bawa jiki haqqin shi, kin karb'i magungunan da zaki yi amfani da su ko?"
"Eh hajiya na Karb'a,"
"Maza jeki jeki kar ya ga kin jima,"
"Kar ki manta da haɗa ni da abokin shi fa"
"An gama qawata, sai na dawo"
Sallama Mommy ta yi musu ta fita sanye da takalmi flat mai igiya kore kalar rigar ta, saman shi nada wasu golden stones masu kyau kamar yanda suke a jikin rigarta ta gaba,ta na isa motar ya buɗe mata yana yi mata murmushi, wani glass mai kyau da tsada ya bata mai duhu da face mask ta Karb'a ta sanya a fuskar ta sannan motar su ta tafi,tafiyar da da ta san qalubalen da zata fuskanta a cikin ta da ko miliyan ɗari yace zai bata baza ta amince da yin ta ba.........
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA: HAERMEEBRAEH
*Assalamualaikum mutanen k'warai masu albarka ina godiya matuqa da addu'o'in ku zuwa ga stepmom ɗina da Allah ya yi wa rasuwa, wanda a bisa wannan dalilin ne yasa ban samu damar ci gaba da rubutun ba, ko a yanzu ma ganin kun damu da ci gaban labarin ne ya sanya ni gwada ci gaba sai kuma aka yi sa'a Allah ya bani ikon rubutawa,a dai-dai lokacin da na san rasuwar na ɗora yatsuna zan ci gaba da rubuta page 23 ne dan har na ma fara,to shi yasa da na zo zan yi rubutun se na ji na kasa,amma alhamdulillahi gashi nan na samu dama zamu ɗora daga inda muka tsaya Allah ya sa mu gama lafiya... Wanda suka kira waya, messages da wanda suka je ta'aziyya har gida da masu niyyar zuwa ina godiya Allah ya jiqan magabatan mu baki ɗaya,Allah ya yi mana kyakkyawan qarshe idan namu lokacin ya zo, na gode sosai da kulawar ku a gare ni Allah ya qara mana lafiya da zaman lafiya a qasar nan da duniya baki ɗaya.*
PAGE 23:
A cikin filin jirgin Aminu Kano motar su Mommy ta tsaya, nan take ta kula da wasu manyan motoci guda uku na daban da suka sauke wasu mata wanda kusan rabin su sanye suke da facemask,dikkanin su qananan kaya ne a jikin su ana ajiye su suka ja akwatunan su suka shiga cikin airport ɗin, a zatan Mommy Alhajinta ne zai zagaya ya buɗe mata mota kamar yanda suka saba, sai ta ganshi ya maqale waya a kunnen shi ya yi gaba, driver ne ya buɗe mata motar ta fita,sororo tayi kafin daga baya ta gyara tsaiwar ta tare da kama qaramin akwatin ta tabi shi cikin airport ɗin,dik yanda taso ta tsaya kusa da shi sai ta ga ya kanga waya a kunne yana magana ya matsa daga inda take.
A haka aka gama dubawa da auna nauyin kayan su suka wuce dan zuwa cikin inda za su jira tashin jirgi,can saman bene ta hango Alhajin ya yi gaba ya barta a baya riqe da qaramin akwatin ta da 'yar jakar ta, cikin sauri ta bi bayan shi itama tana ta mamakin sauyawar shi cikin lokaci qanqani,zuciyar ta ce ta raya mata cewar,
'Mommy bawan Allah'n nan fa yana da iyali, kuma babban attajiri ne taya zai so duniya ta san yana mu'amala da matan da ba nashi ba? Kama kan ki kema yanda ya yi kawai,'
Siririyar jakar ta ta gyara a kafad'ar ta sannan ta hau yi wa kanta hotuna har ta isa can wajen da ta ga kujeru a jere ta samu nesa da Alhajin ta zauna, suna haɗa ido ya yi mata murmushi dan kuwa ya fahimci ta gane me yake nufi.
Cikin abinda be wuce minti goma sha biyar ba Mommy da sauran mutanen da ke jiran jirgi duk sun shiga jirgin kowa ya samu wajen zaman shi ya qame,mazaunin Mommy na bayan na wata budurwa da ta taɓa gani a resort ɗin Alhajin nata, cike da tsoro ta qanqame jikin belt ɗin da ta d'aure qugun ta tin kafin a bada umarnin a d'aura ɗin, kusan hawan ta jirgi na uku kenan kuma dik da Alhajin ta take yin tafiyar zuwa Abuja, ta rasa dalilin da ya sanya ta ganta a bangaren economy ba first classs ba kamar koda yaushe, da dikkan alamu Alhaji na can na jin daɗin shi ya barta a nan cakud'e da mutane kala-kala babu mai lallashin ta da kwantar mata da hankali a lokacin da jirgin zai lula sama.
Wasu hawaye ta ji masu d'umin gaske suna bin kuncin ta, bata san sanda zata dena jin tsoron hawa jirgi ba, maybe kuma ba za ta taɓa dena jin tsoron ba.
Tana nan tana ta tunani da addu'o'i tare da kiran mutanen gidan su kafff tana kuka jirgi ya daidaita a sararin subhana,mommy na nan kulle da idanun ta har na tsawon wasu mintuna kafin cikin sauke ajiyar zuciya ta buɗe idanun ta da ta kulle gam, wata mata ta gani riqe da ruwa cikin wani kofin roba fari tana yi mata murmushi jikin ta sanye da uniform, nan take ta gane ɗaya ce daga cikin ma'aikatan jirgin, da sauri ta karba ta kurɓe ruwan ta na sauke ajiyar zuciya.
Jirgi na nan na ta tafiya har mommy ta samu bacci, Alhaji kuwa na can shi da abokan harqallar shi suna tattaunawa akan business ɗin su,wanda kafin hakan ta faru yariga da ya bada umarnin a kula masa da ita dan kuwa ya san yanda take jin tsoron jirgi.
A Murtala Muhammad airport dake garin Lagos jirgin su ya tsaya, bayan sun fita ne Alhaji ya zo inda mommy take tsaye tana zare ido dan kuwa ta kasa gane ina ne nan ɗin, shin har sun iso Ugandan ne ko kuma ina ne nan ɗin?
"Baby kar ki damu, akwai wani saqo mai mahimmanci da zan karb'a ne shi yasa muka biyo ta lagos,daga nan zamu hau jirgi zuwa qasar Uganda kin gane? Akwai abinda kike so ne?"
"Eh ina so in yi fitsari,kuma ni yunwa nake ji abincin jirgin nan kasan baya wani isa ta ni,"
Cike da shagwab'a ta qarasa maganar ta wanda hakan da take yi yana burge shi sosai, cikin murmushi ya ja hannun ta ya kai ta inda zata yi fitsarin sannan yace ko da ta fito bata ganshi ba ta je ta samu waje a inda kujerun nan suke ta jira shi zai neme ta.
Tana shiga kuwa ya tafi wajen wani Inyamuri da ya isa filin jirgin da wasu zuqa-zuqan 'yan mata guda uku farare tass da su ba irin farin mai ɗin nan ba,kan su ya sha qarin gashi kowa da kalar nata, duk yanda suka kai ga kyawun fata da kyawun jiki sai Alhaji yaga Mommy ta fi su shape mai kyau, sannan fatar ta tafi tasu santsi da taushi,kallon su kawai yake yi dan kuwa ba haka yaso ba, cikin zuciyar shi yana ayyana,
'Yanzu dai dole ne sai na rabu da wannan 'yar shilan idan munje tinda ban samu replacement ɗin ta ba har yanzu'
Hannu suka yi shaking da wannan inyamurin suka yi sallama kowannen su ya kama harkonkin gaban sa kamar basu san juna ba, a haka mommy ta fito ta tarar har an fara kiraye-kirayen tafiya qasar Uganda.
Babu b'ata lokaci Alhaji ya yi wa Mommy alamar ta tashi su tafi, haka kuwa ta tashi ta bi bayan shi tana jin yanda take jin yunwa ta qudirta idan bata qoshi ba wannan karon in an bata abincin jirgi zata ce a qara mata ina dalili ai dai biya suka yi.
Daga turancin da ta ji ma'aikatan jirgin suna yi ta tabbatar da cewa lallai wannan ba irin turancin Nigeria bane, nan take ta sa natsuwar ta dan ta gane me ake faɗi amma ta kasa, dan kuwa turancin Nigeria ɗin ma ba kowanne take ji ba sai sama-sama.
Wannan karon ma sai da ta ji tsoro a lokacin da jirgin ke tashi, yana gama daidaituwa a sama ta sauke ajiyar zuciya ta lunshe idanun ta, kowa ka gani harkar gaban shi yake yi, wasu mata dake kusa da ita taji suna yin wani yare wanda bata ganewa,haka nan taji yaren ya yi mata daɗi,sai kawai ta jingina kanta a jikin kujera tana kallon su tana murmushi, zuciyar ta ce ta ke hango mata mahaifin ta Ɗan liti yanzu idan yasan ba aikatau take yi ba ta zama karuwa ya zai ji? Shin Innoh zata damu ma kuwa da lalacewar ta? Allah sarki Yadiko da tana nan tabbas taji ba aikatau take yi ba karuwanci take yi sai hankalin ta ya tashi, nan take ta hau yi mata addu'a a haka bacci ya ɗauke ta.
Duk rabon abincin da aka yi aka gama Mommy bata sani ba, tana can ta hangame baki cikin facemask tana zuba baccin ta cikin kwanciyar hankali
Tafiyar awanni shida ne cur ya tsaida jirgin su Mommy a Entebbe international airport dake capital city na Kampala dake qasar ta Uganda.
Dikkanin mutanen dake ciki ne suka hau sakko da kayan su daga inda suka ajiye su a saman kujerun jirgin, wanda basu da kaya kuwa haka suka dinga fita suna sauka daga jirgin,Mommy ma tashi tayi tana miqa tare da zabga hamma ta janyo akwatin ta ta jashi zata fita, a hanya ta haɗu da ma'aikatan jirgin suna yi mata murmushi da barka da zuwa qasar Uganda cikin turancin da ke cike da accent ɗin yaren su, murmushi kawai tayi ta sauka ta shiga motar dake tsaye ta kwashe su ta kai su bakin airport ɗin ta ajiye.
Da qafa suka taka suka je suka kammala dik wani abu da ya kamata su yi suka bar filin jirgin zuwa waje dan shiga abun hawa su isa masaukin su, ga mamakin Mommy wasu manyan motoci ta dinga gani suna layi matan nan da ta ga sun taho da su suka dinga shiga, ita kuwa tare da Alhajin ta suka shiga mota ɗaya suka lula sai cikin gari, tafiyar minti goma sha biyar ce ta isar da su Mowicribs hotel and spa.
Kalle-kalle mommy take ta yi, dan kuwa yanda ta zaci qasar da fari sai ta ga ba haka ta ganta ba, amma suna zuwa wannan had'ad'd'en hotel ɗin sai tunanin ta ya sauya ta hau washe baki tana shafa Alhajin tana faɗin,
"Allah ya sa muna isa abinci za a kawo min, muguwar yunwa nake ji, ban samu na ci abinci ba a jirgi ina ta bacci,"
"Kar ki damu, muna isa zaki ci abinci sai kin ture,ina yi maki maraba da zuwa Uganda qasar 'yanci,"
"Lallai na ga alama, dan kuwa su babu ruwan su kowa sai harkar gaban shi yake yi kamar kana kudu a Nigeria, ba ruwan ka da sa ido,"
"K'warai da gaske my love, ina fatan zaki saki jiki ki ji daɗin ki,"
"Sosai ma, kai dai mu je ciki na samu na huta tukunna ka ga sabuwar rayuwar da zamu gina, sai na sa wannan tafiyar ta zame maka tafiya mai kafaffen tarihi a rayuwar ka,"
Kafe ta ya yi da idanun shi da wani irin kallon da ta kasa gane kalar shi sannan yace mata,
"Ah ah ! Ni ne zan kafa maki tarihin da bazaki taɓa mantawa ba a wannan tafiyar Sweet H ! "
Bata san me yasa ba sai ta ji qirjin ta ya yi wata irin mummunar bugawa, shi kuwa Alhaji sai ya sakar mata murmushi mai qayatarwa har dai da Mommy ta saki jikin ta,a daidai wannan lokacin motar ta idasa tsayawa suka fita suka taka suka shiga cikin hotel ɗin.
*********************
Munir ne zaune a sabon office ɗin shi gaban shi takardu ne ko ta ina, dik da tsananin aikin da ya yi masa yawa be hana shi tunanin ta ba,a cikin sati biyu da dawowarsa daga Kano qawayen shi mata babu wadda bata san da zaman Saddeqa ba a cikin zuciyar shi.
A duk lolacin da ya yi yunqurin sanar da Ammin shi dan ta sanar da Alhaji Baban Gida Maganar Saddeqa sai ya kasa, ya rasa dalilin jin nauyin da yake ji a game da bayyana wa iyayen sa soyayyar shi,daga qarshe kawai sai ya sa a ran shi a dik sanda Alhajin ya bijiro masa da maganar aure to fa tabbas zai gabatar musu da Saddeqa a matsayin surukar su, murmushi ya yi mai sauti tare da danna saman biron dake hannun shi har sai da ya fidda sautin qara 'Qasss' sannan ya ja file ɗin gaban shi yace,
"Ya Allah ka mallaka min Beauty a matsayin matar da zata zamo uwar yara na,"
Da kanshi ya d'aga hannayen sa sama ya furta,
"Ameeen"
**********************
Cikin makarantar babu kowa dik ɗalibai sun tafi gidajen su dan cin abincin rana amma banda Saddeqa marainiyar Allah, ta na nan zaune cikin ajin su da ya bab'ure ta sama har rana ta samu nasarar hudowa ta haske cikin ajin ta yanda a dik sanda hakan ta faru d'aliban dake zaune a wajen za su dinga tashi suna neman mafaka.
Muryar ta ke tashi cikin suratul An'am tana rera karatun qur'ani cike da cikakken ilimin tajweed a ciki,qira'a mai daɗi take yi idanun ta rufe suke ta sanya qur'aninta ta rufe fiye da rabin fuskar ta,cike da natsuwa suke tafiya ana nuna masa dik ajujuwan da suka samu matsala suke da buqatar gyara shi kuwa ya na ta gyad'a kai gefe ɗaya kuma qanin shi Sultan na riqe da wani littafi da biro yana rubutu, tsayawa suka ga ya yi cak ba tare da ya ce musu komai ba, Sultan ne ya buɗe baki zai yi magana ya d'aga masa hannu alamar ya yi shiru, cike da natsuwa ya ci gaba da bin hanyar da yake jiyo muryar da ke ratsa zuciyar shi tana samun muhalli ta zauna, yana isa bakin qofar ajin nasu ya sanya qafar shi ta dama ya shiga, fuskar ta ya kalla wadda take fara tasss mai ɗauke da baqin gashin idanu da cikakkiyar gira mai yalwataccen gashi,ba tare da ya san sanda ya furta kalmar.
"Fatabarakallahu ahsanul khaleeqen,"
Ba ya fara takawa zuwa inda take,qamshin turaren shi da muryar shi mai amon sautin muryar cikakkun mazaje ne ta sanya Saddeqa buɗe kyawawan idanun ta ta sauke su akan fuskar shi mai ɗauke da dogon baqin gemu irin na ustazan asali.........
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
PAGE 24:
Bai ce mata komai ba sai da ta kai qarshen ayar da take karantowa ta yi shiru ta na kallon shi sannan yayi gyaran murya yace mata,
"Assalamu alaikum,"
Cikin muryar ta mai daɗin sauraro tace,
"Wa'alaikumussalam...Ina yini?"
"Lafiya qlou alhamdulillahi,me yasa baki tafi gida ba kike zaune ke ɗaya duk yara sun tafi gida cin abinci kafin a shiga islamiyya?"
Sunkuyar da kan ta qasa ta yi a hankali ta furta,
"Babu komai,ina so na yi hadda tane,"
"Hummm"
Juyawa ya yi zai bar ajin ya sake tsayawa ba tare da ya juyo ba yace,
"Yaya sunan ki?"
"Saddeqa shine suna na,"
Gyad'a kai ya yi kawai ya fita ya ci gaba da duba duk inda ke da buqatar gyara a makarantar, basu bar makarantar ba se da yara suka fara zuwa islamiyyah, suna fita ya bawa Sultan kuɗi ya siya wa Saddeqa abinci da lemo da ruwa ya haɗa mata da dubu biyu ya bata, taso taqi Karb'a sai kuma ta ga bata da dalilin qin Karb'a tinda ba da wata manufa ya bayar ba, godiya ta yi sosai ta Karb'a,ta fita daga ajin ta je bakin ajin su Sadeeq ta jira shi har saida ya dawo daga gida, tana kallon idanun shi ta gane yau ma ya yi kuka, murmushin takaici tayi tace,
"Na faɗa maka ka dena komawa cin abinci indai ka ga ban je ba, ta riga ta yi rantsuwa indai ban dafa ba baza ta bamu ba, ni kuma ba zan ajiye karatuna da na fara ba saboda na zauna na yi bautar da ina yi ana zagin uwata dake qasa ba,ka d'inga hakuri da girkin safen da nake yi mu ci wasu ma basu samun na safen,watarana sai labari,"
Cike da qunar rai take yi masa bayanin nan, shi kuwa kuka kawai yake yi saboda yunwa da baqin cikin abinda ke faruwa da su, gashi yau da yaje gida har baban su ya gani amma da ya gaishe shi ma tambayar shi ya yi wai waye? Yace Sadeeq ne, yace wanne Sadeeq ɗin? Kukan da ya ci qarfin sa ne ya hana shi amsa masa ganin haka Ɗan liti ya hau mamakin meye abun kuka daga tambaya ya shige gida ya bar Sadeeq na kuka a qofar gida.
Rungume shi Saddeqa ta yi tana bashi hakuri itama idanun ta fal hawaye, nuna masa abincin da aka bata tayi ta ce masa,
"Mu je mu ci abinci yunwa nake ji nima,"
Murna ce ta kama shi dan kuwa yana jin alamun ulcer ta kama shi saboda yawan zama da yunwa da yake yi, wanda Saddeqa ta jima da kamuwa da muguwar ulcer.
Waje suka samu suka ci abincin su sosai har da nama a ciki suka raba lemon suka sha ta bar masa ruwan gorar yana ta murna kafin ta ɗauki ɗari biyar ta bashi tace,
"Yau dai kaima ka samu ka ci wani abun da kake so da dare a kashe kwad'ayi,wani bawan Allah ne ya bani, sun zo duba ginin makarantar muka gaisa ya ce a kawo min,"
"Allah ya yi masa albarka ya sa ya fi haka mun gode sosai,"
Da fara'a sosai a fuskar Sadeeq suka rabu da yayar tashi dake ta zubawa bawan Allah'n da ko sunan shi bata sani ba addu'a akan sanya su farin ciki da ya yi, a haka ta koma ajin su ta tarar da d'alibai sun zazzo suna ta bitar haddar su kafin azo Karb'a.
************************
Har suka isa gida da qanin nashi be sake cewa komai ba, direct pampon gidan nasu ya nufa ya wanke hannayen shi da qafafun shi sannan ya wuce d'akin Innah Laminde, a saman kujera mai ɗaukan mutum biyu ya zauna ya miqe qafafun sa da kyau ya saki wata ajiyar zuciya,lumshe idanun shi yayi yana hango Kyakkyawan gashin idanun ta da ya kwanta samb'al ga girar ta mai cika da tsaho,yana hango lokacin da ta buɗe idanun ta a fuskar shi sai ya buɗe idon shi da sauri ya miqe zaune da kyau yana sauke ajiyar zuciya.
Innah Laminde ce ta shiga parlourn sanye da hijabi hannun ta riqe da carbi tace,
"Abdul har kun dawo kenan, da alama aikin ba yawa ko? Ai mai martaba ya shigo yana tambayar ina kake nace kaje duba makaranta ne amma kana nan dawowa yanzu, dan haka ya kamata kaje ka same shi yanzu yana can turakar shi,"
Miqewa yayi ba tare da yace komai ba yayi waje dan zuwa jin me yasa mahaifin shi ke neman shi bayan sun gaisa kafin ya fita, murmushi Innah Laminde tayi dan ta san har yanzu fushi yake yi da ita akan maganar da ta kawo masa daren jiya.
Sallama ya tsaya ya yi a bakin kofar shiga turakar mahaifin nashi, saida aka amsa aka yi masa izinin shiga sannan ya shiga bakin shi ɗauke da wata Sallamar, cikin sakin fuska mahaifin nasa da suke tsananin kamanni ya amsa sannan ya yi masa nuni da carpet ɗin dake gefen shi mai ɗauke da wani tuntu mai laushi irin na gidan sarautar nan, zama Abdul yayi ya tankwashe qafar shi ya sake gaishe da mahaifin shi kafin yace,
"Abbu barka da war haka,na dawo daga makarantar yaran can ne Ummah tace kana nema na shine nace bari na zo da wuri kar na sa ku jira,"
"Abdussaboor mahaifiyar ka ta yi gaskiya ina neman ka, ba komai ne yasa nake neman ka ba face ina so na ji ina muka tsaya akan maganar da muka yi da kai last week game da fitar da matar aure? Mahaifiyar ka ta kawo shawara akan had'in auren da take so ayi maku kai da Bilkisu amma na dakatar da maganar, nace kar ta yi maka maganar ma saboda bana son irin wannan auren had'in, nafi so ka zaɓi matar ka da kan ka saboda samun kwanciyar hankalin kan ka da d'orewar zaman lafiya a gidan auren ku,"
Sosa qeya ya ɗan yi kafin daga baya ya sake duqar da kan shi yace,
"Abbu na gode da bani wannan dama da ka yi,kuma alhamdulillahi an yi sara akan gab'a dan kuwa a yau na ga wata yarinya da na ji hankali na ya kwanta da ita a can makarantar da na kai ziyara sai dai ban yi mata magana ba,"
"Asshaa ! To in banda abinka Babana me yasa baka sanar da ita muradin ka ba nan take? Ai a bari ya huce shi ke kawo rabon wani ko? Kuma barin kashi a ciki ai baya maganin yunwa,"
Murmushi Abdussaboor yayi ya sake duqar da kan shi sannan yace,
"Maganar ka gaskiya ne ranka ya dad'e, zan yi wa Sultan magana ya bincika min a wanne gida take, dan kuwa na bashi aike ya kai mata na san ba zai rasa sanin ta ba tinda shi mazaunin gari ne,"
"Da kyau Babana, haka nake son mutum idan zai yi abun alkhairi to ya gaggauta yin shi kar a jinkirta, Allah ya sanya muku albarka da kai da sauran 'yan uwan ka,zaka iya tafiya,"
"Ameeen Abbu na gode, ammm Abbu,"
Cike da kulawa Sarki Ilyas ya d'aga kai ya kalli ɗan nashi yace,
"Na'am Babana akwai wata maganar ne?"
Sosa kai ya yi sannan yace,
"Eh toh ! Dama dan Allah ina neman alfarma wajen ka ne, ka sanar da Ummah na samu mata ta janye maganar yarinyar can bana son ta gaskiya, dan Allah Abbu ka goyi bayana, sannan ina so gobe na koma zamu yi wata tafiya ta gaggawa,zan bar maganar gyaran da za a yi a hannun Sultan,"
"Kar ka ji komai Babana fatan mu dai Allah ya zab'a maka abokiyar zama tagari kamar mahaifiyar ka, koma in ce wadda tafi ta,Allah ya yi maka albarka ya bada ladan abinda ake yi na d'awainiya,Allah ya sa afi haka,"
"Ameeen Abbuna na gode,"
Yana komawa d'akin Innah Laminde ta gan shi ya washe ya dena fushin da yake yi da ita, nan fa ta matsa sai ta ji me yake faruwa yaqi sanar da ita komai,cikin murmushi tace,
"Anya Uban masu gida ba wata qulalliyar kuka qulla ba kai da mahaifin ka tinda kun saba ware ni? Yanzu 'yar 'yar uwar tawa ce baka so? Yarinya me hankali wayayyiya tana son ka, kullum tazo se ta neme ka har lambar wayar ka ta Karb'a dan ta dinga gaishe ka fa,"
"Ta kira ni sau biyu na ga sunan ta ta true caller na qi ɗauka,tin daga nan bata sake kira na ba, kinga alamu sun nuna itama ba so na take yi ba kece dai kike ganin kamar sona take yi, kuma kike son ki haɗa ta aure da gudan jinin ki dan ki faranta musu, to farin ciki na fa Ummah?"
"Kai ma ina son farin cikin ka Baba, na dai so a yi tuwo na mai na ne,amma shikenan dik abinda yake alkhairi Allah ya nufa ya tabbatar,"
"Ameeen, kar ki ma damu ni nayi matar aure ma, idan na sake dawowa zan gabatar da kaina a wajen ta, yanzu tafiyar gaggawa ce ta taso mana saboda zamu shigo da wasu kaya da ake da buqata dan haka ina ga ba zan fi sati biyu zuwa uku ba zan dawo sai na gabatar da kaina wajen ta, kafin nan zan saka Sultan ya binciko min ko 'yar waye a garin nan,"
"Ikon Allah ! To Allah ya sanya albarka, shine kawai abinda zan iya cewa yanzu, amma fa a gaskiyar magana in har yarinyar nan Bilkisu ta nuna tana son ka dole zaka aure ta dan kuwa gida bata qoshi ba wa zai je yana kaiwa dawa?"
"Humm Allah ya zab'a mana abinda ya fi alkhairi, na kula dai kin fi son wannan yarinyar me ruwan fitsararru akaina,"
"A kul na kuma jin kana aibata min 'ya,"
Haka hirar Abdussaboor ta ci gaba da wakana tsakanin sa da mahaifiyar sa cike da shaquwa da kulawa.
Ko da dare yayi yaje kwanciya bacci ma haka ya dinga tunanin Saddeqa yana yi yana maimaita sunan ta a labb'an shi yana murmushi, a haka har bacci b'arawo ya sace shi.
Da sassafe kuwa ya yi shiri ya yi wa iyayen sa sallama ya shige motar shi mai bala'in kyau da tsada ya tafi ya bar Innah Laminde da kewa.
A ranar bayan tafiyar shi aka fara kawo qasa ana jibgewa da katak'waye da langa-langa da qusoshi, duk wani kayan aiki da za a buqata an
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 70