzawa" Mayafi ta yafa a kafadar ta, ta dauki ledar, bata zame ko ina ba sai bangaren su Hussein....... TAUBASHI PGE 56 Sallama ta yi ta dokawa tare da kwankwasa qofa, da kyar Tasneem ta bude saboda gane cewa Aaseeyah ce ke buga masu. Ta na budewa ta tokare hannu a qugu,Aaseeyah kuwa kallon ta tayi daga sama har qasa, ta sake baki, tun da take bata taba ganin Tasneem ta yi kyau haka ba, riga da wandon sun amshe ta sosai sun kama dik wani sashe da lungu na jikin ta,sai dan tumbin ta da ya fito kadan,kan ta ta daure shi da band kalar kayan,duk da ba ya wani kyallin gyara a qalla an wanke shi. "A tsaye za ki bar qanwar taki,ba zaki min izinin shiga ba" Kyabe baki ta yi ta matsawa Aaseeyah ta shiga, "Shigo tauraruwa me wutsiya, dan gin miji ba a iya maku, meke tafe da ke?" Murmushi Aaseeyah ta yi, wato ita ce ma tauraruwa me wutsiyar, da kyau. "Sabon suna na samu me dadi haka, tauraruwa,to na gode,dama dazu gida na wuni, an kai sweets da kudin na gani ina so gidan su Ruqayyah, wannan kason ku ne, na kai wa Yesmeen nata ba sai kin debar mata ba" "Kutu.......uban can kayya sa, kudin I see I love din uban wa aka kai? Aaseeyah ki deben kayan nan ki fita kan na maki dukan mutuwa" "Ni za ki wa dukan mutuwa? Lallai baki da cikakken tarihi na ashe, ni da ki ka ganni ruwan sama ma ba na bari ya taba ni balle hannun mutum,ganin gidan fess ya sa naji a raina zan temake ki a fasa auren nan amma kin san me? Da ni za a kai lefe, kin daken da hujja" Kuka Tasneem ta tsanyara kamar yarinya Hussein ne ya fito a gigice da alama bacci ma yake, fess Aaseeyah ta gan shi amma ya rame,sai ta ji dadi ya kama ta,ficewar ta tayi ya na ta tambayar me ya sa gimbiyar shi kuka. "Dakko makullin mota gidan Mammee zamu yanzu" "To" Shi ne kawai abinda ya ce ya juya dakkowa. Magariba a gidan ta musu,bata bari ya gama tsaida mota ba ta fice, doguwar riga baqa ta sanya da mayafin rigar, sai baqar qatuwar ledar da ke hannun ta cike da alawa kala kala. Da sallamar ta da kiran sunan Mammee a tare ta yi su, Mammee da ke gyara saman dinning ta daga ta kalle ta ta amsa sallamar da kuma kiran sunan nata. "Bismillah qarasa shigowa" "Ba zama ne ya kawo ni ba, na zo na ji dalilin da ya sa ki ke son ki min kishiya bayan ke gaki ke kadai a naki gidan, ku na min baqin cikin zama da miji na lafiya da muke," "Keee Tasneem Mammeen ki ke fada ma magana haka? Zan iya jure komai daga wajen ki ba zan dauki wulaqanta uwa ta ba,ni kaina na zo na ji dalilin qara min aure ne, amma ban zo da rashin kunya ba, kar ki kuskura raina ya baci zan iya amincewa da zabin ta ki kula" Baki Tasneem ta sake, tunda suke Hussein bai taba mata tsawa ba shekara da shekaru sai yau,tabdijam,dole ta tausasa harshe, kar ya juya mata baya, kuka ta fashe da shi ta yarda ledar a qasa, sweets suka zube, durqusawa ta yi a kusa da Mammee ta kama qafar ta sannan ta ce, "Dan Allah Mammee kar ki qarawa Hussein mata,in Hussein ya min kishiya zan kashe kaina, ba zan iya ganin wata ta rabe shi ba da sunan zaman aure, dan Allah Mammee komai ki ke so ki fadan na miki, amma kar ki qara masa wani auren, kin ga ni marainiya ce shi kadai ne uwa ta, shi ne ubana, shine komai nawa" Ta bawa Mammee da Hussein tausayi sosai, saboda kuka take da ke nuna me ne ne a cikin zuciyar ta,dan haka Mammee ta daga ta suka zauna, ta sha wahala kafin ta yi shiru, har sai da Abee ya dawo suka gaisa ya shige daki. "Tasneem, ni ba wai zan qarawa Hussein aure bane dan na tsane ki, ah ah, ke ce fa uwar diyar shi, abu daya ne ya sa na ke son ya qara aure, saboda kinga ke aiki ya miki yawa, baki da lokacin kula da mijin ki,yaro na duk ya bi ya lalace, ki wa kan ki adalci ki fadi gaskiya, wannan shi ne yaron da kika fada soyayyar shi shekarun baya da suka wuce?" Tasneem kallon Hussein ta yi, wanda idan shi ya kada ya yi jawur, sai a sannan ta kula da baqin da ya yi, ya rame, ga shi ba wani askin kirki,kada kai ta yi alamar ah ah, "To fisabillahi Tasneem tunda aiki ya maki yawa baki da lokacin kula da yaro na sai na qi nema masa wadda zata kular min da shi? Ki fa duba ki ga shekaru na, amma har yanzu ni nake ma Abeen ku girki, ni nake gyara gidannan, ni nake ma Abeen ku wanki, na yi guga,sanda ya ga na gaji sosai sai ya kwashe ya kai wanki ba tare da na sani ba, sanda ya ga aiki ya sa na gaji har na yi bacci ban tashi da wuri ba ya shiga kitchen ya mana abun karyawa su shaida ne ki tambaye shi gashi nan, amma inna tashi da wuri zan qarasa abinda ba ai ba, ke bari na cire kunya na fada maki wata magana, kin ganni nan,har yanzu muna wanka tare da miji na, ya cude ni na cude shi,mu na cin abinci tare na bashi a baki ya bani a baki, muna wasanni na soyayya amma akwai girmamawa da mutuntawa, wanda ke kin raina mijin ki, saboda kawai ya na da sauqin kai, daidai da fitsari rannan da yarinyar nan ta yi a gabana kika aike shi ya debo ruwa da tsumma ya saka mata ya goge waje ya sauya mata pant, hauka ake? Ke baki san ki bauta masa b ke d zaki samu aljannah ta dalilin biyayyar aure shi ne zai bauta maki? Kin so kan ki da yawa Tasneem, ki duba tun da kika shigo gidannan kin ji wari? Ko kin ji jiki na wani waje na fidda wari? Ban yi wankan yamma ba amma ki shinshina ni ki fadan ina wari? Tasneem baki san meye amfani da turare ba,suna nan tun na lefe an ce kin jibge baki bayar ba, baki amfani da su ba. Sannan gaki baki san gyara kai ba, balle brush,warin da ke fita daga jikin ki da ga ji na rashin shaving ne, baki aske gaban ki balle hmmtar ki,haba Tasneem, wace ce mace in bata gyara? Ke baki san mutuncin kan ki ba baki gyara kan ki ba balle mijin ki da diyar ku. Yanzu ya dace ace kamar Hussein da ya taso a gidannan da tunda muke ko biki ko suna ko sallah bamu taba siyo abincin waje ba ya na yawon siyan abinci? Ke meye aikin ki, na sani musulunci cewa ya yi maza su ciyar da mata, amma mu a qasar hausa maza na kawo komai na girki mu kuma kyutatawa ne mu girka masu su ci,muma mu ci, to Tasneem ni mai iya janye maganar auren nan ce a yau ba sai gobe ba, amma daga yau zuwa har abada in kika koma qazanta da son jikin ki zan nema masa mata,ke ko ba rai na na bar wasiyya a sama masa mata, ba zan zauna yaro na ya wahala ba, Allah bai yo shi cikin wahala ba." Kuka sosai Tasneem take, kuma maganganun Mammee sun matuqar shigar ta, tabbas bata kyautawa, ita a ganin ta isa ne da mallaka ka dinga bautar da miji, ashe isa da mallaka shi ne miji ya isa da kai, ka bauta masa ya so ka ya girmama ki saboda wannan kyautatawar kema da kike masa. "Mammee inshaa Allahu zan gyara daga yau, b wai na fadi haka bane dan a fasa auren, ah ah ina son gyara wa ne dan hakan shi ne ya dace da rayuwa ta," "Da kyau Tasneem, ina son mutum mai amsar gyara, Allah ya taimake ki, kuma na maki alqawari ko da Aaseeyah bata koya maki girki da kula da miji ba ni da kai na zan koya maki, wa nake da su a duniya da ya wuce ku? Ki dauka ni ce uwa kuma Abee shi ne mahaifin ki, mu ne iyayen ki a yanzu, Allah ya jiqan iyayen ki, kar ki sake jin cewa baki da kowa, mu na nan da rai, amma ban maki alqawarin zan sangarta ki ba, in ki kai ba daidai ba zan nusar da ke, ba zan saka maki ido ba, ina fatan ba zaki dau hakan a takura ba" Kuka sosai Tasneem ta sake fashewa da shi,tabbas ta tafka babban kuskure a baya, mutane masu karamci ta ke wulaqantawa haka, daga yau ta yi alqawari tsakanin ta da Allah zata gyara rayuwar ta. A ranar dai a gidan Mammee suka ci abinci, sai da kwalla ta taru wa Mammee a ido ganin yanda yaron ta ke cin abinci kamar wani mayunwaci, wanka ta sa ya shiga tsohon dakin su ya yi, ta bashi abun shaving ya yi ya gyara fuskar shi ya fito fess, sai qamshi yake zubawa, sabuwar jallabiyya ta Abee ta bashi ya saka, Tasneem na ganin haka ta ce itama sai Mammee ta bata kayan qamshin ta yi wanka zasu tafi. Ba bu kunya ko jin nauyi Mammee da kan ta ta nuna mata yanda za ta yi shaving, da wuraren da ya kamata in ta je wanka ta fi bawa mahimmanci, Qasan nonon ta Wuyan ta Tsakiyar cinyoyi Bayan kunne Tsakanin hannayen ta Cinyoyin ta Bayan qafar ta Bayan ta Da dik wata gaba ta jikin ta. Sannan ta nuna mata yanda zata yi brush mai kyau, da wuraren da ya kamata ta wanke sosai. Saman harshen ta,har ta dan ciki kadan yanda ba zatai amai ba. Dasashin ta Haqoran ta ta ciki da ta waje. Sannan ta sanar da ita kafin duk ta fara wankan ma kai ya kamata ta fara wanke wa, ta nuna mata yanda zata yi amfani da hannun ta wajen wanke kan, sannan ta fita. Tasneem ta jima a bayin kafin ta fito, bathroom din Aaseeyah ne, dan haka kayan wankan dik irin na Aaseeyah ne,sai ta ji ta na qamshi irin na Aaseeyah, dan murmushi ta yi, a da har cikin ran ta take jin tsanar Aaseeyah, amma yanzu sai ta ke jin ta kamar qanwar ta ta jini. Turarukan ta ta fesa ta maida doguwar rigarta, Mammee ta kawo mata wasu kayan bacci masu kyau, ta ce, "Haba Tasneem, ai mace bata wanka ta maida kaya masu datti,ga wannan ki saka, ga hijabin nan, ki saka, maza ku wuce, dare na yi, Abeen ku na ta fadan jimawar ku, bai san me ke faruwa ba," "Ban gane bai san me ke faruwa ba Mammee, bai san za a min kishiya ba?" Murmushi Mammee ta yi sannan ta ce, "Gaskiyar magana ba wata kishiya da za a maki, wannan duk qullin Aaseeyah ne saboda ki gyara halayen ki, bamu zaci zaki sakko da wuri haka ba, dan har sabbin akwati sai da yarinyar nan ta ce zata siyo ta nuna maki na kai lefe ne" Kama baki Tasneem ta yi, daga baya ta fara dariya har da hawaye, "Waiii Allah na, amma Aaseeyah ta san ta kan tsiya, ba komai, ni kuma inshaa Allah wannan mugun fatan ba zai sake rab'a ta ba" "Allah ya sa" Kayan sun amshi jikin ta sosai, kalar orange, hijabin kalar baqi, har ja yake da qasa, sallam suka wa Mammee, suka tafi. Tun a mota Hussein ke sanya hannun shi a hijabin Tasneem ya na taba ta, ita ma dadi take ji dan qamshin da ke fita daga ko ina na jikin ta, abun ba a cewa komai. Sun isa gida qarfe 10 na dare, bangaren su Aaseeyah Tasneem ta nufa, ta dinga bugawa, Suna can suna shan love din su suka ji bugu, Mahboob danna kan shi ya yi a cikin Aaseeyah ya saki qarar takaici, ita kuma hakan sai ya mata kamar cakulkuli ta ding kyalkyala dariya, sauka ta yi daga saman cinyar shi ta dauki rigar ta ta mayar, ta ja mishi tashi ta rufe masa cikin shi da ita, hula ta sanya, ta n dariya ta je ta bude qofa, dariyar ce ta tsaya a wuya da ta shaqi irin qamshin ta,ta kalli Tasneem daga sama har qasa, ita kuma ta na mata wani shu'umin murmushi, hijabin ta ta daga Aaseeyah tai ido biyu da kayan jikin ta,sannan ta sake tai gaba ta na takun yanga ta na dariya, "Aunty Tasneem gidan Mammee kuka je?" "Ina ruwan ki, sai da safe, muma yanzu mun shiga layin 'yan gayu" Tana tafe take magana da qarfi, Aaseeyah kuwa bakin ta ya kasa rufuwa,da ta hango Hussein ya yi shaving fuskar shi, ya yi kyau, Tasneem saqale hannun ta tayi cikin na Hussein suka saka yar diyar su a gaba suka shiga gidan su, Aaseeyah na tsaye ta na dariya mai cike da jin dadi. A haka Mahboob ya same ta, dan haka tsalle ta yi ta fada jikin shi, sannan ta ce, "Ka tuna na ce zan rama me ka mun rannnannn? Sanda ak kawo ni dinnannnn???" Cikin murmushi ya daga kai, ya ce, "Eh na tuna," "To yau ce ranar da zan rama" Daga ta Mahboob ya yi suka shige daki suna dariya, sand'a na yi na je zan bude na leqa na ji sun saka key, dole na na lallaba na koma parlour ina tura baki........ TAUBASHI PAGE 57 Shaquwa ce mai qarfi ta shiga tsakanin Aaseeyah da Tasneem, wanda abun ya ke bawa Yesneen mamaki, sai da Aaseeyah ta mata bayanin komai, tai ta dariya ta na yabawa Mammee da Aaseeyahn kanta da ta kawo wannan shawarar. A hankali Aaseeyah ta fara sanin asalin wace ce Tasneem,wanda sanin nata ya yi matuqar girgiza ta,tare da bata mamaki, shi ya sa aka ce a rayuwa kowa na da labarin bayarwa game da rayuwar shi,kar ka yanke ma kowa hukunci ba tare da ka san shi ba. Watarana Yesmeen, Tasneem da Aaseeyah na wajen da suka mayar wajen zaman su a gidan, waje ne da 'yan shuke-shuken gidan suke, da kujerun siminti,su na ta hira, Yesmeen da Aaseeyah na ba ma Tasneem labarin gidan su, yarintar su da rayuwar makarantar su,Tasneem wadda a yanzu ta zama black beauty, baqin ta mai kyau ya goge ya na sheqi, fuskar nan ba wata cikakkiyar kwalliya sai asalin kyaun da Allah ya mata,ta zama mace mai aji mai ji da gayu da qamshi, murmushi take amma da ka kalli murmushin ka san mai ma'anoni ne da dama. Shiru Aaseeyah ta yi da dariyar da take ta zabgawa,ta kalli Tasneem, ta ce, "Aunty na lafiya kike?" Dan yaqe ta yi ta kalle su, ta ga yanda fuskokin su suka nuna damuwa akan halin da ta shiga, nan da nan idanun ta suka kawo ruwa,abinda take dannewa a zuciyar ta ya yunquro mata, zuciyar ta na tafasa da quncin da take ciki, cikin rudewa su Yesmeen suka nufe ta, suka zauna gefe da gefen ta,suna lallashin ta, sai da ta dau kusan minti biyar ko sama da haka ta na kuka, kafin ta share hawayen ta, ta sanya murmushi mai ciwo a saman fuskar ta, "It's ok,komai ya wuce, yanzu komai ya zama tarihi, ina gidan miji na, mai so na dik da ya san wace ce ni, kuma ina tare da qannen da Allah ya bani ba tare da iyaye na sun haifa ba,ina godiya ga Allah da ni'imomin shi a gare ni wanda ba zan iya qirga su ba,ya bani 'ya kyakkyawa, ya bani ilimi, na gode wa Allah, Allah ya jiqan iyaye na da dikkan musulmi," A sanyaye su Yesmeen suka amsa da, "Ameen" Aaseeyah ce ta koma kujerar da ta tashi, saboda sun matsu a waccan din, kallo ta bi Tasneem da shi, ta na son tambayar ta me ya sanya ta kuka haka, amma ta na ganin Jassasa haramun ne ba kyau, in ta so su sani za ta sanar da su,in bata so ba shi kenan, ciki dama ba dan cin abinci kawai aka halicce shi ba, ya na da amfani wajen boye sirrika. Lemo ta kurba ta na ci gaba da kallon Tasneem din ta cikin glass cup din, juya

Chapter 35 of 41