dinga yi kamar zai shid'e, wani irin tausayin shine ya kama Abdussabour,tabbas Allah yana son shi da shiriya ne shi yasa ya turo masa wannan bawan Allah'n dan ya tsorata shi ya ganar dashi abinda yake yi ba mai kyau bane ya daina, dan haka godiya ma zai yi masa sannan ya bashi tukuicin fargar dashi irin halakar daya tsoma kan shi a ciki,cike da fara'a Abdussabour yace,
"Ranka ya dad'e na janye case d'ina da wannan bawan Allah'n,ina mai nema masa afuwa akan abinda yayi,zamu je na ga mahaifiyar shi idan da gaske yake akan duk abinda ya sanar damu to fa zan taimaka masa da jarin naira dubu ɗari biyu dan ya samu yanda zai yi ya kula da mahaifiyar shi da qanwar shi, idan kuma qarya yake yi zamu dawo nan akai shi kotu a yanke masa hukuncin abinda ya aikata,'
Cikin sauri matashin nan yace,
'Na amince, na amince mahaifiya ta na zaune a can 'yan kaba, idan qarya nake yi ni ku harbe ni ma na yarda,'
Bilal ne ya dalla masa harara yace,
'Ni da kaina zan harbe ka sai dai a d'aure ni, kai kuma Allah yasa hakan shine yafi alkhairi haka ake son mutum mai yawan saka alkhairi ga wanda yayi masa sharri, muje a tabbatar da gaskiyar maganar shi, dan ni har yanzu ina da tantama akan shi,kasan fa dogon mutum ba hankali ya cika ba,'
DPO ne ya kalle shi cikin dariya yace,
'Ah ah fa kar ka sake ka zage mu dogaye, dan kana gajere sai ka yi mana kud'in goro?'
Murmushi Bilal yayi suka fita a motar Abdul, yaron nan kuma a motar 'yan Sanda, bayan tsananta bincike ne suka gano gaskiyar maganar da ya faɗa musu,babu b'ata lokaci Abdussabour ya bashi kud'in da yayi masa alqawari suka koma gida,tin daga wannan ranar Abdussabour ya koma yin azumin litinin da alkhamis, idan ma ya tashi da tsananin buqatar mace to fa zai iya zarcewa da azumi a ranar,a hankali rayuwar shi ta koma ina ka fito aiki, ina zaka je aiki, me kake yi ibada.
Abdussabour na nan kwance bai yi aune ba yaga Bilal ya farka daga baccin da ya ɗauke shi a saman kujerar da yake zaune, band'akin dake d'akin da aka kwantar da Abdul ɗin ya shiga yayi alwala ya zo ya shimfid'a abun sallah ya fara nafila.
Wannan halin na yawan ibadar Bilal na qara sanya wa Abdul qaunar zama da shi dan kuwa ba kaɗan yake nuna masa hanyar gaskiya ba,zama da Bilal alkhairi ne a wajen shi.
Washegari da safe.......
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 46:
Baabaa ce ta dage ita zata yi musu qosa idan yaso Ummi ta dama kunun gyad'a irin wanda take cika masa kindirmon nan yayi shar da shi kamar madarar shanu,nan take kuwa surukan guda uku suka shiga kitchen suna aikin su cike da nishad'i da annashuwa.
Saddiqa na markad'a albasa da attaruhu a blender Baabaa na tsaye tana buga qullin qosai tana mita,
"Fisabillahi bature na kyautawa 'yan zamani kuwa jama'a? Shi yanzu jajjagen attaruhun ne sai an saka a inji ba za a ƙulƙula shi a turmi a tashi ba tsabar son jiki? Allah to ya kyauta idan kin gama ki bani abuna na zuba na hau tuya, ko tuyar ƙosan ma kuna da injin yin tane?"
Dariya Ummi da Saddiqa suka sanya, Ummi ta kalli Baabaa tace,
"Hajiya Baabaata Allah dai ya ƙaara miki lafiya da imani da nisan kwana mai albarka, Baabaa idan ina Abuja sai na dinga kewar ki,dan Allah Baabaa ki bimu mu koma tare dake,"
Murmushi Baabaa tayi dan kuwa da gaske take son Saliha surukar ta har cikin ranta, so ne na gaskiya mara algus a tsakanin su, wannan dalilin ne ya sanya surukar tata itama take son ta tsakani da Allah, cikin magana irin ta dattijan kirki Baabaa tace,
"Saliha kenan ni kaina ina so na kasance da ku a koda yaushe, dan kuwa ina alfahari da jajircewar ki wajen kula da tarbiyyar yaran ki gaba d'aya su ukun, ga kuma uwa uba yanda kike son Baban Gida kike yi masa biyayya, sai dai kashhh ba zan iya bin ku na koma Habuja da zama dindindin ba,anan garin na taso iyaye da kakanni na duka'yan nan garin ne,sannan anan garin iyaye na suka aurar dani har na hayayyafa,sannan anan garin miji na mai so na da ƙaunata ya rasu kan shi a saman cinya ta,dan haka ba zan iya tafiya na bar ɗakin aure na ba Saliha, ina fatan a dik inda mutuwa take ta riske ni a ɗakin aure na a saman gado na inda ta ɗauki miji na,"
Hawaye ne ya gangaro a idanun Baabaa na kewar mijin ta, cikin sauri Saddiqa ta durqusa a gaban ta riqe da tissue ta hau goge mata idanun ta,jikin Ummi ne yayi sanyi tace,
"Ki gafarce ni Baabaa daga yau ba zan sake roƙon ki koma Abuja da zama ba,amma inshaa Allahu jimawar da muke yi bamu zo ba daga yanzu zata kau, na gama Phd ɗina da nake yi, yara ma dik sun gama karatun sakandire shi kuma wannan kin ga ya girma har aure yayi, fatan mu suma 'yan matan Allah ya fitar musu da mijin aure na gari a yi auren su idan yaso sun ci gaba da karatun a ɗakin mijin su,"
"Yauwaa Salihatu shi yasa nake son ki, kina da fahimta, kyawun mace ta zauna a ɗakin mijin ta kar ta gusa idan ba sakin ta akai ba ta bar gidan, to mutuwa ta raba ta da gidan ta,Allah kuma ya amsa addu'ar ki Allah ya basu miji na gari mai albarka kamar Baban Gidana,"
Dariya suka yi saboda jin son kai irin na Hajiya Baabaa,a haka suna hirar su har Baabaa ta gama buga qullin ƙosai ta zuba duk abinda ya dace ta fara suyar shi a wutar da Saddiqa ta jima da kunnawa ta itace, dan kuwa Baabaa tace baza ta yi amfani da gas ba ya babbake ta, Ummi kuwa bayan ta markad'a gyaɗar ta da ginger da kaninfari kaɗan sai ta tace ruwan ta ɗora a wuta ta rufe kaɗan, sai da ya tafaso sannan ta zuba wankakkiyar farar shinkafar ta suka ci gaba da dahuwa, bata sauke ba sai da shinkafar nan ta dahu, sannan ta matsa lemon tsami kaɗan a ciki ta juya, kindirmon ta ta ɗakko ta dinga zubawa kaɗan kaɗan tana juya shi da ƙaramar mixer har sai da ya game jikin shi sosai yayi fari ƙal kamar yanda Baabaa ke son shi,banda tashin ƙamshi babu abinda yake yi, gefe ɗaya kuwa Saddiqa ce ta kashe gas dan kuwa ruwan shayin da ta ɗora ya dahu,Ummi na gama juye kunun gyaɗar ta a mazubin da take da buƙata Saddiqa ta buɗe fridge ta ɗakko ragowar farfesun naman ragon da suka ci da dare ta d'umama musu, yana gama d'umamawa ta juye a kyakkyawan mazubi ta kai parlour, a tare suka gama haɗa komai sannan suka yi hamdala tare da sakar wa da junan su murmushi suka shiga d'akunan su dan yin wanka kafin azo karyawa.
Baabaa ce ta kyab'e baki tace,
"Yo ba dole na koma gida na ba nima tinda ina da nawa d'akin mijin? ita surukar tawa ta wuce d'akin su ita da nata mijin, ita waccan ta shiga ɗakin jikan nawa an barni ni ɗaya a parlour ya munafukar tsohuwar da taje gulma gidan surukai,"
Tana gama faɗin haka ta wuce d'akin ta dake cikin gidan, d'akin nata yafi kowanne d'aki girma a gidan, kayan da aka ƙawata d'akin kaɗai zai sa mutum ya gane lallai wannan na uwar mai gida ne, dan kuwa komai na more rayuwar dattijo an saka a ciki, matsala ɗaya aka samu daga wajen Baabaa domin kuwa dik wannan kayan more rayuwar Baabaa bata da buqatar su acewar ta, ita dai fatan ta ta koma ɗakin da tayi rayuwa da mijin ta ta zauna har ta Allah ta kasance.
Saddiqa ta jima a tsaye tana kallon Munir dake ta baccin gajiyar abubuwan da suka faru a jiya, da kuma hana idon shi bacci da yayi saboda an haɗa su d'aki ɗaya da matar da ya sha warning akan ta, idan sun san basu son komai ya shiga tsakanin shi da matar shi me yasa suka turo ta d'akin shi? Murmushi tayi da ta tuna kalaman shi na daren jiya,
'Babu abinda zan ce da Allah nidai da ya wuce godiya Saddiqa,saboda ya bani duk wani abu da nake so a rayuwa ta, ciki kuwa har da wanda nake so na ci gaba da rayuwa da ita har a aljannah, Saddiqa ina son ki, Ina ƙaunar ki,dan Allah ki so ni kamar yanda nake son ki kin ji?'
Band'aki ta faɗa tana rufe fuskar ta kamar a lokacin yake sanar da ita abinda ke cikin zuciyar shi game da ita, tana shiga Munir da ya jima da farkawa tin shigar ta d'akin yaga yanda take qare masa kallo sai ya tsaya yaƙi motsawa kar ya katse mata hanzari.
Cike da murmushi ya sauka daga gadon ya isa bakin ƙofar band'akin ya hau k'wank'wasawa dan tsokana yana faɗin,
"Ki yi sauri ki fito ko na shigo brush nake so nayi ina jin yunwa,"
Cike da matsanancin tashin hankali Saddiqa ta hau watsa ruwan da ta tara a pampo a cikin wani bokitin roba, tana gamawa ta sanya kayan ta ta buɗe qofa zata fito kanta a qasa saboda kunya da tsoron kar ya shiga band'akin tana tsaka da wanka, tsaye ta gan shi yana jiran ta ta fito, ƙura mata ido yayi yana kallon ta, hannu ya d'aga kamar zai taɓa ta, tayi saurin kaucewa ta bar bakin ƙofar band'akin, murmushi yayi sannan ya shige band'akin dan gabatar da uzirin shi.
K'wank'wasa ƙofar d'akin nasu aka yi, cikin sauri Saddiqa ta isa bakin ƙofar ta buɗe Ummi ta gani riqe da leda irin mai hasken nan da kaya a ciki tana miƙo mata,
"Ga wannan ki sauya dan na san baki da kaya anan zuwa anjima sai kuje ke da mijin ki ku ɗebo kayan ki da kike da buƙata kafin Abbah ya gama yanke hukuncin abinda ya dace muyi kuma,"
"To Ummi na gode Allah ya saka da alkhairi ya jiƙan magabata,"
"Ameeen ya Allah Saddiqa,"
Ummi na tafiya Munir ya fito daga bathroom,ko magana Saddiqa bata yi masa ba ta faɗa band'akin ta sauya kayan jikin ta, riga ce doguwa kalar ruwan zuma mai haske,ko da ta fito Munir kafe ta yayi da idanun shi masu rikitar da ita a dik sanda yake yi mata wannan kallon da bata saba gani a idanun shi ba, cikin wata murya mai taushi yace mata,
"Wife kin yi kyau sosai masha Allah, da alama shigar dogayen riguna za a dinga yi min a cikin gida, idan za a fita kuma a sanya ƙaaaton hijabi har ƙasa da niƙabi,"
"Dik abinda kake so shi za a yi maka a gidan ka Husband,"
Tana faɗin haka ta bar ɗakin cike da jin nauyin shi, wani farin ciki ne ya mamaye zuciyar Munir har bai san sanda ya fara taka rawar murna ba daga ƙarshe ya bi bayan ta dan su je su karya.
Zaune suka tarar da Baabaa har ta kusan cinye nata abincin, tana ganin Saddiqa ta zauna tana gaishe da Abbah da ke kurb'ar kunu yana santi tace,
"Ina kika baro min jika na ko ke kaɗai ce me cikin cin abinci?"
Sadeeq dake murmushi tinda yayar shi ta fito ne ya fashe da dariyar jin abinda Baabaa tace,Munir kuwa da ya qaraso zai zauna a kujerar dining table ne yace,
"Ah ah fa Baabaa kar ki takura wa Mata ta, kuma naga idan taci ai kamar naci ne ko?"
Salati Baabaa ta saki tana kama baki, ta kalli Abbah da Ummi dake yi musu dariya tace,
"Inyeee kun ji yaro wai har yayi auren da zai nuna min iyaka ta,"
Ɗan haɗe fuska Abbah yayi cikin wasa yace
"Manniru ka kiyaye ni fa,"
"Tuba nake yi Abbah, barka da safiya,"
"Ba haushe yace da yawan faɗa gwara yawan gaisuwa ko? Lafiya ƙalau alhamdulillah,yauwa ɗazu muna hanyar dawowa daga masallaci nace maka kuje ku ɗebo kayan Saddiqa ko? A bari sai zuwa yamma bana so kuma idan kun je ku kula kowa a tsaya hayaniya,idan naji an yi faɗa Munir kai zan hukunta domin kowa ya san Saddiqa ba mai rikici bace ba,"
"Inshaa Allahu Abbah babu abinda zai faru sai alkhairi,"
"To Allah yasa,"
"Abbah to ya maganar jarabawar ta ta? Ni fa ina ganin mu koma can ta yi kawai,"
"Idan aka koma can sai dai ta bari wata shekarar ta rubuta kenan,ina ganin kawai ku zauna anan mu zamu koma gobe har da Sadeeq sai a samar masa da wata makarantar a can amma fa idan Baba Ɗanli ya amince,ita kuma idan ta kammala jarabawar sai ku taho Abujan, Baabaa hakan yayi kuwa?"
Abbah ya faɗa yana kallon Baabaa da ta kammala cin abincin ta ta miqe zata koma parlour ta zauna, cikin fara'a da jin daɗin yanda rayuwar Saddiqan ta ta haskaka cikin lokaci qanqani tace,
"K'warai da gaske hakan yayi,Allah yasa ta rubuta jarabawar cikin nasara daga nan ta zama likita kamar yanda Yadikon ta ke fata,"
K'walla ce ta taru a idanun Saddiqa ta sunkuyar da kan ta qasa,tabbas tayi kewar Yadikon ta sosai daurewa kawai take yi dan kar ta d'aga hankalin mutanen dake yi mata alkhairi,Munir ne ya kalle ta cike da so da qauna da tausayawa yace,
"Da yardar Allah sai Saddiqa ta zama babbar consultant a kuma babban asibitin tarayya ta Abuja,"
"Allah ya amince Manniru da kuwa nayi farin cikin da ban taɓa yin irin shi ba, Allah ka bani tsawon rai mai albarka naga wannan ranar,"
"Ameeen ya Allah,"
Haka suka ci gaba da cin abinci suna hira gwanin sha'awa kafin daga baya su kammala Saddiqa ta kwashe dik abinda aka b'ata ta tafi wanke-wanke.
*********************
Da misalin biyu na rana aka sallamo Abdul daga asibiti, zaune suke a gaban Mai martaba a cikin turakar shi, Innah Laminde na zaune a gefen mijin ta Bilal da Abdul na gaban su sun duqar da kai kamar marasa gaskiya.
Cikin in ina Bilal ya qarasa zayyane wa Innah Laminde kafff abinda Mai Martaba ya umarce shi da ya sanar da ita game da rayuwar Abdul ta baya, domin a ganin shi akwai abinda Abdul ya b'oye bai sanar dashi ba a wancan lokacin shi yasa ya roqi Bilal da kar ya b'oye musu komai, sai dai basu sani ba Bilal ya b'oye abubuwa da yawa badan ace Mai Martaba ya san su ba ba zai gane ba, cikin murmushi irin na manya Mai Martaba yace,
"Lallai Bilal kana son wannan abokin naka shi yasa kake rufa masa asiri, to babu damuwa Allah ya bar qauna domin shi ya yi muku albarka,tabbas kai ɗin aboki ne na gari wanda kowanne iyaye za su so ace irin ka na tare da ɗan su, mun gode maka sosai a bisa nusar da shi Babana da ka dinga yi a lokacin da ya kauce hanya ya manta da tarbiyyar da muka bashi, ya manta da cewar idan kai bawa baka ganin ubangijin ka ido da ido, to shi ubangiji yana kallon ka, kallo irin wanda yake har zuciya, dan kuwa ya san me kake saqawa a ran ka mai kyau ko mara kyau.
Dan haka ke yanzu kiyi haƙuri ki daina kukan da kike yi, kin ji dai dik abinda ya faru, dan haka mu ɗauki ƙaddarar da ta sanya Abdul auren Hadiza ya tare da matar shi idan ya tashi komawa aiki ya ɗauke ta su tare a waje ɗaya bana son ya qara zama babu mata tinda yanzu yayi auren,Allah ya sanya albarka ya kare dikkan abun qi,Allah kuma ya kawo wa malam Bilal tashi matar ta gari ko?"
Murmushi Bilal yayi ya sunkuyar da kai qasa sosai cike da girmamawa, Innah Laminde kuwa hawaye take ta sharewa tana kallon Abdussabour dan kuwa bata taɓa zaton irin rayuwar da ya aikata a baya zata bibiye shi ba, lallai abinda ya aikata yayi muni,da k'yar ta buɗe baki ta iya cewa,
"Allah ya sanya albarka,"
"Ameen"
Suka amsa da shi kafin daga baya Mai Martaba ya sallami Abdul da Bilal su wuce d'akin Abdul ɗin,bayan fitar su Sarki yayi wa Innah Laminde nasiha sosai ya bata haƙuri sannan yace a sanar da mata da dare suje su ɗauki amarya a kai ta d'akin ta idan yaso an yi walima dan taya su murnar aure.
********************
Mommy da Ameerah ne suka shirya dan tafiya Saloon ɗin cikin kasuwa dan a wanke musu kai a zana musu qunshi, sun shirya cikin manyan hijabai Mommy har da sanya tsohon niƙabin ta ta rufe fuskar ta, kuɗi ta ɗauka sosai suka bar gidan dan kayan matan da Naja ta kai mata basu yi mata ba,tana so ta siyo wani da kanta.
Suna fita Innoh ta afka d'akin Yadiko tana so tayi bincike a kayan Mommy, sai dai kashh tana shiga taga Mommy ta sanya wa akwatin ta kwad'o ta rufe shi, dukan akwatin tayi da ƙafa ta hau masifa,
"Kaiii wannan yarinya an yi marowaciyar masifa, yanzu fisabillahi menene na rufe akwati da kwad'o? "
Har za ta fita ta koma da baya ta hau lalube d'akin Yadikon, ba tare da ta ji Sallamar su ba taga an ɗaga labule a daidai lokacin da take ɗaga katifar Yadikon........
*Dan Allah kuyi min haƙuri saboda ji na shiru da kuke yi kwana biyu,abubuwa ne suka yi yawa wallahi. Ina yi wa kowa fatan alkhairi...yau Wattpad taqi hausa na fara rubutu sai da nayi mai yawa ya goge, har na yi zuciya nace ba zan sake ba amma ina tunano yanda kuke qaunar littafin nan dai na daure. Son so fisabillah mutanen Hajiya Baabaa😂*
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 47:
"Uhummm ai tinda na ga babu ke a cikin waccan hayaniyar ta ƙofar gida na san bakya kusa, sai dai ban taɓa zaton na taddake a irin wannan halin ba, to yanzu da kike bincike ɗakin mamaciya me kike nema? Ko kin zo satar abinda ba zaki kai shekara ɗari kina mora ba tinda kema dole taki mutuwar zata ɗauke ki a lokacin da baki gama jin daɗin duniyar ba?"
Haɗe fuska Innoh tayi sosai ta qanqance ido ta ɗakko kud'in da ke ƙasan katifar tace,
"Kin ga Yaya ki fita a ido na na rufe, da kike maganar sata ai kema kin san ban yo gadon ta ba, sai dai ki tambayi 'yar so ina ta samu wannan maƙudan kuɗaɗen har take ajiyewa a ƙasan gadon ta,"
A wannan karon dole Baabaa tayi shiru, domin kuwa ita da kan ta za ta so sanin inda Saddiqa ta samu kuɗi masu yawa haka kafin ta zargi Innoh da binciken d'akin mamaciya ba a sanya ta ba,cikin d'aure fuska Baabaa ta kalli Saddiqa dake tsaye a gefen ta kai duƙe idanun ta na zubar da ƙwalla tace,
"Ina jiran jin bayanin inda kika samu kuɗi masu yawa haka Saddiqa, kar kuma kiyi min ƙarya dan ba halin ki bane,"
"Baabaa Yah Munir ne ya bani su tin zuwan da yayi na farko,sai wanda Yadiko ta b'oye na ribar sana'ar ta,kuma ni ban taɓa amfani da kuɗin da Yah Munir ya bani bane saboda Yadiko ta gargad'e ni akan amfani da kuɗin samari, tace dik rintsi duk wuya kar na zaƙe akan cin kuɗin samari domin watarana dole ne su fanshe kuɗin su, zata iya yuwuwa su fanshe da jiki na tin kafin su aure ni, amma idan ya tabbata namiji aure na zai yi to bayan ya aure ni ya kashe min ko nawa ne babu damuwa, ni kuma nayi-nayi na ƙi karɓar kuɗin a lokacin da ya bani amma ya dage sai da na karɓa, shi yasa na ajiye ban taɓa ba,"
Cike da tausayawa Baabaa ke kallon Saddiqa,a hankali ta kama kafaɗar ta tace,
"Haba Saddiqa ! Munniru ai ɗan uwan ki ne me yasa baki yi amfani da kuɗin da ya baki ba? Da kina da waɗannan kuɗin kuka dinga zama da yunwa ke da ɗan uwan ki da rana ko da dare? Yanzu gasu nan me zaki yi dasu bayan baki more su ba a lokacin da kika fi tsananin buƙatar su?"
"Ku dena wannan wasan kwaikwayon dallah malamai, ni da kaina na san yunwa na iya jefa mutum aikata zina da sata dan ya samu abinda zai ci, waya sani ma ko...."
Cikin tsawa Baabaa tace,
"Kar ki kuskura ki danganta zuri'ar Yadiko da sata ko zina,dan kuwa basu sha a mama ba, ke da kan ki sai dai son zuciya ya hana ki fad'ar gaskiya, amma kafin ki samu yarinya mai kamun kai da natsuwar wannan a kaf garin nan sai kin jima kina nema,ke matsa ki baiwa mutane waje ina ruwan wani ma da zarge-zargen ki na iska da wofi? Yarinya dai alhamdulillah yanda kika so ta lalace Allah ya tsare ta bata bi maza ba dan su ciyar da ita,yanda kika so ta zamo mai halin ɓera bata yi ba,sai aka barki da mai halin ɓera a ɗakin ki, domin Ameerah ba barin ki tayi da ɗauke-ɗauke ba balle ni da ta raina take ganin idan ta ɗauka bana ganewa,"
Cike da borin kunya Innoh tazo zata fice ta bar ɗakin, Saddiqa tayi saurin bata hanya, hannun ta data jimqe kud'in Baabaa tayi wuff ta damqe ta matse da ƙarfi sannan tace,
"Sake su tinda ba gadon da Delu ta bar maki bane kan ta tafi ƙiyama,"
Nan take abu ya zama rikici tsakanin Innoh da Baabaa, Munir na gani yaƙi rabawa, Saddiqa kuwa sai kuka take yi tana roƙon shi da ya raba, ya na jin ta yayi wucewar shi ɗakin Yadikon ya hau duba inda kayan ta suke dan ya taya ta kwashewa, ta na ganin haka ta shiga ɗakin a guje ta danne sif ɗin da kayan ta ke ciki tana zaro idanu waje kamar mara gaskiya.
Baabaa ce ta shiga d'akin tana haki tace,
"Mahaukaciyar banza da wofi kawai,ta na nan tana satar kud'in da ba nata ba yaran ta na ƙofar gida suna faɗa da mijin da Allah ya zab'awa ƴar ta ta taƙi karɓar ƙaddara, ah ah ku kuma menene haka kuke yi?"
Kallon Saddiqa da Munir tayi taga suna kici-kicin buɗewa da rufe sif, cikin Sauri Saddiqa tace,
"Baabaa ki ce masa ya bar min kaya na na ɗauka da kai naaaa"
"Taya ta fa zan yi,"
"Kai ni ba zan iya da jarabar ku ba ku cinye kan ku in kun so, na yi ɗakina na ɗauki abinda zan buƙata nima, ai na godewa Allah da Allah yasa na biyo bayan ku, da ku kaɗai ne da waccan baƙar dagar ta ƙulla muku wani sharrin,"
Baabaa na gama maganar ta ta wuce d'akin ta ta hau tattara abubuwan da zata buƙata kafin nan kafin Saddiqa ta gama jarabawa ta dawo, dan ba a can zata ci gaba da zama ba.
Innoh kuwa tinda ta samu ta samfe daga faɗan borin kunya sai ta shige ɗaki tana fatan Allah yasa suyi su tafi kar wani yasan abinda ya faru.
Munir kuwa yayi nasarar janye Saddiqa daga jikin sif ɗin ta na kaya ya hau taya ta kwashe kayan nata a cikin akwatin da ya gani a jingine a ɗakin, wanda dama nata ne Yadiko ta sai mata na musamman saboda tafiye-tafiye zuwa garin kakannin ta fulani.
Yana cikin kwaso kayan ne ya ɗakko da bra ɗin ta da panties ko a jikin shi kuwa ya zuba su a akwatin ya ci gaba da kwashe sauran, matsananciyar kunya ce ta hana Saddiqa tsayuwa a ɗakin sai ta yi waje kawai ta bar shi yana kwasar kaya kamar ya gama sanin wanne ne nata wanne ne ba nata ba, domin kuwa hatta da littattafan ta na islamiyya da boko sai da ya kwashe, yana gamawa ya janyo akwatin nata da na Mommy dake ajiye a gefe ya yo waje da su, ya sake komawa ya ɗakko katifar Mommy da kayan ta da ta baza a saman katifar yayi waje da su dika Innoh na ɗaki bata san ana yi ba.
Yana gama fitarwa Saddiqa tace,
"Me yasa ka fitar mata da kayan ta waje?"
"Saboda ba ɗakin gyatumar ta bane,wannan ɗakin rufe shi zamu yi dik sanda kike da sha'awar zuwa zaki zo gidan ku nan zaki sauka kin gane?"
D'aga masa kai tayi tana kure shi da ido tare da cije leb'en ta na qasa tana murmushi, kallon ta shima yayi sannan yace,
"Ki dena yi min irin kallon
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 31 Chapter of 70