ganin zata fitar dashi ya gwada haƙorin shi na nan a ɓalgace, d'aki ya shiga ya zabga tagumi hawaye na bin kuncin shi, kiran Babyn shi kuwa yana ji yana gani haka ya dinga shiga yana katsewa amma bai ɗauka ba.
Da dare abokan shashancin sa sun ji shi shiru bai hau online ba sai suka dinga kira, Sule na cikin damuwa da tashin hankali, ta yaya zai yi live aga haƙorin shi a haka? Ko dai Facebook zai koma tinda can dama rubutu yake yi a page ɗin shi tare da tallata kanshi zuwa ga matan banzan dake neman wanda zasu lalace da shi ta waya su biya shi? Yana gama ayyana hakan a ran shi ya buɗe data ya shiga Facebook dan ɗebe kewar damuwar da yake ciki.
*****************************
Watanni uku kenan da auren Mommy da Abdussaboor,soyayya ake zubawa kamar su lashe junan su,a haka hutun da Abdul ya ɗauka ya ƙare, Bilal da kan shi ya kira shi yana yi masa tuni da komawa aiki zuwa wani satin,Abdul yaso kwarai ya bar Mommy a nan yaje ya ƙara gyara musu gidan nasu amma ta kafe tace ba zai yuwu ba sai dai su wuce tare a haka, ta gaji da zaman ƙauye akwai abubuwa da dama da take son ci ko sha babu a ƙauyen, dai-dai da suturar da take sakawa dik ta raina tana so ya kai ta ta sayi wasu kamar yanda yayi mata alƙawarin haɗa lefe idan sun koma kano.
Shirye-shiryen komawa Kano ya kankama babu kama hannun yaro, gaba ɗaya Mommy tayi busy ba zama, dan haka da kyar ta samu damar ware ranar da zata kai ziyara gidan sarki tayi musu sallama, washegari kuma ta je gidan su da gidan Ameerah tayi musu nasu sallamar.
Sanye take cikin doguwar rigar da ta zama shigar ta a koda yaushe ta yafa mayafin rigar sai zuba ƙamshi take yi, yanda Mommy ta ƙara cika tayi famm a cikin rigar ne ya ƙara fito da mazaunan ta da qirjin ta, ita da kanta idan tana kallon irin shape ɗin da Allah yayi mata irin wanda mata ke kashe miliyoyin kuɗi dan su mallake shi sai ta godewa Allah.
Abdul ne ya ajiye ta a gidan nasu ya wuce fada wajen mahaifin shi ita kuma ta shiga cikin gidan bakin ta ɗauke da sallama,zaune ta tarar da su Aziza da abokan zaman Innah Laminde a tsakar gida suna hira,tabarmar da Azizah ke kai ta hau ta dafa cinyar ta suka yi wa juna murmushi,cike da sakewa mommy ta gaishe da matan sannan ta kalli Azizah tace,
"Ina Innahr mu?"
"Tana ɗaki karatu take yi."
"Allah sarki, bari na huta na shiga na gaida ta, sallama fa nazo yi muku Hajiya inshaa Allahu jibi zamu wuce kano."
Murna suka dinga taya ta da fatan alkhairi ita kuwa tana amsawa cike da jin daɗi,suna nan zaune mai aikin gidan dake daka kayan ƙamshi ta kwashe ta shiga madafi ta zuba kayan ƙamshin da ya haɗa da tafarnuwa da citta da masoro a miya ta juya, ƙamshin miyar ne ya taso ya cika tsakar gidan kamar ba miyar ƙauye ba, nan take kuwa ya daki hancin Mommy dake ta ƙoƙarin maida aman da take jin yana taso mata,dik ƙoƙarin ta na ganin ta danne aman nan da take ji ya gagara dan haka a guje ta miƙe ta nufi bakin tap ɗin tsakar gidan tana ta kwarara amai.
Guda ɗaya daga cikin mata masu kula da ɗakin Innah Laminde ce ta zabga guɗa tare da faɗin,
"Allah yayi dare gari ya waye,magajin yariman Sarkin garin Ba mugu ya bayyana da dikkan alamu,Allah ya sanya alkhairi ya raba lafiya, ayyiiiiiriiiiii."
Dik budirin da ake yi a saman kan Mommy ba wani ganewa take yi ba saboda jirin dake ɗibar ta, a hankali ta miƙe tsaye bayan ta wanke fuskar ta da bakin ta sannan ta goge fuskar da zanin da Azizah ta bata tana murmushi,jiri ne ya ɗebe ta a dai-dai lokacin da ta miƙe tsaye, cikin sauri Azizah ta kama ta suka wuce parlourn Innah Laminde dake zaune tana jin dik abubuwan da ake faɗi,ji tayi zuciyar ta tayi sanyi daga ƙin da take yi wa Mommy, murmushi tayi a lokacin da idanun ta suka sauka akan Mommy da halittar ta dik ta sauya, jinjina kai Innah Laminde tayi a ranta ta ayyana,
'Lallai babu shakka yarinyar nan da alama ciki ne da ita, Allah ya inganta mana ya bada rayayye mai albarka.'
A zahiri kuwa tashi tayi ta isa gaban Mommyn tana yi mata sannu kamar bata gane meke faruwa ba tace mata,
"Sannu Hadiza ya jikin naki?"
A hankali Mommy tace,
"Da sauƙi, lafiya ta ƙalau fa babu inda ke yi min ciwo,dama na kwana biyu ina jin irin wannan yanayin a duk sanda miya ko ruwan jellop ya tafaso,sai in yi ta amai ina jin jiri, banda haka lafiya ta ƙalau bana jin ciwon komai a a jiki na."
"Allah sarki Allah ya baki lafiya, idan kun tafi can kanon ya kai ki kiga likita."
"Haka yace dama shima."
"To Allah yasa ku koma a sa'a,Allah ya kiyaye dikkan abun ƙi, idan kun tafi dai Hadiza ki kula, ki kiyaye dikkan dokokin Allah da suka rataya akan ki, tsaida sallah, kare mutuncin auren ki da kula da mijin ki,kar ki kuskura ki sake kulla abota da duk wani wanda kika yi rayuwa dashi a baya a wannan garin gudun fad'awa cikin halaka koda kuwa Bilkisu ce tinda taƙi dawowa gaban mu,Allah yayi muku albarka."
Cike da jin kunyar abubuwan da ta aikata a baya ta amsa da,
"Ameen Innah in Allah ya yarda zan kiyaye."
Daga nan bacci mai daɗi ya ɗauki Mommy hirar da ta ci burin idan ta je su yi da Azizah bata samu ba, Sultan ma da ya shiga gidan ya tarar da ita tana bacci Innah Laminde korar shi tayi tace ya je dakin shi ba zai zauna yana kallon ta ba tana bacci,fita yayi yana mamakin yanda Innah ke nesanta tsakanin shi da Hadizan.
Tinda Mommy ta fara bacci bata farka ba sai bayan azahar, tana tashi tayi sallah a gaggauce ta hau neman abinci, har za a zubo mata shinkafa da miyar kajin da aka yi tace bata son da miya a saka mata manja da yaji taci.
Nan take Innah Laminde ta sake gasgata zargin ta na samuwar ciki a a tattare da Mommyn, nan da nan kuwa ta sa aka soya mata manja da albasa sosai aka daka mata sabon yaji mai daɗi aka zuba mata shinkafar, soyayyan nama da dambun nama Innah ta bayar aka kai mata sai zob'o mai sanyi,Mommy kuwa mamakin hidimar da Innah Laminde ke yi mata ce ta kama ta, dan kuwa idan bata manta ba tsakanin su daga gaisuwa sai tambayar iyayen ta da mai gidan shikenan, Innah Laminde bata sakar mata fuska balle har ta yi hidima da ita irin haka, rasa gane dalilin samun sauyin da take gani ne ya sanya ta ɗauke hankalin ta da tunanin ta akan nemo dalilin ta mori kayan daɗin dake gaban ta, dan kuwa bata tashi ba sai da ta ci ta ƙoshi ta gyatse sannan ta zabga hamma ta yi miƙa, lalubo wayar ta tayi ta kira Abdul tace masa idan ya gama abinda yake yaje su tafi.
Abincin Innah Laminde tasa aka sake ɗebar musu da nama sannan ta kwashe mata gorinan zob'on da suka rage tace su je da shi tinda tana so, godiya Mommy ta dinga yi tana mamakin wannan sauyi da ta samu na soyayya da kulawa daga wajen surukar ta.
Sai da aka yi sallar la'asar Abdul ya iso ya ɗauke ta bayan ya gaida iyayen nashi mata suka wuce gida. Tin a hanya Mommy ke bashi labarin sabon sauyin da ta gani a wajen surukar tata da kuma murnar da matan gidan keyi akan aman da tayi tare da hasashen su akai,murmushi yayi yace,
"To ai ke sai dai na taya ki murna tinda ko babu komai an samu daidaito a tsakanin ki da surukar ki ko? Sannan kuma ni kaina na jima ina hasashen nan duba da cewa yanzu kusan watannin ki biyu baki ga al'adar ki ba, ko kin manta ke da kanki kike yi min complain akan hakan?"
Shiru tayi tana nazari,a hankali ta kalle shi tace,
"Yanzu Baby kana ganin ciki gare ni kaima?"
"K'warai da gaske i am 99% positive,ki bari mu je kano dai na kai ki a duba min ke da kyau a tabbatar zaki ce na faɗa maki."
Ranta ne taji gaba ɗaya ya baci, hankalin ta ya tashi,cikin wani irin yanayi ta furta........
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA: HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 65:
"Kai ni gidan mu zan karb'i abu wajen Innoh."
Time ya kalla a jikin motar tashi sannan ya juya ya kalle ta, ganin tayi bala'in b'ata rai alamar bata nufin wasa sai kawai ya juya kan motar tashi zuwa gidan su,sun isa gidan da misalin ƙarfe 9:16pm, ko da ta shiga cikin gidan ta tarar da gidan shiru kamar babu kowa saboda sanyin da ake busawa sosai kowa ta shige ɗaki ta rufe da kaskon wuta ,a ƙofar d'akin Innoh ta tsaya tana k'wank'wasawa hawaye na zuba a idanun ta,Innoh na cikin zanin gado ta furta,
"Ka shigo mana ko ɗakin baƙon ka ya zama da kake yi min ƙwanƙwasa, ko kuma zuwa zan yi na ɗakko ka kamar jinjiri na shimfiɗe a gado?"
Mommy ce ta kutsa kai cikin ɗakin tare da fashe wa da kuka mai tsanani,a gigice Innoh ta diro a gado, da sauri ta ja gefe saboda ƙafar ta da ta kusan taɓa kaskon wutar da ta kai ɗaki domin shan ɗumi. Cikin damuwa da tashin hankali ta kalli Mommy tace,
"Ke lafiya kika zo mana gida a wannan tsohon daren kina kuka? Idan ma sakin ki yayi to ki koma ki faɗa masa ni Innoh nace auren ku mutu ka raba ne, bai isa ya sake ki ki saku ba,taso muje yaga yawa na, na kula shirun da muka yi kwana biyu bamu kai sunan shi wajen malam ba shi yas....."
Cikin kuka Mommy ta katse Innoh da cewa,
"Ni fa Innoh ba saki na yayi ba,ni ce da kai na nace ya kawo ni gida na faɗa maki mummunan labarin da ya same ni."
"To be sake ki ba uwar ki da uban ki na raye basu mutu ba kukan uban me kike yi haka Hadiza...Uffararan me sunan da ba a fad'e gatsal,sanar dani me yake faruwa to?"
Cikin kuka Mommy tace,
"Innoh wai fa mutanen gidan sarki ne ke ta murna wai suna zargin ina da ciki, shima uban gayyar har da cewa ya tabbata ba zargi yake ba ciki gare ni, jibi da mun je kano zai kai ni a duba ni a ga shin ciki gare ni da gaske?"
Gud'a Innoh ta damƙi hancin ta ta rotsa a tsakiyar kan Mommy da ta toshe kunnen ta ta rintse idanun ta dan baƙin ciki,cikin tsananin kuka tace,
"Innoh zuwa nayi ki bani shawarar yanda zan salwantar da cikin nan ba tare da kowa ya sani ba amma kike murna, Innoh cikin nan ba ƙaramin matsala zai zame min ba,zai lalata surar jiki na, zan zama ƙatuwar mace me tumbi, dan Allah Innoh ki taimake ni."
Wata uwar harara Innoh ta sakar wa Mommy sannan ta ja da baya ta nuna ta tace,
"Kin san Allah? A dik sanda na ji labarin ƙwarzane ya samu cikin jikin ki ta dalilin ki zaki ga yanda zan tsine maki ki bi duniya,ke kin san amfanin da cikin nan zai yi maki kuwa? Jikan gidan sarkin garin Ba mugu fa kike ɗauke da shi, ki sani a duk sanda kika haihu wannan abinda ke cikin naki zai jawo maki arziqi,Ameerah ma me auren talaka dan turin waya ta samu ciki suke murna ake ririta ta balle ke da kike da uwar kuɗi da mulki da kyakkyawar rayuwa? Ahir ɗin ki da zubar da ciki ko salwantar da shi,ki rungumi cikin nan da kyau da kulawa ya zame maki babban jari, kiyi maza ki koma wajen mijin ki, sannan kiyi nazari akan magana ta zaki gano me nake nufi da hakan."
Ba dan Mommy ta gama gamsuwa da Maganar Innoh ba ta yi mata sallama ta fita ta koma wajen Abdul dake ta chatting da Bilal yana sanar da shi zuwa jibi za su isa kano.
Ko da suka koma gida Mommy bata ce komai ba game da maganar cikin da suke hasashen tana da shi sai kawai ta ci gaba da harkokin ta,bayan sun kwanta kuwa duk yanda Abdul yaso ya samu natsuwa da ita ƙin yarda tayi saboda haushin shi take ji.
Bai jima da gama yi mata naci ba bacci mai daɗi ya ɗauke shi, juyi tayi tana shafa cikin nata dake shafe zuwa cikakken ƙugun ta, sannan ta maida hannun ta saman ƙirjin ta dake a cike, tsaki ta ja a hankali ta furta.
"Allah ya kaimu kanon a gwada a gani,idan ta tabbata ciki ne dani gaskiya ba zan bari ba, Allah ya bani kyakkyawan jiki haka kawai na bari haihuwa da rainon yara ya tsufar dani? Inaaa ba zai yuwu ba, a gaban ido na Billy ta sanar dani BBL tayi a mazaunan ta dan kawai ta samu irin jiki na,mata da dama na kashe millions of dollars dan su samu irin sura ta se kawai na bari ta lalace da haihuwa? Sam ba zai yiwu ba gaskiya,da Innoh ke wani cewa Ameerah nada ciki ita taga zata iya ɗauka ta raina har ta haife amma ni kam ba zan iya ba inaaa sam-sam ba zata sab'u ba bindiga a ruwa."
Haka ta kwana tana tunani da ƙyar bacci ya ɗauke ta da goshin asuba,bata farka ba kuwa har aka idar da sallah a masallatai,dik yanda Abdul yaso tada ita taƙi bashi had'in kai ƙarshe ma ƙarya tayi masa tace tayi sallar komawa baccin tayi, dole ya ƙyale ta ya koma d'ayan d'akin yana shirye-shiryen yin meeting da abokan aikin shi da misalin goma na safiya.
Mommy kuwa tana can tana bacci bata farka ba sai 11am, tana farkawa wayar ta ta fara jawowa, ta buɗe data ta fara duba WhatsApp bata amsa saƙo ko ɗaya ba ta fita ta shiga TikTok ta tsaya taga video guda ɗaya sannan ta ajiye wayar tana saurarar wani videon da ta ke gani, a haka tayi alwala tayi brush ta tada sallah bayan ta fito tayi sallar hankalin ta duk na kan wayar.
Tana idarwa bata tsaya addu'a ba ta miƙe ta ɗauki wayar ta ta nufi parlour daga ita sai wata guntuwar rigar bacci kanta sai sheƙi yake yi saboda na nusamman taje Saloon aka gyara mata shi.
Abdul ta hango alamar yana yin video call dan haka sai ta samu gefe ta zauna ta natsu tana danna wayar ta,Abdul bai samu damar gama meeting ɗin shi ba sai 12pm dai-dai,cike da shagwab'a ta kalle shi tace,
"Baby yunwa nake ji ina abinda zan ci yanzu?"
Murmushi yayi kafin yace,
"Ina fatan kin yi sallah da kika tashi dan nasan baki yi ba kyale ki kawai nayi, And Maganar abinci kuma Baby ba ke kike dafa mana ba dama? Amma tinda naga alamar kin gaji ko zaki daure ki d'umama mana abincin da muka zo dashi jiya mu ci?"
Kallon shi tayi cike da rashin mutunci sannan tace,
"Ban gane ba? Baby yunwa fa nace maka ina ji sannan kace naje nayi dumame? Impossible!"
"Inyeee wato Impossible ko? Da kyau, bari ni naje na d'umama mu ci,Allah ya huci zuciyar maman biyu?"
Yana tashi ta ɗauki pillow ta wurga masa tana mita da dire-diren shagwab'a,shi kuwa gocewa yayi yana dariya ya gudu kitchen.
Ƙin komawa gidan su tayi kamar yanda tayi alƙawari suyi sallama,a cewar ta tana ganin babu abinda zai maida ta, dama Baban sune kawai ta damu suyi sallama,to akwai waya ta kira shi suyi ba sai sun haɗu ba.
Ranar lahari da zasu tafi kano kuwa da sassafe Mommy da Abdul suka gama shiri suka ɗauki hanyar garin kano.
**************************
"Babe na faɗa maki ki daina yi min bincike a d'akin can ko? Ko baki yarda dani bane akwai abinda kike neman ƙarin bayani akai naƙi yi maki?"
"Baby i am sorry, babu abinda nake bincike fa na musamman,kawai ni ina da karambanin taɓa duk wata na'ura mai ƙwaƙwalwa idan na ganta,"
"Tooo ! To ki guji bincike musamman a can d'akin gudun nar ki ga abinda zai hana ki Zaman lafiya a rayuwar ki baki dayan ta."
Rungume juna Billy da Amy suka yi suka hau soyayya kafin daga ƙarshe Amy tayi mata sallama ta tafi aiki,Billy kuwa na jin ta ita kaɗai sai ta hau TikTok tana kallon Videos tare da yin sababbi tana ɗora nata.
A haka taci gaba da latse-latse har ta gaji ta kashe computer sannan ta koma parlour,zaman ta keda wuya taji ƙarar ƙararrawar shiga gidan,rigar ta wadda da kaɗan ta rufe ƙirjin ta ta gyara kafin ta tashi cikin yanga ta isa bakin ƙofar ta buɗe.
Wata baturiya ta gani tana kallon ta a tsorace, tana waige-waige, cikin sauri tace mata,
"You have to leave,you have t...to...to leave before it's too late for you, leave before it is too late for you, leave while you can...."
Tana gama faɗin haka matar ta bar wajen da gudu tana kare fuskar ta daga CCTV camera ɗin unguwar,kafin Billy ta gama tuna a inda ta taɓa ganin matar matar ta bace wa ganin ta, kyab'e baki tayi ta d'aga kafad'a sannan ta koma ciki ta zauna tana kallo,hankalin ta gaba ɗaya ya tafi wajen maganganun matar nan, dan haka ta ƙudirta a ranta zata tuntub'i Amy taji anya babu abinda take boye mata da ya danganci rayuwar ta ta baya kuwa?...........
[09/08, 10:38 pm] Aunty Hameeda: GIDAN ƊAN LITI
RUBUTAWA : HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 66:
Tin daga gate ɗin shiga gidan ta fara ganin sauye-sauye, domin kuwa an sakewa ƙofar gate ɗin fenti daga baƙi zuwa brown da ratsin golden a jiki, fentin dake jikin gidan kuwa gaba ɗaya milk ne,murmushi ta saki ta kalli Abdul wanda tini ita yake kallo dan yaga yanayin fuskar ta,cikin farin ciki tace,
"Baby naga an cire ƙarafan dake jikin ginin gidan nan an ƙara tsawon katangar kuma an sauya fentin gate ɗin?"
Kallon ta yayi cikin fara'a yace,
"Aikin Bilal ne wannan,ni dai kawai na san nace masa ina son ya maida gidan nan yayi kyau yanda zai ƙayatar da ganin ki,ina fatan kwalliya ta biya kud'in sabulu?"
"Ai kuɗin sabulai ma ta biya wannan ba kud'in sabulu ba baby,gaskiya na gode sosai Allah yasa kafi haka."
"Amin ya Allah, li am glad you like it."
Motar shi ya shigar gidanbayan dattijon mai gadin ya buɗe masu gate ɗin,Bilal suka tarar a tsaye yana latsar wayar shi, ko d'aga kai beyi ba balle ya kalle su, fuskar nan tayi kicin-kicin kamar ta mai jin kashi,bai motsa daga inda yake ba har sai da Abdul da Mommy suka isa gaban shi ɗauke da akwatinan su,Abdul na jan biyu mommy na jan ɗaya hannun ta ɗaya riƙe da handbag,Abdul ne ya kalle shi yace,
"Man ya dai na gan ka ka wani tsume kamar wanda ya sha maɗaci?"
Yatsina fuska yayi ya amsa gaisuwar Mommy a shaƙe sannan ta rab'e su ta wuce ciki,a shaƙe Bilal yace,
"Lafiya ragas nake ni raini ne bana maraba da shi shi yasa nake kama mutunci na tin kafin a ga wajen kwana na a kawo min raini."
Sai yanzu Abdul ya gane me yasa yake ɓata rai, wato ganin mommy ne ya dagula masa lissafi, tinawa yayi da yanda suka yi da Bilal ɗin a waya a lokacin da Abdul yace masa idan ya gama da gyaran gidan ya siyo musu abinci sannan ya jira su iso a haɗu a ci gaba ɗaya a yi hirar yaushe gamo,dagewa yayi akan shi fa sam ba zai zauna inuwa ɗaya da Mommy ba dan shi har yanzu ba wani ƙaunar ta yake ba, shi dai da yaji ya kuma gani to yaje can su ƙarata,da kyar Abdul ya shawo kanshi ya amince zai jira su iso a gaisa amma ba zai zauna wani cin abinci da su ba, abincin ma da ba ita ta dafa ba shi ya siyo? Murmushi Abdul yayi yace.
"Man kana da matsala gaskiya,mu je ciki ni a gajiye nake bana maraba da wannan sabon halin naka sam."
"Ni ma ba maraba nake da naka sabon halin ba,kaga tafiya ta, ina maka barka da dawowa lafiya, kar ka manta gobe a fito aiki."
Hannu ya miƙawa Abdul suyi sallama Abdul ya saki baki yana kallon Bilal, kallon wai da gaske baza ka shiga mu ci abinci tare ba yake masa,har Bilal zai wuce Mommy ta leƙo kai babu ɗan-kwali sanye da matsattsun riga da skirt na atampa tace,
"Baby ka shigo ka huta mana ka tsaya a waje tin ɗazu."
Bilal ne ya kalli Abdul yace,
"Idanun ka sun gane maka dalilin ƙin shiga ta gidan ka yanzu ko?"
Ba tare da ya sake magana ba ya wuce ya hau machine ɗin shi roba-roba fari mai kyau ya bar gidan,Abdul ne ya ja akwatinan shi ya shige cikin gidan,direct bedroom ya kai kayan ya ajiye sannan ya fito ya zube a kujerar dake zagaye da babban parlourn nasu,cikin muryar gajiya yace,
"Washhh Allah na na gaji,Baby ɗan duba dinning ki kwaso mana abinci nan mu ci yunwa nake ji."
Mommy dake ta zagaye gidan tana kallo tare da santin yanda aka ƙawata gidan ne tace,
"To ina zuwa ɗan bani minti biyar."
Sai da ta koma d'akin da ta ajiye kayan ta sannan ta sauya kayan jikin ta zuwa wata ƙaramar riga dan taji dad'in sakewa sannan taje ta kai musu abinci ta ajiye a center table ɗin dake parlour tayi serving ɗin su.
Sakwara ce da miyar agushi taji nama da kifi kala-kala, sai lemon kwali da farfesun kifi, buɗe ciki mommy tayi sosai taci ta ƙoshi kafin ta saki wata gyatsa mai ƙarfi sanna ta zame ta na hamdala, kallon ta Abdul yayi yana dariya yace,
"Waiii baby wannan wace iriyar gyatsa ce haka, da alama kin ƙoshi da yawa."
"Alhamdulillahi,tinda nake a rayuwa ta ban taɓa cin irin wannan abincin ba,sai dai nakan ji ana ce sakwara da miyar taushe ko agushi amma ban taɓa ci ba sai yau,ni fa ba dan na taɓa shigowa garin nan ba ma akwai abubuwa da dama da ban taɓa ci ba ko gani da ido na."
Kallon ta Abdul yayi da tausayawa sannan yace,
"Ai kuwa inshaa Allahu zaki ji daɗi a garin nan,dik wani abu da kike son ki ci sai kin ci shi indai ina da hali."
Washe baki tayi ta koma inda yake ta zauna a jikin shi tana farin ciki,cikin ɗan ƙanƙanin lokaci Mommy ta hau birkitawa Abdul lissafi, sun jima suna zuba tsantsar tsagwaron soyayya a sabon parlourn nasu Mommy ta sake sauya sabon salo dan gamsar da Abdul,murya a shaƙe ta furta,
"Baby gobe ka kaini asibiti a zubar da cikin nan saboda mu ci gaba da zuba soyayyar mu babu takura."
Abdul jin shi yayi kamar wanda aka zubawa zuma a baki yana cikin sha a buɗe bakin a watsa masa maɗaci,cikin wani irin yanayi ya zame jikin shi a nata yana maida numfashi ya kalle ta dan son jin shin da gaske ne ita tayi magana ko jimawar da gidan yayi babu kowa ne ya jawo aljanu suka samu mahalli a gidan? Kallon shi tayi ta kafe shi da ido sannan ta sake kai hannu tana shafa jikin shi tace,
"Baby i am serious,zubar da cikin nan ne kawai zai sa mu..."
"Shut up Hadiza ! Yi min shiru nace ! Kina da hankali kuwa? Kin san me kike faɗa kuwa? Na zubar da gudan jini na fa kike nufi? Ashe baki da hankali ban sani ba? To menene ribar soyayya idan ba haihuwar ba? Haihuwa na daga cikin ribar da kowanne ma'aurata ke fata da burin samu, shine ni Allah yayi min kyauta sai kice na zubar? To idan kuma wannan ne kawai ƙwan mu a duniya da ni dake fa? Shikenan sai mu zauna babu haihuwa? Amma kin bani mamaki Hadiza dama ba sona kike yi ba nake ta wahal da kaina akan ki?"
Cikin kuka Mommy ta taro shi tace,
"Haba baby ya zaka ce bana son ka daga faɗa maka gaskiya...."
Cikin tsananin ɓacin rai da tada jijiyoyin kanshi Abdul ya kalle ta yace,
"Ko da ganganci cikin nan ya zube ba da son ranki ba ki sa a ranki ni Abdussabour na gama auren ki kenan."
Tashi yayi ya ɗauki kayan shi ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 42 Chapter of 70