Mommy ta gano su ta tarwatsa abun a tashi ɗaya.
Ajiyar zuciya ya sauke ya wuce wani joint na shan iska,abinci yasa aka kawo masa ya hau ci kamar wanda ya yi kwanaki be ci ba,wata matashiyar budurwa ce tazo ta zauna a gefen table ɗin shi tana masa dariya,cikin ƙasa da muryar ta tace,
"Ran ka ya jima dan Allah ka rage saurin nan da kake yi, ka ga can ni da Ƴan'uwana ne ke zaune muna hango ka, sai dariya suke yi maka,ni kuma ban ji daɗin hakan ba, shine na ce bari nazo na faɗa maka ka ci a hankali akwai ƴan sa ido ba kai ɗaya bane a wajen."
Tin da ta fara magana Abdul ya kafe karamin bakin ta da ido yana kallo,baƙa ce kyakkyawa ajin farko,irin baƙin mutanen katsina mai kyau da ɗaukar hankali,daga jin hausar ta ya gane ba bakanuwa bace,da ƙyar ya rufe bakin shi ya gyara zaman shi ya kalle ta yace,
"Na gode sosai,inshaa Allahu zan gyara,kin san idan mutum ya fito daga ƙwadago yunwa ta cinye masa ciki sai a hankali,"
Murmushi tayi ta miƙe za ta bar wajen ya yi saurin cewa,
"Ammm baiwar Allah nace ba."
Juyawa tayi ta kalle shi tace,
"Na'am?"
"Nace dan Allah ko zan iya samun No wayar kyakkyawar?"
Babu ɓata lokaci ta karanto masa lambar wayar ta ya saka, har zata tafi ya ce,
"Da wanne suna zan yi saving?"
"Huzaimah"
"Masha Allah,what a nice name you have dear,ammm nace ba tsaya in kira kiyi saving tawa, dan ban gama yarda da no gaske kika bani ba, na san halin ƴan matan yanzu idan basu son ka basu bada No mai kyau"
Dariya tayi sannan tace,
"To gwada ka gani mana."
Kiran No yayi sai ya ga wayar ta na ringing, murmushi suka yi a tare yace,
"Ki saka Abdussaboor a sunan."
Daga haka ya koma mazaunin shi ya ƙarasa cin abicin shi,ba jimawa ya ga ƴan matan sun bar wajen zaman nasu sun shiga wata mota sun bar wajen gaba ɗaya,shima be wani jima ba ya tashi ya shiga tashi motar,yawo ya dinga yi a gari dan baya son komawa gida ya tadda mommy da masifar ta.
Da misalin sha ɗaya na dare ya kira No Huzaimah,babu jimawa ta ɗauka da alamar bacci ta fara ma,bayan yayi mata sallama sun gaisa ne,ya tambaye ta ko tana da tsayayyen mijin aure? Cikin dariya tace,
"Haba malam, daga haɗuwa d'azu zai zancen aure? Ni fa baƙuwa ce gidan yayata nazo hutu daga katsina, jibi ma zamu koma gida."
"Da dikkan alama Allah ya nufe ki da zuwa Kano ne dan ki samu mijin aure shi yasa ya haɗa mu Huzaimah................."
[09/08, 10:39 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 84:
Motsi Abdussabour ya ji a bakin ƙofar ɗakin shi ya yi saurin kashe wayar ya ajiye a gefen shi,Mommy ce ta buɗe ƙofar ta shiga sanye da kayan bacci mai kyau riga da wando,kanta babu hula sai sheƙi yake yi alamar ya sha gyara,cikin zuciyar ta baƙiƙƙirin take jin shi saboda baƙin cikin abinda Abdul ɗin ya yi, amma hakan bai hana ta shanye damuwar ta ba dan ta faranta masa,Amir ta ajiye a ƙaramin gadon shi dake ɗakin ta wuce zata hau gado ta kwanta,a hankali Abdul yace mata,
"Ya zaki ajiye yaro baki yi masa addu'a ba? Kullum idan kika ajiye shi sai na yi maki magana akan yi masa addu'a sai kice wai kin yi masa,a gaskiya bana son irin abinda kike yi Hadiza."
Idanun Mommy ne suka tara k'wallar baƙin ciki,amma sai ta shanye ta koma ta tsaya a saman kan yaron ta yi a'u'ziyyah kawai ta tofa masa zata koma saman gado da niyyar kwantawa,tsaki Abdul ya ɗan ja kafin ya tashi ya ɗauki yaron ya rungume shi a ƙirjin shi,sai da ya karanta ayatul kursiyyu,sannan ya yi falaƙi,nasi da iklas zuwa amanarrasulu ya shafawa yaron sannan ya ajiye shi ya koma ya kwanta, shi kanshi bai kwanta bacci ba sai da ya yi wa kan shi addu'a ya shafa sannan ya juya mata baya,dik abinnan da yake yi da ido kawai mommy ke bin shi, sai da ya natsu har bacci ya fara ɗaukan shi sannan ta tada shi,yana farkawa sai ta fashe da matsanancin kuka,dik yanda Abdul yaso ya kyale ta ta ci kukan ta ta gama tai bacci kasawa ya yi,a hankali ya dafe kan shi ya rintse idanun shi,cikin sassanyar murya ya ce,
"Ya isa haka kukan, matso ki faɗa min me kike so ayi yanzu."
Babu kunya babu tsoron Allah Mommy ta hau share hawaye tana jan majina ta ja jiki ta kwanta a saman cinyar Abdul tana ci gaba da matsar ƙwalla,cike da shagwab'a ta mirgina ta yanda za su dinga kallon junan su sannan ta ce,
"Ni dai so nake ka jaddada min alƙawarin da ka yi min,Abdul ka sani ina son ka bana son kishiya,dan Allah kayi min alƙawarin ba zaka yi mini kishiya ba."
Janta ya sake yi jikin shi ya sumbace ta a goshin ta sannan ya ce,
"Baby baki ga alƙawarin dana yi maki na farko ma na kasa sauke shi ba ballantana na sake yi maki wani? ki yi tunani da kyau mana, ta yaya lafiyayyen namiji kama ta zan iya zama da mace ɗaya? Idan kina period da ƙyar nake iya bari ki kammala,kafin ki gama dik inda hankalina yake ya gama tashi, bani da natsuwa bani da sukuni,yanzu kin haihu jinin nan kafin ya tsaya sai da kika yi sati biyu currr,a haka ma an ce kin yi sauri,to ki faɗa min haka zan ƙare rayuwa ta zuciya ta na hango min wasu matan bayan Allah ya hore min arziƙin da zan iya ƙara aure? Sannan ina da gidan da zan iya saka matar dik da na aura saboda ko gidan nan zai iya ɗaukan mata biyu,dan haka ki yi haƙuri ki taimaka min na kare kaina daga aikata zina,na yi kafin aure na, na kuma yi bayan aure dan Allah kar ki jawo ya zamo ɗabi'a a gare ni."
"Ai kuwa in dai ni Hadiza Ɗan Liti ina raye babu kai babu wata mace a duniya Abdul ! dik wannan bayanin da ka zuba ba shiga ta ya yi ba,kai na na sani,kai nawa ne, ka aure ni,kana so na nima ina son ka,babu wata ƴar iska ƴar karuwa jinin karuwan da za ta raɓe ka ban sabauta ta na illata ta ba,Abdul ko a aure ko a zina ni kaɗai ce matar ka,kai yanzu baka ji kunya ba dan Allah? Ko dake ba abun kunya bane bama wannan, sai dai nace baka da godiyar Allah,a rana sai ka neme ni sama da biyu,yaushe na taɓa hana ka? Idan ina period bana barin ka haka,ni na san dabarun da nake yi maka har ka samu gamsuwa,to me kake nema wanda bana yi maka?"
"Ke Hadiza na gaji da yin abu ɗaya da ke ke kaɗai ne shikenan? Ina ta yi maki kara ina boyewa bana so na faɗa maki kiji babu daɗi amma kina matsa min dole sai na bayyana maki abinda zai dame ki,ba fa ke ɗaya Allah ya halatta min ba,Allah ya halatta min zama da mata huɗu ne,dan haka ke baki isa ki hana ni ƙara aure ba, idan kika ga ban ƙara aure ba sai dai idan Allah ne bai nufa ba,haba! Ayi mace sai masifa da bala'i,to akan ki zasu ƙare."
Masifa Mommy ta dinga zazzagawa, ta inda take shiga ba ta nan take fita ba,ƙarshe sai ta fashe da kuka kamar wadda ake duka,ganin abun nata ba na ƙare bane sai kawai ya ɗauki pillow da wayar shi zai bar ɗakin,ƙofa ta tare ta hau jijjiga jiki tana ci gaba da kuka tana kiran Allah ya saka mata akan abubuwan da yake yi mata,tsabar ma mamakin da ta bashi kawai sai ya fashe da dariyar takaici,tin yana dariyar takaici har dariyar gaske ta maye gurbin haushin dake cikin zuciyar shi,kallon yanda take ta zumɓura baki ya yi,sai ya ajiye pillow da wayar shi ya ɗauke ta gaba ɗayan ta ya wurga ta a gado,kamar wadda take jira kuwa sai ta zira hannu ta kashe fitilar ɗakin ganin duhu ya mamaye wajen ne ya sanya ni haska waya ta na buɗe ɗakin na bawa masoyan waje.
Da safe haka suka tashi kamar basu ne suka yi rikici da masifa da bala'i ba da dare,Abdul sai wani nan nan yake yi da Mommy ita kuwa tana masa shagwab'a,hatta da wanka da shafa mai shi ya yi mata.
Dik yanda Aunty Naja taso ta baiwa Mommy hakuri su bari ta yi arba'in kafin su je wajen boka ƙin yarda tayi, ganin ta ƙi yarda ne yasa ta ce mata,
"Ke yanzu a wannan halin da ake ciki ina kika ga na yin tafiya? Ai bari zaki yi sai kin jiƙa shi da ruwan ƙaunar ki kafin nan kafin kiyi arba'in,ta yanda ko kwana ɗaya kika yi baki nan zai gigice ya yi kewar ki,ta haka ne zai gane kowacce mace zai nema in dai bake ba to fa ba wata gamsuwa da zai samu,sannan shi wannan aikin da za a yi maki da nayiwa boka bayani yace za a ɗauki kwana uku ana yi,kin ga a yanzu kina tafiya kika yi kwana uku baki nan sai dai ki dawo ki ga ya yi maki abinda baki so,tinda na kula a shirye yake ya yi auren nan ko kina so ko baki so."
Shiru Mommy tayi tana nazari kafin tace,
"Maganar ki gaskiya ne Aunty Naja,zan yi haƙuri har nayi arba'in,inshaa Allahu dik sanda naje gida sai an yi min zazzafan aikin da zai cire masa ra'ayin kowacce mace a rayuwar shi."
"Yauwaa ta waje na ko ke fa? Allah ya kaimu lokacin da rai da lafiya."
Tinda su Mommy suka yi wannan tattaunawar sai ta samu natsuwar zuciya, gaba ɗaya ta maida hankalin ta akan kula da mijin ta da yaron ta,ita ce shan magugunan mata ita ce gyaran jiki da dik wani abu da ta san zai riƙe mata Abdul gam a hannu.
A gefe ɗaya kuwa Abdul na yaba mata matuƙa akan ƙoƙarin da take yi akan shi,shi yasa yake sakar mata kuɗi take yin yanda take so,amma hakan bai hana shi ci gaba da soyayya da Huzaimah ba,dan kuwa har Katsina sun je wajen ta shi da Bilal sau biyu,Bilal ya yaba da tarbiyya da kamun kan yarinyar dan haka sai ya dinga baiwa Abdul goyon baya akan ya aure ta kawai,idan yaso ko can garin Ba Mugu sai ya ajiye ta dik ƙarshen sati ya dinga zuwa wajen ta, tinda yarinyar da iyayen ta suna da fahimta,zuwan su na farko sai da ta ce ya gaishe da Yayar ta da ɗan ta tinda ya sanar da ita yana da mata da yaro ɗaya, hakan da ta yi ba ƙaramin farin ciki ya dasa wa Abdul a ran shi ba,sanda suka koma kuwa har rigar yara da atampa da turare ta bashi tace ya kai wa Yayar ta da ɗan ta.
Abdul kuwa da ya dawo sai ya kaiwa Mommy ya yi gum da bakin shi bai faɗi daga inda kaya suka fito ba, Mommy kuwa da ya bata kayan sai ta dinga murna tana godiya dan kuwa kaya ne masu kyau da tsada,da dare da ta yi wa Amir wanka sai ta sanya masa riga guda ɗaya a cikin kayan da Huzaimah ta bayar a kawo,tinda Abdul yaga kayan a jikin yaron ya hau ɗaukan shi a hoto yana murmushi, Mommy na fita ya tura wa Huzaimah hoton Amir yana godiya sannan yace ɗanta da Yayar ta dik suna godiya da kyautar da ta aika musu dashi.
Haka soyayyar Huzaimah da Abdussaboor ta ci gaba da gudana cikin sirri ba tare da Mommy ta san da zancen ba, har dai wata rana Abdul ya samu dama yaje ƙauye ya sanar da su Innah Laminde maganar ƙarin auren shi,Innah ta yi farin ciki da maganar sosai sannan ta sanya albarka ta kuma bashi goyon baya ɗari bisa ɗari,Sarki ma ya sanya albarka sannan ya yi masa nasiha sosai akan zama da mace sama da ɗaya, da yanda zai gudanar da adalci a tsakanin su.
Iyayen Huzaimah sun amince zata zauna a ƙauyen Ba mugu tinda ya nuna mata gidan a waya,ta ga haɗuwa da tsaruwar shi,dan haka ko da aka je tambaya Abdul da Uncles ɗin shi biyu da waziri sai suka bada har da sadaki sannan suka roƙi kada bikin ya wuce sati biyu,iyayen Huzaimah dake ba ƙananan mutane bane,suna so ƴar su tayi aure da mutum na gari sai suka amince da hakan, already dama suna nan suna ta ƴan siye-siye da ba a rasa iyayen da ke da budurwa yi ba,musamman abinda ya ƙunshi kayan kitchen da abubuwan da ba a rasa ba.
Nan da nan maganar auren Huzaimah ya yaɗu a dangin su da dangin Abdussaboor,dik abinnan da ake yi ko da suɓutar baki Abdul bai taɓa sanar da Mommy zai yi aure ba.
***************
Wataranar laraba Shamsu na zaune a parlour riƙe da kunu zai sha maganin ciwon kai,saboda yanda yake jin kan shi na tsananin sara masa saboda damuwar da yake ciki,Ameerah kuwa na zaune da yaron ta tana bashi abincin shi tana sheƙa dariya kamar mahaukaciya sabon kamu,cikin dariya tace,
"Sannu Shamsi na Allah ya baka lafiyar zuciya da jiki,gaskiya wannan bazawara bata kyauta ba,Allah ya kiyaye gaba idan kwaɗayi be sake janka ba,nan gaba a dinga gina soyayya domin Allah ba dan son zuciya ba."
Ƙwafa shamsu ya yi sannan ya ce,
"Ke har kin isa ki yi wa wani wa'azin yin abu domin Allah? Ita kuma da ta guje ni saboda wani dama can ƴar iska ce,Allah ne ya cece ni ba zan sake auro mugun iri ba shi yasa ya kai ni shagon na ga komai da ido na."
"Oho muku can ta matse muku, ni yanzu na dena damun kai na akan ka Shamsu,tinda baka ɗauke ni da mahimmanci ba ni ma ba zan kahye kai na akan ka ba,daga yau idan kaso ka yi soyayya da mata sama da dubu ma ruwan ka,sannan mugun iri ai ba a mugun iri ɗaya sai biyu."
"Dama na jima da sanin ba ƙauna ta kike yi ba ai."
"Ka ji da shi wai ciwon ajali a ɗan yatsa,idan na yi kishin ka kace min mahaukaciya,idan na ƙyale ka kace bana son ka,ni dai kawai abinda na sani shine na dena damun kai na akan ka, na riga na san ko mace aka baka sadaka sai dai ka kalla kace baka so,tinda baka da wajen aje hatsi ma balle mata biyu."
Suna nan suna ciwa juna mutunci Azizah ta yi sallama ta shiga gidan,Ta Annabi da Fadilah ne suka amsa mata,har ƙasa ta kai tana gaishe da Innar ta ta kafin su tafa da Fadilah su gaisa,zama tayi ta ajiye babbar ledar da ta shiga gidan da ita a gaban Innah Laminde sannan ta ce,
"Innah ce ta aiko ni tace na kawo maki goron saka ranar Yah Abdul,sannan tace na sanar dake nan da sati biyu masu zuwa za a ɗaura auren,ganin nisan waje ne ya sanya Kawu Sidi da waziri suka yanke shawarar kawai a saka rana baki ɗaya."
Gud'a Ta Annabi ta sanya sannan ta yi shewa ta ce,
"Alhamdulillahi Allah na gode maka da ka nuna min Sarauta zai ƙara aure,wancan lokacin gaba ɗaya bana cikin natsuwa ta akai hidimar bikin sa, wannan karon kuwa inshaa Allahu dani za a yi komai cikin daɗin rai."
Ameerah uwar son jin gulma kuwa fitowa tayi saɓe da yaro a kafad'a,riga da skirt ne a jikin ta sun zauna cif a jikinta,tinda ta dawo gidan ta jego ya karɓe ta saboda Ta Annabi na matuƙar ƙoƙari wajen kula da ita da jaririn ta,cikin washe baki ta duƙa ta ɗauki chewing gum ta hau ɓarewa ta jefa a baki sannan ta zauna a saman turmin dake tsakar gidan, Fadilah ce cike da tsokana tace,
"Babbar yaya wato kema murna kike za a yi wa Ƴar'uwar ki abokiyar zama ko? Shine har da ɗaukan cingam ki watsa a baki tin kafin a yi maki tayi."
Cikin rashin fahimta Ameerah ta dakata da taunar Chewing gum ta kalli Fadilah,sannan ta maida kallon ta kan Ta Annabi da ta rage fara'a,Azizah ce ta miƙe tsaye ta ce musu,
"Ni bari na koma gida, dama rabon goro nake yi kar a ga na jima."
"To ki gaida Yayah ki ce nace Allah ya sanya alkhairi,ga wannan tukuicin albishir ne,Allah ya kaimu lokacin da rai da lafiya."
Da ƙyar Azizah ta karb'i dubu dayan ta yi musu sallama ta wuce gida,hararar Fadilah Ameerah tayi sannan ta ɗauki biscuit ta fara buɗewa kafin ta ce,
"Ƴar rainin hankali har kin faɗar min da gaba ɗazu,ashe auren Azizah ne ya taso, to Allah ya sanya albarka ya nuna mana lokacin da rai da lafiya,Innah ni dai a raba a bani nawa dan Allah na tafi wajen majinyaci na."
Da jin haka Fadilah ta manta da tsokanar da zata yi ta ce,
"Me ya samu Yayan naji kin kirashi da majinyaci?"
Dariya Ameerah ta fashe da ita kafin tace,
"Ai ke baki sani ba Fadilah, yayan ki amana ta yake ci da wata bazawara,soyayya tayi zafi sosai na ɗaga hankali na na dinga yi masa magiya da rashin mutunci akan ya dena ya ƙi,ashe dai yarinya ƴar hannu ce,ina sabon mai turin nan da ya buɗe shago a kasuwa? To yanzu can take zuwa a tura mata kallon soyayya sannan a yi mata soyayya a zahiri a nan cikin shagon,shine ɗazu wani ya kawowa yayan ki rahoto ya tafi yaje ya gane wa idanun sa har aka ɗan baiwa hammata iska a wajan,da alama malam Shamsu bayan cin amanar shi da bazawarar shi tayi ya sha duka shine yake kwance yana jinya tin ɗazu"
Dariya sosai Ameerah ta fashe da ita a ƙarshen labarin ta, ita kuwa Ta Annabi da ta gane inda zancen ya dosa sai ta tattare tarkacen ta tawuce ɗaki ta bar su Ameerah da Fadila na tattaunawa game da mayaudariyar budurwar shamsu.
****************
A can Australia kuwa Billy ta rasa hanyar da zata kub'utar da kanta daga wajen Any,duk wata dabara da salo da take tunanin zata yi dan kuɓutar da kan ta abun ya gagare ta, kuɗi dai gasu nan dik sati samun su take yi masu tsananin yawa,gefe ɗaya kuma Any har takan tuna mata tace ta tura wa iyayen ta wani abu mana,ta haka ne za su san tana cikin ƙoshin lafiya,ko Billy ta ƙi turawa Any zata tura musu ta kuma yi amfani da wayar Billy ta yi wa Shamsu ko Baban Billyn message tace ta tura masu kuɗi ne dan ayi hidimar gida.
Gaba ɗaya Billy ta rame sosai saboda damuwa,a hankali ta fara wani irin zazzaɓi mai zafi,Any ta danganta hakan da yawan damuwar da ta sanya wa ranta ne da kuma yawan aikin da suke yi kwana biyu a kamfanin su na fina-finan porn,amma dik da haka sai ta yi mata alƙawarin kai ta asibiti dan ta ga likita,kafin satin da Any tayi alƙawarin kai Billy asibiti ya zagayo Billy ta fara yin wasu ƙuraje a bakin ta masu zafi ta ciki da wajen leɓen ta,dan haka cikin sauri Any ta ɗauke ta suka wuce asibiti,ko da suka je aka yi wa Billy gwaje-gwaje sai aka gano ta kamu da ciwon nan da ake ɗauka ta hanyar yin oral sex wato syphilis, hankalin Any ba karamin tashi ya yi ba,Billy kuwa da ta ga tashin hankalin da Any ke ciki sai ya gigita ta ta hau kuka tana faɗin,
"Shikenan na san ma mutuwa zan yi,na shiga uku ni Bilkisu na bi son zuciya na halaka rayuwa ta da kai na,dan Allah k taimake ni ki maida ni Nigeria bana so na mutu ban ga iyaye na ba."
Hawaye Any ta share kafin ta rungume Billy,cikin taushin murya ta kalli likita ta roƙe ta akan ta basu maganin da zai warkar da ciwon cikin sauri.
Har aka gama basu magani da dik abida ya dace Billy bata dena kuka ba,a haka suka koma gida Billy na sanye da face mask,wunin ranar gaba ɗaya a kwance ta yi shi,Any kuwa sai hidimta wa Billy take yi,fatan ta kawai Allah ya sa ta dage da shan Antibiotics ɗin da aka bata ta warke da wuri.
Yanda Any taga Billy ta rame a kwana biyu ga ciwon na ƙara yaɗuwa sai ya firgita Any,dan haka a cikin satin ta hau nema masu visa dan su koma gida Nigeria,idan ta kama ta ci gaba da jinyar Billy har ta warke ne sannan su dawo sai ta yi,idan kuwa taga abun bana ƙare bane sai ta lallaɓa ta barta a Nigeria ta gudu,ko babu komai ta mori Billy fiye da yanda ta mori sauran matan da ta yi tarayya da su.
*************************
Bikin Abdul da Huzaimah na ta matsowa amarya da ango tare da dangi da iyayen su suna ta shiri uwar gida bata san ana yi ba,ranar da za a kai lefe ta zagayo wanda ya yi dai-dai da sauran sati ɗaya ɗaurin auren Abdul da Huzaimah.
Ta Annabi na cikin wanda za su tafi katsina kai lefe,dan haka tin tafiyar saura kwana ɗaya ta fara shirin tafiya katsina,washegari da sassafe motar da Sultan zai kai su Katsina ta tsaya a ƙofar gida ta na danna wa Ta Annabi oda akan ta fito su tafi,a shirye ta fito tsaf cikin shiri sanye da kaya na alfarma,a ƙofar ɗakin Ameerah ta tsaya ta na ƙarasa sanya ɗan kunnen ta na zinare da ta siya babu jimawa cikin irin kuɗaɗen da Billy ke aika masu,Ameerah ce ta fito tana hamma da miƙa tace,
"Innah ina zaki je na gan ki cikin shiri haka da sassafe?"
"Ah ah ! Wai har kin manta alawa da biskit ɗin da Azizah ta kawo na saka ranar auren Abdussaboor? Ai yau zamu je kai lefe ma ni da Yaya Ta Zariya da Goggon shi Marka,ga ruwan wanka nan na mayar maku yau ki ƙoƙarta ki yi wa yaron nan wanka da kan ki,kunun gyaɗar ki na nan na dama a kula da gida sai na dawo "
A sheƙe Ameerah ke bin Ta Annabi da kallo kafin ta ɗura wani hanshaƙin ashar tace,
"Wai kina nufin Yah Abdul ɗin Yah Mommy ne zai ƙara aure shine bamu sani ba saboda baƙin cin amana da rashin mutunci?"
Da jin ashar ɗin da Ameerah ta saki Shamsu ya fito, ita kuwa Ta Annabi gaba tayi dan ta tsammaci abinda ya fi haka ma a wajen zuri'ar gidan Ɗan liti, Shamsi ne yace,
"Ke Ameerah wa kike zabgawa wannan ashar ɗin?"
A hasale tace,
"Da kafatanin zuri'ar maciya amana nake Shamsi idan zuri'ar ku na ciki ban ware ta ba,matsa ka bani waje."
Wani irin tsoron Ameerah ne ya kama Shamsi,dan kuwa sai yaga ta juye ta koma masa wata iriyar kumurcin maciji,cike da ɓacin rai ta hau dube-dube,can jikin soket ta hango wayar ta tana caji,a zabure ta nufi wayar ta ɗauka ta hau latsa lambobin Mommy,dan tsayawa searching a wajen ta ɓata lokaci ne...............
[09/08, 10:39 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 85:
Mommy na ɗaukar wayar ta ji muryar Ameerah a sama kamar tana magana da mutanen da ke nesa,zare wayar tayi daga kunnen ta ta sanya ta a handsfree sannan ta riƙe a hannunta ta ce,
"Ameerah ke da wa kike wannan maganganun da bana gane komai a cikin su? Dan Allah ki natsu ki yi min magana ta yanda zan fahimce ki."
'Ni da wannan zuri'ar masu cin amanar nake mana,ki na nan ki kwana da miji ki tashi da shi zai yi aure amma baki sani ba,ahhh baki sani ba mana,tinda na tabbata da kin sani da yanzu hankalin kowa a tashe yake.'
Wani ashar Mommy ta saki sannan ta dangwara Amir a cinyar Aunty Naja ta miƙe tsaye tana bin ta da wani mugun kallo kamar itace Abdussaboor ɗin,cikin wata iriyar murya Mommy ta ce,
"Ki ka ce me? Waye zai yi aure Ameerah? Kar ki sake kiyi min ƙarya saboda gudun aikata aikin dana sani."
'Mijin ki Abdussabour Abdulkarim Yariman Sarkin Garin Ba Mugu shine zai yi maki kishiya Hadiza Ɗan Liti.'
Ameerah ta faɗa tana wata iriyar jijjiga kamar ita za a yi wa kishiyar,Shamsu mamakin halin da Ameerah ta shiga yake yi,su kenan zuri'ar su ba za a yi masu kishiya ta daɗin rai ba sai hankalin kowa ya tashi? Haka fa ta dinga yi masa tijara da rashin mutunci akan budurwar da ya yi,yanzu kuma sai wani
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 53 Chapter of 70