same shi a cikin wani irin mawuyacin halin da ya sanya ta fita da gudu ta nufi dakin Innah Laminde tana ihu,
"Innah ! Innah ki zo yayah ya na ta nishi da kyar a ɗakin shi,"
Cikin sauri kafin Innah Laminde ta fito daga ɗakin ta Billy ta yi ɗakin nashi da gudu, kwance ta ganshi a qasa yana murqususu yana numfashi da k'yar, d'ago shi ta hau qoqarin yi amma ta kasa, Innah Laminde ce ta shiga ɗakin taga halin da yake ciki da gudu ta koma ɗakin ta ta ɗauki waya ta kirawo Sultan,bata jima tana ringing ba ya ɗauka, cikin muryar dake bayyanar da tashin hankalin da take ciki tace,
"Sultan ka bar dik abinda kake yi kazo da mota mu kai yayan ku asibiti bashi da lafiya,"
"Gani nan zuwa ina qofar gida,"
Kashe wayar yayi ya shiga gidan cikin sauri, direct d'akin Abdussaboor suka nufa a tare da Innah Laminde dake ta salati da kiran sunayen Allah.
Koda suka shiga sun tarar da Billy na zaune a gefen Abdul tana ta kuka kamar ranta zai fita,da kyar Sultan ya iya kama Abdussaboor ya fita da shi zuwa mota, Innah Laminde ta so a tafi da ita amma tayi kawaici Ummah matar sarki ta biyu ta bi su ita da azizah.
***************************
Tinda Abdul yace wa Mommy da Innoh su wuce gida sai suka taka suka fara tafiya,basu bi su Baabaa dake ta'ajibin abinda ya faru a fada ba sai suka ratse gidan su Innoh, daga nan suka ɗauki Naja suka wuce gidan bokan su dan sanar dashi dik abinda yake faruwa.
Innoh ce ta sake muskuta manyan mazaunan ta ta kalli bokan su dake ta murmushi yana gyad'a kai tace,
"Ran bokan dik duniya ya dad'e muna godiya akan wannan babban aiki da ka yi mana, aiki naka nasara tamu, sai dai fa babban bokan duniya ina jin tsoro, ina jin tsoron abinda zai je ya zo a game da abinda ya faru na zuwan waɗannan 'yan daudu da karuwan,anya kana ganin lamarin nan ba zai lalace ba?.................."
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 43:
"Kar ku ji komai ku dai kawai ku ajiye kuɗin aiki dubu hamsin idan kuna da shi, kafin safiya maganar nan zata zama kamar ba a taɓa yin ta ba, dik wani mai ganin aibun ki a gidan sirikan ki zai koma ganin farin ki, za su so ki, za kuma ki zauna zaman aure da ɗan su har ku hayayyafa ma,"
Cike da murna Mommy ta buɗe baki zata yi magana Innoh ta riga ta tace,
"Ran boka ya jima yayi qarko gaskiya bamu da wannan maqudan kuɗaɗen a yanzu amma..."
"Innoh kar ki damu ya bamu account No idan yana da shi zan tura masa, idan babu kuma muna zuwa gida zan bayar a bashi,"
Kallon Mommy Innoh tayi baki sake, ashe Mommy nada kuɗi a boye amma taqi bata duk irin faɗi tashin da take yi akan ta sama mata soyayyar Abdul? Ɗauke kai tayi cikin ɓacin rai tace wa boka,
"To kaji me tace,idan akwai afwun lambar se ka bata ta tura maka ko ba haka ba Naja? Masu abu da abun su kura da kallabin kitse?"
Naja ce ta gyad'a kai cikin sauri sannan tace,
"Aiko dai Yayah kin ga shikenan ma ta zo gidan sauqi,dake yanzu kusan kowa na da wannan lambobin bankin sai kawai ta tura masa baki alekum,"
Boka be b'ata lokaci ba wajen karantowa Mommy account No ɗin shi, Mommy kuwa nan take ta lode a wayar ta, kafin su tashi a wajen ta tura masa dubu ɗari, sanda ya duba wayar shi yaga kuɗin murna ya hau yi tare da faɗin,
"Kar ku ji komai zan yi maki aiki yarinya har da wanda ma baki san da shi ba,nifa ina son mutumin da ya san darajar kan shi yanzu duniyar ai ba a zama sai da neman taimakon masana, ku tashi kuyi tafiyar ku a ci gaba da shirin biki, aure ya riga ya qullu mutuwa ce kawai zata raba shi,"
Cike da tsananin farin ciki suka tashi suka tafi, tin a hanya Innoh ta tura baki gaba ta wuce ta bar Mommy da Naja a baya ranta a matuqar haɗe ta isa gida, ko da ta shiga ta hango sashen Baabaa ba a buɗe ba sai bata kawo komai a ranta ba ta shige d'akin ta, Ameerah ta gani kwance a gado tana ta kukan baqin ciki, sai a sannan ta tuna da sanda Ameerah ta bar wajen taron cikin ihun kuka shamsu na biye da ita yana aikin lallashi,tausayin ta ne ya kama Innoh sai kawai ta qudirta a ranta dole ne ta aika Naja wajen boka ya san yanda zai yi ya raba Ameerah da soyayyar Munir amaye gurbin shi da soyayyar Shamsu, ta haka ne kawai zaman auren su zai yi daɗi a huta da tashin hankalin da Ameerah zata dinga b'allo musu a duk sanda tsiyar ta ta tashi.
Mommy da Naja sun iso gida shajaran majaran dan haka a tsakar gida suka zube, ganin Baabaa da tawagar ta basa nan ne ya sanya Naja buɗe baki tace,
"Ah ah Yayah ina wannan qarmasasshiyar tsohuwar tayi ita da ayarin ta kuma?"
Innoh ce ta fito tsakar gidan da d'aurin qirji kai ba d'ankwali ta zauna a dokin qofa ta ce,
"Ina na san inda take ni da na dawo yanzu? Naja dan Allah idan zaki wuce gida ki tuna min zan baki saqo wajen bawan Allah'n nan da ba a kama sunan shi a tsakar gida,"
Innoh na fad'ar haka Naja ta gane wa ake nufi sai suka sanya shewa, Mommy tace,
"Wai Ameerah har yanzu kuka kike yi baza kiyi hakuri ki sanya wa kan ki salama ba?"
Cikin faɗa Innoh tace,
"Taqi sanya wa kan nata salama mara mutunci,ai dama jira nake yi mu dawo gida na ci uban ki son rai na,ashe kina da waɗannan arnan kuɗin muke zaune haka ? Anya Mommy kina da tausayi kuwa? Da alama dai zuwan ki birni an sauya min ke dan kuwa a iya sani na dik cikin yaran nan kin fi kowa tausayi na, amma ace kina nan maqale da maqudan kud'ad'e ki kasa jifana da ko hamsin ɗin ce bayan a kan idon ki nake ta faɗi tashi dan kawai burin ki ya cika, maganar Ameerah dai ita ke neman zama gaskiya,ke da nake wahaltawa kece ke bani wahala,"
"Haba Innoh,yaushe ma hankali na ya kwanta balle har na hau baki kuɗi? Yanzu da amfanin su yazo ba gashi ana morar su ba? Ki kwantar da hankalin ki Sule ya dawo na bashi ya ciro wani abun sai na baki ke da Aunty Naja,"
Naja na jin maganar kuɗi ta ce,
"Habaa Innoh me yasa kike da gajen hakuri ne uhumm? Ai shi ɗan yau lallab'a shi ake yi ba wai ki kama yi mata faɗa irin haka ba, to yanzu dai ba wannan ba, tashi zaku yi na gyara maku jiki da abubuwan mu na amfanin yau da kullum tinda abubuwan sun zo a qurarren lokaci bamu samu damar yi muku gyaran amare ba,Yayah maza samo min waɗannan abubuwan a haɗa a gyara amare dasu,"
Lalle
Ganyen magarya
Farar shinkafa
Kurkur
Gishiri
Ruwan tsamiya/lemon tsami
Manja
Innoh ce ta miqe da kyar ta shiga d'aki tana ci gaba da mita akan yanda Mommy ke maqale kuɗi bayan ta san tana da buqatar su, dan wa take faɗi tashin idan ba su ba? Ita dai Mommy hakuri ta dinga bata da alqawarin bata dubu ɗari cash ita kuwa Naja tayi mata alqawarin dubu hamsin ita da Ameerah, Ameerah kuwa jin za a bata maqudan kuɗi masu yawa haka ne ya sanya ta fitowa tsakar gidan tana tura baki ta zauna dan ayi gyaran jikin har da ita.
Bayan an kawo wa Naja waɗannan abubuwan data nema ne ta miqe ta hade shinkafa, ganyen lalle, ganyen magarya,da kurkur ta sa a injin niqan Innoh ta niqe su tasss sai da suka yi laushi sosai sannan ta karb'i ruwan tsamiyar da ta sa Mommy jiqawa ta tace akan garin shinkafar nan ta zuba gishiri kaɗan,qaramar jarkar manja ta ɗauka ta karkata ta d'ebi marfi uku ta zuba sannan ta saka hannun ta ta juya sosai ta ajiye a gefe tace,
"To Yayah fa se kin yi hakuri dan kuwa dole ki bamu kaji biyu a kajin nan naki da bakya ci bakya sadaka da su mu yi amfani dasu,"
Wata harara Innoh ta makawa Naja sannan tace,
"Haka kawai sai in bada kajin da na sha wahalar kula da su suka yi girma haka babu ko sisi?"
"Innoh kiyi wa Kajin naki kuɗi zan siya,"
"Yanzu naji magana, gasu nan a bani dubu bakwai-bakwai idan an siya a haka a ɗauka idan ba a siya ba a aje min abuna babu shegen da ya taya ni watsa musu hatsi acikin ku ah toh,"
Babu b'ata lokaci Naja ta kame kaji ta yanka ta kira Mommy tace ta fige, cike da kyankyamin kajin Mommy ta toshe hanci tana kallon Ameerah bata ce komai ba,cikin zabgawa Mommy harara Ameerah tace,
"Kike wani kallo na dan kin siyi kajin wato ni se in fige ko? To kar Allah yasa a ci kajin a bar su, ke fa na kula wani jin kan ki kike yi kamar wadda tayi tashin turai ba qauyen Ba mugu ba, dika-dika watan ki nawa a birnin? Ko fa shekara baki yi ba rayuwar ki kaf a qauyen nan kika yi ta amma da an yi magana ki dinga maida mutane kidahumai, mtswww aikin banza kawai,"
Qarshe dai da Naja taga abun zai zama rikici ita ta zauna ta fige kajin ta daka kayan qamshi da attaruhu ta zuba daddawa sosai ta hura wuta ta dora su dan yin farfesu tinda lokaci ya qure da za su bazama neman kayan mata na musamman.
Suna ji ana kiran Sallahr la'asar amma dik cikin su babu wadda ta motsa dan yin sallar sai ma d'akko wannan haɗin farar shinkafar da Naja tayi ta sa su Mommy su tub'e ta gyara su, babu b'ata lokaci kuwa suka d'aura zani mommy ta ja under skirt ɗin ta zuwa qirjin ta Naja ta zauna ta murje su da wannan haɗin na shinkafar.
Shiru Mommy tayi tana tunano sanda tana gidan Hajiya K'waisa irin gyaran da ta dinga sha kamar wata sarauniya, k'wallar baqin cikin abubuwan da suka faru da ita a baya ne ta sirnano mata, cikin zuciyar ta take ayyana,
'Ko ya ake ciki a gidan su Yah Abdul yanzu? Anya Billy zata kyale ni na yi rayuwar aure cikin farin ciki kuwa? Bari na gama na kirawo Yah Abdul naji ya ake ciki dan naji shi shiru bai kira ni ba,'
Ameerah ta kalla taga yanda ta jingina kanta a jikin gini ta rintse idanun ta hawaye na zuba daga idanun nata dik da a kulle suke, tausayin tane ya kama mommy cikin sanyin murya ta dafa Ameerah tace,
"Ameerah kiyi hakuri da qaddarar data same ki, ina faɗa maki haka ne saboda ina son ki kuma na san ko auren ki Munir yayi ba zai kula dake da kalar soyayyar da kike yi masa ba sai dai ma ya wulaqanta ki,ni kaina badan wannan abin da aka yi wa Yah Abdul ba dan ya so ni na tabbata wahala zan sha a gidan shi bayan auren dik da cewar yana so na tin kafin mu dawo, amma kin ga shamsu na son ki sosai zaki murza kambun ki a gidan su, sai fa yanda kika yi dashi,ke ce zaki sama sitiyarin saita rayuwar shi sai abinda kika ce shi zai yi, ke yanzu dan Allah hakan bai fiye maki auren wanda zaki sha wahala a hannun shi ba?"
Cikin sharce majinar dake shatata a hancin ta Ameerah tayi murmushi mai ciwo tace,
"Humm Mommy kenan, ai yanzu aikin gama ya gama kawai ba yanda zan yi dole na karb'i qaddara ta, amma ni na tabbata dan bani da kuɗin da kike da shi ne yasa Innoh ke nuna mana banbanci, da ace nima ina da irin kuɗin ki ta san zata fanshe su ko ba jima ko ba dad'e nima da ta shiga ta fita na auri zaɓin raina, ke yanzu ba gaki kin samu farin cikin ranki ba?"
"Ameerah ba zaki..."
"Dan Allah Mommy mu bar wannan Maganar kawai, kema kin san gaskiya na faɗa,Allah ya bamu zaman lafiya kawai shine abinda zan ce,"
Cikin sanyin jiki Mommy tace,
"Ameeen,"
Ta ja bakin ta ta tsuke,suna nan zaune Mommy ta ja Naja zuwa d'akin Yadiko ta qirga kuɗi dubu ashirin ta bata tace ta je ta samo mata maganin mata mai kyau a islamic chemist din cikin kasuwar dare ta garin nasu, Naja ta sha mamakin lamarin nan sosai, ita kuwa Mommy ta riga ta saba da shan irin kayayyakin nan a wajen su Hajiya K'waisa kafin taje ta haɗu da maza,dan haka ta san darajar su,sune suke yi mata kallon ta Allah amma abinda ta sani a iya watannin nan su basu san shi ba.
****************************
Da misalin tara na dare Sultan ya tafi bakin tasha d'akko Bilal da ya iso daga Bauchi, dan kuwa tin bayan d'aurin auren Mommy da Abdussaboor Sultan ya sanar dashi komai ta waya anan take Bilal ya sanar dashi cewar dama ko bai sanar dashi maganar auren ba dole zai zo saboda abinda aka tura masa a wayar shi ya munana,direct asibitin da aka kwantar da Abdul suka je, zaune suka tadda shi yana shan lemo da ayaba Innah Laminde na ta jera masa sannu, ji take yi kamar ta zare masa ciwon ta mayar jikin ta, bayan sun gaisa da Bilal da jajanta abinda ya faru dan kuwa ba murna suke yi da wannan auren ba balle su taya juna murna, sai Innah Laminde ta kalli Abdul tace,
"Allah dai ya baka lafiya SARAUTA, ka kula da kan ka sosai dan Allah, ka dai ji me likita yace d'azu da ya zo,likita yace da alama ka shiga rud'ani ne na ji ko ganin wani abun da ya tada hankalin kane har yayi sanadiyyar da jinin ka ya hau kaɗan,se kuma ciwon dake kama mutum idan ya cika zirga-zirga, (stress) ita zirga-zirgar dama har ciwon ta ake yi Bilal, gaskiya baturen mutum sai dai a bar shi, Allah kuma ya baiwa mutanen qauye hakuri,mu nan mutum idan ya tashi tun safe ba sai ya wuni a tsaye ba yana lodar aiki be huta ba?"
Murmushi kaɗan Abdul yayi cikin muryar shi mai cike da natsuwa yace mata,
"Innah ai dole ciwo ya kama ni, ki duba fa ki ga hutu na zo yi amma abubuwa duk sun rincab'e min daga wannan sai wancan, na kasa samun hutun da nake so zuciya ta da gangar jiki na ta gaji Innah,gashi matar da nake so kuma ana so a raba ni da ita ko ta halin qaqa kin ga kuwa ai dole na kamu da ciwo,"
Hoton Mommy ne tsirara ya gilma a idanun Innah Laminde, nan take ta rintse idanun ta tana jin wata iriyar tsana da qin Mommy a cikin ranta,cikin haɗe fuska sosai tace,
"SARAUTA bana son ka sake yi min maganar yarinyar nan, kai dai ka maida hankalin ka wajen samun sauqin abinda ke damun ka, daga baya zaka ji hukuncin da mahaifin ka zai yanke akan ta,da alama kai baka san komai ba game da yarinyar da ka aura Bilkisu ta sanar dani komai kuma ta nuna min komai dan haka ni dai ban yarda da auren nan ba, ba kuma zan yarda da shi ba har gaban abada,"
Cike da tashin hankali Abdul ya kalli Innah Laminde sannan ya kalli Bilal da Sultan cikin kad'uwa yace,
"Kema ta nuna maki abinda ta tura min a wayata?"
"K'warai ta nuna min, ta kuma tabbatar min da cewa yarinyar nan karuwa ce dan...."
Cikin rintse idanu Abdul yace
"Dan Allah Innah ki daina faɗin haka, bafa da wani aka kama yarinyar nan tana zina ba, ki sake duba videon da hotunan da kyau zaki ga a wajen gyaran jiki aka yi mata su ba da sanin ta bane sharri kawai ake son a qulla mata dan kawai a raba mu, ita Bilkisun da ta turo a ina ta samu? Idan har Hadiza karuwa ce ita kuma fa?,"
Mamakin Abdul ne ya sanya Innah Laminde kasa cewa komai, kallon shi kawai take yi tana ayyanawa a ranta,
'Anya yarinyar nan haka ta bar min ɗa na kuwa bata sabauta min shi da baqin asiri ba?'
Jin kalmar shi ta qarshe ne ya sanya ta miqewa cikin ɓacin rai tace,
"Abdul baza ka yi zaman aure da Hadiza ba har abada, dole ne ka sawwaqe mata dan ba zan zauna da karuwa a matsayin suruka ta ba,idan kuwa ka qi bin umarni na kaqi sawwaqe mata to tabbas sai dai ka nemi wata uwar amma ba Laminde ba kaji na faɗa maka,"
Cike da fushi Innah Laminde ta juya zata bar asibitin Sultan da Bilal suka hau bata hakuri amma taqi zama firrr tace tafiya gida zata yi, cikin sauri Sultan ya bi bayan ta dan ya maida ita gida.
Hankalin Abdussaboor ne yayi bala'in tashi dan jin furucin mahaifiyar shi akan auren shi da yake jin a duk sanda ya datse shi to fa kamar ya datse numfashin shi ne, Bilal ne ya dafa kafad'ar shi yace,
"Shin abinda aka tura min a wayata gaskiya ne game da Hadiza? Indai ta tabbata yarinyar nan haka take dole ne ka daure ka riqe auren nan da kyau saboda babu macen da ta fi dacewa ka aura sama da Hadiza a rayuwar ka............"
*Ko meye dalilin Bilal na faɗin haka?.....ku ci gaba da bi na dan jin yanda zata kaya...... ku qara hakuri a kai qarshen labarin dik zaren da ya qulle maku zan warware muku shi a sannu...kar ku manta sannu bata hana zuwa sai dai a jima ba aje ba.*
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA: HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 44:
Ganin Sultan na wajen ne ya sanya Bilal kawar da maganar da yake so yayi wa Abdussabour,wajen zama ya samu yana yi wa Abdussabour bayanin yanda yana zaune wata No ta tura masa hotuna da videos ɗin Mommy tsirara, cikin tsananin baqin ciki da takaici Abdul yace,
"Ya qarshen No yake?"
"90 ne qarshen ta, ka san me No ne?"
Girgiza kai Abdul yayi domin kuwa bai san mai No ba, amma ya tabbata ko wanene sai ya nemo shi kuma sai ya miqa shi wajen hukuma an hukunta masa shi gwargwadon abinda ya aikata na fitar da tsiraicin matar shi, Sultan ne ya ja bakin shi ya tsuke dan kuwa shima an tura masa, fad'ar an tura masan zai iya sake jefa Abdul a wani mummunan hali dan haka sai ya ɗauki plate ya zubawa Bilal abinci ya ɗauki ruwan roba ya kai masa yace,
"Yah Bilal ka ci abinci ka je gida ka kwanta ka huta ka d'ebo gajiyar hanya, ni zan kwana da Yah Abdul ɗin, ina ga dik muyi haƙuri da Maganar nan for now har Allah ya baka lafiya, dama so ake a raba ku, ni kuma a gani na tinda har kana son ta kawai ka rufa mata asiri ka riqe igiyar auren ku da kyau, wataqila za a rage samuwar irin su a society,"
Cikin ɓacin rai Abdul ya kalle shi yace,
"Wai kana nufin ka yarda da abinda ake faɗa akan Hadiza? Sharri ne fa da neman b'ata mata suna kawai, kana ganin wajen da take ka san wajen gyaran jiki ne aka samu wani marar imanin yayi mata videon, sannan...."
Bilal ne ya tari numfashin Abdul yace,
"Kaga Abdul a bar maganar kawai kamar yanda yaron nan yace,hakan shine kawai samun natsuwar ka a yanzu, ba dai kana son matar ka ba? To ai magana ta qare babu wanda zai zauna maka da ita dan haka mu rufe wannan maganar kai Sultan bani waku na wake tabahuwa nake ji,"
Abincin da Sultan ya zubawa Bilal ya miqa masa, Bilal ya Karb'a yana yi musu hira amma Sultan ne kawai ke amsa masa,Abdul kuwa ya lula duniyar tinanin rayuwar da ta tinkaro shi da wadda ya bari a baya, lallai maganar Bilal gaskiya ne, shine yafi dacewa ya auri Mommy,domin kuwa dama an faɗa abinda dik kayi sai an yi maka, dik wayon ka da zillewar ka watarana zaka girbi abinda ka shuka, to ga ranar girbi tazo masa, ranar da yayi zaton komai ya wuce har abada tinda ya dena abinda yake yi a lokacin da quruciya na jan shi,a hankali ya furta,
"Astaghfirullah wa'atubu ilaih,"
Nan take tunanin shi ya ɗauke shi ya maida shi shekaru takwas da suka gabata.
A shekarar da Abdussaboor ya kammala karatun shi a shekarar ya samu aiki saboda gata da connection da yake da shi, dik da cewa shi ɗin haziqi ne amma hazaqar shi ba ita ta bashi wannan aikin ba, idan da hazaqa na bada aiki nan take tabbas da wanda suka fishi hazaqa sun jima da zama manyan ma'aikata a qasar nan.
Cikin shekara ɗaya da fara aikin shi ya samu mahaukatan kud'in da ya sai fili da su a cikin garin kano da qauyen Ba Mugu,a haka ya ci gaba da rayuwa a gidan haya har ya samu ikon ɗora ginin gida mai ɗakuna uku da parlour biyu sai kitchen,store room da wani band'aki guda ɗaya a general parlourn gidan,gida ne mai kyau da ya amsa sunan shi gida domin kuwa ya samu zane daga k'wararrun masu zane, sannan maginan da suka yi ginin suka baiwa zanen nan haqqin sa.
Tinda ya kammala gidan ya fara kiciniyar sanya furniture a gidan wanda Sarki da kan shi ya bada tashi gudummawar saboda ganin qoqarin da Abdul ɗin ke yi birni da qauye na ganin ya samarwa kan shi muhallin, wanda a zaton su da ya kammala ginin nashi aure zai yi, sai dai bayan kammala gina gida Abdul sai ya koma tara kuɗin siyan mota mai kyau da zata dace da gayun shi da matsayin shi a wajen aikin shi da kuma nuna isa da taqamar shi na mulkin gidan su.
Dik abun nan da yake yi daga Sarki har Innah Laminde babu wanda ya taɓa yi masa maganar aure saboda ganin shi ɗin yaro ne mai hankali da hangen nesa, yana yin komai a bisa tsari da cancanta da duba buqatuwar yin hakan a gare shi,gefe ɗaya kuma basu san cewar yaron su Abdussaboor na da matsananciyar sha'awa ba ta yanda baya taɓa kwana ɗaya zuwa biyu ba tare da ya nemi wadda zata ɗebe masa kewa ba, a zahiri ko kuma ta wayar nan ta zamani har buqatar shi ta biya ya samu natsuwa.
(Qalubale a gare ku iyaye, dik natsuwa da hankalin ɗan ku yana da sha'awa a cikin halittar shi take, dan haka kar ku sake ku kauda kai akan wannan bangaren wajen kula da tarbiyyar yaran ku maza da mata)
A cikin shekaru huɗu Abdussabour ya gama gina gidajen shi na cikin garin Kano da na qauyen Ba Mugu, sannan ya sayi mota mai azabar kyau da tsada, kuɗi ne suke ci gaba da shigo masa ko ta ina saboda aikin shi da yake yi ba dare ba rana, ganin yanda ya zama busy ne ya sanya Sarki qara ganin bari ya kyale ɗan nashi har sai ya bijiro masa da zancen yana son yayi aure, idan yaso sai a yi a wuce wajen, dan kuwa ya kula a yanzu bashi da lokacin kanshi ma balle na mace, neman kuɗi kawai ya sanya a gaba, nan kuwa bai sani bane da zarar ya gama da aikin shi yake wucewa joint ɗin da yake samun macen da zata ɗebe masa kewar gajiyar aikin da ya sha da rana.
(Wannan shine dalilin da yasa maza komai gajiyar da suka yi a waje idan dare yayi suke buqatar matan su a kusa da su, dan haka dik kamun kan yaron ku iyaye idan ya kai minzalin aure kar ku yi qasa a guiwa wajen tirsasa shi ya yi aure, ko ku taya shi neman matar da zai aura, ko ku bashi dama da 'yancin nema da kan shi)
A kwana a tashi Abdul na neman matan banza yana kaiwa gidan shi ya hole da su ba tare da sanin iyayen shi ba balle dangin shi,a haka har ya haɗu da Bilal dan garin Bauchin Yakubu,Bilal mutum ne mai rawar kai da wayewa tare da ɗaukan wanka na garari, dik da cewa Abdul sama yake dashi a wajen aiki hakan be hana su yin abota ba,qarshe Abdul ya gane
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 29 Chapter of 70