farka?"
Kuka sosai K'waisa yake yi,damuwa da tashin hankali sun haɗu sun yi masa yawa,Sallau zama ya yi yana lallashin K'waisa tare da ɗaukar masa alƙawarin dik inda Mommy take sai ya taimaka masa ya samo masa ita...........o......"[09/08, 10:39 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 81:
Tin daren ranar asabar ɗin da Ummi tayo waya daga Abuja ta sanar da haiwar Saddiqa ake fama da Baaba akan ta yarda ta je suna ta ƙi sam,an kaɗa ta dambu taliya taƙi yarda tace Allah ya raya abinda aka samu ita dai babu inda zata je ta bar ɗakin mijin ta,wannan dalilin ne ya sanya Alhaji Baban Gida ya haɗa baki da Ɗan liti akan su ce mata shi zai kai ta Abujar a motar shi, sannan ana gama suna a ranar za su dawo tare,dan haka tana iya tattaro dik wanda take so taje da shi a tafi gaba ɗaya.
Baaba na jin haka sai hankalin ta ya kwanta,tinda a ranar za a je a ranar kuma za a dawo babu matsala,shiri ta fara yi sosai cike da farin ciki,da daddare tana zaune ita da Sadeeq dake murna zai je yaga Yah Saddiqan shi da babyn da ta haifa musu ta kalli Sadeeq ɗin ta ce,
"Ka ga abun Allah ko? Na gama haɗa mata kafff kayan gara na uwa da ake yi da niyyar Abbee da Shalele su kai se gashi ashe ma ni zan kai da hannu na."
"Da alama kina yin auren ne da wannan mai gidan naki shi yasa,to ke yanzu Baaba da kika dage sai an tafi da Aunty Shalele ba tace mijin ta ba zai bari ba? Shi fa yace ya gaji da yawon suna da bikin nan da take yawan zuwa,ki ɗauki Aunty Abbe ku tafi kawai abun ku."
"Yo ai magana ta ƙare tinda na masa waya da magariba nace tayi zaman ta Ɗanli zai kai ni har Habujar,ba se ya kwaɗa ta ya cinye ba,masifaffen banza kawai."
Dariya Sadeeq ya yi sannan ya tashi ya ɗauki singiletin shi da ya gama ninkewa ya zuba su a akwatin shi ya zuge,Baaba ma ƙarasa haɗe babban buhun da ta cika da kayan garar da za ta kai wa Saddiqa tayi,suka yi wa juna sai da safe ta shige ɗaki ta kwanta.
A dai-dai wannan lokacin da Baaba da Sadeeq ke shirin zuwa Abuja uwar gayya Innoh na can na masifar babu inda Ɗan Liti zai kai su Baaba a mota,idan suna son zuwa Abujar su hau ta haka su tafi,dik yanda Ɗan Liti yake ta ƙoƙarin yi mata bayani ta ƙi fahimtar shi,wani irin kishi da baƙin ciki ne yake nuƙurƙusar zuciyar ta,jin kunnen ta taji irin maƙudan kuɗin da Alhajin ya aiko wa Ɗan liti wai a sha mai dasu a hanya,dan haka ta ci alwashin babu inda zai je sai dai ya zauna su cinye kud'in,ko da Ɗan liti ya gaji da yi wa Innoh bayani sai kawai ya ƙyale ta ya juya mata baya ya kulle yana jiran bacci ya ɗauke shi,tafiya dai babu fashi in dai Allah ya tashe shi da ran shi da lafiyar shi,ganin abinda Ɗan Liti ya yi ne ya baiwa Innoh tabbacin sai fa yaje kenan,kuka ta fashe dashi tana faɗin,
"Da yake su masu kuɗi ne ai gashi zaka je Abujar wajen sunan ƴar ka,amma nan nan Mommy ta haihu kaje ne? Kuma kana cikin garin kanon baka nemi gidan ta kaje ba,ga Sulena ya ɓata yau sati uku kenan babu amon shi balle bayanin inda yake,amma dake abun bai dame ka ba shine za ka tafi Abuja, to Allah ya bada sa'a."
Banza ya yi mata ya hau munsharin ƙarya dan kawai ta zaci ya yi bacci ta dena mitar da take yi masa akai,da ƙyar ya samu ta hakura ta muskuta mazaunan ta ta kwanta tana jan majina kamar wata yarinyar goye har bacci ya ɗauke ta.
Ameerah kuwa tinda taji za a je sunan taji kwad'ayin zuwa,sai dai ta san babu yanda za a yi taje tinda itama jegon take yi,ita gaba ɗaya zaman gidan ma ya ishe ta,dik abinda shamsu ya kawo mata na ƙwalama akan idon Innoh,bata jin nauyi ko kunya sai an raba da ita ko an ɗebar mata ta lasa ko babu yawa,yaron ta da yaci sunan Mai Dusa wato Abubakar ta ja gaban ta,kallon shi tayi taga yanda yake kama da su ita da shamsu sai dai ya ɗakko farar fatar ta sak,murmushi tayi sannan ta sake rungume jinjirin a ƙirjin ta,a hankali ta furta,
"Ohhh rayuwa kenan,wani baya haihuwar ɗan wani, sai yanzu na gane tin asali ba son Yah Munir nake yi ba,haushin yanda yake baiwa Saddiqa mahimmanci ne ya sa na kafe nake ganin kamar ina son shi,dik da dai na san ƙamshin shi da gashin kan shi sun ja ra'ayi na a wancan lokacin,amma a yanzu ne na san menene so,ina son ka Shamsu na Allah ya barmu tare har a aljannah."
Murmushi ta sake yi ta rungume jinjirin ta dake bacci sannan ta sumbace shi,wayar ta ta lalubo ta kunna ta danna wa shamsu kira dan taji muryar shi ta rage kewa,cikin rashin sa'a kuwa da ta kira taji alamun waya yake yi,cikin sauri ta cire wayar a kunnen ta tare da dire jinjirin ta a gefen ta ta miƙe tsaye,sake kiran shi tayi aka tabbatar mata da cewa mamallakin wayar yana amfani da abar shi a dai-dai wannan lokacin,wani ashar Ameerah ta lailaya ta saki.
"Da uwar wa shamsi ke waya a daren nan? Ƙarfe sha biyu na dare saura minti takwas fa, tabdijam lallai za a yi ruwan masifa da bala'i a garin Ba Mugu."
Tini bacci ya ƙaurcewa idanun Ameerah da kishi ke narkar da zuciyar ta, zama tayi a katifa tana hawaye,cikin kuka tace,
"Sai da zuciya ta ta kamu da son ka zaka fara tsalle-tsalle shamsu? Ni dai a gaskiya gobe zan koma ɗaki na,dan banga amfanin da zaman nan yake yi min ba a gidan nan,tinda har yanzu ni ke yi wa yaro wanka idan Baaba bata yi masa ba,ɗaki sai na share watarana ma Innoh tace na haɗa da tsakar gida, haka ake jegon? Masu jego ba lallaɓa su ake yi ba a basu cima mai kyau dan su maida abinda suka rasa a jikin su wajen haihuwa? To a gaskiya ni dai gobe zan koma d'aki na."
Zama tayi ta rubuta wa Shamsu message ta tura masa, Shamsu na can na waya da budurwar shi da yayi a shagon shi na turi,ƙarar shigar message ɗin ya tsaida shi daga abubuwan da yake yi dan biyawa kan shi buƙata, a hankali ya zare wayar ya sanya ta a handsfree saboda ya dinga jin me budurwar tashi take faɗa,karanta message ɗin ya yi a cikin zuciyar shi kamar haka,
'Idan baka zo da adaidaita sahu ba gobe da safe ka ɗauke ni ka maida ni ɗaki na ba zan je gidan Goggon ka na sanar musu abinda ya faru a daren mu na farko,kuma ko da wacce shegiya kake waya ka yi mata albishir da ajalin ta ya gabato ta zaɓi maƙabartar da za a binne ta'
Cikin sauri Shamsu ya daƙile wayar da suke ya hau waige-waige,nan take ya nemi wutar sha'awar da ta kunno masa kai ya rasa ta,sai da ya tabbatar da Ameerah fa bata ganin shi da dikkan alamu kira tayi taji busy shi yasa ta faɗi haka,zama yayi a bakin gado yana maida kayan shi a jikin shi,wayar ta ya kira ya ji ta a kashe, cike da damuwa ya ja tsaki ya ce,
"Kaiiii amma yarinyar nan Ameerah bata yi ba,sai da na d'akko hanya ana zuba min kalamai masu rikita kwanya ta rusa komai,ita bata iya yanda zata sama wa mutum natsuwa ba,ta kuma hana wasu su jiyar da ni daɗi,yanzu dole goben na je na d'akko ta kafin tayi min bankaɗa."
Tsaki ya ja ya ƙarasa gyara zariyar wandonsa sannan ya haye gado ya kwanta,ya jima sosai kafin bacci ya ɗauke shi. Be jima da fara baccin ba wayar shi ta hau ruri,cikin magagin bacci ya amsa tare da faɗin,
"Ameerah goben fa zan zo na ɗauko ki,ni bana son fitina dan Allah,kuma da kike cewa zaki je ki tona abinda ya faru a daren mu na farko,ai idan asiri na ya buɗe kema naki ba rufuwa zai yi ba,dan haka ki dena yi min barazanar banza."
'Yah Shamsu Bilkisu ce fa,ya mai jegon da Babana?'
Da sauri Shamsu ya buɗe ido ya na kallon wayar,lambobin da bai saba gani ba ya gani a jiki,cikin rawar murya yace
"Baiwar Allah ke wacece? Kuma wannan wacce iriyar lambar waya ce? Me ya sami Bilkin"
'Yah Shamsu nice Bilkisu, wannan No ƙasar waje ce shi yasa ka ganta a haka, na kira ne nayi maka barka akan haihuwar da aka yi mana, ina yawan ganin posting ɗin ka a Facebook ai,na jima ina so na kira ka mu gaisa na kasa,Yah Shamsu dan Allah ku taya ni da addu'a ina cikin masifa,ina cikin hatsarin rayuwa,ban sani ba ko zan dawo gare ku a raye ko kuma gawata za a kawo muku,wataƙila ma ko gawar tawa ba za ku gani ba,Yah Shamsu kwaɗayi da dogon buri yasa na kai kaina ga halaka.'
Kuka ne ya ƙwace mata,nan ta hau yin shi babu ƙaƙƙautawa,shamsu kuwa jikin shi ne ya hau rawa saboda jin kalaman ta, buɗe baki yayi domin ya mata magana yaji ana faɗin,
'Da wa kike magana?'
Kafin Billy tayi magana an kashe wayar,cikin sauri ya hau bin layin da ta kirawo shi dashi da kira,cikin rashin sa'a ta fara ringing ya ji ta katse,sake kira yayi ya ji wayar a kashe,hankali tashe ya miƙe tsaye ya yi hanyar fita tsakar gida,tinda ya fita daga ɗakin shi bai tsaya a ko ina ba sai a ƙofar ɗakin iyayen shi,sallama ya dinga yi musu tare da ƙwanƙwasa ƙofar,cikin magagin bacci mahaifin shi ya tashi,wayar shi ya ɗauka ya duba lokaci,gani yayi ƙarfe ɗaya da minti biyar na dare,cike da tsoro ya durƙusa ƙasan gado ya ɗauki barandami da gora,Ta Annabi na ganin haka jikin ta ya hau makyarkyata cikin yin ƙasa da murya tace
"Malam me yake faruwa ne?"
"Nima ban sani ba,muryar shamsu nake ji yana sallama cikin damuwa, ban sani ba ko miyagun da suka shiga gidan Alhaji Tanimu ne suka hauro mana tinda sun ga kwana biyu muna cikin alheri."
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'una."
Wani bugun ƙofar tare da sallamar shamsu ne suka sake firgita su Mai Dusa, a kiɗime Ta Annabi ta zagaya gefen gadon ta tayi goho ta b'oye kanta, shi kuwa Mai Dusa cike da tattaro dika jarumtar shi ya nufi ƙofar ɗakin nashi yana rage murya yace,
"Shamsu kai da su waye?"
"Baba dan Allah kuyi sauri ku buɗe mana ni ne fa."
Da jin haka sai Mai Dusa ya zuba makaman shi a bayan ƙofa ya buɗe a hankali ya fita, ganin shamsu shi kaɗai ne ya kwantar masa da hankali yace,
"Ah ah ɗan Baba kai kaɗai ne?"
Cike da mamaki Shamsu yace,
"To da ni da su wa zamu zo? Baba ba wannan ba dai,Bilkisu ce ta kirawo ni tana kuka yanzu,da alama tana ciki tashin hankali da damuwa."
Murmushi Mai Dusa yayi sannan yace,
"Kai babu wata damuwa da take ciki,ko jiya mun gaisa da ita ni da mahaifiyar ku,har ma ta turo kud'in da ka ga an siyo abinci an raba wa mutane."
"Baba baka ji me nake faɗa maka bane? Ita da kanta ta kirawo ni yanzu tace mu taya ta a addu'a rayuwar ta tana cikin hatsari,har tana maganar kisa da mutuwa,dan Allah Baba a kai maganar nan wajen Sarkin malamai a hau yi mata addu'a Allah ya dawo da ita gida lafiya."
Ta Annabi ce ta fito ta tsaya tana dariya tace,
"Yo malam ka barni can gefen gado nayi goho ina boye kamar kaza."
"Ke ba ɓarayi bane,wai kin ji Bilkisu ce take cikin matsala ana mata barazana da rayuwar ta,shine ta kirawo yayan ta take cewa a taya ta da addu'a."
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'una,Allah ka kare min ƴata a duk inda take daga dikkan sharrin mai sharri."
"Amin ya Allah, kuma maganar ka shamsu gaskiya ne, Allah ya kaimu gobe zan je wajen sarkin malamai a sa abun a addu'a,Allah ya kare mana ita a duk inda take."
"Amin Baba,sai da safen ku."
Bayan sun yi sallama sai kowa ya koma ɗaki,amma gaba ɗayan su bacci ya ƙaurace wa idanun su,banda tinani da addu'o'i babu abinda suke yi,su ba masu dogon ilimin addini bane balle su yi alwala su yi nafila har su roƙi Allah mafita, amma a hakan ma da suke zaune bakin su bai dena neman taimako daga wajen Allah ba.
****************************
Da sassafe motar Ɗan liti da ta kwashi Baaba da Sadeeq da Abbe zuwa Abuja ta tashi, Innoh taji baƙin ciki sosai kamar ta kurma ihu,amma haka suka wuce babu wanda ya bi ta kan ta,Ameerah kuwa ba tare da ta sanar da kowa ba ta gama haɗa kaff kayan ta tana zaune zaman jiran Shamsu yazo su wuce gida.
*********************
Sule ne ke ƙarasa sanya wasu riga da wando masu kyau da suka karb'i kalar fatar shi da hutun kusan wata guda ya sanya shi murmurewa,dik wata muguwar ramar nan da ƙobarewar da sule ke da shi a baya ta miƙe,farin shi ya fito fess saboda a rana Hajiya kan saka shi yayi wanka sama da biyu.
Da ƙyar yanzu ma ta yarda zata barshi ya tafi Abuja saboda sunan Saddiqa da ya nuna mata sanarwar da ya gani a Facebook Munir ya saka,gefe ɗaya kuwa ya fake da sunan ne yana son ya je wajen wasu abokan shi da suka kwaɗaita masa harka da manyan matan Abuja.
Shi yanzu Hajiyar shi ta buɗe masa ido ya gane daɗin harka da manyan mata,ririta shi take kamar ƙwai,tattalin shi take yi kamar wani jinjiri,dan haka yanzu ya gane komai munin mace, komai kyawun ta in dai irin su Hajiyar shi ne zai bi su dan ya samu nerori, tinda yake account ɗin shi bai taɓa ɗaukan dukiyar da yake da ita ba a yanzu,dan haka shi kam wannan harka ta karɓe shi bai ga ranar bari ba,a ciki yake so yayi gida da mota ya kama sana'a,wataƙila ma har yayi aure.
Sai da ya gama shiri tsaff ta riƙo masa ɗan ƙaramin akwatin shi wanda suka siyo a shopping ɗin da suka fita a daren jiya,sai wani Shagwab'a take yi tana yi masa mitar kar ya jima idan ya tafi,cikin nuna mata kulawa yace,
"Haba Baby Nice d'ina ni kaɗaiiii, idan na je na jima in samu natsuwa a ina? Ai ana gama suna zan dawo, kin ga ita ƙanwata da na zo suna wajen ta jego take, d'ayar mai suna Ameerah itama jegon take ba za su samu damar zuwa ba, to wannan uban mu ɗaya idan ban je ba za su ga na yi wariya a tsakanin su,dan haka idan naje ana gama suna zan dawo."
"To Allah ya kiyaye Habibina,Allah ya dawo min da kai lafiya I love you."
Yaƙe haƙori Sule yayi ya kasa mayar da martanin I love you ɗin da aka faɗa masa,akwatin shi ya karɓa ya manna mata kiss sannan ya bar parlourn ya tafi yana ɗaga mata hannu,ya na buɗe ƙofar gidan zai fita ya ci karo da wani mutum baƙi kan shi sol babu gashi sai sheƙi yake yi,a tsorace Sule ya duba bayan mutumin yaga wasu ƙattin maza biyu na take masa baya ɗaya da jaka a hannun shi riƙe wadda da alama ta wannan bawan Allah'n dake gaban shi ne tsaye, wani irin yawu Sule ya had'iya ya fara ja da baya yana komawa cikin gidan....
[09/08, 10:39 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 82:
Ganin yanda jikin Sule ya hau makyarkyata ne ya baiwa Hajiya dariya,da kanta ta ƙarasa gaban Sule ta sake buɗe masa ƙofar ta ce,
"Sai mun yi waya ko? Allah ya kiyaye hanya."
Cike da tsananin mamaki ya kalli wajen da Alhajin yake sai ya ga wayam babu kowa,murmushi Hajiya tayi masa sannan ta ce,
"Kar ka wani samu damuwa,babu abinda zai ce dan ya gan ka, a tunanin ka da waye yake bani kud'in da nake kashewa irin ku idan ba shi ba? He was never around,zan yi ta zama ne a haka ba ɗan ɗebe kewa?"
Wani yawu Sule ya haɗiya cikin sauri ya ja akwatin shi ya bar gidan,hankalin shi har a wannan lokacin bai kwanta ba,ga yanayin unguwar irin ta masu hannu da shuni ce ko machine ɗaya be gani ba ballantana adaidaita sahu,tafe yake yana magana shi kaɗai kamar wanda ya zare,cikin tsananin mamaki ya furta,
"Amma dai mijin matar nan mugun kidahumi ne,ta yaya zai dawo daga tafiya yaga namijin da bai sani ba a gidan shi kuma ya ƙyale shi? Idan ni ne ai sai na yi ajalin duk wanda na gani a gida na da sunan kwartanci."
Ƙarar mota yaji a bayan shi ta tsaya da ƙarfi, a kiɗime ya juya ya na rarraba idanu,ƙartin da ke takewa Alhaji baya ya gani sun buɗe mota sun fito, ɗaya daga cikin su ne baƙi tittirna ya yi wa Sule fito tare da nuna masa ya shiga su tafi,sakin akwatin hannun sa Sule ya yi ya durƙusa a ƙasa yana kuka,cikin tsananin tashin hankali ya ce,
"Dan girman Allah ku yi hakuri,ba zan sake zuwa gidan nan ba,yanda na bar nonon uwa ta har abada na bar maku gidan ku har abada,dan Allah kar ku kashe ni."
Fitsari ne ya fara tarara a jikin Sule bakin shi kuwa ya ƙi dena bada hakuri,wani gigitaccen mari yaji an sauke masa, ko uffan bai sake cewa ba ya shiga motar ya na hawaye tare da wani irin nishin damuwa da tashin hankali,yana shiga motar sauran mazajen da suka fito suma suka afka suka ja mota da ƙarfi suka bar unguwar da Sule.
Waya suka yi wa Alhaji yana ɗauka suka ce,
"Alhaji gashi fa mun damƙo ma shegen a kai shi can ma'ajiya ko?"
'Eh a ajiye min shi ina da wasu tambayoyi da zan yi masa,domin kuwa da alama nema na ne na wata da watanni yazo ƙarshe,dik yanda aka yi yaron nan na da alaƙa da Sweet H.'
"To Alhaji an gama."
*****************************
Da la'asar sakaliya su Baabaa suka isa garin Abuja,tinda Baaba take zuwan ta bai fi biyu ba,shi ma da ƙyar da siɗin goshi ta je,dan haka sai taga wajen kamar an sauya mata shi,gidan ya haɗu matuƙa,cike da murna Ummi da su Khaleesat suka fito tarbon su,itan ma banda washe baki babu abinda take yi.
Drivern da ya yi wa su Ɗan Liti jagora ne bayan sun yi waya sun sanar da sun shigo Abuja ne ya tintsire da dariya,kallon yanda Ɗan litin ke sake buɗe haƙora yana kallon gidan ya yi,cikin dariya yace wa Ɗan liti,
"Aboki na rufe bakin ka kar ƙuda ya faɗa,ko da yake shi ƙudan Abuja daban yake da na ƙauye."
"Ai dole ya zo daban da irin wanda muka sani, ka duba ka ga waje aljannar duniya malam,ashe haka Baban gida ke da arziƙi muke ƙauye muke fama da na masara?"
Sadeeq ne ya ce,
"Ai Baba kowa na duniya da arziƙin da Allah ya rubuta masa zai ci in ji malamin mu,dan yana da kuɗi be zama dole sai ya yaye maka rayuwar talaucin da kake ciki ba, shi Allah ya zaɓa ya baiwa dukiya saboda ta zame masa jarabawar shi,idan ya yi amfani da ita yanda ya dace ta yi sanadiyyar shigar shi aljannah,idan kuma ya kauce hanya saboda yana da dukiya zata iya kai shi wuta,haka abun yake a ɓangaren dik wani talaka,idan talaka ya zama mai wadatar zuciya ya yi ibada tsakanin shi da Allah, sannan ya yi hakuri da abinda Allah ya hore masa to sai ta kai shi aljannah,idan ya yi akasin haka wuta zata kai shi,ai Abbah na ƙoƙari ma Baba,yana fitar da zakka ya baiwa dangin shi,ya na yi mana ihsani, sai dai duk wannan abubuwan da yake mana ba zai taba yanke mana talauci ba idan Allah bai nufa ba."
"To suda ya isa haka,ahhh nace to suda ya isa haka,mu je ciki mun tsaya anan wajen masu aikin gida."
Kayan jikin Ɗan Liti mai gadi ya kalla suka haɗa ido da driver sai suka bushe da dariya suka tafa,Sadeeq gaba ya yi cikin sauri dan baya son yaji me za su faɗa akan Mahaifin nashi,ko da ya shiga sai ya tarar da Saddiqa zaune daf da Baaba kamar wata ƙaramar yarinyar da ta ga mahaifiyar ta,da sauri ya isa gare ta ta tashi cikin sauri itama suka rungume junan su,a tare suka sauke ajiyar zuciya kafin Saddiqa ta ɗaga kan Sadeeq ta kalle shi,gani tayi ya ƙara girma ya yi haske sosai fiye da da,ga wasu ƴan kumatuttuka da ya yi,hamdala tayi a zuciyar ta dan kuwa dik wanda ya ga Sadeeq zai gane yana cikin kwanciyar hankali.
Munir ne ya ce,
"Hello malam Sadeeq ko har an manta dani ne?"
Da sauri Sadeeq ya je wajen Munir ya bashi hannu suka gaisa cike da farin ciki, Baaba ce ta miƙawa Ɗan liti jaririn a dai-dai lokacin da Saddiqa ta durƙusa a gefen shi tana gaida shi,ƙarbar yaron yayi yana mai jin ƙaunar shi a cikin ran shi,kallon Saddiqa ya yi ya ce,
"Allah ya jiƙan Yadikon Sule, da tana nan da nasan ba za ta zo ba saboda kunya,amma kuma na san zata so shi kamar ta maida shi cikin ta,zuciyar ta cike take da soyayya,bata ƙin kowa, bata nufin kowa da sharri sai alkhairi."
Kuka ne ya ƙwace wa Ɗan liti wanda hakan yayi sanadiyyar sanya mutane da dama matsar ƙwalla, ciki har da Sadeeq da yake tsananin kewar mahaifiyar tashi a koda yaushe.
Munir ne ya zauna a gefen Ɗan liti ya ce,
"Ka san sunan da muka sanya wa babyn kuwa?"
Girgiza kai Ɗan liti ya yi yana share hawaye da hannu ɗaya,
"Sunan shi Zubair amma za mu dinga kiran shi da Suhail."
Washe baki Ɗan liti ya yi ya kalli Saddiqa dake bin Munir da kallon mamaki,dan kuwa ba haka suka yi da shi ba, sunan Abbah za a saka wato Alhaji Baban gida, sai gashi ya sauya ya ce sunan shi Zubair,cike da farin ciki Ɗan liti ya hau godiya mutanen parlour duk sai suka hau yi masa dariya.
Saddiqa kuwa kallon Munir take da tsantsar so da ƙauna tare da girmamawa,Baabaa ce tace,
"Alhamdulillahi Ɗanli an yi takwara,Allah ya raya mana ya sanya albarka, to ba wannan ba, wai ni ba cewa aka yi yau ne suna ba da an gama a yau zamu juya?"
Dariya kowa ya hau yi mata a wajen, Ummi tace,
"Ai ba yau bane suna Hajiya Baabata sai gobe in Allah ya kaimu,goben da an gama suna sai kawai a maida ke gidan ki tinda dai dama darajar jinjiri muka ci aka zo mana."
"Ahh toh, gwanda a hanzarta a yi abinda za a yi a maida ni ɗakin miji na."
Tashi tayi tana takawa tare da neman inda zata shiga bayi, Anisah ce ta kama hannun ta tayi mata jagora har ɗakin da aka gyara mata,ko da Baaba ta shiga ɗakin sai ta tsaya turus tana kallon yanda aka tsara shi,ɗaki ne da ya ji kayan more rayuwa an kafe ƙaton hoton Baaba kamar a kirawo ta ta amsa,washe baki tayi ta zauna a bakin gado tace,
"Allah sarki Baban Gida, tinda na ƙi dawowa nan sai ya ajiye hoto na ya dinga gani yana jin daɗi."
"Ah toh ba dole ba Baaba, ke da gidan ɗan ki amma kin ƙi zuwa ki sakata ki wala ki bararraje,kowa so yake yaga yana da wani makusanci me kuɗi a Abuja ya zo,amma ke kin kafe kin nace sai dai a bar ki a ƙauye."
Murmushi Baaba tayi kafin tace,
"Yaro yaro ne,ai bari ki ji ƴannan,a yanda zamani ya koma yaran yanzu basu son zaman surukan su a gidan su,ke ko ma ana so a gani na uwar miji idan tana da nata muhalli to tayi zaman ta a can shine mutuncin ta, shi kuma ɗan nata da matar shi su ji tsoron Allah su dinga kyautata mata, su dinga kai mata ziyara akai-akai,abun duk da suka ci ko da ba za su baiwa mahaifiyar mijin sak irin shi ba to su kwatanta,idan akai haka kowa sai ya zauna a inda yake cikin aminci,kai baka takurawa surukar ka ba, itama bata gaji da kai ba ta takura maka."
Gyad'a kai Anisah tayi cike da gamsuwa da bayanin Baaba, banɗaki ta raka Baabaa ta cika mata ruwa a buta, sai ta haɗa mata
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 51 Chapter of 70