shi cikin hawaye tana so tayi magana, cikin sauri Shamsu ya hau buɗe labulen ɗakin da window dan iska ta ratsa d'akin, muryar ta yaji tana faɗin,
"Anya shamsi kana so ka ga Annabin rahama kuwa?"
A mamakance ya juya ya kalle ta tare da kama ƙugu yana son jin me ya aikata me muni haka ake masa irin wannan maganar,cikin kuka tace,
"Yo ai dole na tambaye ka ko kana son ganin Annabin rahama shamsu, fisabillahi kana ganin halin da nake ciki kayi min alƙawarin kawo min abinda zan ci amma shiru,nan nan na fita wajen Ummah nace ta sammin abinci idan sun dafa amma haka ta hana ni wai me yasa ba zan rage son jiki ba na girka namu,ai kowacce mace a gidan mijin ta ita ke hidima dashi, ka fita daga ƙarƙashin ta dan haka ba abinda zata sammini,ina ji ina gani suka shige da abincin su d'aki ita da su Fadila yawu nata zuba min, ga yunwa ga ƙwadayi ina ji,yau ko zaman gidan haya muke da Ummah ai sai haka."
Majina ta sharce ta ƙyalla ido akan ledar hannun shi ta sake marairacewa dan ya yarda da maganganun ta,cikin ran shamsu sam bai ji daɗin abinda aka yi wa Ameerah ba,tinanin miƙa mata ledar hannun shi yayi dan taci naman ta ƙoshi,sai dai wata zuciyar na tuna masa tayaya zasu sa abu a gaba shi da matar shi su cinye ya hana mahaifiyar shi? A baya yana yo musu nasu ƙunshin amma Ameerah tayi kutun-kutun da kirsa da kisisina ta hana kuma sam bai fahimci makircin ta ba, yanzu ya koma siyo musu su kaɗai sai dai su ɗebar musu tana so shima ta hana da makirci.
Sassauta fuska Shamsu yayi ya zauna yace,
"Kiyi haƙuri,ni idan na samu ma yanda nake so barin gidan zamu yi,ko mu kama haya ko na fara gini a filin da Baba ya bani."
"Au da kana ma da fili shine baka taɓa faɗa min ba?"
"Yanzu ba gashi dalili yayi kin sani ba? Ina da fili ina da gona dik shekara ana ara ana noma a bani wani abu."
Shiruuu Ameerah tayi na ɗan wani lokaci, zuciyar ta na raya mata a yanzu ta miƙa wuya ɗari bisa ɗari zata yi zaman Aure da Shamsu da zuciya ɗaya tinda dai-dai gwargwado yana da kadara.
Hira Ameerah ta dinga jan shi da ita har suka cinye nama da gurasa ba tare da Shamsu ya kula ba,suna gamawa yace,
"Gaskiya dole ne kiyi wanka kafin mu kwanta,kin ji yanda kike tashi kuwa? Daurewa kawai nake ina cin abicin nan."
"Shamsu ba zaka gane halin da nake ciki bane,tinda cikin nan ba a jikin ka yake ba,ni ko warin sabulu bana so,bana son ƙamshin komai saboda yawan haraswa."
"Ikon Allah, to yanzu bari na jiƙa maki toka a ruwa na tace miki kiyi wankan da ita sai ki d'auraye jiki da ruwa me kyau idan kin gama."
"Ashe shamsu haka ka tsane ni ban sani ba? Wanka da toka se kace wata kifi?"
"To Ameerah ya kike so nayi ne dan Allah? Yanda fa kike jin haraswa idan kin shaƙi ƙamshi ni kuma ina jin haraswa idan na ji wannan ɗoyin na tashi."
Kuka sosai Ameerah ta fashe dashi ta tashi cikin fushi da borin kunya ta fita, zaune ta tarar da Ta Annabi ta cika tayi fammm, dan kuwa kusan dik abinda suka tattauna ta ji shi sarai a kunnen ta, kasancewar ƙofar su Ameerah buɗe take,ita kuma tinda shamsu ya dawo take zaune a wajen tana jiran a miƙo mata nata kason ta tanɗe ta koma ɗaki,cikin ɓata rai Ameerah ta wuce ta ɗauki bokiti ta d'ebi ruwa a rijiya ta ɗauki sabulun wanki ta shiga bayi, ita da kanta da ta zo cire rigar ta ta shaƙi warin hammatar da take yi sai da taji kamar zata yi amai,da sauri ta ƙarasa cirewa ta ja iska mai tsawo sannan ta hau wanka,tasss ta dirje jikin ta ta d'aura alwala ta koma ɗaki.
Kwance ta ga shamsu yana chatting, yana ganin ta yayi saurin kife wayar yana zare ido alamun rashin gaskiya sun bayyana,cike da mamaki tace,
"Yau kuma dan na kama ka kana kallon abun duniya shine ka tsorata? Bari nayi sallah nazo mu gani tare maye a ciki?"
Dariya tayi ta tada sallah, cikin abinda bai fi minti uku ba ta idar da magariba da isha'in da ta haɗe waje ɗaya, tana idarwa shamsu yayi saurin kashe data ya shiga wajen films ɗin da suka zame musu jiki wajen kallon su,sun jima suna kallo kafin daga baya su ajiye wayar su kashe fitila, tankad'a ni waje shamsu yayi ya rufe musu ƙofar su yace ɗaukan rahoton ya isa haka.
Bayan wata uku.............
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 69:
Fuskar shi mutuk yake d'aura agogon hannun shi tare da gyara zaman wuyan rigar shi a kafaɗun shi,cikin sauri ta fito sanye da atampa ɗinkin doguwar riga da hijabi iya guiwar ta,hannun ta riƙe yake da ƙaramar jaka,takalmin ta baƙi flat ta ƙarasa sanyawa ta kalle shi tace,
"Dan Allah ka kaini gidan Ummi na yi kewar su,"
Cikin wani irin yanayin da ta kasa fassarawa ya kalle ta yayi gaba, shiru tayi riƙe da jakarta ta turo baki gaba tace,
"In taho?"
Ɗan guntun tsaki ya ja kafin yace,
"Kiyi sauri kar ki ɓata min lokaci."
Da gudu tabi bayan shi tana murna, a zafafe ya kalle ta yace,
"Gudun na menene? Ohhh so kike kiyi gudu wani tsautsayin ya same ki ki samu abun da kike so ko? To ki buɗe kunnen ki da kyau kiji Saddiqa, akan cikin nan sai na soke komawar ki makaranta sokewa ta har abada,ai ba jahila bace ke balle kice rashin ilimi zai zame maki tawaya, wuce muje idan zaki je."
Hawaye ta fara zubarwa masu mugun zafi, cikin kuka ta kalle shi kamar zata yi magana, sai ta fasa,gaba tayi ya bi bayan ta ya kulle gidan, a jikin motar shi ya same ta tsaye tana sharar hawaye,tsananin tausayin tane ya kama shi, amma haka ya ɗauke kan shi ya shige motar shi ya tada ta, cikin sauri itama ta buɗe ta shiga ta zauna tana ci gaba da share hawaye,kallon ta yayi cikin sassauta murya ba dan ya dena fushin da yake yi ba yace,
"Ki dena yi min kuka tinda ba dukan ki nayi ba ko zagin ki,idan kuma kuka zaki yi na ajiye ki anjima na aiko a kai ki wajen su Anisan."
Da sauri ta hau goge hawayen ta tana bin shi da kallon mamaki,dama wai Munir ya iya fushi haka? Idan wani yace mata Munir ɗin ta zai yi fushi da ita har na tsawon kwana ɗaya ba zata yarda ba, wai sai gashi yau Munir ke fushi da ita har na tsawon sati guda currr babu ɗaga ƙafa,lallai dik wanda ya ɗauka a gidan aure soyayya kawai za a yi ta ci babu irin wannan tsarabe-tsaraben na rashin jituwa tsakanin ma'aurata to fa tabbas ya d'akkowa kan shi dala babu gammo.
Har suka isa gidan Ummi tana tunani bata san sun isa ba,mai gadi ne ya gaishe ta sannan ta yi saurin fitowa daga duniyar da ta lula ta kalle shi tana sake gaida shi cikin girmamawa, a parking space ya ajiye motar tashi ya kashe yayi ficewar shi ba tare da ya jira ta fito ba,jiki babu ƙwari ta buɗe ɓangaren da take ciki ta fita tabi bayan shi.
Zaune ta ganshi yana gaishe da Ummi su Anisa na gaida shi, kallon Saddiqa Ummi tayi tana murmushi tace,
"Oyoyo oyoyo mu daughter,wa ya taɓa min ke ne na gan ki haka kamar kin yi kuka?"
Saddiqa na jin haka ta ɓare baki tin ƙarfin ta tana kuka irin na shagwab'ar nan da bata san ta iya shi bama ta tafi da sauri ta faɗa jikin Ummi,baki Munir ya sake yana binta da kallo dan ya kula so take ta ƙulla masa wata ƙullakiyar, cikin sauri Ummi da su Anisah suka tare ta suka kama ta suka zaunar da ita a kujerar da Ummi ta tashi akai suna tambayar ta lafiya take kuka?
Ummi ce ta ga Munir na sanɗa zai bar parlourn cikin haɗe fuska tace,
"Zo nan Munir ! Ina zaka je? Me kayi mata take cikin damuwa bayan kasan condition ɗin da take ciki bata buƙatar damuwa?"
Sosa kai yayi ya koma da baya ya coge a jikin kujera bai ce komai ba, shi fa bai so abun ya kai haka ba, so yayi ya ɗan hora ta ta yanda gobe baza ta sake nuna tafi son karatun boko sama da haihuwa dashi ba,sai gashi yarinyar ta kasa jure ɗan fushin da yake yi tana neman ja masa faɗa wajen Ummi dake da mita.
Cikin kuka suka ji Saddiqa na faɗin,
"Ummi ki bashi haƙuri yayi fushi dani sosai,ya dena yin hira dani komai nayi faɗa yake yi min,ko nayi dai-dai ko banyi dai-dai ba faɗa yake yi min."
Kama ƙugu Ummi tayi tana binshi da kallo, Anisah ma kallon shi take tana tura baki tare da lallashin Saddiqa,zama yayi yana hararar Saddiqa yace,
"Ai sai ki sanar da ita me kika yi last week ko?"
Sunne kai tayi ƙasa tana marairacewa,yana ganin haka ya saki murmushi sannan yace,
"Ummi gata nan ta faɗa maki me tayi da kanta, idan kuma baza ki iya ba bari ni na sawwaƙe maki jin kunya,cewa tayi bata son haɗa zuri'a dani."
Cikin sauri Saddiqa ta kyab'e baki tana kuka tana shura ƙafa dan kuwa yayi mata ƙarya ita ba haka suka yi ba, mamaki ne ya kama Ummi ta maida kallon ta kan Saddiqa da alamar tambaya a kan fuskar ta,da sauri Saddiqa tace
"Ummi ba fa haka muka yi dashi ba,shine fa yayi min alƙawarin zan ci gaba da karatu Ummi, kawai wai daga kaini asibiti last week suka ce wai ina da...uhummm..inaa da....uhummm wai ciki gare ni...kuma Ummi shi yace zai kaini makaranta, shikenan wai dan nayi kuka nace ina alƙawarin da yayi min to shine yake ta min faɗa har da ture ni ƙasa na faɗiiiiii."
Ta ƙarasa maganar ta tana rushewa da kuka, murmushi Ummi tayi sannan tace,
"To ai Saddiqa tin wata biyu da suka gabata na san kina ɗauke da juna biyu, shi yasa kika ga na ninka kulawar da nake baki, kune dai baku gane hakan ba kasancewar dikan ku baku da experience akai,kai kuma menene abun yin fushi har haka? Ai is normal ta nuna ɓacin ran ta kai kuma sai ka lallashe ta ka bata baki, tinda koni dama ba zan so ta fara zuwa makaranta ba tare da ta yi haihuwa ko guda ɗaya bace duba da irin karatun da take so tayi,idan kika yi haihuwa ɗaya sai kuje asibiti a duba tsarin iyali mara cutarwa sai ku fara yin shi,ni a gani na hakan shine zai fi muku, kai koda amfani da condom ne ya kama kuyi sai kuyi,saboda dai ku samu maslaha,yaro ko yarinya ko yara idan an haife su ana iya kawo min su nan raino i will be more than happy to help,me nake yi?"
Kunya ce ta kama Saddiqa sosai kanta manne da ƙirjin Anisah take sauraron Ummi, shi kuwa Munir sai yanzu ya fuskanci kuskuren shi, cikin sanyin jiki ya kalli Saddiqa wadda taƙi ɗago kanta,shima maida kanshi yayi ƙasa yana kallon wayar shi,Ummi ce tace,
"Dan haka daga yau bana son na sake jin wai ana fushi har na kwana ɗaya ma ba a daidaita ba balle na sati, ita mace ƴar lallashi ce, wadda ma ba ayi mata alƙawarin karatu ba aka ce tana da ciki reaction ɗin farko sai ya baka takaici kafin ta dawo tana ririta cikin kamar ƙwai, dan haka kar ka takura mata, ba kowanne ciki bane da an ce an same shi ake farin ciki da farko, wani sai daga baya ake nuna masa tsantsar soyayya da kulawa, ka lallashe ta ka bata hakuri yanzun nan,Anisah ku muje ciki."
Waje suka basu, Saddiqa sai shan majina take tana wani tura baki,Munir na ganin kowa ya tafi sai ya tashi ya shammace ta ya sumbace ta har sai da taji iska na neman yi mata kaɗan,tin tana ture shi har sai da ta kasa ture shi ta miƙa kai, a hankali ya janye ya kalle ta ya raɗa mata wata magana, cikin sauri ta kalli hanyar da su Ummi suka bi tana dariya ƙasa-ƙasa tare da kulle fuskar ta da tafukan hannayen ta,hannun ta ya kama suka bar gidan suna dariya, aikin da Munir bai je ba kenan a wannan ranar saboda da gaske yake son wanke laifin shi a wajen Saddiqan shi.
Washegari da safe haka suka tashi cikin farin ciki, dika aikin gidan shi yayi, hatta da girkin safe shi ya dafa musu indomie da k'wai ya haɗa musu shayin da yaji kayan ƙamshi irin wanda Ummi ta haɗa wa Saddiqa.
A baki ya dinga bata bayan tayi wanka ta sanya wata rigar sanyi mai dogon hannu da dogon wando siriri da ya kama ta a kowacce kwana ta jikin ta da ta dace,kanta Munir ya kalla yace,
"Baby ya kamata Anisah ta kai ki inda ake yi musu kitso a taimaka wa kan nan,masha Allah gashin ki na da kyau na tabbata idan aka zana masa kitso ba ƙaramin kyau zai ƙara ba."
"Dik yanda kace haka za a yi Rouh."
Wayar shi ce ta fara ringing a saman kujerar dake parlour,da sauri ya bar dinning area ya d'akko ya amsa,gaishe da Ummi yayi cike da jin nauyin ta, bayan ta amsa tace,
"Idan ka gama lallashin kazo ka karb'ar mata jakar ta da wayar ta tin jiya Baabaa ke kiran ta."
A hankali ya furta,
"Ummi dan Allah kiyi haƙu...."
Kashe wayar Ummi tayi tana murmushi ta bar shi da jin nauyin ta, wajen Saddiqa ya koma ya kama ƙugu yana kallon ta yana gimtse dariya yace,
"To kin ji saƙon Ummi dai, tace ki je ki ɗauki wayar ki da kika bar mata a gidan ta kika bi miji,ni dai babu ruwa na dan ba zan iya komawa gidan nan ba nan kusa saboda kunya nake ji."
Wata iriyar kunya da nauyin Ummi ne suka mamaye Saddiqa tana jin ta kamar tana gaban Ummi,cikin yin ƙwalƙwal da idanu kamar na mai shirin tsaga kuka tace,
"Masoyi dan Allah ka taimake ni idan ka fita office ka ɗakko min kaji tinda hanyar kace? Kaga bani da cikakkiyar lafiya a jiki na jiri ma nake ji."
"Ai kuwa zaki warware ko wayar ki ta tabbata a can ni babu ruwa na ke da Ummi."
Dariya ya dinga yi mata har sai da yaga tana shirin yin kuka sannan ya ƙyale ta ya kirawo mata Baabaa dan su gaisa, tinda ance tana ta kiran wayar ta,bata wani jima tana ringing ba aka amsa,muryar Sadeeq Munir yaji, cikin fara'a yace,
"Aboki na yane? Ashe kai ne kake kiran matata da sassafe haka?"
Murmushi Sadeeq yayi yace,
'Lafiya ƙalou alhamdulillahi,na kira ne dama mu gaisa kuma naji bata ɗauka ba, kwana biyu Baabaa na yawan zancen ta,shine nace bari na kira dik sai mu gaisa.'
"Allah sarki gata to."
Miƙa mata wayar yayi ya basu waje dan bai sani ba ko akwai maganar da za su yi da ɗan uwan ta,yana tashi kuwa suka hau hirar yaushe gamo, anan take jin dangin mahaifiyar ta sun zo yi musu ta'aziyya har da kawunan su maza dan su gan su, amma Baabaa ta sanar da su a Abuja Saddiqa ta tare da mijin ta,sun kawo musu tsaraba sosai har da awaki biyu mata da tumaki biyu da raguna biyu,sai kaji guda biyar da ƙwan zabi da ƙwarya manya biyu da ƙanana uku,gajiya yayi dayi mata lissafi sai yace,
'Ke da abubuwa sosai suka kawo fa, Innahr mu ma taso nabi su nace ta bari idan mun yi hutu sai naje nayi musu hutu idan mun dawo sai muzo da ita taga ɗakin ki,baki ga yanda Baba ya dinga murna ba da ya gansu,Baabaa tace babu shegen da zai taɓa kayan nan sai abinda kika ce ayi dasu za a yi,to fa shine Innoh ke ta jin haushi,ta daina kula kowa har gaishe da Baabaa ta dena yi.'
"Ohhh Sadeeq yaushe ka iya surutu haka? To Allah ya saka musu da alkhairi,inshaa Allahu zamu kai musu ziyara baki ɗayan mu wata rana,yanzu Baabaa yana kula ka?"
'Humm baya wani yi min magana fa har yanzu idan bani na gaishe shi ba, sai dai yayi ta kallo na idan na wuce ko ya hau matse k'walla ya fita ya bar gidan, ko kuma ya kore ni a inda yake,amma kullum Baabaa nace min nayi hakuri ba yin kanshi bane, to wai Yah Saddiqa yin waye idan ba yin kanshi ba?'
K'wallar da ta gangaro mata ta share tace,
"Ina Baabaa bani ita mu gaisa kar kud'in ya ƙare, kai dai kawai ka ci gaba da hakuri, ka kuma riƙe azkar ɗin ka na safe da yamma, koda ka ji ƙiwar yi dika kar ka manta yin falaƙi,nasi,da suratul ikhlas,kar ka manta da yin ayatul kursiyyu da faɗin Bismillahi alladhi layadurru....zuwa ƙarshe da kuma Hasbuyallahu....zuwa ƙarshe itama idan kayi haka yau da gobe sai kaga Allah ya baka ikon zama kayi su dika kaji? Allah yayi maka albarka yasa ka gama karatun ka lafiya."
'Amin Yah Saddiqa inshaa Allahu zan ƙara kiyayewa, ga Baabaan.'
Bai wani jima ba ya shiga uwar ɗakin Baabaa ya miƙa mata wayar, tana nan kwance a gado saboda sanyin da ake bugawa ta Karb'a tana yin sallama, bayan sun gaisa ta sake maimaita mata dik abinda Sadeeq ya sanar da ita sannan ta sanar da Saddiqa babu mai taɓa komai sai da izinin ta,cikin murmushi da jin daɗin yanda Baabaa ke nuna musu soyayya Saddiqa tace,
"Hajiya Baabaa tawa ni kaɗai ko Sadeeq ma na fishi matsayi a wajen ki,Baabaa ai da kai da kaya dik mallakar wuya ne ko? Me zai hana a yi amfani da ƙwan saboda kar su lalace har wajen su Yah Ameerah dik a aika,kaji da awaki da sauran su dik sai a zuba su a gidan awakin Yadiko na da da aka dena amfani dashi,ga Sadeeq nan sai ya dinga kula dasu zan dinga aiko kud'in sai musu abinci koda yaushe da maganin da za a dinga basu."
Cikin jimami Baabaa tace,
'Ina jin tsoron a dinga yi musu ɗauki d'ai-d'ai kamar yanda aka yiwa na Yadikon Sule har aka yi nasarar ƙarar mata dasu, kin san mutum mugun icce ne.'
"Babu komai Baabaa kowa yayi nagari ai dan kanshi ko?"
'Hakane, to ina shi wancan dan tsomodon yake ana ta hira ban ji ya ce uffan ba?'
Dariya sosai Saddiqa tayi da jin sunan da Baabaa ta baiwa munir, cikin dariya tace,
"Baabaa ai baki ganshi ba yanzu,yayi ƙiba kamar ba shi ba."
'Ai dole yayi ƙiba Saddiqa, amarci wasa ne? naji ma kin tara yawu a bakin naki da alama ina da rabon ganin jikana.'
Cikin jin kunya Saddiqa tace,
"Baabaa sai anjima a gaishe min da Baabaa idan ya dawo."
Dariya Baabaa tayi tana hamdala, gorin da Innoh ke yawan yi mata akan su Mommy nada ciki Ƴan Abuja kuwa shiru ya ƙare, yaye bargon ta tayi ta sakko cike da fara'a da wani k'warin guiwa ta saka rigar sanyin ta tin ta marigayi baban su Alhaji Baban Gida,tayi mata yawa rigar k'warai amma haka take zumbula ta kamar jamfa idan sanyi yazo,cike da fara'a ta kama hanyar fita daga d'akin nata zuwa tsakar gida...........
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 70:
Cike sa farin ciki Baabaa ta miƙawa Sadeeq dake kwance a saman gadon karan parlourn nata waya tace,
"Maza kirawo min Saliha."
"Wai kina nufin Ummin Abuja?"
"Akwai wata bayan ita ne?"
Girgiza kai yayi alamar ah ah babu, ya karb'i wayar ya kira Ummi,bayan ta ɗauki wayar ya gaishe ta ne ya bawa Baabaa da bakin ta yaƙi rufuwa,gaisawa suka yi sannan Baabaa tace,
"Saliha ashe jika kuka kusan yi shine ba za a sanar dani ba na fara tanadin daddawar daka yaji?"
'Kai amma yaran yanzu dai basu da kunya, har sun sanar dake Baabaa?'
"Yo meye aciki? Ai ba zunubi suka aikata ba, kuma ni ba sanar dani suka yi ba, wannan yarinyar na kirawo naji tana tara yawu shine daga nayi mata magana ta kashe min waya,nace to bari na kira naji darrr."
'To Baabaa sai a taya ta da addu'a Allah ya bada rayayye mai albarka, Allah kuma ya sauƙaƙa mata rainon ciki da goyo.'
"To Amin dai Saliha, Allah yasa tayo gadon mahaifiyar ta wajen rainon ciki da goyo."
'Amin Baabaa.'
Hira suka ɗan taɓa kafin daga ƙarshe suka yi sallama da junan su, Sadeeq Baabaa ta k'wala wa kira bayan ta fita waje tace,
"Kai taho ka ɗakko dusa da ruwa a baiwa waɗannan ragunan, wa ya sani ma ko su zan aika Abuja a yanka idan wannan ƴar albarkar ta haihu? Ko kuma acan Baban gida zai sai masu raguna da shanu a yanka Allah masani,to abinka da masu hannu da shuni baka sanin me za su yi sai dai kaga sun aikata kawai."
Cikin sauri Innoh dake ƙulla alale a leda ta kalli Baabaa tace,
"Wai kina nufin itama Saddiqan ciki gare ta?"
"To ƴaƴan ki ne kaɗai masu mahaifar ɗaukan ciki a duniya da baza ta samu ciki ba itama? yau naji wata tambayar banza yarinya da mijin ta? Ai ina sane da duk iya shegen da kike shukawa a gidan nan, Innoh kin ƙi fita a sabga ta ko? Kin raina ni saboda kawai ina matar wan mijin ki,baki ganin tsufa na balle ki raga masa,a haife na haife ki Innoh,idan baki raga min dan furfurata ba to ban san dan me zaki raga min ba kuma."
Tura baki gaba Innoh tayi bata ce komai ba,tinda suka yi arangama da aljanun shalele ta ke ɗan d'aga wa Baabaa ƙafa, bata cika yi mata rashin kunya kai tsaye ba, sai dai tayi ta zabga habaici da shaguɓe.
Ranar nan Baabaa har sadaka tayi sannan tayi alƙawarin washegari ma zata sake yin sadakar ƙosai mai zafi da safe dan ta sake godewa Allah akan kyautar da yayi musu na samun jika daga wajen Saddiqa.
Bayan kwana huɗu da sanin samuwar cikin Saddiqa, Innoh ta fara shiri zata je Kano dan duba Mommy,rawar kai kawai take zubawa kamar mai zuwa makka,kayan ta kaff ta sa ta wanke ta yi musu ninki mai kyau ta jera a jaka, Sule ne ya zauna yana sanar da ita ta bari su tafi tare ko babu komai zai riƙe mata kaya tinda ta dage ita zata je ba zata bar Naja taje ba,cikin sauri tace,
"Yau na fara zuwa gidan Mommyn da zan buƙaci ɗan jagora? Kuma haka kawai dan mune mahaukata sai mu rakita mu dika muje mata gida? Ah ah wannan ma dan tayi waya tace bata jin daɗi ne da babu inda zan je,"
"Innoh tinda akai auren yarinyar nan ta koma kano fa kike yi musu zarya, ba a rufa sati uku baki samu dalili kin je kin cinye sati ɗaya ba, haba Innoh ! Sannan naga dai ma bake tace tana so kije ba,Aunty Naja tace ki kira mata taje ta zauna da ita har sai ta haihu."
Dafe ƙirji Innoh tayi tace,
"Kana nufin nabar Naja taje tayi kusan wata biyu ko uku gidan Mommy ni ina nan zaune baki sake kamar ita tayi min naƙudar yarinyar? Ba zai yu ba, ni zan je da kai na nima na ci daɗin da ake ci, haka kawai Allah ya kawo min hanyar hutu sai na ƙi Karb'a tinda kai kaƙi ka je ko ɗan aikin nan a firamare ka kama ana baka albashi, daga ƙarya sai yawo da waya ka iya babu fuss balle ka dinga kashe min ƴan silalla,itama waccan marowaciyar ko zuwa nayi na tarar da nama gidan ta sai tace na mijin ne ta b'oye abinta, an saka maka naman miya gidanta ka ci uku to ina dalili? Ku barni naje inda zan huta, itama Najar da ta haihu tana da kamar Mommyn ba bari na zatai naje gidan ƴarta ba."
Kuka suka ji an fashe dashi a tsakar gida,ba kuma kukan kowa bane face na Naja da ta gama sauraron dik abinda Innoh ke faɗi akan ta,tayi matuƙar mamaki da jin kalaman Innoh akan ta,dama Mommy ce tayi mata waya akan taje ta zauna da ita har ta haihu shi yasa ta shiryo dan ta sanar da Innoh tinda duk kusancin ta da Mommy dole ta sanar da Innoh,ashe ashe Innon bata bata wannan matsayin da kusancin ba a rayuwa, ashe abun duniya zai iya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 44 Chapter of 70