nan ko kuma....."
"Ni babu wani kallo da nake yi maka na musamman haka kallo na yake,Yah Munir to ka mayar musu da kayan su d'akin su mana bai kamata a bar mata a waje ba gaskiya,"
"Ni ba bawan gidan su bane,"
Bata sake kula shi ba dan ta san ba yi zai yi ba tinda ya nuna bayi zai yi ba ɗin, dan haka da kan ta ta kwashe kayan Mommy dika ta mayar d'akin su na 'yammata ta ja ƙofar, suna nan tsaye suna hira sama-sama Ɗan liti ya dawo, tin daga waje suka jiyo ƙarar adaidaita sahun shi wanda ya sanya gaban Saddiqa faɗuwa sosai, Baabaa ce ta fito daga ɗakin ta ɗauke da jakar kayan ta a hannu ta tsaya tana rufe ɗakin tare da tambayar Munir ya saka kwaɗo a ƙofar Yadikon ko?
"Eh na saka na rufe ga makullin ma nan,"
"To da kyau mu je ko akwai abinda baku gama ba kuma?"
"Ah ah mun gama komai ke muke jira,"
Baabaa na ganin Ɗan liti amma tayi banza dashi zata wuce shi, cikin sauri ya tsaida ita yana bata hakuri, kallon shi tayi a sheƙe sannan tace,
"Ɗanli ai haƙuri kai ya gani kuma kai ya kama, tinda dai kai ka zama shanyayye to mu munyi nan,Allah ya sada mu da alkhairi, uhumm dangane da maganar Sadeequ kuma zai bi su Baban Gida can Habuja idan za su tafi gobe, amma dai nace dole a sanar dakai dan kai ne uban sa, idan ka amince tom,in baka amince ba shikenan ya bar maka ɗan ka a ƙarasa lalata rayuwar shi da rashin zuwa makaranta,"
Cikin zuciyar Ɗan liti zai so ace ya bar ɗan nashi an tafi dashi dan inganta rayuwar shi, amma bai san me ya ja ra'ayin shi har yace,
"Ah ah babu inda Sadeeq zai je, a bar min shi anan ina ganin shi ina jin daɗi, ni dai ina sake bada haƙuri akan..."
"Ai magana kuma ta ƙare kuma Ɗanli, Sadeequ zai zauna anan garin, amma ba zai dawo gidan nan ba sai sanda na dawo nima,Allah ya ganar da kai, gaskiya"
Yana kallon sanda Baabaa da Munir suka bar gidan ɗauke da kaya a hannun su,Saddiqa kuma na tsaye ta kasa gaba ta kasa baya kamar mai neman izinin shi, cike da zubar hawaye ta durqusa a gaban shi tace,
"Baba ka yafe min dik abinda nayi maka da wanda nake yi maka yake ɓata maka rai har ka daina nuna kulawar ka a kai na ni da Sadeeq, Baba bamu da kowa yanzu sai kai Yadiko ta rasu, me yasa kake jin haushin mu a koda yaushe kake kyarar mu?"
Shiru Ɗanliti yayi dan bai san amsar da zai bata ba, kallon ta kawai yake yi idanun shi sun kad'a sun yi jawur kamar gauta,shirun da ta ji yayi yawa ne ya sanya ta cewa,
"Baba ka sanya min albarka, sannan kayi min addu'a zan zama jarabawa ta ta qarshe kwanan nan,"
Kallon ta yayi ya d'aga hannu kamar zai dafa kan ta, wani irin zafi yaji kamar zai manna hannun shi a wuta,dan haka cikin sauri ya janye hannun shi yace mata,
"Allah ya sanya wa rayuwar ku albarka ya bada sakamako mai kyau,"
Yana gama faɗin haka ya shige d'akin Innoh dake lab'e a jikin window tana ganin duk abinda ke faruwa a tsakar gidan nasu.
Da kuka Saddiqa ta isa mota ta buɗe gefen da Munir ke zaune yana jiran ta ta zauna, Baabaa bata ce komai ba dan kuwa ita kanta zuciyar ta na ƙuna akan halin da yaran ke ciki a gidan uban su, sai dai ta sani dik daren dad'ewa asirin Innoh sai ya tonu,wannan rayuwar da yaran ke ciki ba zata dore ba.
************************
A can kasuwa kuwa a gaban idon Shamsu aka gama gyara wa Ameerah da Mommy kai har aka fara yi musu ƙunshi ja da baƙi, wani shago ya tafi da sauri ya siyo lemo mai sanyi da pure water ya kawo wa Ameerah ya buɗe ya miƙa mata yana faɗin,
"Karɓi ki sha gimbiyar mata na san ana zafi,"
Cike da jin takaicin Shamsu ta Karb'a tace,
"To ɗan anace na Karb'a ai sai ka koma waje ko?"
Dariya mommy tayi da ta tina sanda suka fito daga gida ya tare su yace sai ya raka su, sun sha artabu sosai kafin Ameerah ta kyale shi ta bar shi ya biyo su, cikin dariya Mommy tace,
"Amma dai Shamsu baka da kirki babu kuma amana, Ameerah ce kaɗai anan da zaka siyo wa matar ka lemo ni ka barni cikin ƙishi? Babu komai ke zo nan karb'i wannan ki siyo wa dik wanda ke cikin shagon nan lemo ɗaya da ruwa da cincin,"
Yarinyar shagon ce ta isa gaban Mommy tana washe baki ta karb'i kuɗin hannun Mommy ta tafi siyo lemo, shamsu kuwa ko kula ta bai yi ba yana gefen Ameerah yana zuba mata surutun yanda aka gyara sashen da zata zauna, wato tsohon ɗakin shi da tin asali yake a killace da langa-langa a cikin gidan nasu, wani irin haushin shi ne ya kama ta taji kamar ta shaqe shi wataqila ta huta da baƙin cikin shi.
Haka su Mommy suka zauna har bayan magariba sannan aka gama yi musu dik wani gyara da suke da buƙata, ana gamawa ta ɗauki hoton ƙunshin ta turawa Abdussabour dake ta zabga mata waya, yana gani kuwa hankalin shi ya kwanta, dan kuwa da har ya sanar da Bilal su shirya ya raka shi wajen Mommy, Bilal yace ba zai je ba, cikin ɓacin rai Abdul yace shi zashi ganin matar shi kar ya raka shi ɗin,ya kula kamar adawa yake yi da auren shi ma.
Bayan Mommy da Ameerah sun koma gida ne suka tarar da Naja da wasu 'yan uwan Innoh suna zaune ana hira ana cin shinkafa dafa dika, suna ganin su Mommy suka b'arke da gud'a da shewa tare da faɗin,
"Ga amare ! Ga amaren nan sun dawo,"
Naja ce ta ja su d'akin su na 'yammata ta ɗakko wani tsumi na kayan mata tace wa Mommy,
"Ga wannan,na musamman na karb'o shi gidan boka, idan kuka sha wannan mallaka ce ta har abada, mazan ku babu su babu maganar ƙarin aure,"
Cike da murna Mommy ta rungume Naja tace,
"Kaiii Aunty Naja Allah ya biya ki, kin ga bamu dawo ba tinda aka gama yi mana qunshi sai da na biya na siyo maganin nan na mata, ashe kina nan kina yi mana tanadi na musamman,Allah Allah ka sa maganin nan yaci,bana son kishiya, bana ƙaunar kishiya, Allah ka nesanta ni da ita har abada,"
Ameerah kuwa taɓe baki tayi ta wuce su ta kwanta a katifa dan ta huta,kallon ta Naja tayi tace,
"Ke baza ki tashi ki sha bane? Maganin mallaka ne fa,"
Cike da fushi fa masifa Ameerah ta hayyaqo wa Naja tace,
"Nabi mallakar da gudu babu wando, yau na ji maganar banza, ai kun san wanda nake son na mallake amma baku yi hakan ba, sai yanzu dan na auri lusarin miji kamar wannan shine zaku dame ni da wani maganin mallaka?"
Juyawa tayi ta kwanta tana matse k'wallar baqin ciki,Mommy kuwa zama tayi ta kwankwad'e maganin nan duka, ta haɗa da wanda ta siyo dika ta shanye,sai da ta gama ne ta kula da an dawo mata da akwatin ta da katifar ta d'akin su na 'yammata, taso tayi Maganar ta basar dan kuwa ta sani yau ba a gidan zata kwana ba,to menene na damuwa? Wanka ta fita yi domin ta shirya kanta da kanta dan bata ga alamar 'yan gayun da za su yi mata kwalliyar arziqi ba a wajen ballantana a yi mata shiri mai kyau.
***************************
Gidan sarki ya cika maqil ana ta hidimar biki da ware masu ɗakko amarya, dik da cewa a qurarren lokaci bikin yazo hakan bai hana mutane zuwa taya babban ɗan sarkin murna ba,gidan amarya an gyara shi ya haɗu ya gaji da haɗuwa dan kuwa a kaff ƙauyen ba lallai a samu kamar shi ba, Abdussabour ya yi wanka cikin wata babbar shadda fara k'wal ta sha aiki daga sama har qasa, an yi masa rawani mai bala'in kyau da ash colour rawani kalar aikin jikin kayan shi, wani ash colour ɗin takalmi ne a ƙafar shi irin na sarakai an yi masa ado da farin zare,banda tashin qamshi babu abinda Abdussabour ke yi, dik inda ya gilma kuwa sai taya shi murna ake yi shi kuwa yana wage baki yana amsawa cikin farin ciki .
A cikin gida kuwa Innah Laminde sai yaqe take yi dan kuwa rashin ganin qanwar ta ta a bikin Abdussaboor ba qaramin damun ta yayi ba,ita kanta ba wani son auren nan take yi ba dan dai ya zamana bata da yanda zata yi ne, da baza ta bari Abdul ya auri Mommy ba, amsa sallamar cousin ɗin ta tayi sannan ta bata izinin shiga ɗakin nata, kallon ta 'yar uwar ta ta tayi tace,
"Laminde hakuri zaki yi ki fito cikin mutane a yi shagalin nan a gama, abinda dare ma yayi yanzu zamu je ɗakko amaryar? To me ya rage kuma? Ita dai Ta Annabi dole ta sanya wa zuciyar ta salama ta gane komai muƙaddari ne daga Allah,matar mutum kuma kabarin shi ce ko ba haka ba?"
Wani abu Innah Laminde ta had'iya mai ɗaci sannan tace,
"Hakane,gani nan fitowa, amma da kin barni a ɗakin tinda ko na fita ba dani za a je ɗakko yarinyar nan ba ko?"
"Ah ah, gwanda kowa yaga idanun uwar ango, ba dan mun raina ƙoƙarin abokan zaman ki ba,"
Murmushi Innah Laminde tayi suka fita a tare cikin jama'a, nan waje ya b'arke da gud'a da kirari daga wajen maroƙa, babu b'ata lokaci kuwa Innah Laminde ta dinga kyautar kudi da turamen atampa dan nuna farin cikin ta.
Da misalin qarfe goma dai-dai mata daga gidan sarki suka shirya dan tafiya ɗakko amarya Mommy a dangana ta da gidan mijin ta Abdussabour..........
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 48:
Motoci uku ne zasu tafi ɗaukan Mommy dan su kai ta gidan ta dake cikin ƙauyen Ba Mugu, dik yanda Bilal ya dinga zillewa dan kar ya zama drivern motar Abdul da Mommy hakan bai samu ba, dan kuwa har ɗaki Abdul ya kira Bilal ɗin suka zauna ya roqe shi alfarmar ya tuƙa shi zuwa ɗaukan amaryar shi,cikin ɓata fuska Bilal yace,
"Malam ba dan ka ji na amince ka aure ta ba zai sa ka zaci wai ina son tane, bana jin akwai ranar da zan so yarinyar nan fa, gaba ɗaya aljanun kammu maƙiyan juna ne, wataƙila a duniyar su ma sun taɓa gwabza yaƙi,na amince zan tuƙa ku sannan jibi zan koma Kano na sa a gyara maku can gidan zan baku waje a ci soyayya lafiya Allah sanya alkhairi,"
"No babu inda zaka je,bayan akwai d'akuna har uku a gidan akwai parlour biyu kawai sai na barka ka kama haya? Ai wannan idan sarki yaji ma sai ka jawo min faɗa a wajen shi,"
Galala Bilal yayi yana kallon Abdul yana tinanin anya yana lissafi kuwa? Gani yayi dare nayi dan haka bai sake kula shi ba kawai ya miƙe yayi gaba, direct wajen motar Abdul ya nufa ya buɗe ya shiga yana fad'in,
"Idan kai baka da hankali ni ina da shi, har yanzu zargin yarinyar nan nake yi,ba zan iya zama gida ɗaya da ita ba inaaa,kai da ka ji ka gani Allah ya bada sa'a,"
Abdul na shiga Bilal ya tashi mota suna hira har suka isa ƙofar gidan su Mommy, anan suka tarar da motocin su Sultan da wani cousin ɗin su Abdul ɗin sun ajiye matan da suka je ɗaukan amarya.
Bayan fitar Motar su Bilal da minti 3 ne Ta Annabi mahaifiyar Billy ta faɗa gidan sarki a gigice numfashin ta na fita da kyar, direct parlourn Innah Laminde ta shiga ta zube a ƙasan carpet ta rushe da wani irin matsanancin kuka mai ban tausayi.
Innah Laminde na tare da 'yan tsirarun dangin su da basu tafi ba sai ta miƙe cikin azama ta kama Ta Annabi suka bar ɗakin gaba ɗaya suka nufi na Abdul ta sa sakata ta kulle su ta ciki,zaunar da ƙanwar ta ta tayi a bakin gadon Abdul da har a wannan lokacin d'akin na fitar da ƙamshin turaren da ya fesa, cikin murya mai taushi Innah Laminde ta fara baiwa ƙanwar ta ta hakuri akan abubuwan da suka faru, cikin kuka da fyace majina Ta Annabi tace,
"A gaskiya Yaya idan nace maki abinda ya faru bai yi min ciwo ba nayi ƙarya, akan wannan baƙin cikin muke ta shirin gyara wa Shamsu inda tashi amaryar zata tare, yaro yabi ya firgice ya gigice ji yake yi kamar aje a ɗakko masa ita su yi rayuwa a wannan akurkin ɗakin nashi,ganin halin da ake ciki sai Bilkisu ta amince zata kwashe kayan ta dika ta mayar d'akin shamsu shi kuma ya gyara nata saboda amaryar shi,idan dangin ta sun yi mata jere su suka sani, idan basu yi ba su zauna a haka a tsohuwar katifar shi ai su suka san shige da ficen da suka yi aka ƙulla auren.
Mun gama magana rimi-rimi da yarinyar nan kamar ta haƙura da maganar auren da Abdul yayi kawai ɗazu da almuru naji tana waya da wani tana sanar dashi zata zo su je dik inda yake so amma wannan karon zai biya ta kuɗi masu yawa sannan zai saya mata gida da mota, ba zata sake komawa ta jingina da kowa ba, wannan karon so take yi ta zama....so take ta zama...ka...karuwa...mai lasisiiiiii yayahhhh,"
Cikin kuka mai tsanani Ta Annabi ta ƙarashe maganar ta, da sauri Innah Laminde ta dafe ƙirjin ta ta zauna tana salatin da bata san iya adadin da tayi ba kafin ta sake maimaita kalmar ƙarshe da ƙanwar ta ta faɗa,cikin jimanta lamarin Innah Laminde ta dafa kafad'ar Ta Annabi tace,
"Yanzu ina ita Bilkin take?"
"Shine tashin hankalin da nake ciki Yayah, daga jin kalaman ta a waya na shiga ɗakin na daki kayan banza da icce sannan nace kar ta sake ta saka ƙafa ko da ƙofar gida ne sai da izini na, a take ta fashe da kuka tace,
'Ba zan taɓa zama talauci da babu su kashe ni ba,idan ke kin ji kin gani zaki ci gaba da rayuwar ƙauye ni ba zan iya ba, kala ta da ƙira ta ba ta zaman ƙauye bane,na gama yawon duniya na san maza kala-kala sai na dawo ku aura min wa kenan? Ina ji ina gani kun hana ni auren Yah Abdul saboda baku ƙauna ta daga ke har munafukar yayar ki dake nuna min son ƙarya, ita kanta Hadizan wanne irin tarko ne ban ɗana mata ba akan na kusance ta......amma yarinyar nan tana tsallakewa, ina son ta, ina tsananin son kasancewa da ita, amma kun aura mata Yah Abdul, ku aura min shi mana na shiga rayuwar su dikan su tinda ina son su? Idan kika yi alƙawarin aura min shi zan zauna babu inda zan je, amma sab'anin haka a daren nan zan bar ƙauyen nan ke baki isa ki hana ni yin abinda zan yi ba,'
"Yaya tinda yarinyar nan ta fara magana na gane mun baro gini tun ranar zane, anan na gane MUN MAKARO wajen yi mata tarbiyya, Yayah a ƙarshe na gane Bilki na bin maza da mata dan kawar da sha'awar dake cikin zuciyar ta, anan na gano har yanzu Bilki bata san menene so ba biyan buƙatar sha'awar ta shi ta ɗauka a so,Yayah na gane cewa Bilki na da tsananin sha'awa tin tana ƙarama nayi sakaci nayi ganganci bamu ɗauki mataki ba muka sakar wa duniya ita har ta hora ta da tarbiyyar karnuka,Yayah yanzu maganar danake yi maki Bilki ta bi wani ƙato a mota sun bar garin nan a gaban idona, dik irin kira da alƙawarin tsinuwa da masifa da bala'in da na dinga jawo mata bai sa ta waigo bama balle ta dawo,"
Salati Innah Laminde ta sake sauke wa sannan tace,
"Na shiga uku ni Laminde, innalillahi wa inna'ilaihirraji'una, ke duniya ina zaki je damu? A zuri'ar mu ake ta samun irin wannan lalacewar? Me duniyar nan ta zama ne yanzu? Lallai mu iyaye muna da babban ƙalubale a gaban mu, ashe kana tarbiyyantar da yaran ka su kuma suna yi maka kallon kai ba ɗan cikin mu bane mun san yanda za mu tafiyar da rayuwar mu yanda zamanin mu yazo mana da shi, yanzu meye abun yi? Kin san inda take aiki a lokacin da take aikin?"
"Ina fa Yayah, shine babban kuskuren da muka sake tafkawa a rayuwar mu,mun saki yarinya tana abinda ta ga dama ba tare da sanin ina take ba, wajen wa take, shin aikatau ɗin take yi ko karuwanci? Yanzu dai kin ga da kunne na naji kalmar da ta kirawo kanta da shi ba wani ne ya sanar dani ba, Yaya ina zan saka raina yanzu ni Ta Annabi? Na ci amanar haihuwa, na ci amanar Allah da manzon sa, ban kula da tarbiyyar yara na ba,dan Allah Yaya ki sama min mafita zuciya ta zafi take yi,"
Innah Laminde kanta ji take yi kamar ta saka kuka ko zata ji sauqin abinda ke cikin zuciyar ta, cikin sauri ta dafa kafaɗar Ta Annabi tace,
"Yauwaa bari zuwa gobe idan Allah ya kaimu da dare zan sa Abdul ya kawo min matar shi nan, sai a tambaye ta gidan da suke aiki, wataqila acan za a samo bakin zaren,"
Sauke ajiyar zuciya Ta Annabi tayi sannan tayi wa yayar ta godiya sannan suka ci gaba da tattaunawa akan yanda za su bullowa lamarin, suna nan zaune suka ji ƙarar motoci da gud'a ana shigowa da amarya, band'akin dake cikin d'akin Innah Laminde tace Ta Annabi ta shiga ta wanke fuskar ta ta same su a parlourn ta a tarbi matar Abdul da ita, ba dan ta so ba haka ta shiga bayin ta wanke fuskar ta ta isa parlourn Innah Laminde, zaune ta ga Mommy cikin alkyabbar da Innah Laminde ta jima da siya ta ajiye tace ta matar Abdul ce, a kullum taga rigar sai tayi mafarkin ace Bilkisun tace ta sanya rigar, sai gashi ashe ba rabon ta bace 'yan d'akko amarya sun sanya wa Hadizan gidan Ɗanli,Mommy ce zaune gaban Innah Laminde wadda ta amsa gaisuwar ta, ta yi mata nasiha, sannan 'Yan uwan Innah Laminde suka shiga suka d'akko mata kyaututtukan auren da aka tanada domin ta, wanda ya haɗa da turarukan jiki da na wuta sai atampopi da laffaya da alkyabba guda biyu, sai dogayen riguna irin na sarauta guda uku, godiya Mommy da su Naja suka yi, nan dai kishiyoyin Innah ma suka yi kara suka ajiye nasu kyaututtukan har da kuɗi, daga nan aka ɗauki amarya aka nufi gidan ta da ita.
Ko da aka kai amarya ango ne ya fita ya kama hannun matar shi ya tsaya yayi wa kowa godiya sannan yace ga motoci nan za su maida kowa gida, daga fad'ar haka kowa ya gane ango dai baya son 'yan rakiya, dan haka babu musu kowa ya shiga mota aka maida shi gidan da ya sauka daga bangaren amaryar har zuwa na angon.
Amarya da ango kuwa da bismillah suka shiga gidan su bayan ya shigar da motar shi ya kulle da kyau tinda kyaututtukan amarya Mommy ma na ciki gobe sun kwashe abun su, kallon gaban gidan da suke fatan gina rayuwa ta musamman a cikin shi suka tsaya suna yi, gidan da suke fatan tara nasu zuri'ar a cikin shi, gidan da Mommy ke fatan ya kasance nata ita kaɗai har abada, dan kuwa yanda take so da ƙaunar Abdul ne ya sanya ta ƙin ƙarasawa cikin gidan ta coge suka tsaya kallon kallo ita da angon nata..............
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAEH ✍️✨
PAGE 49:
Kallon Mommy Abdul yayi fuskar shi ɗauke da annashuwa da annuri sannan yace,
"Bismillah mana ko kuma so kike yi na ɗauke ki na kai ki ciki da kai na kamar yanda ake yi a films ko a littafan hausa?"
Fara'ar fuskar shi ce ta ɗauke dan ganin yanda Mommy ta yi serious babu alamun wasa a fuskar ta tace,
"Abdussabour ba zan shiga gidan ka ba dik son ka da nake yi har sai ka yi min alƙawarin da zai sanya zuciya ta natsuwa da kai,"
Cikin rashin fahimta Abdul ya kalle ya yace,
"Sanar dani alƙawarin da kike so nayi maki yanzun nan na yi miki shi,farin cikin ki shine nawa Habibty,"
Hannun shi ta kama dika biyun ta riqe su a nata kamar wadda aka ce za a raba su sannan tace,
"Ina so kayi min alƙawarin baza ka yi min kishiya ba har ƙarshen rayuwar mu,ko da nan gaba wani zai ce ka ƙara aure in dai bani bace ba baza ka ƙara ba,"
Ba tare da zurfin tunani da nazari akan kalar girma da matsayin alƙawarin da yake shirin amincewa akai ba ya sake jimƙe hannayen mommy yace mata,
"Na yi maki alƙawari har abada ba zan yi maki kishiya ba, Hadiza ni Abdussabour naki ne ke kaɗai zuciya ta ke kaɗai take so take kuma kwad'ayin kammala rayuwar ta da ita har abada,zamu iya shiga yanzu?"
Sunkuyar da kanta tayi ƙasa tana jin wani irin farin ciki da annashuwa na kama ta,sai kawai ta sanya hannun ta ta rataye nashi suka ci gaba da takawa a tare har suka kai bakin ƙofar da zata sada mutum zuwa cikin main house ɗin,makulli ya sanya a ƙofar ya buɗe sannan ya sanya ƙafar dama ya shiga da amaryar shi,babu wutar lantarki dama jannareta aka kunna a gidan dan haka suna rufe ƙofar ƙarar ta ragu,kallon gidan Mommy ta dinga yi tana godewa Allah da ya nuna mata zata yi rayuwa a irin wannan muhallin,basu samu suka zauna ba har sai da Abdul ya gama nuna mata ko ina na cikin gidan tana ta murmushi tare da yi masa godiya.
A master bedroom suka yada zango,inda suna shiga Abdul ya cire babbar rigar shi sannan ya cire wa Mommy alkyabbar jikin ta ya rataye musu a jikin wani royal ƙarfe na rataye kaya,kayan ɗakin gaba ɗaya kalar gold ne mai kyalli da ɗaukan idanu, sai glass mai kyau dake haska su manya manya a jikin wardrobe.
Zama Mommy tayi a bakin gado jikin ta yayi mugun sanyi, yanzu to gata an yi auren fari amma babu budurcin da za a baiwa ango, wata iriyar matsananciyar nadamar yawon da tayi ce ta mamaye ta lokaci ɗaya,cikin sauri ta miqe ta nufi band'aki ta rufe qofa, a jikin qofar ta jingina ta fashe da kuka mai ƙuna, tin tana yi a tsaye har sai da ta zauna a ƙasan tiles ɗin banɗakin dake a tsaftace,jin alamun kamar kuka take yi ne ya sanya Abdul zuwa jikin ƙofar yana k'wank'wasa cike da damuwa mommy tace,
"Yah Abdul kayi hakuri,kayi hakuri da abinda na aikata wa rayuwa ta dan kuwa kai mummunar ƙaddarar ta afkawa,Yah Abdul ni ba budurwa bace, bana tattare da budurci na na zubar da shi ba ta hanyar da ta dace ba, wannan video da hotuna da Billy ta tura maku tabbas ni ce ba ƙarya, kuma ina cikin wajen gyaran jiki ne kamar yanda ka yi hasashe, amma ...."
"Ya isa haka Hadiza, abinda ya faru a rayuwar ki ta baya yariga da ya wuce, abinda ya faru a rayuwa ta ta baya nima yariga da ya wuce, a yanzu rayuwa zamu gina ta tsakani da Allah, babu cuta babu cutarwa, aure muka yi a yanzu kuma aure zamu raya har mu hayayyafa da izinin Allah,dan haka ki dena tada hankalin ki komai ya wuce,amma tambaya ta anan shine ya aka yi kika san Bilkisu ce ta tura min hotunan nan?"
"Yah Abdul na gode da zaka karɓe ni a yanda nake, na yi maka aƙawarin zama mace ta gari wadda zata tsare maka mutuncin ka har abada,ba zan sake shashancin da na aikata a baya ba,na gano Billy ce ta tura saboda ita da bakin ta ta sanar dani ta waya d'azu da ana rububin d'akko amarya, ta kira ta sanar dani dik abinda ta aikata wanda ya sanya jini na tafasa naji na tsani kaina na tsane ta, ta nuna wa Innah Laminde, ta turawa Yah Bilal da Sultan sannan har yanzu akwai a wayar ta bata goge ba,kuma ta yi alƙawarin sai ta yaɗa a
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 32 Chapter of 70