a zaune,murmushi ya yi sannan ya shafa gemun shi ya ce,
"Da alama Bilal yau yana so na bishi har gida na ji saƙona."
Yana nan zaune mutane suka fara zuwa jefi-jefi,Bilal kuwa be zo ba sai da takwas ta buga,tin daga nesa Abdul ya hango sabuwar motar Bilal na shiga building ɗin,cikin sauri ya buɗe tashi motar tare da rufe ta da makulli ya isa wajen aminin nashi,gani ya yi Bilal ya fito fuskar shi a tamke kamar wanda aka baiwa wani mummunan labari,gaban shi ne ya yi wani irin faɗuwa har sai da ya jingina da jikin motar shi,jiki babu ƙwari ya fara takawa zuwa wajen Bilal,a hankali Bilal ya kalle shi ya yi masa nuni da ka su haɗu a office,Abdul ji ya yi kamar ƙafafun shi ba za su iya ɗaukar gangar jikin shi ba,a hankali ya furta.
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'una,ya Allah ka bani wuyan ɗaukan duk abinda zan ji daga Bilal,mai kyau ko akasin hakan."...........
*Soyayya ruwan zuma ce...idan da Deejee a gefen Abdul ba zai ƙi murmushi baaaaa.*
[09/08, 10:39 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 108:
A office ɗin Bilal suka yada zango, Abdul dai sai zare idanu yake yi yana jiran Bilal ya sanar dashi abinda iyayen shi suka yanke game da auren shi da Hadiza. Bilal kuwa sai ja masa rai yake yi ta hanyar yin wasu ƙananun ayyukan da basu da wani mahimmanci a wajen Abdul,cike da ƙosawa Abdul ya ce,
"Wai dan Allah meye ka ke yi haka? Ka yi sauri ka sanar dani abinda kuka tattauna kada zuciya ta ta buga saboda zullumi."
"Lallai Abdul ka isa,yanzu a gabana ka ke ikirarin bugawar zuciyar ka saboda Hadiza? Hadiza fa."
Haɗe fuska Abdul ya yi sosai kafin ya ce,
"Ban gane Hadiza fa ba? Me kake nufi da maganar ka? Dan Allah ni ka ajiye maganar wasa ka sanar dani abinda Mai Martaba ya ce, ko dai basu amince bane?"
Ajiyar zuciya Bilal ya sauke kafin ya ce,
"To magana ta gaskiya dai haƙuri zan fara baka dan kuwa....."
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'un ! Shikenan sun yanke min farin ciki na,Bilal ya zan yi yanzu? ina zan...."
Dakatar da Abdul bilal ya yi kafin ya ce,
"Ka taimake ni ka natsu Abdul,ina baka haƙuri ne akan ja maka ran da na yi ne,amma mai martaba da Innah duka sun amince da auren ku kai da Hadiza a karo na biyu."
Galala Abdul ya saki baki yana kallon Bilal,kafin daga baya ya miƙe tsaye cike da farin ciki ya rungume Bilal yana murna,cikin sauri ya fita daga office ɗin Bilal ya faɗa nashi,sai da ya kulle ƙofar da makulli dan kar ma a dame shi sannan ya samu waje ya zauna a kujera. Wayar shi ya ɗakko daga aljihun rigar shi ya nemo No Hadiza da ya mayar mata da sunan ta na da wato Baby. Bata wani jima tana ringing ba Mommy ta ɗauka,cikin kashe murya Abdul ya ce,
"Baby ya kike?"
Jimm Mommy ta ɗan yi tana wani lumshe idanu saboda jin sunan da ya kira ta da shi,ta jima tana mafarkin sake jin wannan sunan a bakin shi,ashe dai da rabon mafarkin ta zai zama gaske,shirun da ta yi ne ya sanya shi gane halin da ta shiga,wani murmushi ya saki dake can ƙasan maƙoshin shi,har sai da Mommy ta ƙanƙame wayar saboda vibration ɗin murmushin da ya sauka a kunnen ta,cikin sake maƙale murya yanda ya san yana rikita ta a baya Abdul ya sake cewa,
"Baby ko baki jina ne? Hello?"
A sanyaye Mommy ta ce,
'Ina jin ka mana,kawai ina mamakin saurin zaƙewar ka ne bayan babu wata ƙwaƙƙwarar maganar iyaye a tsakanin mu.'
"Ki kwantar da hankalin ki Babyna,Mai Martaba da Innah sun amince ki sake zama surukar su,uwar jikokin da zaki sake haifa musu anan gaba,dan haka idan kin bani dama ko yau ɗin nan ma sai aje nema min auren ki."
Zaro ido tayi waje,sannan ta karɓe hannun ta da ake zanawa baƙin lalle ta tashi tsam daga wajen ta koma ɗaki,saman gado ta haye ta na lumshe idanu ta ce,
'Sorry ka jini shiru ko? Na ɗan tashi ne daga wajen mutane,ammm game da amsar abinda kace,ka ɗan jira har mu dawo daga tafiyar da muka yi,saboda har Baban muka taho Abuja.'
"Wait ! Dama kina nufin bada saurayi ki ka tafi ba da Baba ne?"
Dariya Mommy ta yi kafin tace,
'Ni dama na ce maka na yi tafiya Abuja da saurayi ne? Daga ni sai Baba se Yah sule muka tafi.'
Shiru ya yi yana nazarin maganar ta,nan take ya gane me ta yi masa,murmushi kawai ya yi suka ci gaba da zubawa junan su kalaman soyayya kamar ba za su rabu ba,da ƙyar mommy ta yi nasarar bashi haƙuri suka yi sallama tare da alƙawarin kafin ya koma gida za su yi waya.
Wunin ranar Mommy da Abdul sun yi shine cikin farin ciki,a haka aka ci gaba da hidimar bikin su Anisah da Khaleesat,ranar Juma'a na zuwa aka ɗaura aure washegari aka yi dinner,sanda aka tashi daga dinner angwaye suka kwashi matan su da kansu babu ƴan rakiya suka wuce da su gidajen su. Tin a daren ranar Ɗan Liti ya ce wa Mommy da sule su shirya da sassafe za su koma, zai ɗauki fasinjan kano a tasha,dan haka kar su ɓata masa lokaci.
Ranar Mommy a gidan Saddiqa ta kwana ita da Sule da Sadeeq,sun sha hira sosai,inda Sule yake basu labarin abokin shi da ya ɗana masa tarko a nan Abujan,ashe neman maza abokin yake yi ya b'oye masa,duk tsawon lokacin da suka ɗauka a baya suna abota a Facebook shi son Sule yake yi ba tare da Sule ya sani ba,dan haka shida abokan shi sun gama haɗa duk ranar da Sule ya shigo gari to fa za su haɗu a yi party da murnar haɗuwar su ta farko. Ganin Sule ya jima da haƙura da rayuwar da ya yi a baya ne ya ga bashi da dalilin haɗuwa da abokan shi na Facebook har a haɗa party da mata da maza,wannan dalilin ne yasa duk yanda suka yi ya je ya ƙi,ƙarshe shine abokin ya kira shi ya dinga ɗura masa ashar yana sanar da shi da ya kuskura ya je da sai an yi masa ɗinki a bayan shi,domin kuwa kaca-kaca ya yi niyyar yi masa ya kauda kwad'ayin sa akan Sulen. Tinda Sule ya ji wannan mugun tanadin da suka yi masa sai ya ƙi zuwa koda wajen ɗaurin auren ne,bashi da burin da ya wuce ya wayi gari ya ganshi a ƙauyen Ba Mugu.
Dariya Mommy da Saddiqa suka dinga yi masa,domin kuwa har a wannan lokacin da yake basu wannan mugun labarin zufa yake yi,duk da sanyin Ac dake parlourn.
Suna tsaka da dariyar sule ne Mommy ta sanar da su abinda ke tsakanin ta da Abdul,murna suka taya ta sosai,Sule ya hau yabon Abdul sannan yana yiwa Mommy faɗa akan yanda zata zauna da mijin ta da abokiyar zaman ta lafiya,shiru tayi tana sauraron shi, dan kuwa ko be faɗa ba yanzu ta yi karatun ta nutsu,kishi ba nata bane tinda a yanzu wata zata tarar,sannan ta yi zama da Meron Malam da Tsahare ta koyi yanda zata yi controlling kishin ta akan Abdul.
Tsaraba sosai Saddiqa ta haɗa musu,sannan ta bada wanda za su baiwa Sadeeq da ya maƙale wajen Munir,ba ta manta da su Innoh da Baaba ba a tsarabar ta,har ma da Amir. Alƙawarin zuwa auren Hadiza ta yi koda kuwa kwana ɗaya zata yi ta juyo a jirgi duba da yanayin karatun ta baya buƙatar wasa.
Suna nan suna hira Sadeeq da Munir suka dawo,suma zama suka yi aka dasa sabuwar hira da su,kafin daga baya kowa ya wuce makwancin shi.
Washegari da asubar fari bayan sun yi sallah Munir ya kwashe su ya kai su gidan Alhaji Baban Gidan,koda Sule ya leƙa ɗakin baƙi sai ya tarar da Ɗan Liti dake ta faɗan da sassafe za su wuce ya baje a ƙatuwar katifa yana bacci abun shi. Dariya ya yi ya ja masa ƙofa,Ummi ce ta fito sanye da wani ɗanyan leshi a jikin ta sai baza ƙamshi take yi, idanun nan nata duk sun zurma ciki,da alama bata samu isasshen bacci ba da dare,jikin ta duk babu wani kuzari suka gaisa da su Mommy,cike da tausayawa Mommy ta ce,
"Ummi ya kewar su Anisah kuma? To Allah ya basu zaman lafiya da zuri'a masu albarka,ya kamata yanzu da basu nan ki samo masu aiki saboda ki samu masu ɗebe maki kewa da taya ki aiki."
Kallon gidan Ummi ta yi sannan ta sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi kafin ta ce,
"Ke dai bari Mommy,ji nake yi kamar na rabu da wani ɓangare na jiki na,ban shiryawa tafiyar yaran nan gaba ɗaya ba a lokaci ɗaya,tsakanin jiya da yanzu da na fito na san tabbas zan sha wuya kafin na saba da rashin su."
"Inshaa Allahu komai zai zo maki da sauƙi Ummi,ga ƙaramin mai gidan ki nan yana taya ki hira ai baki da matsala."
Murmushi Ummi tayi kafin ta ce,
"Dama Baban ku zai bar min ke koda na sati biyu ne,da na ji daɗi."
Cike da zaƙewa Sule ya ce,
"Tabdijam ! Ai idan Baba ya bar maki ita na wata ɗaya ma tsohon mijin ta ba zai bar maki ita na sati ɗaya ba,dan kuwa ya dawo da zafin shi,so yake a sake ɗaura musu aure kwanan nan."
Mommy ce ta sunne kai cike da jin kunya kafin ta ce,
"Kaiii Yah sule faɗi ba a tambaye ka ba sannu da aiki,kai Sadeeq je ka ka taso Baba kar ya ga laifin mu kuma ya ce bamu tada shi ba."
Murna sosai Ummi ta taya mommy,kafin ta miƙe ta shiga ɗakin da ta tara gift ɗin su Anisah da suka yi saura,kaya ta dinga ɗibarwa Mommy har bata san iyakar su ba,ta dai san zannuwan gado sun fi yawa a ciki,sai da ta cika mata wata babbar jaka sannan ta kira Sadeeq ya je ya fito da jakar,albarka ta sanya wa Mommy sannan ta yi mata alƙawarin zuwa auren ta idan lokaci ya yi,cike da murna ta ce,
"Za mu zo har da Sadeeqa itama ta ga gida,ta jima bata zo ba saboda makaranta,gashi yanzu lokaci na ta tafiya ta yi nisa da karatun,Allah ya nuna mana lokacin,kar a manta a sanar damu da wuri."
Shiru Mommy ta yi tana jin kunya,Sule kuwa ya amshe addu'ar sannan ya ce,
"Da kaina zan sanar dake Hajiya Ummi,"
Munir ma ba a barshi a baya ba wajen baiwa Mommy kuɗi yace ta sayi wani abu,da ƙyar ta karɓa saboda nauyin shi da take ji,Ɗan Liti na fitowa sai ya hau masifa yana zagin yaran tare da faɗin,
"Idan na rasa fasinja a tasha dik se kun biya kud'in mota."
Dariya suka hau yi masa,kafin Ummi ta ce,
"Ai kuwa duk saurin ku kun tsaya ku ci abinci ko? Ina nan da sauran abinci Mommy biyo ni mu dumama kowa ya ci ya koshi,akwai abubuwan da na tanada saboda Baaba da Innoh da basu samu halartar bikin ba."
Bayan ta Mommy ta bi suka je suka haɗa abinci suka dawo,kowa ya zauna ya ci ya ƙoshi suka ɗebi wanda za su ci a hanya,suna tsaka da shiri Alhaji ya sakko suka gaisa, kuɗi mai yawa ya baiwa Ɗan Liti ya ce a sha mai, godiya sosai suka yi musu har da shi aka fita raka su Ɗan Liti,motar shi ya buɗe ya shiga ya kunna, nan da nan Sule da Saddiq suka zuba kaya a bayan motar ta cika famm,sannan suka zauna a baya,a haka ya wuce dasu tasha ya kwashi mutum biyu da za su je kano, ɗaya a baya, daya a gaba sannan suka bar garin.
*************************
Tafiya ta yi kyau dan kuwa da misalin karfe ɗaya suka isa kano,direct tasha Ɗan liti ya nufa ya ajiye mutanen nan,sannan ya yi lodin ƙauyen Ba Mugu,daga nan suka sake kama hanya sai gida.
Sun isa garin Ba Mugu ana kiran sallar la'asar,Ɗan Liti har cikin gari ya shiga da mutanen nan ya ajiye su a ƙofar gidan shi,kowa ya ɗauki dan ƙullin kayan shi da babu wani yawa ya wuce gidan shi,suna shiga gidan suka tarar da Ameerah zaune tana ta tsartar da yawu saboda sabon cikin dake tattare da ita,cike da murna suka hau gaisawa da mutanen gidan,nan suka baje a tsakar gidan aka raba tsaraba,Baaba sai murna take yi da farin ciki,ƙarshe sai da ta yi kukan murna jikokin ta sun samu mijin aure a lokaci ɗaya, addu'a ta yi musu sannan ta ce,
"Hadiza kema Allah ya fitar maki da miji na gari ki yi auren ki."
Cike da zumuɗi Saddiq ya ce,
"Ai Baban Amir ya ce zai turo a yi maganar komawar ta gidan shi in ji Yah Sule."
Takalmi Mommy ta ɗauka ta jefe shi da shi kafin ta miƙe da jakar kayan da Ummi ta bata ta wuce ɗakin ta,dariya Sule ya kwashe da ita ya ce,
"To ai gashi nan kin kwashe kayan auren naki da aka baki,idan baki son auren se ki faɗa mana amma ba ki hau jifan yaro ba dan ya faɗi gaskiya."
Kowa ya taya Mommy murna banda Ameerah da Ɗan Liti,Ɗan Liti jira yake yi ya ji shin Mommy ta amince da sake auren Abdul? Ita kuwa gwaskiya Ameerah takaicin ta bai wuce na Abdul yana da wata matar a gidan ba,Mommy zata je a ta biyu kenan,nan take ta karkace baki ta ce,
"Ai da mun san haka zata kasance da baki kashe auren ki ba kin yi zaman ki a ɗakin ki,gashi nan yanzu zaki koma a ta biyu."
Innoh ce ta ce,
"To bismillahi zaki fara halin ko? Ki raba ni da kunji-kunji Ameerahh,ai yanzu dai magana ta ƙare,abinda ya faru ya riga ya faru sai a tari gaba,Allah ya basu zaman lafiya."
"Amin"
Shine abinda kowa ya ce kafin su tashi zuwa yin sallar la'asar.
Da misalin shida na yamma wazirin sarkin garin Ba Mugu da sarkin Fada da wasu baffanin Abdul ne suka zo har ƙofar gidan Ɗan Liti a mota,rasa inda zai saka su Ɗan Liti ya yi,koda ya shiga gida ɗakin Baaba ya wuce direct,ita ce ke da carpet da babbar tabarma,kwasar su ya yi bayan ya sanar da ita me ke faruwa, ya wuce soro ya shimfiɗa musu suka zauna,sai da ya tabbatar sun zauna sannan ya koma ciki dan sama masu ruwan sha,Baaba ce ta bashi ruwan roba da Alhaji Baban Gida kan siya mata guda sha biyu,komawa ya yi ya ajiye musu sannan ya zauna dan a gaisa,suna tsaka da tattaunawa akan neman auren Hadiza da suka zo Baaba ta baiwa Sule dake ɗaki yana hutawa sauran snacks ɗin da suka kai mata tsaraba ya kai soro,sai da ya saka shaddar shi da ya yi niyyar sakawa ranar ɗaurin aure tsoro ya hana shi fita sannan ya kai musu snacks ɗin, godiya suka dinga yi suna washe baki,dan kuwa wasun su basu taɓa cin kayan fulawa irin wannan ba.
Babu ɓata lokaci Ɗan Liti ya kira Alhaji Baban Gida a waya akai komai akan kunnen shi,dan kuwa bashi da wani da ya fi kusanci da shi sama da Alhajin,ba tare da ɓata lokaci ba aka saka rana, Juma'a mai zuwa za a ɗaura auren Hadiza da Abdussabour a sabon masallacin Juma'a na garin Ba Mugu,wanda Abdussaboor ɗin ne ya gina shi da kud'in shi.
Sallama suka yi da juna kowa ya tafi yana farin ciki da sake kulluwar alaƙar auren Mommy da Abdul ɗin.
Tinda suka tafi aka sanar da Abdul yanda abubuwan suka kasance ya kira Mommy dan su sha hirar soyayya,tana ganin kiran shi ta ƙi d'agawa, hankalin Abdul ba ƙaramin tashi ya yi ba,nan da nan ya kasa zaune ya kasa tsaye saboda tunanin abinda ya hana ta daukan wayar shi. Ganin irin halin tashin hankalin da yake ciki ne ya sanya Suhailah tashi daga parlour ta komawar ta ɗakin ta ta kunna TVn dake ɗakin ta ci gaba da kallon ta. Ranta ba karamin sosuwa ya yi ba da irin rawar kan da Abdul ke nunawa akan maida auren shi da Mommy,amma dole ta danne ɓacin ranta dan tin kafin ta aure shi ta san labarin soyayyar su a wajen yayan ta Bilal.
Ta ɓangaren Mommy kuwa taƙi amsawa ne saboda ta san yana gida a dai-dai wannan lokacin,idan ita ce yake kiran wata yana cikin gida ba zata ji daɗi ba,dan haka itama ba zata yiwa Suhailah da ko uhum bata ji ance ta ce ba game da komawar ta gidan mijin ta.
A hankali ta furta,
"Ai dole ma na kirawo ka gobe da kaina idan ka fita aiki,dan kuwa akwai mahimmiyar maganar da nake so na sanar da kai kafin na yarda a ɗaura wannan auren.".........
*Wata sabuwa...*
[09/08, 10:39 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 109:
Abdul ya jima bai yi bacci ba yana ta duba message ɗin da ya yi wa Mommy amma shiru babu amsa,gajiya ya yi da zaman jiran reply ɗin ta ya kashe data ya kwanta bacci ba dan ya so ba.
Washegari da safe haka ya tashi duk jikin shi babu ƙwari,a hankali yake shiryawa,yana kammalawa ya fita parlour ɗauke da jakar shi da wayoyin shi a hannu,Suhailah ya kalla ya ga fuskar ta babu walwala ko kaɗan,zama ya yi a kujerar dinning suna fuskantar juna,murmushi ya sakar mata a dai-dai lokacin da ta deb'i abinci zata kai bakin ta idanun ta suka sauka akan nashi. Juya idanun ta tayi ta ci abincin ta ba tare da ta mayar masa da murmushin ba,a hankali ya sauke ajiyar zuciya ya ce,
"Good morning my love."
"Morning."
Ta furta fuska a haɗe,hannun shi ya miƙa ya kama nata dake zaune a saman dinning ɗin,cikin salo yake murza yatsun hannun nata,a hankali ta zame hannun ta ta miƙe tsaye riƙe da plate ɗin da bata ƙarasa cin abincin ta ba,mayar da abincin cikin wata roba tayi ta saka a fridge dan kuwa ta san babu kyau zubar da abinci. Kanshi ya dafe cikin wata iriyar murya ya ce,
"Ki yi haƙuri dan Allah idan na ɓata maki rai akan abinda nayi jiya,a jiyan ne aka yi min tambayar auren Hadiza,har an saka ranar aure ma nan da Juma'a mai zuwa,shi yasa kika ga ina ta kiran ta sai kuma naga bata ɗauki wayar ba."
Cikin hanzari Suhailah ta katse shi ta ce,
"Ta ya zata ɗauki wayar ka tinda hankali ya shige ta ta gane bata son ta yi min abinda idan wata tayi mata baza ta ji daɗi ba? Sai dai kash kai da ya kamata ka kiyaye hakan bai dame ka ba,damuwar ka shine kawai Hadiza ta ɗauki waya ku sha soyayya koda hakan zai sosa zuciyar Suhailah,ina so ka san wani abu Abdussaboor,idan har baka damu dani ba to nima ba zan damu da kai ba,sannan idan ka tsaya ka nuna min damuwa da soyayya to nima zaka samu sama da haka a waje na,ni ba irin matan nan bane da ke bin namiji koda baya son su ka gane?"
Mamakin kalaman ta ne suka sanya shi kasa furta koda kalma ɗaya ne,a haka ta yi masa sallama ta wucewar ta motar ta ta fita zuwa asibiti. Da ƙyar Abdul ya samu ya tura abincin shi ba dan yana jin daɗin shi ba,nanata kalaman Suhailah ya dinga yi a ran shi,cikin mutuwar jiki ya sauke ajiyar zuciya tare da furta,
"Maganar ki gaskiya ne Suhailah,dole ne na maida hankali na tsaya akan adalci gudun kar na faɗa halaka,ya Allah ka bani ikon kamanta adalci a tsakanin matana,Allah kasa kar na cutar da kowacce a cikin su,Allah ka bamu zaman lafiya."
Tinda ya yi wannan addu'o'in sai ya samu natsuwar zuciya,ƙarasa cin abincin shi ya yi ya fita office,yana zuwa ko zama bai yi ba Mommy ta kira shi,murmushi ya yi ya amsa wayar cikin amsa sallamar da ta yi masa,a shagwab'e Hadiza ta ce,
'Shine baka fito office da wuri ba kooo?'
"Ya akai kika gane yanzu na shigo office?"
'Ya kake amsa min tambaya da tambaya? Sannan ta yaya ba zan san lokacin zuwan ka office da tashin ka ba? Ai a ganina duk macen da bata san lokacin tashin mijin ta aiki da zuwan shi ba ta binciki kanta gaskiya."
"Wannan gaskiya ne,to me yasa jiya kika ƙi ɗaukan waya ta na kira na taya mu murna?"
'Humm Abban Amir kenan,wato so kake yi na shiga lokacin ƙanwata ko? Auu yayata zan ce,dan yanzu na koma nice ƙarama.'
"Har abada kece a gaban kowacce mace a zuciyata Hadiza."
Kalaman shi sun sanyaya mata zuciya sai ta ji kamar ta taka rawa dan murna,murmushi mai sauti ta saki kafin ta ce,
'Uhumm ni fa baka sanar dani inda zan zauna ba bayan auren mu.'
"Duk inda kike son zama anan zaki zauna Baby,abu ɗaya nake son sanar dake dama,kar ki damu da siyan komai ni da kaina zan yi maki duk abinda ya dace."
'To dama ni dai ina son sanar da kai nafi son zama anan bana son sake zama a kano sai idan Allah ne ya nufa kuma.'
Ba ƙaramin daɗi maganarta ta yi masa ba,domin kuwa ya riga da ya san idan aka haɗa mommy da suhailah a gida ɗaya,watarana sai ya zo ya ga sun haɗa masa tashin hankalin da ba zai iya warware shi ba,sai gashi ta sauƙaƙa masa ta kawar masa da tsoron da yake ji. A hankali ya furta,
"To shikenan tinda haka kike so,amma naso ace kina kusa dani a koda yaushe."
"Kar ka damu,idan bana tare da kai a zahiri ai ina tare da kai a zuciya ko? Sannan sai wani abu da nake so kayi min,ina son ka yi zaman ka a kano ka dinga zuwa waje na duk ranar Juma'a da ka tashi daga aiki, sai ka koma ranar lahadi da yamma.'
"Kaiii inaaa ba zai yuwu ba gaskiya,zan dai dinga zuwa duk ranar girkin ki,na yi maki kwanakin ki, sannan itama na yi mata kwanakin ta ranar nata girkin."
'Baby ya za ayi ka dinga yawo a hanya koda yaushe?'
Sunan da ta kira shi dashi ne ya sanya shi murmusawa kafin ya ce,
"Tafiyar ai ba wata mai nisa bane,dan haka kar ki damu."
Da ƙyar Mommy ta shawo kan Abdussaboor ya amince da abinda take so kafin suka yi sallama,suna kashe waya ya tura mata dubu ɗari uku sannan ya yi mata message ya ce gashi nan ta yi hidimar biki dasu,godiya ta yi masa sosai kafin ta tashi ta tafi ɗakin Innoh cike da murna ta sanar da ita yanda suka yi da Abdul ɗin,shiru Innoh ta yi kafin ta ce,
"Wannan magana ai Yayah ya kamata ki sanarwa dan ni ban wani san ya za ai ba."
Dariya Mommy ta yi sannan ta tashi ta je d'akin Baaba,zaune ta gansu ita da Sadeeq wanda ke ta tilawar karatun ƙur'ani,Baaba kuwa sai gyangyaɗi take zabgawa abunta,dira a gefen ta Mommy tayi sannan ta ce,
"Baaba ki farka ki bi ayari kar su wuce su barki."
A gigice Baaba ta buɗe idon ta tana so ta miƙe tsaye,bakin ta sai surutai yake saki wanda ba a gane inda ta dosa,Sadeeq ne ya rufe ƙur'anin shi yake ta sheƙa dariya,Mommy kuwa tsabar dariya har kwantawa ta yi a wajen,sai da Baaba ta dawo hayyacinta ne ta ɗauki maficin dake gefen ta ta kwaɗawa Mommy akai sannan ta ce,
"Kin tsorata uban ki Ɗanli,kafira me ƙaton baki."
"Ah ah fa Baaba, Ah ah fa Baaba, dan na ga ƴan'uwan ki zasu wuce na faɗa maki laifi ne? Meye na zagi na haka?"
"Ki rama in kin so,dama uwar ki ta kwana biyu bata min tijara ba,se ki fanshe ta."
Dariya Mommy tayi kafin ta ce,
"To ni dai ba faɗa bane ya kawo ni wajen ki,dama kuɗi Abdul ya turo yace nayi hidimar biki,shine na kaiwa Innoh tace na same ki na baki,da ke yafi dacewa nayi maganar ba da ita ba."
"Masha Allahu,Innohn Ɗanli ta fara hankali,haka ake so ai idan an girma asan an girma,yanzu abinda nake so dake shine,alewa za a raba da cingam a gari ayi gayya sosai saboda kowa ya shaida wannan aure,abinda ba a yi ba a baya dole ne mu yi shi a wannan karon,yanzu ne nasan Uwar masu gida za tai aure,aro min hanci na zabga guɗa."
Nan take Baaba ta karkace ta sheƙa guɗa,Innoh na ɗaki ta jiyo guɗar Baaba sai ta saki murmushin farin ciki,ashe dama zaman lafiya daɗi ne da shi? Ashe ƙiyayya ciwo ne da ke cinye farin ciki da zaman lafiyar mai yin ta?
Da wannan shawarar Mommy ta kira Aunty Naja ta sanar
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 68 Chapter of 70