nan,ta naɗi romon nama da narkakken kitse,sai nama yanka uku,da gani ma ci ya yi ya rage mata,kamar mayunwaciyar da ta shekara bata ci komai ba haka ta dinga tura gurasar nan tana korawa da ruwa,sai da ta zo cin nama ne ta fashe da kuka,cikin kuka baki a cike da gurasa ta ce,
"Ohhh ni Hadiza na ga ta kai na ! Wai yau ni ce nake cin nama yanka uku kacal kamar wata mayya? Allah ka kawo min sassauci,Allah na tuba akan dikkan laifukan da na aikata dan nasan sune dalilin shiga ta wannan rayuwa ta ƙasƙanci."
Kuka sosai Mommy ta sha har sai da ta fara tinanin anya bata samu matsala a kanta ba kuwa? A haka ta gama cin abincin ta ta miƙe ta haye gado ta hau baccin gajiya. Da asuba ta tashi ta yi sallah,kafin ta haye gado ta maida bacci Tsahare ta aika yaro a kira ta ta hura murhu a dora ruwan koko,dan shi ake fara damawa kafin dumame,idan kuma sabon tuwon da ake yi wa Malam ne dik safiya Tsahare ce ke yi masa,domin ita kaɗai ya yarda ta dinga yi masa abincin da zai ci da safe.
Kuka Mommy ta sanya kafin ta hau buga ƙafa a ƙasa tana jin yanda idanun ta ke rufewa kamar wadda tasha maganin maye,jiki babu ƙwari ta fita ta hau ɗiban ledoji a tsakar gidan,har da plate ɗin su na roba sai da ta saka ta ƙone kafin wutar ta kama,tana gamawa ta debo ruwa ta zuba a ƙatuwar tukunya,a wajen ta zauna ta rakuɓe a jikin gini tana bacci. Malam na shigowa ya ganta zaune ta saki leɓe tana bacci,murmushi ya yi ya wuce ɗakin mahaifiyar shi ya gaishe ta,ruwan na tafasa Tsahare ta nuna mata yanda ake dama kunun gidan yawa irin nasu,tana gamawa ta ce,
"To ina sugar?"
Dariya Asabe dake gefe ta yi ta buga cinya sannan ta ce,
"To kema wanda kika sha jiya rabon ki ne ya tsaga saboda amarci,kowa na gidan nan haka yake shan kunu babu sugar,idan uwar yaro nada kuɗi sai ta sai masa mazarƙwaila ya saka a ciki,in bata da shi sai ya kalli sauran ƴan'uwan shi dake da shi suna sha."
Shiru Mommy ta yi ta ɗauki tuwon da ta tarar an yanka an zuba a miya, da alama Tsahare ce ta yi mata haka ko kuma ta saka yaranta su yi mata hakan,dan tana da yaƙinin yanda Mero da Asabe ke nuna mata kishi a fili baza su yi mata hakan ba,godiya ta yi sosai sannan ta ɗora tuwon ta ja gefe ta zauna tana jiran ya yi,nan take ta tina da nata da bata ci ba a daren jiya, ɗakin ta ta tafi da azama ta ɗakko ta yanka ta zuba.
Saida Malam yazo wucewa ta durƙusa tana gaida shi,gani tayi yana yi mata wannan mayen murmushin nashi da kan faɗar mata da gaba, itama yake ta yi masa,ko babu komai jiya bata yi kwanan yunwa ba.
A gaban idanun ta Asabe ta kwashi abincin Malam da Tsahare ta gama jerawa ta wuce dashi ɗakin ta inda Malam ɗin ya shiga,anan ta gane kenan a ɗakin Asabe ya kwana,yatsine baki ta yi sannan ta kauda kai gefe,dan kuwa ko a jikin ta wai an tsikari kakkausa da mashi.
Tana kammala ɗumamen tuwon ta zubawa kowa nashi yanda Tsahare ta koya mata,da kanta ta ɗauki abincin surukar su ta kai mata har ɗakin ta sannan ta fito ta wuce da nata ɗakin ta,zaune take ta rabka uban tagumi tana tunanin Amir ta ji Tsahare ta sallama ta miƙa mata man shanu ta ce,
"Ki tsiyaya wannan kin fi jin daɗin tuwon,idan kina son yajin daddawa ma sai na kawo miki duk ina da shi."
K'walla ce ta taru a idanun Mommy,godiya ta dinga yi wa Tsahare sannan ta ce,
"Ina so a kawo min yajin Iyah,ko kuma muje na karb'o da kaina ba sai na wahal da yaran ba."
"Ah ah yi zaman ki kawai bari na baiwa Abashiyya ta kawo miki."
Tafiya ɗakin ta tayi,ta bar mommy na jin daɗi a ran ta, dan kuwa ko babu komai man shanun zai sa ta ji daɗin abincin,babu jimawa Abashiyya ta kaiwa Mommy yajin,zama ta yi ta dinga cin tuwon kamar ta samu nama,tana gamawa ta kora kunun cikin sauri ta haye gado dan ta rama baccin dake kanta,ga shi har a wannan lokacin jikin ta be bar ciwo ba.
Da rana dambu Mommy tayi musu,ta ji daɗin hakan sosai dan kuwa itama ta ci mai yawa,Ameerah ma da ta kai mata ziyara sai da ta ci ta ƙoshi,kamar ta san Mommy na cikin babu haka ta kai mata kayan maƙulashe da dakakken yaji mai daɗi,sai kuɗi dubu uku wanda Ɗan Liti ne ya bayar yace ta kai mata. Mommy ta yi farin ciki sosai sannan ta godewa Ameerah, cikin damuwa ta zayyanewa Ameerah dik irin zaman da take yi a gidan. Ameerah kuwa sai ta kada baki ta ce,
"Ai Allah ya kara tinda baki ɗaukar shawarata sai ta Aunty Naja,lokacin da kika sanar dani irin auren da zaki yi ban hana ki ba? Na san ni ba wani ilimi gare ni ba kamar ku,amma da jin sunan auren ma AUREN KISAN WUTA bashi da kyau,ki cire ran ki ki akan zaki rabu da mijin ki, ki tuba ga Allah, sannan ki faɗa masa ke kin tuba baza ki ci gaba da wannan auren kisan wutar ba,idan ya ga dama ya barki a ɗakin ki haka ƙaddarar ki tazo,zaki rungume ta hannu bibbiyu,kina dai ganin yanda aure na ya kasance da Shamsu,na ƙi auren shi ne? Ai ban ƙi ba,a haka na zauna dashi har na haihu,gashi yanzu ina jin son shi a cikin zuciya ta,shi kan shi idan kika ji yanda yake yabo na tare da furta min kalaman soyayya zaki sha mamaki,dan haka ki saki ran ki shi Abdul na can amaryar ma ta gudu,to ta ji bashi da kayan aiki shine ta gudu,yanzu dai baida aure babu kuma wadda zata aure shi tinda ya rabu dake akan gaskiyar ki."
"Na ji shawarwarin ki Ameerah inshaa Allahu zan ɗauka,amma kuma kar ki manta Abdul fa ba abun zagi bane a wajen mu,ya yi min halacci, ni ce dai na ƙi yarda na danni zuciya ta,gashi ta kaini ta baro,Allah ya bashi wata matar ta gari,ni dai kam na riga na yi asarar miji mai so na."
Hawaye ta fara zubarwa har sai da ta karyawa Ameerah zuciya,ita kuwa bata iya lallashi ba, dan ko ɗanta ke kukan banza a ƙananan watannin shi zazzane shi take yi balle wata Mommy,goya yaronta tayi ta miƙe tana faɗin,
"To ni dai na yi can,sai kuma wani lokacin idan Allah ya nufa, duk abinda kike so wanda be fi karfi na ba ki min waya zan kawo miki ko na aiko shamsu ya kawo miki."
Godiya Mommy ta yi mata sannan ta raka ta bakin ƙofa,da harara Ameerah tabi ɗakin da Malam ke aikin bokancin shi kafin ta wuce ta bar gidan,Mommy na dawowa ta haye gado ta hau bacci kafin la'asar tayi ta ɗora tuwon dare.
*************************
A hankali shagon su Billy yake ta buƙasa,mutane na ta zuwa siyayyar kayan gyaran jiki,amare kuwa anan ake yi musu gyaran jikin sannan su sayi kayan mata wanda su Billy ke haɗawa da natural abubuwa marasa cutarwa da kan su,kayan su na matan aure ne zalla a cewar Any banda ƴan mata ko zawarawa,dan kuwa sun yi alƙawarin babu budurwar da zata zo siyan kaya su sayar mata,tinda su sun san yanda ƴan mata ke siyan maganin mata har sun fi matan auren ma siya,wasu kuma zawarawa ne ma kuma ba wani auren za su sake ba,haka kawai za a siya a sha a dinga rabawa mazan aure da samari jiki a waje.
Watarana haka suke faɗa kaca-kaca da ƴan mata ko zawarawa,amma hakan baya damun su ko kaɗan,da suna da ikon daƙile karuwanci a duniya ma baki ɗaya tabbas da za su yi hakan,dan kuwa su sun san illar shi.
Gefe ɗaya kuma duk wani taro ko wa'azi da za a yi da ya ƙunshi mata zalla,ba a barin su a baya,mataimakiyar shugaban Hisba kan kira su a waya ta sanar da su,sai suma su dunguma a tafi wa'azi,ba su dawowa gida sai an gama komai tare da su.
Soyayya ce mai tsafta ta ƙullu tsakanin Man da Billy,sai dai babbar matsalar da suke fuskanta,iyayen shi sun ce ba zai auri yarinyar da ta gama yawon bariki ba,sannan sun ji ƙishin-ƙishin ɗin videon tsiraicin ta na yawo a duniya.
To ni anan ina da tambaya makaranta,shi wai iskancin nan kashi-kashi ne ko kuwa dik abu ɗaya ne? Na ga dai abinda Billy tayi shi Man ya yi,to me yasa ita Billy ake ƙyamar auren ta shi kuma ba a jin wata damuwa game da abinda ya aikata?
[09/08, 10:39 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA: HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 99:
Kwana Billy ta yi tana kukan baƙin ciki tare da data sanin baƙar rayuwar da ta zaɓi ta yi a baya,da kanta ta ɗauki kanta ta jefa a masifa da bala'in da ba zai taɓa gogewa a idanun mutane ba. Bawa zai iya aikata babban zunubi koda kuwa shirka ne ya tuba zuwa ga Allah,Allah ya yafe masa,amma mutane sam basa yafiya,ba kuma sa mantuwa musamman akan mummunan abinda ya shafi rayuwar wasu. Cikin kuka ta miƙe ta shiga toilet ta gabatar da uzirin ta ta fito tana dafe gini saboda yanda take jin jiri na ɗibar ta,sakamakon rashin cin abincin da bata yi ba a gaba ɗaya wunin ranar. Any ce ta kalle ta cike da takaici tace,
"Wai ke kashe kan ki zaki yi akan mutane da basu damu da rayuwar ki ba? Wani shege yana da wuta ko aljannah ne a cikin su? Idan babu mai son ya bar ɗan shi ya aure ki ba akan ki aka fara zama kuma a ƙare rayuwa babu aure ba,ki tsaya ki nemi gafarar Allah akan abinda kika yi a baya har iya tsawon rayuwar ki,sannan ki nemi kuɗi ki huce takaicin talauci da babu,ki fi karfin abinda zaki ci da abinda zaki sanya a jikin ki,dama duk dan me ake fita karuwancin da yawan zinace-zinace a cikin gidajen? Ina ce saboda a ci abinci me kyau dangin su nama da kayan ƙwalama da maƙulashe ne? Sai kuma a sanya sutura ta kece raini a hau manyan motoci,to a yanzu idan kika dage da sana'a ta halal i promise you zaki fi karfin dik abinda kike nema,dan haka ki jajirce ki kama Allah ki rabu da duk wani shegen da zai dami zuciyar ki da kwanciyar hankalin ki."
Any na gama masifar ta ta ɗauki wayoyin ta ta bar ɗakin ta koma wani ɗakin ta kwanta tana ci gaba da mita,Billy kuwa a wajen ta samu ta tsugunna ta ci gaba da rusa kuka. Ba da wasa take son Man ba,tin fil azal shine namiji na farko da ta fara so,kafin son zuciya ya shige ta su ƙulla soyayya da Any,da shiriya ta shige su kuwa nan take suka gane ba soyayya bace sha'awa ce da ingizawar shaid'an kawai a tsakanin su,soyayyar da ta yi wa Abdul kuwa ta gano har da hassada da baƙin ciki da take yi wa Mommy,sannan a tinanin ta zata iya yiwa Allah wayo ne,ta gama bariki sannan ta je ta auri miji kalar nunawa sa'a. Cikin kuka ta miƙe tsaye tana layi kamar wadda ta shawu,wayar ta ta ɗauka ta hau neman layin mahaifin ta,tinda suka baro garin Ba Mugu bata fasa neman shi tana bashi haƙuri ba,da fari baya ɗauka,amma daga baya yana ɗauka daga gaisuwa babu wani abu dake sake shiga tsakanin su,mahaifiyar ta kuwa tini ta yafe mata,sai dai ta ce tayi zaman ta anan inda take ba sai ta koma gida ba,dan kuwa har yanzu a garin ana zancen ta da abinda ta aikata.
Cikin sa'a bata jima tana ringing ba ya ɗauka,sallama ya yi cikin dakewar murya kamar koda yaushe,kukan da ya ji Billy nayi ne kamar zata rasa ranta ya sassauta masa fushin sa,abinka da ɗa da mahaifi,nan take ya ji wani irin tausayin ta ya lulluɓe zuciyar shi,murya na rawa ya ce,
"Bilkisu ki daina kukan haka ya isa,idan bera na da sata to fa bahaushe ya ce laifin daddawane,dan kuwa itama tana da wari,da bamu barki sakaka babu tarbiyya ba,da haka bata faru ba,sannan da bamu rufe ido muna ta karb'ar abun hannun ki ba tabbas da bamu kawo wa yau ba,dan haka na yafe miki da zuciya ɗaya,ban riƙe ki da komai a raina ba sai alkhairi,ki yi shiru ki dena kukan haka ya isa."
Nan take Billy ta sake ɓarkewa da wani sabon kukan da ke nuni da farin cikin da take ciki, cikin tsananin murna ta ajiye wayar ta yi sujjada ga Allah tana gode masa kafin ta sake ɗaukar wayar ta ce,
"Hello Baba kana...ji...na?"
"Ina jin ki Bilkin Baba duk murna ce haka?"
Dariya ta saki hawaye na zuba a kuncin ta sannan ta ce,
"Baba a yau na haƙura da Man tinda iyayen shi sun ce ba zai aure ni ba saboda ni lalatacciya ce,iyakar yafe min da ka yi ta wanke min baƙin cikin rasa shi da na yi, alhamdulillah na godewa Allah Baba,yanda ka yafe min Allah ubangiji ya gafarta min ya yi min afuwar zunubai na."
"Amin Bilki,ina Anam ɗin take yau bata ce a gaishe ni ba? Ki kwantar da hankalin ki,duk inda mijin ki yake zai zo har inda kike ya same ki,ko kuma ke kije ki same shi."
"Humm Anam fushi take yi dani Baba,saboda ina kuka akan dangin Man sun ce ba zai aure ni ba."
"Subhanallah fushi kuma? Ko da yake ai dole ta yi fushi dake,dan kuwa a duniyar nan kowa yana aikata zunubi,wanda Allah yafi so shine wanda idan ya aikata ya gane ya yi kuskure ya gyara,sannan ya tuba ga Allah,dan haka ki rabu da su tinda ba kwaɗanta shi za su yi ba su cinye,Allah zai kawo maki wanda ya fishi albarka kin ji?"
Godiya Billy ta yi sosai kafin ta tashi ta je har ɗakin da Any take,tana zuwa ta ƙwanƙwasa ta miƙa mata wayar,nan take ta washe baki suka gaisa da Baba mai Dusa kafin daga baya ya basu Ta Annabi su kafa sabuwar hira,sun jima sosai suna hira irin ta sabo da shaƙuwa tsakanin uwa da ƴar ta kafin daga baya su yi sallama.
Da dare bayan Billy da Any sun yi wanka sun sha gayu da dogayen abaya sun buɗe shago suna zaune ana ta ciniki,sai ga Man ya zo a hargitse kamar wanda aka koro,cike da murna ya fara rawa a gaban Billy,kallon shi kawai suke yi ita da Any suna jiran su ji ƙarin bayanin murnar da yake yi,hamdala ya yi sannan ya ce,
"Alhamdulillahi Baby you are going to be my wife very soon ishaa Allah,ai nake faɗa maki na kasa jure tsaurin da Daddy ƙarami ya ɗauka akan maganar nan,ina tashi tin safe na wuce hisbah, acan aka kira su dika aka dinga yi musu nasiha da nuna masu illar guje maki da za su yi,sannan nima na zauna na tonawa kaina asiri a gaban su,Aunty na ta Abuja har suma tayi da ta ji abubuwan da nake aikatawa a baya, saboda su a cewar su kullum a mutumin kirki suke ɗauka ta,anan ne ake nuna masu da mace da namiji idan suka aikata zunubi iri ɗaya,matsawar sun balaga,hukuncin su ɗaya,mu mutane ne ke ware laifin namiji a koda yaushe,a ce dik abinda ya yi ado ne,ita kuma mace ita ce mai laifi koda kuwa sau ɗaya ta aikata zunubin,bayan doguwar nasiha suka yanke jibi za su je ƙauyen ku a nema min auren ki wataƙila ma idan muka samu yanda muke so a ranar za a ɗaura mana aure."
Tsallen murna Any da Billy suka saka,daga baya kuma Billy sai ta fashe da kukan farin ciki,Any lallashin ta ta hau yi tana yi mata video tana faɗin,
"Yau ranar farin ciki ce dole na ajiye video nan dan tarihi,Allah ya sanya alkhairi ya sa albarka,Allah ya nuna mana ranar auren ku da rai da lafiya."
"Amin Anam,Allah kema ya dube ki da idanun rahamar shi ya kawo maki miji na gari."
"Amin ya Allah.
Da haka suka zauna suka dinga hira,ƙarfe goma na yi Man ya yi musu sallama suka rufe shago suka tafi gida cike da farin ciki.
Bayan kwana biyu iyayen Man suka shirya cikin shiga ta alfarma kasancewar shi cikin zuri'ar manya masu hannu da shuni,motoci biyar ne masu tsada suka tafi nemawa Man auren Billy,motar Man ce ke gaba kasancewar shi yasan waje,dan haka sai suka sanya shi ya zamo musu ɗan jagora.
Tin kafin su isa Billy ta sanar da iyayen ta,har ta ce zata tura kud'in da za a tarbe su da kyau, faɗa sosai Ta Annabi ta yi mata akan hakan, sannan ta ce a baya ma son zuciya ne da mutuwar zuciya ya sanya su karɓa abun hannun ta,dan haka kar ta sake yi musu irin haka. Haƙuri Billy ta bata ta kashe waya jikin ta na ta mazari tsabar murna,sai kaiwa da komowa take yi tana tinanin ya abubuwa ke wakana a can,Any kuwa sai dariya take yi mata kafin daga ƙarshe Man ya kira Billy yana murna ya sanar da ita iyayen ta sun bashi ita, su kuwa sun bayar da kuɗin sadaki Mahaifin Billy ya kirawo ƙannen shi da yayun shi biyu aka daura auren. Sakin wayar Billy tayi a gado ta yi sujjada tana yi wa Allah godiya, ko da ta ɗago ma bata bi ta kan wayar ba,hannayen ta kawai ta daka tana ta zabgawa Allah kirari da godiya,bata sauke hannayen ta ba har sai da ta ji babu wasu kalamai da suka rage a bakin ta sannan ta zauna jiki a sanyaye,Any kuwa dik abinnan da Billy ke yi ashe tana tsaye tana yi mata video,sai da ta gama ɗaukan ta sannan ta ajiye wayar ta tafi da gudu suka rungume juna suna murna,hamdala suka dinga yi tare da fatan samun zaman lafiya.
*****************************
Kwanan mommy goma sha ɗaya a gidan Malam gaba ɗaya ta sauya,ta rame ta yi duhu sosai saboda wahala,idanun ta sun yi ciki sosai haƙoran ta sun bayyana a waje fiye da da,nan da nan Sweet H ta koma Hadizan Ɗan Liti ta ƙauyen Ba Mugu,banda hips ɗin ta na da cika sosai tabbas da babu abinda zai hana su zubewa.
Tsugunne take gaban Malam tana hawaye,cikin dakewa ya ce,
"Ki fa daina roƙo na dan ba amince maki zan yi ki je gidan tsofaffin surukan ki ki ga ɗan ki ba,idan su suna da hankali ai sun san inda uwar ɗan take ko? Me zai hana su kawo maki shi? Sai ke ce zaki ce zaki wani je gidan su? Hadiza kina neman ki dinga karya min dokokin da na gindaya a gida na,bana so,ina faɗa maki bana so."
"Dan Allah Baban Bukari ka bari na je,na yi maka alƙawarin ko awa ɗaya ba zan cika ba zan dawo,kewar ɗana zata yi ajali na,ka tausaya min ka duba ka ga yanda na koma a gidan ka,na yi zaton tausayi na ne ya sa ka kawo shawarar nan ashe kai muradin ka akai na daban?"
"Ke dallah rufe min baki ya ishe ki haka ! Kin san asarar da na tafka kuwa tinda na aure ki? Idan ba ma tsananin tausaya makin da na yi ba ai da ba zan aure ki ba ina ji ina gani babu tauraron arziƙi ko ɗaya a tsakanin mu,ke ba haihuwa zan dake ba,ke ba kuɗi zan samu ta dalilin aure na da ke ba, gaba ɗaya babu wani haske sai duhu da asara shine zaki zo kina faɗa min maganar banza anan,tashi ki ɓace min da gani kafin na wulaƙanta ki."
Cikin kuka Mommy ta mike zata fita, da kallo ya bita yana jan tsaki,dole ma ya gaggauta rabuwa da ita dan kuwa babu wani arziƙi a cikin auren su da zai sa ya ci gaba da riƙon ta,jikin nata da yake kwad'ayi ya duba ƙasa ya gano idan ya ci gaba da mu'amala da ita zai ci gaba da tabka asara kala-kala a dukiyar shi,dan haka tinda ya kusance ta sau ɗaya yana ji yana gani tana gilmawa ta gaban shi bashi da halin bin ta.
Ko da ta koma ɗakin ta gado ta faɗa ta hau rusa kuka iya ƙarfin ta,nadama da data sani babu wanda bata yi shi ba a wannan lokacin,ji take yi kamar ta fito da zuciyar ta ta manna mata ƙanƙara ko zata dena zafin da take yi mata,rashin hankali da rashin sanin ciwon kai ya ja ta yakice yaro ta yaye shi a lokacin da yake da buƙatar ta,gashi yanzu soyayyar shi da tausayin shi na neman illata ta,tinda ta ji Innah Laminde ta karɓe shi kuwa nutsuwa ta ƙaura daga gare ta,tabbas idan har suka ƙarbe shi ta san ba za a sake bata riƙon shi ba,dan kuwa ta san a yanda Innah Laminde ta tsane ta ba zata so jikan ta ya zauna a hannun ta ba balle ya yi agolanci a wani gidan.
Tana tsaka da kukan ta Mero ta shiga da garin masara a wata shirgegiyar ƙwarya tana wani taunar chewing gum kamar irin karuwan lagos ɗin nan,dire ƙwaryar ta yi a tsakar ɗakin Mommy ta na yatsina ta ce,
"To akoke sai a fito a ɗora sanwa tinda ba a kan ki aka fara haihuwa ba,yo ɗa ɗaya ma wata tsiyar ce har da zaki cika mana gida da ihu se kace kin haifi taron idi?"
Kafin ta juya ta bar ɗakin Mommy ta yi sufa ta dira akan ƙwaryar garin ta hau tsalle,gari na ta tashi sama yana zubewa a ƙasa,daga ƙarshe ta duƙa ta ɗauki ƙwaryar ta yi wurgi da ita a tsakar gidan ta rarumi Mero ta damfara ta da kasa ta haye ruwan cikin ta,Malam na sanya takalmin shi daga ƙofar ɗakin Meron ya ga an wurgo ƙwaryar gari waje ta zube,ihun Mommy kuwa shi ne ya sanya shi fitowa daga ɗakin tin farko,dan haka bai tsaya ƙarasa sanya takalmin ba ya bazamo d'akin Mommy dake ta dukan Mero har da cire mata kitson ta guda ɗaya da ya tsufa ya ci duniya,kuka Mero take yi tana kiran Allah ya isar mata a je a taimake ta,amma babu mai karfin guiwar isa ɗakin mommy,Tsahare ce ta riga Malam isa ɗakin ta yi kan Mommy ta na faɗin,
"Subhanallahi Amarya me yake faruwa haka? Yi hakuri ba halin ki bane wannan,idan kika daka ta rashin kunyar Mero kullum sai kun yi hayaniya a gidan nan,shi yasa basu ga maciji da Asabe."
Cikin haki Mommy ta ce,
"Ni illata ta zan yi idan tace zata shiga gona ta,yanzu ma ba zan barta ba sai na shata mata billen da Malam be taɓa yi mata ba dik dake-daken shi."
Juyi Mommy ta yi ta warto wuƙar dake hannun Tsahare,dik warin albasa ke tashi a jikin wuƙar,albasa take yankawa za ta yi wa Malam farfesu ta ji ana rikitiɓar faɗan ta shiga,a guje Malam ya karasa ya amshe wuƙar ya wurgar a waje sannan ya fizge Mero da ta sha shaƙa a hannun Mommy,banda tari da numfashi babu abinda Mero ke yi,Mommy kuwa sake kai mata duka take yi amma Malam na tarewa,ganin faɗan ya ƙi rabuwa ne ya sanya shi hantsila Mero waje ya riƙe Mommy ya wurga ta saman gadon ta,kuka ta fashe da shi tana so ta yi masa bayanin abinda ya faru,cikin fushi da ɓacin rai ya ce,
"Bana son na ji komai,haka kawai ina tare da Mero taurarin mu sun haɗu ina samun arziƙi ta dalilin ta kizo ki nakasa min ita, bayan ke ba tauraruwar arziƙi na bace,Hadiza ki tattara naki ya naki na sake ki saki biyu,ba zan iya ci gaba da zama da ƴar ta'adda me faɗa da wuƙa ba,dama haka kike? Haka kike haukacewa idan ana faɗa dake? Haka kawai ina zaune watarana na ɓata maki rai nima ki hallaka ni irin yanda kika yi wa tsohon mijin ki? To ba zai yiwu ba,maza ki tattara ki bar min gida kin yi iddar a ɗakin tsohuwar ki."
Mommy rasa me zata yi ta yi,shin murna zata yi an sake ta ko baƙin ciki zata yi,tinda ta riga da ta sanyawa ranta zata yi haƙuri ta zauna tayi zaman aure a gidan Malam tsakanin ta da Allah,yanzu
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 62 Chapter of 70