Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
komai ga kuɗi na cassss a hannu" Baabaa ce ta fito riqe da dankwali a hannu ta na nuna Innoh cikin kanne idanun ta guda ɗaya, ta na magana goron da take taunawa ya na tsalle ya na fita tsabar masifar da ta ciyo ta, "Wai ni Innoh ni ce kishiyar ki ko Yadikon Sule? ki bani amsa" "Yadikon su ce kishiya ta,amma ita sam bata kishin da ni idan ba 'yan baƙin halin nata ne suka motsa ba, amma ke Yaya ji ki ke yi kamar mu mace ni da 'ya'ya na a gidan nan ki huta tsabar yanda ki ka tsane mu" Salati Baabaa ta sanya ta na matsar kwalla saboda abinda Innoh ta faɗa game da ita, cikin kuka ta bar wajen ta shige d'akin ta ta na nemo mayafin ta, a can bayan kujerar palourn ta ta same shi,irin ginin da take sha'awa kenan tun ta na amarya sai marigayi mijin ta ya yi mata hakan dan faranta ran ta. Ta na fitowa ta ja k'ofar ta ta zo zata wuce ta gaban su Innoh cikin sauri kamar wata tsuntsuwa tsabar rashin qiba da tsawo, Innoh da Ameerah ne suka kwashe mata da dariya, k'wafa ta yi ta wuce gidan aminiyar ta dan su yi hira ko zuciyar ta ta yi sanyi akan abinda Innoh ke guma mata a gidan,gashi da ta faɗa wa Baban Gida zai ce zai aiko Munir a maida ta Abuja ita kuma bata son zaman Abuja ta taɓa yin shi bata ji dad'in zama ba a cewar ta kaɗaici ya yi yawa dik da irin soyayyar da matar shi da yaran ke nuna mata,musamman Munir da yake babba mai kinanin shekaru ashirin da bakwai. Innoh da Ameerah na tsaka da lissafa cinikin da aka yi a ranar Mommy ta fito idanun nan sun kad'a sun yi jawur dasu, babu sannu balle Allah sawaqe ta wuce su ta ɗauki bokiti a bakin rijiya ta zuba ruwan wanka, ta na gama zubawa ta wuce band'aki wanka ta hau yi ta na ta dirzar jikin ta kamar zata cire fatar ta,sai da ta fita sosai sannan ta d'auraye jikin ta ta fito ta na karkad'e ruwan da ke kan ta, tsayawa ta yi a Saman kan Innoh ta ce, "Inno dan Allah ki bani ɗari biyu idan Shamsu ya zo anjima zan biya ki" " 'Yannan ai idan ɗari biyar Zaki Karb'a bashi zan baki,tun da bahaushe ya ce ai ka gaida mai gaida ka ko ba zai amsa ba ko?" Murmushi ta yi ta juya ta koma d'akin su, ta na shiga ta tsane jikin ta tare da sanya kayan ta da har a wannan lokacin basu wani risina ba su na nan a cukuikuyen su,kwalliya ta zabga ta gyara guida yaran kan ta ta yi acuci maza ya yi tush da kyau a bayan kanta,da alama dai Mommy aka buɗe mata saloon ba karamin kuɗi za ta samu ba saboda yanda ta iya tsara kwalliya. Turaren ta ɗan d'uri ta d'akko ta lakata ta shafa sannan ta d'akko wayar ta ta shuri takalmin ta baƙi ta yi waje,ko da ta fita Yadiko kawai ta tarar a tsakar gidan ta na jiqa garin kwaki za su sha da yaranta,dama duk ranar girkin Innoh da rana bata abinci sai ta ga dama, gata da yara mata ba zata saka su su girka ba ko dan saboda fita hak'k'in mutanen gidan da kuma koyawa yaran ta girki, ah ah sai dai kowa ya nemi abinda zai ci da dare ta tuƙa tuwo da miyar da ta ga dama kowa ya ci, da safe a yi d'umamen tuwon da kunu idan akwai kamu, idan babu tuwon babu kamun ma kowa sai dai ya san yanda zai yi, ita dai za ta ɗora abincin siyarwar ta a fitar mata da shi. Yadiko na Saida kuka,maggi,gishiri,daddawa,citta, kaninfari da sauran kayan miya na cikin gida da mata kan siyar,sannan ta na wankau da sirfe duk dan a rufa wa kai asiri, shi yasa idan ma ba a bata ba za ta siyi abinda take so su ci da yaran ta,duk randa Ɗan liti be bata na cefane ba zata yi amfani da na wajen ta,bata tambayar shi sai idan taga zai yi rashin adalcin nashi da ya saba na baiwa Innoh kuɗi mai yawa ita ya bata kaɗan duk da cewa ta fi taimaka masa a gidan, to a sannan ne yake ganin asalin kalar ta, zata karta masa rashin mutunci ne har sai ya yi rabon adalci sannan take kyale su dika. Zaman Yadiko da Innoh kuwa zama ne kadaran kadahan, Innoh bata cika jan Yadiko faɗa ba kamar yanda take jan Baaba faɗa,ba dan komai ba sai dan hakuri irin na Yadiko ko ta ja ta da faɗa shiru take yi bata kula ta har ta ƙarata da faɗa da masifar ta ta gaji ta kyale ta dan dole, dan kuwa bahaushe ya ce k'arfe ɗaya baya amo, a duk sanda kuwa aka yi rashin sa'a Yadiko ta biye mata aka yi faɗa a gidan abun baya yin kyau dan kuwa bata iya faɗa ba sam idan ta tashi,tsoron hakan ke ƙara nesanta Innoh neman faɗa da Yadikon. Bangaren Mommy kuwa ta na fita soron gidan su ta fito da face mask d'in ta da ke maqale a jikin 'yar kwab'irar wayar ta ta saka ta rufe bakin ta,sannan ta sa kafarta fara tass mai dogayen yatsun qafa da suka sha baƙin dayis suka yi wani irin kyau kai ka ce bata taka ƙasa a waje ta na wani lumshe ido ta na ware su a hankali,in dai kyan ido ne da dogayen gashin ido da Kyakkyawar gira da dogon hanci ne Allah ya ba wa Mommy,in dai ba buɗe wa mutum bakin ta ta yi ba babu mai yarda bata haɗa jini da jinsin buzaye ko Larabawa ba. Direct gidan su Balki ta nufa wadda tun da ta isa gidan su take ta sharara wa mutanen gidan su k'arya, Balki bata taɓa iya zama ba tare da ta yanka k'arya ba,hankali kwance zuciya zaune za ta yi dabarar da duk zata yi ta kawo labari mai daɗi ta yanda za ta samu gab'ar da take so ta gilla ta ta qaryar ba tare da an gano ta ba, wannan shine babban dalilin da ya sa ta tara masoya a accounts ɗin ta na social media. Da sallama Mommy ta shiga gidan ta na wata tafiya kamar 'yar wani hanshaƙin,kamar mutuniyar kirki haka ta durƙusa har ƙasa ta na gaishe da Mahaifiyar su Balki, Balki kuwa tunda ta ga ƙawarta ta miqe ta na ta murna,amma sai Mommy ta nuna mata ita a natse ta zo ba da hauragiya ba,wannan sabon halin kuwa ba k'aramin bawa Balki mamaki ya yi ba, sai da suka shiga d'akin Balki ne wanda ta k'awata abinta kamar na 'yar masu kuɗin gaske Mommy ta daka tsalle ta rungume ta suka hau murnar ganin juna. "Ke banza ina ki ka shiga ki ka manta da mu, yau fa shekarar ki ɗaya da watanni biyu rabon ki da qauyen nan fa? Habaa Billy ai ya kamata ace ki dinga waigo mu ko da a wata biyu ko uku ne" "Ke dalla bar ni ba zan zo ba ɗin,haka kawai ina can ina cin shinkafa da kaza,ga shayin da ya ji madara da soyayyen kwai duk safiya kawai sai in dawo? To idan na dawo me za ku dinga bani ina ci ko kina nufin tuwon nima zan dinga ci? To sam ba zai yu ba, ki duba fata ta mana ki gani ke kin san ta na shan AC kuma k'wai ya zauna a cikin ta,na faɗa maki a bar batun bakin ki yanda Allah ya yi maki fata mai kyau da tsarin Kyakkyawar surar nan zaki yi kyau da zaman birni,dan haka ki biyo ni mu koma cikin garin Kano Hajiya ta ki samu wani gidan aikin irin nawa ki ga yanda Zaki koma,amma inaa kin bi kin nace kin makale kamar wani abun ki ke samu da ya fi wanda Zaki samu a can birnin,ko ni da ubana ke sayar da dusar awaki da ta kajin gidan gona ya amince min na tafi neman kuɗi balle ke da naki uban ke yin Kabu-kabu,na wa yake samu a rana gaba ɗaya idan ya fita tun safe? Gaskiya ya kamata ki san abin yi akan wannan lamarin ki tashi ki nema ki taimaka wa iyayen ki da ke kan ki da sauran 'yan uwan ki, ki dubi mahaifiyata leshin da ke jikin ta kin taɓa ganin irin shi a jikin matar sarkin ƙauyen nan? Ko kin taɓa ganin wata na yafa mayafin da take yafawa a kaf garin nan? Ki duba motar da Babana yake ja ni na sai masa muka fake da cewa shi ya sai abar shi,yau ko motar ki ka sai wa Baban ki ba sai ya dinga tuƙawa ba ya na jeka ka dawo daga wancan ƙauyen zuwa wancan?" "Hummmm Billy ba Zaki gane bane,Baba ya hana, ya ce aure zan yi bai yarda da ci gaba da karatu ba, kuma bai yarda da zuwa aikatau ba, yanzu haka fitowar nan da na yi sai da ya yi min warning akan yawon da muke yi dan samun baground mu yi hoto" "Ai kuwa sai mun fita,ki na ganin wannan wankan naki zai tafi a banza ne? Ai ba zai yu ba inaaa, bari ki ga wayar da Hajiya ta sauya min" Tashi ta yi ta koma tsakar gida ta d'akko iphone ɗin ta ta kawo ta damqawa Mommy a hannun ta, cikin zaro ido Mommy ta kalli wayar da take jin labari ta na tashe da tsada, cike da mamaki take juya wayar ta na kallo Billy da ke wani kad'a ƙafa ita a dole ta kai wata yar duniyar. "Billy kin tabbata Hajiya ce ta baki wannan wayar?" "K'warai kuwa, ke ba fa gidan qananan mutane nake aiki ba,gidan Ambasada nake aiki idan baki sani ba ki sani, kuɗi gare su kamar ya kashe su, ba ni kaɗai ba ma hatta da masu gadin gidan wasu arnan wayoyi ne a hannun su, ya na da gidaje a Nigeria masu tarin yawa har da Abuja,ke ki na tunanin in ba gidan manya ba a ina zan dinga cin daɗin da nake ci na kwanta a AC ?Hajiya ta idan Zaki lallab'a Baba ya barki ki lallab'a shi kema ki shiga gari idanun ki ya buɗe ki ga duniya duniya ta gan ki" Shiru Mommy ta yi ta na nazari, Billy kuwa ta kafe ta da ido ta na so ta samu nasara akan ta, ta jima ta na son ta tsoma Mommy a harkar da take yi,ta rasa ta inda zata bullowa lamarin,ta ɓangare ɗaya kuma tinda Hajiyar da take tare da ita ta k'yalla ido ta ga wani video na Mommy ta na magana cikin salo da iyayi jikin ta babu suturar arziqi ko ina na jikin ta a bayyane take so a kawo mata ita dan ta sanya ta a irin harkar su, dan ta kula Mommy za ta iya duk abinda suke da buk'ata a ƙungiyar tasu. Wannan dalilin ne ya sa duk kafiyar Billy akan bata so ta zo ƙauye ta wahala sai da ta matsa mata akan ta na so ta zo ta yaudaro mata Mommy da kuɗi ko za su samu nasara a wannan karon. "Ke ina zuwa na shirya mu je gidan sarki mu sha hotuna media ta san yau ƙawayen juna sun haɗu, maza tashi ki sauya kaya, na zo maki da wasu sabbin kaya wanda na samo a gidan aiki na, kema ko ba komai a san cewa ke kawar Billy ce a ƙauyen nan,dan ba Zaki dinga bi na da abayar da ta yi shekara da shekaru ana sa mata filter ba" Jiki ba kwari Mommy ta kalli Balki da ita kaɗai ke kiran ta da Billy,ta ga tana zuge akwati ta na fitar da wasu arnan kaya masu kyau da tsada wanda duk ta samo su ne daga wajen Hajiyar ta a birni,wata pink abaya ta baiwa Mommy mai haɗe da mayafin ta ta ce ta sauya,sai ta bata takalmi da jakar da za su shiga da kayan sannan ta bata turarika ta ƙara nuna mata wasu kayan ta ce nata ne, amma sai sun dawo daga ɗaukan hoto za ta bata ta wuce da su gida. Har Billy za ta fita dan sake wanke fuska saboda ta ji daɗin shafa powder Mommy ta riqe hannun ta ta ce, "Ke wai ina Yah Shamsu ne? Yau tunda na zo ban ga koda gilmawar shi ba?" Qanqance idanu Billy ta yi ta na kallon ƙawarta cikin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa ta ce, "Ban gane ba ! me yasa ki ke son ganin shi? Ko dai ko dai?" Dariya suka yi a tare sannan suka tafa,Mommy ta ce, "Ba Zaki gane ba, a wani group mu ka haɗu da shi ya na tura mana kayan lamura kin dai gane,sai yake amfani da Sunan mace ya ce duk mai so ya bi shi Private ya biya kuɗi a tura masa, ni kuma bani da sisi kin dai sani,shine na je na dinga daɗin baki bud'ar bakin sa ya yi min audio note ya ce, 'Mommy kar ki damu ai ana tare ko gida ki ke so na zo na tura maki a waya sai na zo ai'daga nan hankali na ya tashi ta ya aka yi matar ta sanni? Tinda da Maman Fadwa nake amfani a social Media,ke na tak'aita maki labari dai muka haɗa za mu haɗu a gidan mu, ina ta jin tsoro amma da na ga mace ce sai na ce ba komai,kawai sanda ta zo ta kira ni,ko da ta iso na yi na yi ta shigo ta ce na dai je na ga waye tukunna, ina zuwa na ga Yah Shamsu" "Dan Allah ki bari? Yah Shamsu dama ya san wannan harkar? Kan bala'i kin ga yanda yake faɗa idan ya ganni da waya kuwa sai ya ce su Baba ne suke shagwab'a ni nake abinda nake so ashe shima ɗan hannu ne," "Ai ba shi kaɗai ba, a hankali na gane Yah Sule ma ya na wannan harkar kin san yanzu duk yawancin matasa an raja'a neman abinda zai ɗebe kewa, wannan harkar kuma ita ce muke ganin ta fi mana samun nishad'i da ɗebe kewar talaucin da ƙasar ke ciki," Sun manta da karanta qur'ani,sun manta da tasbihi ga Allah da salatin Annabi da istighfari wanda shine ya kawo mu duniyar ba neman abun ɗebe kewa ba,sun manta Allah da kan shi ya na cewa bai halicci mutum da aljan ba face sai dan su bauta masa, sai suka juya bautar Allah'n ta koma sab'on Allah, to ta yaya za mu ga dai-dai a wannan yanayin da muke ciki? Billy na gama sauraron Mommy ta gyad'a kai ta ce, "Ehhh tabbas haka ne,ina zuwa" Da wannan hirar suka gama shiri tsaf suka fita zuwa gidan Sarki dan ɗaukan hotuna da videos domin posting ɗin su zuwa social Media...... [09/08, 10:37 pm] Aunty Hameeda: *GIDAN ƊAN LITI* RUBUTAWA: HAMIDA SANUSI AHMAD (HAERMEEBRAEH) *PAGE 3:* Wata iriyar kwalliya suka tsara wadda duk wanda ya kalle su sai ya qara, dan kuwa daga Mommy har Billy suna da kyawun sura sai kuma suka ƙara da wanka ga wayewa da iya gayu. Tafe suke suna rausaya kamar wasu furanni a lambu, sai latsa waya suke yi suna hotuna a Snapchat, a haka suka isa gidan Sarki bakin su ɗauke da sallama, su na shiga suka yi arba da uwar gidan Sarkin mai suna Innah Laminde wadda ta na ganin su ta washe baki tare da fad'in, "Ah ah ahhhh kanawan dabo ne yau a gidan namu? Lale maraba da 'ya ta, jiya na gama zancen ki a gidan nan da Umman yara, na ce 'ya ta ta shekara ɗaya da watanni ban sanya ta a idanu na ba,ashe kina nan tafe yau." "Sai gashi kin yi zancen ƴar halak, 'yar halal ta bayyana a gaban ki, Ina yini Innata? Ya gida ya iyali ya Baba Sarki da fatan ya na nan lafiya bai sake cin daɗi ya taso da ciwon sugar ɗin nashi ba ko? Na zo masa da magani ai daga birni ya zo ya sha ko Allah ya sa a dace" D'aki Innah Laminde ta wuce su Billy na bin ta a baya, babban parlour ne wajen wawakeke mai ɗauke da kayan more rayuwa kala-kala kamar ba a qauye ba, gefe kuma ga wata qofa nan da za ta Sada ka da asalin bedroom ɗin mamallakiyar d'akin, waje suka samu suka zube a cikin kujerun dake zagaye da tsakar palourn, Billy ta sanya hannu a cikin jakar ta ta d'akko maganin masu ciwon sugar da ta siyo wa Sarki wanda yake mijin yayar mahaifiyar ta ne ta miqa mata, Innah Laminde ce tace, "Allah dai ya yi miki albarka Billyn Lamindedeee, ki na taya ni kula da ɗan tsohon miji na baki ko gajiya, yanzu dai fata na Allah ya sa ya sha maganin nan, saboda kin ga Abdussaboor ma da ya kawo masa daga can kano qin sha ya yi, wai a bar shi da tafasar shi da cabbage da garahuni yafi gane musu," "Ohhh Baba Sarki da gargajiya 5&6 ne ai, Allah ya sa to ya sha wannan ɗin dan ya na da kyau, Hajiyar da nake wa aiki da shi take amfani,kuma ya karɓe ta sosai" "To Ameen dai, ya qanwata kin ɗauke min hankali ban ko tambaye ta ba, ina fatan dai ta na nan lafiya da sauran 'yan uwan naki?" "Ahhh alhamdulillahi ta na nan lafiya tace ma a gaishe ki sosai, kowa ma na lafiya qlou,Innah Laminde yaushe Yah Abdul ɗin zai dawo gida zai jima kuwa?" "Eh toh bana ce ba,dan be jima da komawa ba, kin san babban injiniya a Koda yaushe ana bukatar shi a kusa musamman a irin kamfanin da yake aiki shi yasa ya na zuwa kwanan shi biyu ya koma" Jiki a sanyaye Billy ta ce, "Ayyaaa ! ba rabon mu gana ashe wannan karon ma,Allah ya kaimu wani lokacin in da rai ai da rabo,ya kamata dai a bani sabuwar lambar wayar shi dan idan na koma kanon na neme shi mu gaisa." "Hummmm Allah ya sa ya ɗauki wayar taki kar ki zo ki na min k'orafi irin na wancan karon," "Ameen dai, kin san shi ɗin ɗan ra'ayi ne," Innah Laminde kallon Mommy da ta yi zukud'iii ta na kalle-kalle ta yi ta ce, "Ita waccan tunda aka gaisa ta ja baki ta tsuke,gashi ta sha takunkumi kamar jaki mai cizo daga ina take?" Dariya Billy ta yi sosai sannan ta ce, "Kaiii Innaah Laminde qawata ce fa Mommy 'yar gidan Ɗan liti,mun sha zuwa gidan nan da ita kuma kullum muka zo sai kin faɗi wannan kalmar da ke bata haushi" "Aiii haushi na ki ke ji ashe ƴannan? To in kin ji haushi ki dena qunshe baki kamar mahaukaciyar kura a tsakiyar gari,haka kawai ki kama baki ki qumshe shi gummm ya dinga miki azabar wari? Wannan ai duk sanda ki ka cire takunkumin wani na kusa sai ki sumar da shi da warin baki,qudaje kuwa sai dai su dinga zubewa su na mutuwa saboda wari." Haka Innah Laminde ta dinga yankar Mommy wadda ta qi hasala dan kuwa bata taɓa sanya kayan da ta sa a wannan rana ba,so take ta hasala ta ko hoton aka zo yi idanun ta su fallasa b'acin ran ta,dan haka yaqe ta dinga yi kawai, karshe ma ta ce a sammata ruwa zata sha. Kwala wa mai aikin gidan kira Innah Lamide ta yi, ta na zuwa ta bada umarnin a kawo wa baqi abin motsa baki bari ta shiga ciki ta qarasa abinda take yi. Ta na shiga kuwa su Billy suka miqe suka hau yin abinda ya kawo su,dan kuwa ba wai dan gaishe da Innah Laminde kawai suka zo ba, ɗaukan hotuna ne da kuma ganin Abdussaboor ne maƙasudin zuwan Billy. Bayan sun gama hotunan su ne suka zauna cin kayan flour da shinkafa dafadika da ta ji kifi soyayye sai zob'o mai sanyi da pure water, suna ci suna hira a haka Innah Laminde ta fito ta tarar da su,duk zuwan da suke yi bata taɓa yin arba da bakin Mommy ba sai wannan zuwan,salati ta sanya sannan daga qarshe ta kece da dariya ta ce, "Ahhh ban ga laifin ki ba yarinya, ina da wani takunkumin ma tun na lokacin kwarona (corona) da wannan yaron ya kawo min ban yi amfani da shi ba zan baki aje a yi ta sanya wa, ke Fure taho ki d'akko min wannan takunkumin na 'yan asibiti, ki d'akko dika kwalin" Madadin Mommy ta ji haushin kalaman Innar sai ta washe dasorin ta ta na zabga godiya tare da fatan Allah ya sa Innah laminde ta fi qarfin babu a rayuwar ta. A baqar Leda aka sanya mata face mask d'in ta dinga godiya, bayan sun tafi ne suka tsaya a hanya Mommy ta sai data a wajen wani mai saka caji, suna tafe suna hira Billy na tura wa Mommy hotuna da videos da suka yi ta xender dan kuwa bata da isasshiyar datar da za ta iya buɗe su idan an tura mata ta WhatsApp,ko a kan wannan rashin datar ma sai da Billy ta yi wa Mommy surutu tare da kwad'aita mata tafiya kano ta ga yanda zata wadatu da data har ta sawa wasu ma. Kamar an ce Mommy ta d'aga kan ta ta kalli tsallaken titin gidan su,ta na d'aga wa suka yi ido biyu da Ɗan liti da ya qura wa inda suke ido ya na so ya tantance shin 'yar shi Mommy yake gani da kaya masu kyau haka ko wata ce daban? Su na ganin haka Mommy ta juya wa hanya baya ta hau tafiya, basu tsaya a ko ina ba sai a gidan su Billy cikin sauri ta sauya kayan ta zata tafi gida jiki na rawa, Billy ta saki wani wawan tsaki sannan ta ce, "Gaskiya ki na min abinda bana so, ki na min abinda ke sa na ji kunya, habaa ! Sai kace ba mace mai 'yanci ba? Meye abin jin tsoro haka kamar wadda aka kama ta na aikata masha'a? Dan ya gan ki sai me ? Kashe ki zai yi?" "Humm ba zaki gane ba, ba wai tsoron faɗan nake yi ba mita ce bana so," "Karb'i wannan ki na zuwa ki bashi ki ga idan zai maki faɗa" Kuɗi Billy ta zaro dubu biyar cass ta ba wa Mommy sannan ta tashi ta sake haɗa mata wasu kayan,bata bar Mommy ba sai da ta tabbata ta gama buga mata kai da kyauta har ta rasa bakin magana, cike da godiya da sanya albarka Billy ta raka Mommy har kwanar gidan su sannan suka rabu. A kafe ta hango babur ɗin Ɗan liti ya na zaune a saman babur ɗin ana ta kiraye-kirayen sallar magariba amma ya qi tafiya ya na jiran isar ta, fuskar nan ta yi jawur, haqoran nan sai qara suke saboda yanda yake taune su, jira yake ta isa ya ga uban da ya tsaya mata take taake dokar da ya ke saka mata a matsayin sa na uban ta. Qara damqe kud'in da Billy ta bata dan ta ba wa Ɗan litin ta yi,dan kuwa a ganin ta ko ta bashi sai ya yi mitar nan da ya saba,cikin dabara ta zare dubu uku ta b'oye ,ta bar dubu biyu a hannun ta,ta na isa ta tura baki ta na harare-harare ta tsaya a gaban shi ba tare da ta ce masa komai ba, "Ke dan Babar ki Innoh wa ya ce ki je ki dad'e haka? Ke wato ga tinkiya uwar tinb'ele ba ki san gida ba sai an nemo ki ko? Tun da na ga wannan me kama da birran uwar tsalle-tsalle ta dawo na san shi kenan yanzu ganin ki zai yi wuya, gidan uban wa ku ka je?" Bata bashi amsa ba sai ta miqa masa kud'in hannun ta zata yi magana ya riga ta cikin washe baki yace, "Ah ah, uwar masu gida Hadizatul kubura 'yar albarka,a Ina ki ka samo wannan uban kud'in haka? Ai sai ki yi magana kin bar ni ina ta b'arin zance sai kace wanda aka haifa a tsakiyar kasuwa" "To Baba ba kai bane,kai komai faɗa ni bana son mita ka sani kuma, amma idan ka

Chapter 2 of 70