social media idan ban amince mata ba,"
"Ban gane idan baki amince mata ba? Ki amince mata ayi me?"
Buɗe ƙofa mommy tayi ta fita ta zauna a gefen gado tace,
"Billy na so na, ko ince tana sha'awa ta, ta jima tana so na amince mata mu keb'e na ƙi, to shine yanzu take bani tsoro da videos da hotuna na akan idan ban saka rana na amince mata mun keb'e ba zata watsa ni a duniya,"
"Innalillahi wa inna'ilaihirraji'una, what ! Kina nufin ku aikata mad'igo fa kenan? Kin taɓa yi ne?"
Cikin sauri Mommy tace,
"Haram, ban taɓa aikata mad'igo ba,wannan dalilin ne ma yasa muka dinga samun saɓani da ita Billyn, ta neme ni na ƙi amincewa,"
"Kar ki damu, Allah ya kaimu gobe zan ji da komai, yanzu ki tashi kiyo alwala mu gabatar da nafila, na fara jin yunwa akwai abinci a kitchen da Sultan ya ajiye mana sai mu ci, ko bakya jin yunwa?"
Cikin sauri Mommy tace,
"Kaiii ina ji mana sosai ma"
"Da kyau amarya ta, maza shiga kiyi alwala bari nazo,"
Tana faɗawa band'aki ya fita ya zauna a parlour tare da tallabe kan shi ya zabga tagumi,yanzu shikenan ya auri macen da ta gama rayuwa da wasu? Shikenan Bilal da Sultan da mutanen da bai san adadin su ba sun gama gane masa jikin matar shi,gashi kuma yanzu bai san iya ina videos da pictures ɗin ta zai tsaya ba.
Wani irin ƙunci yake ji a cikin ran shi da rad'ad'i,tabbas ya aikata mummunan kuskure na lalata yaran mutane da yayi a baya,wasu yaran ma makaranta aka aiko su suyi amma haka ya dinga amfani da kyan shi da kud'in shi ya ja ra'ayin su har sai da suka amince masa suka aikata masha'a,wasu kuma dama can sun baro gidajen iyayen su da nufin zaman kan su ba shi ya fara lalata da su ba,ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi sannan ya miqe yace,
"Tabbas dik abinda bawa ya shuka sai ya girbe shi, ko a duniya ko a lahira, na godewa Allah da abun ya tsaya akai na, Allah ka kare min zuri'a ta da ƙanne na mata, Allah ka basu mazaje na gari ba iri na ba, Allah kasa daga wannan darasin ya zama mun kiyaye gaba dani da ita kanta Hadizar, yanzu na riga na gane cewar da na aikata zina gwara na ƙara aure,"
Wata iriyar fad'uwar gaba ce ta riske shi a lokacin da ya tuna da alƙawarin da yayi wa Mommy, kallon hanyar d'akin nata yayi sannan ya sake furta,
"Allah ka shiga dikkan lamura na,"
Motsin Mommy yaji daga bayan shi ta fito sanye da wata arniyar rigar bacci mai santsi iya cinyoyin ta sutum-sutum masu laushi da ɗaukan idanu,cinyoyin da mata da yawa suke biyan miliyoyin kuɗi dan a yi musu dashen irin ta,gashin ta da ya sha wanki ta tattare a tsakiyar kanta sannan ta nufe shi sai baza qamshi take yi,Abdul na ganin haka ya washe baki, dan kuwa abun nema ne ya samu, dik da yana jin yunwa ba zai bari wannan damar ta wuce shi ba,har ya tunkare ta ya tuna da ko nafila da addu'ar da ake yiwa amarya bai yi ba dan haka sai ya ci burki yana nazari, wannan fa aure yayi ba bariki ba, da sauri ya kauda kan shi ya juya ya wuce kitchen, Mommy kuwa tsayawa tayi dindiris kamar an dasa ta a wajen me hakan ke nufi? dik sai taji guiwar ta ta sage kunya ta kama ta( dama in ba dan sabo da bariki ba amarya a daren farko ina ita ina irin wannan abun?) a hankali ta juya ta koma ɗakin ta ta samu abayar ta ta zira a saman kayan ta ta zauna a bakin gado tana hawaye, da ta san haka zai yi mata da bata zubar da ajin ta ba, ai a zaton ta ya waye haka shine ya dace suyi a daren su na farko.
Ko da Abdussabour ya dawo d'akin ɗauke da leda mai layi layi sai plates da cups tare da ruwan sha roba biyu ya ganta zaune tana hawaye, sai ya ajiye kayan hannun shi a gaban ta sannan ya miqa mata hannu alamar ta sauka taje gare shi, cikin tura baki ta kama hannun nashi ta zauna tana shagwab'a,murmushi yayi sannan yace,
"Haba amaryata fushin fari ai ba naki bane ko? Ai bana so mu fara abinda zamu tsaya bamu cimma burin mu ba shi yasa kika ga na gudu,ina so mu ci mu ƙoshi sannan muyi nafila mu godewa Allah sai kuma koma mai zai faru ha biyo baya ko?"
"Hakane kuma, na zaci ko ƙyamata kake yi,"
Da sauri ya kama fuskar ta ya ƙurawa fuskar tata idanu yace,
"Habaa ƙyama kuma? Bari ki ga mu ci abinci na nuna maki wani abu."
Murmushi suka yi a tare sannan suka hau cin abincin su,sai da suka ci suka ƙoshi sannan Abdul ya koma ɗakin da yake mallakin shi ne ya watsa ruwa a gaggauce yayi alwala sannan ya sanya jallabiyya mai haɗe da wandon ta ya sanya turaruka masu ƙamshi ya wuce d'akin ta, zaune ya ganta saman abun sallah da alama tayi alwala ma, sai kawai ya shiga gaba ya tada sallah.
Tinda suka fara basu tsaya ba saida suka yi raka'a biyun nan da ake yi, sannan Abdul ya yi wa Mommy addu'a ya ja ta ya hau cire mata mayafin jallabiyyar ta, Mommy na ganin haka kuwa bata yi ƙasa a guiwa ba wajen miƙewa ta kashe fitilar d'akin ta fara karantawa Abdul haddar da ta kwaso a gidan Hajiya K'waisa.
Washegari da safe haka suka farka a gajiye da misalin bakwai na safe, a gurguje Abdul ya miqe ya shiga band'aki dan ya tsarkake jikin shi, Mommy na lalubawa taji baya nan sai ta miƙe ta bi bayan shi,nan ma bata bar su sun fito sun yi sallar asuba ba sai da suka b'ata lokaci.
Abdul ne ya ja su sallah suna idarwa ya miqe yaje d'akin shi ya ɗakko wayar shi yana ta zabga murmushi saboda nishad'in da ya samu a daren jiya da kuma safiyar yau din,yana duba wayar sai yaga missed calls ɗin Innah Laminde dana Bilal da Sultan sai Sudaif wani cousin ɗin su ta bangaren mahaifin su,cikin sauri ya kirawo Innah, cike da ladabi ya gaishe ta ta amsa, sannan tace masa,
'Sarauta ina son da dare misalin takwas na dare ka kawo min matar ka akwai tambayar danake so nayi mata,'
Shiru ya d'anyi kafin yace,
"To Innah Allah yasa dai lafiya,"
Muryar ta ta saki kamar babu wata matsala sannan tace masa,
'Babu komai Babana kai dai Allah ya kaimu kuzo ɗin kaji koma menene, a gaishe ta,'
"Za ta ji na gode, sai mun zo ɗin,"
Bayan yayi sallama da mahaifiyar shi ne ya kirawo Bilal da Sultan da Sudaif, dika gaisuwa ce sai tsokana da ya samu daga wajen Bilal, gaba ɗayan su haushin su ma yake ki yanzu dan sun gane masa matar shi babu kaya,a gaggauce ya gama wayar da su ya koma d'akin Mommy, samun ta yayi zaune tana waya da Sule,zama yayi a gefen ta yana sunsunar ta yana lumshe idanu.
"....eh dan Allah ka d'akko min dika ka kawo min yanzu, idan yaso in kazo zan baka sai aje a siyo mata masu kyau a je a ajera mata itama a kaita d'akin ta.....tom sai ka zo,"
Tana kammala wayar ta ajiye ta kwanta a jikin Abdul tana yi masa kukan shagwab'a,
"Yah Abdul yunwa nake jii,"
"Ni kaina yunwar nake ji, da zan samu ƙari da na so,"
Ture shi tayi a jikin ta tana dariya ta fita daga d'akin da gudu ya bi bayan ta yana dariya, haka suka yi ta zagaye parlourn suna dariya har yayi nasarar kama ta suka zube a kujera,cikin maida numfashi da sauri da sauri tace,
"Da gaske fa yunwa nake ji, har wani jiri jiri nake ji,"
"Kina jin jiri kika wahal dani? Anyway babu komai Sultan zai kawo mana abinci yanzun nan, dan Allah ina son yi maki wata magana Sweety.."
Cikin sauri Mommy ta b'ata rai ta kalle shi tace,
"Ka kira ni da kowanne suna amma banda wannan bana so,"
Mamakin b'ata ran nata ne ya kama shi, amma sai ya danne ya ce,
"To baby yayi maki?"
Murmushi tayi ta narke a jikin shi tace,
"Eh yayi min Babyna,"
"Tooo gidan baby da baby kenan ko?"
D'aga kai tayi tana dariya,ci gaba da magana yayi yace,
"Na roqe ki dan Allah kar hanya ta haɗa ki da Sultan ki tsaya gaisawa da shi ko Bilal, ni yanzu dik haushin su ma nake ji, ita kuma waccan mara kunyar zan sa a nemo ta dan na karb'i duk wani abu naki dake wajen ta gudun kar ta yi min b'arna,"
"Inshaa Allahu haka ma baza ta samu ba, ai shege shi yasan makwancin shege, na san maganin ta ka barni da ita"
"Ah ah fa, bana son ki sake involving kan ki cikin rayuwar ta,"
"Ko ɗaya,inshaa Allahu Hadiza ta gama shashanci Yah Abdul, amma dole ne sai na ɗana mata tarko kafin na kama ta ko?"
"Haka ne kuma,"
Suna nan zaune suna ta hira sultan ya zo kawo abinci, Mommy ta shiga d'aki har ya tafi basu haɗu ba, sai da ya wuce ne ta fita suka zauna suka ci suka sha.
Da rana bayan Abdul ya fita gidan su gaida iyayen shi, Sule ya je ya kai mata kayan ta, ita kuwa ta buɗe ta ɗakko ATM card ɗin ta ta sanar da Sule pin ɗin ta tace yayi amfani dashi a sai wa Ameerah kayan d'aki a yi mata jere na kece raini, kar ya sake ya baiwa kowa nera a hannu Ameerah kawai take so a yi wa kayan d'aki mai kyau, dan tasan halin Innoh da kud'in nan sun shiga hannun ta shikenan ba lallai ayi abinda ya dace ba.
Sule bai bar gidan ba sai da yaci ya sha ya qoshi sannan ya tafi gida dan isar da saƙon Hajiya Hadiza.
************************
Ihun murna mata da mazan dake tsaye a cikin wani madaidaicin gida ke tayi kamar qananan yara, Billy ce jingine da wata mota mai shegen kyau da tsada kalar maroon sai walqiya da ɗaukan idanu take yi,hotuna kawai ake zabga mata da video,nan da nan social media ta ɗauka ana haska ta, YouTube channels kala kala kuwa na bayyana shahararriyar 'yar TikTok ta samu kyautar gida da mota daga boyayyen saurayin ta.
Wasu irin matsattsun riga da wando ne farare tass a jikin ta, sai makeup da aka tsara mata da ya fitar da kyawun ta,ga wani uban kitson da aka yi mata har yana tab'o mazaunan ta, wayar ta mai tsada ta buɗe a kwali tana nuna wa sabbin ƙawayen ta da kuma tsoffin ƙawayen ta na TikTok, ihu wajen ya sake ɗauka da shi ana kyasce ta da hotuna da ɗaukan sabbin Videos ana watsawa a social media.
Drinks da kaji matasa ke ta d'iba suna guziri dashi a lokacin da taro ya tashi za su tafi gidajen su,da misalin qarfe sha biyu da rabi kuwa kowa ya watse an bar gidan babu kowa daga Billy sai halin ta, a dai-dai wannan lokacin kuwa da kowa ya tafi sai ta samu ta rufe ko ina na gidan ta kunna kiɗa ta fito da kayan shaye-shayen ta ta baje su a gaban ta tana kallon su, wani irin farin ciki take ji mara misaltuwa, da ta san haka rayuwar 'yanci take da daɗi ai da ta jima da barin Hajiya K'waisa ta sa Man ya sai mata gida,amma yanzu ma lokaci be ƙure mata ba ai zata shana ta wataya ta ji daɗin rayuwar ta tinda iyayen da suka haife ta sun gaza wajen wadata ta da abubuwan more rayuwar duniya.
Har ta zauna ta d'aga kwalbar Syrup zata kwankwad'e wayar ta ta fara ringing,kallon No ta sake yi da kyau dan ta tabbatar shin da gaske ita me wannan No ke kira ko kuma gizo idanun ta keyi mata?......................
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 50:
Ɗaukan wayar tayi ta kara ta a kunnen ta sannan tace,
"Uhummm lafiya kike kira na a wannan daren?"
Daga can ɓangaren ne aka yi dariya da wata siririyar murya, kafin daga bisani mai kiran wayar ta furta,
'Lafiya ƙalou Billisious 'Yar sanata masu nerori gida da mota hajji duk sati, na ji irin abun alkhairin da ya same ki ne ya sanya ni zuwa har gidan naki na taya ki murna amma ina ga kamar nayi latti bari na juya..."
Cikin hanzari Billy tace,
"Noo baki yi latti ba, bari nazo na buɗe miki gate ɗin,"
'Ok ina jiran ki a waje,ina fatan gidan naki zai iya ɗaukan mota uku dan baby na a matsayin mota biyu take,'
"Har huɗu ma filin gidan nan zai iya ɗauka dan haka ki jira ni kawai,"
Koda Billy ta fita waje sai taci karo da wata hamshaqiyar motar da ta dame tata ta shanye,wata siririyar mace ce fara fat mai kyau a cikin motar, sai da ta samu wajen yin parking sannan ta yi ta fito tana kulle motar hannun ta riƙe da manyan wayoyi 'yan yayi, jaka ce mai tsadar gaske rataye a kafad'ar ta,ƙafafun ta kuwa sun coge a saman takalmi mai tsananin tsinin da ta sanya musu,gashin dokin dake kanta ta gyara ya kauce daga fuskar ta ta fara taku cikin yanga ta isa wajen Billy dake ƙare mata kallo, siririyar matar na isa gaban Billy sai ta rungume ta tsam a jikin ta cikin wani irin salo na 'yan bariki, jikin Billy ne ya karb'i saƙon da aka aika masa dashi dan kuwa kar ta san kar ce a tsakanin su, nan take ta rintse idon ta saboda bata so ta saki jikin ta da matar daga baya azo ana samun saɓani.
Ciki Billy ta ja matar suka shiga, banda kallon parlourn babu abinda matar keyi,a tsakiyar parlourn ta cire takalmin ta da ya dami ƙafafun ta da ciwo, sannan ta ajiye wayoyin ta da makullin motar ta tare da jakar ta a saman center table na glass dake tsakiyar parloun,zama tayi ta shafa cinyoyin ta dake waje da siraran hannayen ta da suka sha dogayen farata sannan ta harɗe ƙafafun ta waje ɗaya taa wani kwarkwasa,sake maida gashin ta baya tayi kafin cikin yanga ta karb'i glass cup ɗin da Billy ta zubo mata shampain a ciki ta miqa mata,baki ta yatsina sannan tace,
"Thank you, and congratulations 'yar uwa, kema da alama kan mage ya waye kin gane zaman kan ki ba tare da kin jingina da kowa ba ya fiye maki,na yi matuƙar mamaki da naji su Sally na maganar wai kun ɓata da K'waisan alheri kema kin kafu har ma ta nuna min gida da motar da aka yi maki kyautar su, to kin dai gani ko? Taya zaka zauna kana neman kuɗi da jikin ka amma ace sai ka raba da wani ƙaton da shima neman nakan shi yake yi? Yaci naka ya ci nashi duk shi ɗaya, ina taya ki murna da samun 'yancin kai sister,"
Cikin murmushi Billy tace,
"Lallai sai yanzu na gane dalilin ki na barin gidan Hajiya K'waisa Amy,amma dik da haka ba zan fasa faɗa maki gaskiya ba, ta yanda kika bar gidan be kamata ba saboda ko babu komai ya taimaka maki a rayuwa,ni kin ganni nan, garin mu suka je su taya ni faɗa aka rarako su yaji haushi ya kore ni, na tabbata da an kwana biyu naje na marairaice zai hakura, iyaka dai ba zan sake zama a ƙarƙashin shi bane kawai,"
Murmushin gefen baki wadda aka kira da Army tayi sannan tace,
"Uhumm ku kuka sani, ni dai na zama free daga cutarwar da ake yi min, ni nasan maƙudan milliyoyin da gardin nan yaci min,wataƙila bai taɓa sanar dake bane saboda kar a ga laifin shi,Allah dai ya kyauta, gaskiya gidan ki yayi kyau ba ƙarya,nima zan so na kai ki nawa ki gani watarana,ban ma jima da komawa cikin shi ba, tsohon sai na barwa ƙani na da yayi aure last 2 months,"
"Woww ! lallai kina wuta Amy,Allah ya kaimu watarana a nuna min gidan, ai ina jin yanda ake maganar gidan ki rannan a wani live da na hau na Sally,"
"Hummm ke ni fa bana son ƙaramar harka da kika ganni nan, dan kuwa yanzu ba safai ma nake harkoki da mutanen Africa ba, nafi son inda zan tsallaka masu jajayen kunne mata ko maza su biya ni da dollars,"
Ihu sosai Billy tayi ta jijjiga shampain ɗin hannun ta ta d'aga sama kumfa ta zube,miƙewa Amy tayi suka hau taka rawa suna shan shampain suna haɗawa da kayan maye,kayan cajin na fara faɗa masu gabas ta koma kallon kudu sai suka fara neman junan su kamar mayunwatan zakuna a daji,ina ganin haka nayi tir da wannan mummunar dabi'ar shaye-shaye da neman jinsi da ya shigo mana cikin al'ummar Annabi muhammad yaran musulmi suka maida shi ba komai ba,na bar gidan na koma gidan Mommy.
*****************************
Tinda suka dawo daga gidan Sarki Mommy ke kuka a jikin Abdul, yayi lallashin duniya taƙi shiru, sai ya samu ta rage sautin kukan sai ta sake fashewa da wani sabo,cikin muryar lallashi yace,
"Dan Allah Baby kiyi hakuri komai ai ya wuce ko? Bilal ɗin ma ya koma Kano yau kuma kin ga ban kyale shi ba sai da na yi masa tataa,sannan kin riga kin sanar dasu Innahta Billy bata gidan da kika santa a da dan kuwa da bakin ta ta sanar da ke bazata koma can ba sun kore ta to kukan na menene?"
Kallon shi tayi ta fyace majina da tissue sannan ta mele manyan leb'unan ta tace,
"Habaa baby...tayaya zaka ce bazan yi kuka ba bayan a gaban ka Innah ta gama kallo na tana harara ta tare da faɗa min baƙaƙen maganganun dake nuni da cewa bata so na ita da Umman Billy? Na tabbata sai an shiga rayuwar auren mu ba zamuyi rayuwar farin ciki ba ni da kai,shi kuma Bilal da har ya iya kallon ido na ya sanar dani baya so na baya ƙauna ta kara yake yi maka yaje na bar shi da Allah, Allah ya saka min,"
Kuka ta sake fashewa dashi ta kwanta a jikin Abdul ɗin da gaba ɗaya ya gaji da jin mitar ta, a hankali ya fara aika mata da saƙon da ya mantar da ita akan me ma take kukan,cikin sauri suka kashe fitila suka barni ina lalube a duhu ina neman hanyar fita.
Washegari da asuba Abdul ya tashi ya saisaita ruwan wanka ya ɗauki Mommy dake ta yi masa qananun mitar ya tashe ta tana tsaka da bacci ya je ya tsoma ta a kwamin wankan su, tana jin ta a ruwa ta buɗe ido ta hau kukan Shagwab'a, dariya yayi kawai ya shiga suka yi wanka tare kafin daga ƙarshe suka yi wankan tsarki suka fito daga band'akin.
Wajen kayan ta yaje ya ɗakko mata jallabiyya dan ya kula bata da hijabai sai dogayen riguna ya sanya mata ya bata d'ankwalin yace ta sanya dan bai iya ba, baya so ya tafi masallaci ya barta ta koma bacci shi yasa ya tsaya dan ya taya ta da kan shi.
Bai fita ba sai da ya ga ta tada kabbara sannan ya fita ya rufe gidan ya wuce masallaci, tana tabbatar da ya bar gidan ta cire kayan ta ta haye gado tana hamma, idanun ta har wani hawaye yake ji da yaji saboda baccin da take ji,cikin muryar bacci tace,
"Sallar nan fa koma nayi ta ance ba Karb'a za a yi ba tinda naje wajen mai duba,to ina dalilin wahal da gab'ob'i na bayan gajiyar da ka tara min jiya? Anjima idan na farka na haɗe su da azahar."
Baccin ta ta koma tasha dan kuwa da Abdul ya dawo ya ganta tana bacci shima sai ya cire rigar shi ya kwanta a bayan ta suka ci gaba da baccin tare.
**************************
Dik yanda Mommy taso Abdul ya bar ta taje a ƙarasa siyayyar kayan d'akin Ameerah ƙi yayi ya ajiye ta gidan su ya wuce nasu gidan dan gaida mahaifin shi, sanda tana sanar da Innoh abinda Abdul yayi mata sai Innoh tayi dariya tace,
"Ki kawo kuɗi anjima Naja ta koma maki wajen malam, ai an yi masa bita zai-zai ne shi yasa baya son kina yin nesa da shi, idan taje an sanar da malam ya dinga barin ki kina fita a sanda kike so ki koma a sanda kike so,dan idan aka sa maki ido abubuwa baza su na tafiya daidai ba."
"To ai shikenan bari Sule ya dawo min da ATM card d'ina,Innoh ina Baba ne? Ji nake yi kamar na jima ban gan shi ba,"
"Ai kuwa bai jima da fita ba ya shiga kasuwa sai dai muyi fatan Allah yasa a samu kasuwa mai albarka,kin san yanzu lamuran sun ƙara matsewa talaka na ganin rayuwa"
Da jin haka Mommy sarkin tausayi sai ta dakko jakar ta ta zaro dubu uku ta baiwa Innoh tace a ƙara a cefanen ranar,Ameerah kuwa tsaye tayi mata tace,
"Kin san dai har yanzu ban warke ba ciwon nan da ƙaiƙayi na nan na damu na,"
"Subhanallahi, to yanzu yanda za a yi Innoh ta sammana sabarar ta ki tafasa da kaninfari da ganyen bishiyar nim wato maina,wasu kuma su ce mata dogon yaro kiyi tsarki kuma ki sha kaɗan na tsawon sati daya zuwa biyu mu gani, ko an kai ki gidan ki ki dinga sa yana nemowa kuna sha ai magani ne,"
Cikin ikon Allah kuwa Ameerah na dafa maganin nan ta sanya gishiri kaɗan tayi tsarki sauƙin susar ya samu,kallon Mommy Ameerah tayi sannan tace,
"Ni fa Mommy ba zan yarda a kaini ɗakin miji babu lefe ba, yanda zamuyi musu kayan d'aki dole ne suma suyi min lefe ko babu yawa, idan babu lefen me zan d'aura idan na je gidan nasu har na yi masa kwalliyar da zata burge shi?"
"Haka ne kuma fa kema kin ce wani abu sister."
Haka suka dinga hirar su suna kitsa yanda za su sanar da shamsu suna jiran lefe kafin a kai masa ita ...................................[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA: HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 51:
Dik yanda Shamsu yaso Ameerah ta tare a cikin satin nan ƙi tayi, domin kuwa ta ƙeƙasa ƙasa tace dole sai yayi mata lefe kamar yanda ake yiwa kowacce mace lefe idan za a yi auren ta,hankalin shamsu ya tashi k'warai da jin wannan sabon lamarin da Ameerah ta tinkare shi da shi, cikin damuwa da tashin hankali ya wuce kasuwa shagon Baban su.
Sanda ya je ya tarar da mutane ana ta ciniki sai shima ya faɗa ya shiga karb'ar kuɗi yana ƙullawa mutane kalar dusar da suke son saye, ya kai azahar yana aiki bai samu damar keɓewa da mahaifin shi ba har sai da suka fito daga shagon domin gabatar da sallar azahar, anan ne ya matsa ya shiga cikin shagon ya sanar da Mahaifin shi abinda ke faruwa, murmushi yayi yace,
"Na san a rina wai an saci zanin mahaukaciya,banza bata kai zomo kasuwa,yau kaga amfanin abinda nake faɗa maka ko? Shamsu babu irin bin kan ka da banyi ba akan ka dinga biyo ni shagon nan muna aiki tare duk wata ko ƙarshen sati na dinga fitar da kai kamar yanda nake yiwa su Idi ka ce kai Allah ya kashe ka ba za ka saida dusa ba,ka kama waya ka riƙe ƙam kamar ran ka, kai ne danne danne kullum wai kana kiristo/crypto,ko ka ɗauki wanka ka fita da yamma ba zaka dawo gida ba sai dare ya raba, to faɗa min tinda ka fara kiriston nawa ka samu? Ai na san zai ishe ka haɗa lefe tinda an jima ana fama,dan haka babu abinda zan ce maka da ya wuce Allah bada sa'a,sai kaje ka samu babar ku ta haɗa maka dan ni ba sanin kan atampa ko lehyi nayi ba,"
Mahaifin su Shamsu na gama fad'in haka ya wuce shamsu da baƙin ciki da takaici suka cikawa zuciya,alwala yayi ya shimfiɗa buhu a bakin shagon shi ya kabbara sallah,sallah ce dai irin ta 'wasu yan kasuwan da basa natsuwa a cikin ta,wato ana yi ana nuni da hannu da ido da baki,wani lokacin ma sai ya kauda kan shi daga alƙiblah sai ya gama kallon abinda yake so ya kalla sai ya tafi ruku'u ko sujjada, raka'a huɗu yayi ya miƙe,gani yayi shamsu ya fita daga inda yake ya bar wajen,girgiza kai yayi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 33 Chapter of 70